Biyar! Ko ba su da karfi fa akwai yawa.
Sarkin Yawa kuwa ya fi Sarkin Karfi!"
Biri ya ce, "Ai duk kanana ne, babban ma da tsawon kafa
kadai ya fi ni. Kuma a nan duniya ai babu naman dajin da ya fi ki
karfi, in ba zaki da giwa ba."
Kura ta ce, "Kai, yi mini shiru! Namun dajin da suka fi ni karfi
nan duniya wa ya san iyakarsu? Kai dai mu tafi mu gani, in da
riba mu fafata, in kuwa babu mu yi ta kammu."
Ko da bunsuru ya hango su sai ya ce wa matarsa, "Tura
'ya'yanki cikin kogo, in sun shige kuma su yi ta kuka baki daya."
Da suka shige duk suka barke da kuka baki daya, Ba-a-a-a-a-aa-a! Bunsuru ya ce, "Kai, me ya sami yaran nan?"
Akuya ta ce, "Wai sun ce duk cikin naman da ke gidan nan ba
su cin naman kowa sai na kura kadai, wai ya fi dadi."
Bunsuru уa се, "То, a ba su sauran na kuran nan da na kashe
jiya mana su karasa."
Akuya ta ce, "Na ba su, sun ce ba su cin naman da ya fara
bashi, wai sai sabo su ke so."
Bunsuru уa сe, "Tоo, su hakura kadan su bar motsi, don na ji
biri ya ce wai kura yau tana tafe, za mu yi fada, in Allah ya kawo
mana ita ai kin ga yau sa wadata in dai don nama ne, don na ji an
ce ta yi mai kwarai."
Kura ta dubi biri, ta ce, "Ka ji ko, gaskiyata ce da na ce lalle
abin nan ya fi ni karfi, ka ji jiya ma sai da ya kashe wani kura. Na
san lalle bunsuru ba ya iya daurewa ya yi mini haka ba, ko daji
ma ba ya yarda ya fito ba, wanda kullum yana can boye cikin
gari. Ni zan koma tun bai rigaya ya gan ni ba!"
Biri ya ce, "Kada ki lura da zancensa, fankama kawai ya ke yi
80
miki da karairayi, na gan shi dan karamin abu ne, kuma da ganin
tafiyarsa ka ga raggo.
Da kura ta ji haka zuciyarta ta yi dan karfi, ta ce, "To, mu
tafi." Ko da bunsuru ya hango ta, sai ya tura 'ya'yansa a cikin
kogon kura, suka soma kuka gaba daya. Ya ce wa akuya, "Don
Allah gaya musu su yi shiru, biri ya yi mini alwashin zai yi dabara
ya kawo mini kura har nan gidana, in sun yi hayaniya yaya za ta
yarda ta iso, balle mu samu mu kashe ta mu sami abin kalacin?
Kun gani fa yau saboda ita ba mu yi tanajin kome ba, a gare ta
muka dogara."
Da kura ta ji haka sai ta kama biri, ta ce, "Ashe da munafunci
aka kulla da kai, don ka sa a kashe ni a banza? To, Allah ya tona
asirinka, dan banza!" Zai yi magana ta sa kafa ta taka shi, ta
kashe. Ita kuwa ta yi baya da gudu tana zawo.
Da bunsuru ya ga sun sami sa'a haka sai suka kwashe duk
kayan da ke gidan suka kama hanya suka koma gari gidansu.
Aku ya dubi Musa, ya ce, "To, mu tafi, kyaun dan halas duk
abin da ya yi niyya ya cika. Abin da ke aukuwa ga mai yin
alkawari ba ya cikawa, in ka ji ai sai ka yi kurum."
Musa ya ce, "Me ke faruwa ga mai saba alkawari? Don mutum
ya yi niyyar abu, ya koma ya fasa, sai wani abu ya same shi?"
Aku ya ce, "Babban mugun abu kuwa zai same shi."
81
Labarin Sarkin Busa
Abin da ya sa na ce haka, a wani gari can ketaren Bahar Maliya a
cikin kasar Jamus, tun shekaru da yawa da suka wuce, Allah ya
saukar musu da wani babbar bala'i. Aka saukar musu da beraye
ko'ina cikin garin. Berayen nan suka yi ta karuwa, har mutane
suka rasa abin da su ke ciki, duk inda mutum-ya duba garin ba ya
ganin kome sai beraye. Ko wajen barci mutum in ya zo sai ya
tarad da kamar ashirin tuku-tuku suna kwance. In hula ka ajiye,
ko riga, kafin da safe sai ka tarar aljihun cike da beraye. In
takaice maka labari, yawansu ba su kidayuwa. In da za ka kidaya
su, ka kidaya kudajen da ke garin, sai ka ga sun fi yawan kudajen
nan kamar sau dari. Gari dai ba wajen sa kafa, duk beraye ne.
Abinci kuwa mutum ko ya fi Aula dabara, ba yadda zai yi ya
ajiye shi. Kome za a dafa sai a yi daidai da yadda za a iya cinyewa,
don ko cikin akwati ka sa abinci ka kulle, sa san yadda za su yi wa
akwatin nan huda, su shiga su cinye.
Duk wani abu da ka sani ana yi da fata sun cinye. Ba ka ganin
mai takalmi, ko matashin kai, ko gafaka, ko buzu a garin. In ko
sun kai ga abin da ba su ci, sai su yi masa hudoji, su bata shi. Ta
ishe ka ma ko jariri suka tarar yana barci, sai su tasam masa da
cizo za su cinye. Sai in ya yi kuka iyayen su kwace shi.
In dare ya yi kuma su kan hana mutane barci da kuka da gujeguje. In sun ga jikin mutum waje, sai su kama da cizo, wai za su
cinye shi. To, kada ka zargi mutanen garin, ka ga kamar sakarci
ya hana su kashe su. Bala'i sai sa'ad da Mai abu ya sawwake
abinsa. Da sun ga kare sai su tasam masa, su nuna masa Sarkin
Yawa ya fi Sarkin Karfi. Don kyanwa kuwa, wannan karamar
alhaki, ba su kula da ita ba.
Abin mamaki, mutane kuma in sun tasam ma kashe su, sai ka
ga kamar kara su su ke yi. Don a sa tarko kuwa, ko a sa dafi cikin
abinci a ajiye, duk wannan ba ya rudinsu. Da sun gani sai su
kewaye, kamar gaya musu a ke yi.
Duk mutanen gari suka rasa yadda za su yi, sai suka tasam ma
mai garin, suna cewa shi ne ke da gashin tsiya, don tun da aka
82
halicci duniya ba su taba jin irin wannan ba, sai cikin wannan
zamani da ya ke sarauta. Suka ce ko dai ya san yadda zai yi da
berayen nan, ko kuwa su fitad da shi, su kore shi daga kasar.
Sarkin ya rasa inda zai sa kansa. Mutanen gari kuwa sai kara
matsa masa lamba su ke yi. Ran nan yana zaune zugum,
wadannan dattijai su zö su zazzage shi su wuce, wadannan su zo
su zunzungure shí su wuce. Sai ga wani dan tsoho bako ya zo, ya
duka ya gai da Sarki.
Sarki ya dube shi, ya gan shi wani iri, sai ya ce, "Malam, daga
ina? Wace sana'a ka ke yi?"
Tsoho ya ce, "Ga ni dai. Inda na fito da nisa, amma sana'ata busa, har mutane na kirana Sarkin Busa."
Sarki ya ce, "To, sai ka je ka sauka, in kana iya sauka nan, mu
ba ta busa mu ke yi ba yanzu, ta kawunammu mu ke yi da wannan bala'i."
Sarkin Busa ya ce, "Ai ni ma ba busar banza na ke yi ba, wani
asiri Allah ya ba ni wanda in na yi busa duk ko wane abu mai rai
ya biyo ni. Da kwadi, da macizai, da beraye, da dukan naman
ruwa da na tudu, da tsuntsaye, har da masu tafiya da kafa biyu,
duk wanda ya ji na yi busa, ba sauran zama, sai ya yi ta bi na.
Don wadannan 'yan berayen da suka dame ku, in ka iya ba ni
abin da na ce, yanzu sai in raba ku da su."
Sarkin ya ce, "Don Allah ka taimake mu! Kome ka ke so nan
duniya na ba ka. Tambayi, mu ji."
Sarkin Busa ya ce, "Ka ba ni sule dari, in na raba ku da su?"
Sarkin ya dube shi, ya ce, "Yau ga abin mamaki, mene ne sule
dari kuma! Sule dubu goma ma, in kana so sai in ba ka. Kai dai
mu rabu da wannan bala'i."
Sarkin Busa ya ce, To, madalla." Ya sa wata irin mabusa
bakinsa, ya yi ta-busa, yana yawo cikin gari rariya rariya. Sai berayen nan suka yi ta fitowa ko ta ina, suna binsa tururururu,
wadansu manya, wadansu kanana, wadansu tultul, wadansu
kyamas-kyamas. Ga wadansu ja wur, wadansu fari fat, abin har
da shudda da rawaya. Ka ga wadansu ruku-ruku da ciki wadansu
kuwa ga 'ya'ya kanana ke biye da su. Sai tsalle-tsalle su ke yi,
suna 'yan kuka tsui tsui, kamar suna fara'a da wata bushara.
Da ya kwashe duk, sai ya nufi kogi yana busa, suna biye,
mutane na kallo na murna. Da isarsa bakin kogi sai ya fada cikin
ruwa yana busa, beraye kuma ba su san sa'ad da suka bi shi ba,
duk suka mutu cikin ruwa, sai daya kadai ya tsere. Mutane suka
yi ta yi wa juna barka. A tsaya ma a fadi farin cikin da mutanen
garin nan su ke yi da rabuwa. da wannan bala'i, ya zama
kauyanci.
83
Da Sarki ya hangi Sarkin Busa na dawowa, sai ya ce wa mutane
kowa ya koma gidansa, su kwaba kasa su lillike ramummukan da
berayen nan süka giggina.
Da Sarkin Busa ya iso, Sarki ya yi masa godiya kwarai. Sarkin
Busa ya ce, "To, madalla, sai ka cika alkawarinka ko? Allah ya
ba ka nasara."
Sarki ya bata fuska, ya ce a ransa, "To; yanzu in na ba shi sule
dai dai har dari, to, ni yaushe zan tara kudi in ina haka? Beraye
dai ne ganin idon kowa sun mace, ba su ko komowa. In ma ba
zarinsa ba dan tsoho da shi tukuf haka, me zai yi da sule dari?"
Ya dubi Sarkin Busa, ya ce, "Ai da wasa na ke yi maka da na ce
zan ba ka sule dari. Ashe kai ba ka san wasa ba? Ga dai sule sha
biyar sun ishe ka. Me za ka yi da kudi da yawa ga shi ka tsufa?".
Sarkin Busa ya harari Sarki, ya ce, "Zancen banza. Kai din ba
ka tsufa ba da ka ke alkawari ba ka cikawa? Yi maza ka ba ni in
kana ba ni, in ci gaba. Ba a kanku na fara ba!"
Sarki ya ce, "In ba rashin hankalinka ba, yanzu yanzu da isowarka har ka yi aikin sule dari? Ko sha biyar din da na ce ai don
dad'in girmana ne. In an bi kididdiga ne, ni ke uku da sisi ba ka ci
ba. Dubi fa tun da safe har la'asar mutum ke aiki a ba shi sisi,
balle kai yanzu yanzu!".
Sarkin Busa ya ce, "In fa ba ka ba ni abin da ka yi alkawari ba,
yanzu na sake mabusa, ka ga kuma abin da zai faru."
Sarki ya yi fushi, ya ce, "Sake mana! Mu-ze a ci da burga, sai
ka ce ba mutanen birni ba? Wanda ya mutu ban da Allah wa ke
iya rayad da shi?"
&4
Sarkin Busa ya ce, "Ko ni ban ce ina iyawa ba, amma ka ga
abin da zai faru." Sai ya dauko wata mabusa ya fara busa, ya
shiga gari titi titi yana busawa. Sai yaran gari duk mai iya tafiya,
tun daga mai shekara uku har goma, suka yi ta fitowa suna binsa
da gudu, suna tafa hannu suna rawa. Wani yaro mai dan dama
daga cikin 'ya'yan Sarki ya rika ba da waka, saura na amsawa
baki daya. In ya fadi ta farko, su kuma su fadi ta biyu, suna
cewa:
Ku zo ga daula wa zai ki,
Alo alo, mu ci daďi!
Kowa ya bari ta gota shi,
Alo alo, mu ci daďi!
Tuwo, nama, sai mun koshi,
Alo alo, mu ci daďi!
Nono da zuma ba mai zari,
Alo alo, mu ci daďi!
Siliki ran Salla ba datti,
Alo alo, mu ci daďi!
Zagi, mari, mun huta shi,
Alo alo, mu ci daďi!
Aikin wahala duk ba ma yi,
Alo alo, mu ci daďi!
Alo alo, mu ci daďi!
Alo alo, mu ci daďi!
Mutane ba su san abin da suka yi da Sarki ba, suna tsammani
wasa Sarkin Busa ke yi da 'ya'yansu, sai suka tsaya suna daáriya,
su ga ikon Allah. Amma da suka ga ya nufi kogi duk sai ransu ya
baci, suna tsammani zai fada ne.
Da Sarkin Busa ya fita bayan gari, sai ya tasam ma wani tsauni
nan kusa da gari. Sarki da mutanensa na tsaye na kallonsu. Sarki
ya ce a ransa, "Na san dai yaran nan ba su iya hawa wannan
tsauni, na ga yadda zai yi da su."
Ko da Sarkin Busa ya isa gindin tsaunin, sai mutane suka ga
tsauni ya bude. Sarkin Busa ya kutsa ciki, duk yaran nan suka
duru bayansa. Da suka shige duka, saura daya da aka bari can
baya yana d'ingishi, sai tsauni ya rufe.
Mutane suka yi ta kuka saboda batan 'ya'yansu. A cikin yaran
nan akwai 'ya'yan Sarki su hudu, su ko ke nan gare shi, duk suka
bace.
85
Inda Allah ya kyauta wa Sarki da ya ke mutane ba su san rashin
tsaida maganarsa ta sa wannan abu ya faru gare su ba. Da sun
sani nan take su ke halaka shi duk da zuriyarsa. To, ga shi kuma
duk nasa sun bace, balle a ce wani makirci aka kulla da shi.
Da uban yaron nan mai dingishi ya ga abin da ya faru, sai ya
ruga ya jawo dansa, yana murna. Aka tambayi yaro me ya sa su
ke bin mutumin nan? Yaro ya ce, "Ai mun ji yana cewa mu biyo
shi, duk abin dadi na duniya ya ba mu. Ya ce akwai tabkin zuma,
da nono, mu yi ta sha. Ga nama soyayye da dafaffe, wai inda zai nuna mana shinkafa ba a maganarta. Ni yanzu, duk bakin ciki na ke
yi da aka bar ni baya. Yanzu suna can suna cin dadinsu, ni ina nan."
Beran nan guda kuwa da ya haye, sai ya tafi ya iske wadansu
beraye can, ba irin wadannan na bala'i ba. Ya rika ba su labari,
yana cewa, "Ba ku sani ba, na yi daron cin dadi. A can ketaren
rafi wani mai busa ya tara mu zai nuna mana inda daddawa ta ke
banza, ga nama, ga mai, ga abinci iri iri, ba mai hana ka ci. Ya ce
wajen nan da zai nuna mana ba a taba sanin akwai wani abu wai
shi kare ba balle kyanwa, karamar alhaki. Zan isa, saura kadan,
sai na ji na fada cikin ruwa. Yanzu 'yan'uwana na can sun yi kiba
ni rashin sa'a ya sa ni na tabe!"
Saura suka yi ta cewa, "Allah ya sa wata rana mai busan nan ya
zo nan kasar, ya tafi da mu mu ma!"
Sarki ya baza mutane cikin duniya, ko a sami labarin ya bulla
wani wuri da 'ya'yansu. Aka yi nema, ko labari. Suka gaji suka
dangana.
Manyan gari suka ce, "Kai, ba ku sani ba fa, Sarkin nan ke da
duk wannan gashin tsiya. Tun da aka halicci duniya kun taba ko
jin inda irin wadannan al'amura suka faru?""
Saura suka ce, "A'a, lalle in ba tasam masa muka yi ba, har mu
kuma zai sa a halaka mu."
Sai suka taru suka tafi gidan, suka kunna masa wuta. Mai gari
ya fito da gudu, suka bi shi da jifa, suka kore shi garin, ya fita
tsirara. Iyalinsa kuwa suka fid da su, kowace ta nufi gidansu.
Suka kwashe dukiyar da ya tara, da akwatunan kudi da ya jibge.
Suka kona gidan, don kada sabon Sarkin da za su yi ya kwashi
ciwon wancan na tsiya.
Ka ji abin da ke aukuwa ga
mai yin alkawari ba ya cikawa.
Musa ya duba ya ga wuri ya yi
haske, ashe har rana ta fito ba su
sani ba. Sai ya ce wa aku, "Na ji
abin da ke aukuwa ga mai
alkawari ba ya cikawa. To, me
86
ke faruwa ga irinku masu hana a cika alkawari? Bai tsaya garin
jiran amsa ba, sai ya shiga gida a fusace.
Da azahar ta yi Waziri ya kira tsohuwan nán ya yi mata
kwando goma na zagi, don har yanzu ta kasa dabarar da za ta yi
tfito da Musa. Tsohuwan nan ta ce, "Kullum ina kokari, wani
dan aku gare shi mai tsai da shi da labaru ko yaushe har gari ya
waye."
Waziri ya tashi ya mangare ta, ya ce, "Tun da ba ki da wata
dabarar da za ki wayace dan tsuntsu, tafi, yau na sa wani." Sai ya
kira bawansa Barakai, wannan da ya aika wajen Sarkin Sinari
kwanan baya, ya gaya masa abin da ya ke so, da kuma yadda aku
ke hana Musa zuwa da labaru.
Barakai ya yi shiri irin na mata, ya tafi gidan Sarki, ya tarad da
Musa inda tsohuwan nan ta yi masa kwatanci. Ya yi masa
maganar Mahmudu na can rai ga Allah, ya ce wai Mahmudu ya сe
a gaya masa, tun da ba ya kaurfar zuwa su gana, shi ma ko lahira
kada Allah ya gama su. Musa ya fashe da kúka, ya ce, "Kullum
ina so in tafi, dan akun-nan ke tsaishe ni da labari. Ga ko Sarki ya
ce in na yi wani abu ba da na shawarce shi ba, bai yarda mini ba
duniya da lahira."
Barakai ya ce, "Don dai wannan dan tsuntsu, yau ka tafi. Nan
zan kwana, da mun ji bayin nan sun yi barci mu je tare ka sallami
akun, in hana shi ya tsai da kai."
Musa ya ce, "Da kin kyauta.". (Don yana tsammani mace ce.)
Suka zauna nan, har barci ya share bayin da ke zaure. Suka tashi
suka nufi wajen aku.
Ko da aku ya hango su tafe su biyu, sai ya gane Barakai namiji
ne, ba mace ba ce. Saboda haka, kafin su iso su yi masa wata
magana, ya riga su ya ce, "Don Allah, yallabai, yau ka tafi. Ni ba
na iya ba ka wani labari. Duk inda ka ke son zuwa, ka tafi."
Barakai ya dubi aku, ya ce, "Ko ba ka ce ba, da ma yau ba mu
son wani labari naka."
Aku ya langabe kai kurum, sai tausayi ya kama Musa, ya ce
masa, "Me ya same ka yau?"
Aku ya ce, "Tunani na ke yi."
Da ya ke Musa ba ya son ya yi wa akun nan abin da zai motsa
masa rai, sai ya tambaye shi tunanin da ya ke yi. Aku ya ce, "Ina
tunanin abin da ya faru ga wani masassaki ne, wanda ya yi kokari
ya tara fiye da abin da Allah ya ba shi."
Musa ya ce, "Wannan masassaki ýa ja wa kansa halaka."
Aku ya ce, "Da. ma ka ji abin da ya same shi, ai da ka san
lalaçewar ba ta da iyaka." Bai tsaya a ko ce ya fadi ba, sai ya
fara:
87
Kowa Ya Yi Kokarin Ya Sami Fiye Da Abin Da
Allah Ya Nufe Shi Da Shi, Ya Ja Wa Kansa
Lalacewa
Domin wai akwai wani masassaki a Katako, yana da 'yarsa mai
shekara biyar da haihuwa, sunanta Halima. Ko da ya ke an sanyaro a kan son tambayar kome ya ji ko ya gani, duk da haka son
tambaye-tambayen Halima sun wuce kima.
Wata rana da safe uban na zaune na sassakar wata kujera, sai
Halima ta shigo, ta ce masa, "Baba, inna ta ga mussa ta ce mata
kyanwa, ashe ba ta san sunanta ba, ko ta sani ke nan?"
Kafin uban ya bayyana mata da mussa da kyanwa duk daya ne,
sai ta sake masa wata tambaya, ta ce, "Baba, kawu ya ce wai
akwai giwa na yawo nan sama, ita ce ke yin fitsari da damina
muna cewa ruwan sama, gaskiya ne?"
Uban ya fashe da dariya, zai bayyana mata ba gaskiya ba ne,
sai ta ce, "Baba, wai kai ma inna ce ta haife ka?"
Uban ya ga za ta hana shi aiki da surutu, sai ya ce mata, "Fita
waje can, ki yi wasa da yara, sai in na kare ki dawo."
Sai ta tashi ta ruga. Tana fita, sai ta ji yara na bin wani wada,
suna cewa, "Malam Dogo, Malam Dogo!
Halima kuwa ko wane karambani ya ja ta, da ganinsa sai ta
tsaya daga kofar zaurensu, ta ce, "Malam Dogo, Malam Dogo,
ka zo, baba na kira."
Malam Dogo da ya ji haka sai ya nufo zauren. Halima ko ta
ruga zaure wajen ubanta, ta rungume shi tana kuka.
Tsammaninta wani dan sanho da wadan ke rataye a bayansa duk
ba kome ciki sai 'yan yara kamarta. Malam Dogo ya zo, ya
durkusa gaban masassaki, ya ce, "Ga ni, 'yar matan nan tawa ta
ce kana kirana.""
Masassaki ya kawo sadakar abinci da goro da kwabo, ya ba shi,
ya ce, "Tun da Halima ta kira ka, ai lalle in sallame ka." Malam
Dogo ya yi godiya, ya bude sanho ya fitad da wata 'yar nakiya da
aka ba shi sadaka, ya mika mata, ta ki karba, don ita ce
gamuwarsu ta fari.
Daga ran nan kullum kuma in zai wuce sai yar biyo ta zauren
-gidan, in ya ga Halima a waje ya ba ta dan wani abin da ya samo
sadaka. Tun tana gudu, yau da gobe har ta saba da shi, ta rika
tsayawa tana karba.
Da ya gan ta dai sai ya zauna, ta hau bisa kafarsa suna wasa. In
ta fara irin 'yan tambayoyin nan nata na yara, sai shi kuma ya
rika ba ta amsa irin yadda ya kamata. In ta tambaye shi, "Me ke
cikin sanhonka?" Sai ya amsa mata, "Tuwo da nama da sukar."
In ta ce, "Ina innarka?" Sai ya nuna ungulu ko shirwa, ya ce,
"Ga ta nan tana tashi." Sai su bushe da dariya. Duk sa'ad da
yarinyan nan ta ga ungulu ko shirwa sai ta ce, "A! Ga innar
Malam Dogo." Ta dubi uwarta, ta ce, "Inna, ke ba ki iya tashi
kamar innar Malam Dogo?" Uwar ba ta ko kulawa da ita in ta
fara tambayarta.
Suna nan haka, ashe wadan nan wani mai sihiri ne, ba a sani
ba. Ran nan sai ya zo wurin masassaki dauke da 'yan kayansa
duka, ya ce, "Na yi niyya yau zan koma kasarmu. Amma in
Halima ta tambaye ka inda na ke, ka ce ni ma na yi fiffike na
tashi kamar innata, don kada ta yi kuka. Kullum ku ce mata zan
dawo gobe."
Masassaki ya yi bakin ciki, don 'yarsa ta rasa abokin wasa. Ya
shiga gida ya dauko wata tsumman riga, ya ba Halima ya ce ta
kawo wa Malam Dogo a zaure. Yarinya ta jawo riga da gudu, ta
kawo masa. Ta fada jikinsa tana murna.
Malam Dogo ya dube ta, duk idonsa suka cika da hawaye
domin sabo. Ya zauna nan har magariba. Da suka yi salla, ya ci
abinci, sai ya kira masassaki, suka fita bayan gari, suka yi tafiyar
kamar loko guda cikin daji, sai suka kai ga wani dutse. Da suka
isa, wada ya dubi masassaki, ya ce, "Ka san an ce soyayya gamon
jini ce, ko ba haka ba?"
Masassaki ya ce, "Hakanan ne."
Wada ya ce, "To, tun da na zo garin nan, ban ga wanda jinina
ya hadu da shi kamar 'yarka ba, Halima. Tun da tana tsorona,
har ka ga yanzu ba wanda ta ke so da gani irina. Kome ta ci ta
rage mini. Kai kuma kana yi mini alheri iyakar gwargwado.
Saboda haka ni kuma zan saka maka. Ko da ya ke kana ganina
haka a wulakance, don in jarrabi mutane shi ya sa na wulakanta
kaina. Nan kasar duk kafin ka sami wanda ya ke al'amari da
aljanu kamata, ka dade." Ya tsuguna ya tara 'yan hakukkuwa,
ya debi ganyayen kan dutse, ya yi turare.
Masassaki ya rike baki ya ga al'ajibi. Da hayaki ya tashi, sai
Malam Dogo ya dubi dutse, ya ce, "Fayau, bude dutsen kudi!"
Nan da nan sai dutse ya bude. Da budewarsa sai Malam Dogo ya
dauki wata 'yar fitila nan rataye cikin dutsen, ya kunna.
Másassaki ya duba cikin kogon dutsen nan, ba abin da ke ciki sai
89
karfe ja wur cikin wata katuwar randa. Ya bude baki yana
mamaki.
Malam Dogo ya ce, "Na ba ka abin da ke cikin dutsen nan
duka, amma da sharadi guda. Duk sa'ad da ka zo, kada ka debi
abin da ya fi fam guda kowane zuwa. Na san fam guda dai ya ishe
ka kashewa yini guda. Daga nan har ka mutu ba ka ganin kudin
nan na raguwa. Ka lura in Halima ta isa aure ka yi mata kaya
masu kyau, ga dai gudummuwata nan na bayar."
Masassaki ya fadi yana godiya, yana rokon Malam Dogo
gafara in ya yi masa wani laifi da. Suka gafarta wa juna. Malam
Dogo ya ce, "Ko da rana ka zo sai ka diba, in dai ba ka gudun
kada mutane su gan ka. In ko da dare za ka zo, in ka fita, ka yi
turare da ganyen nan, ka tabbata ba wani abin firgita da zai dame
ka. In ko ka zo, ka ga abin da na yi ba wani abu ba ne mai wuya.
Sai ka debi ganyen nan na bisa dutse, ka yi turare da shi a gindin
dutsen, ka ce, 'Fayau, bude dutsen kudfi.' In ka shigo, ga fitila ka
kunna, in da dare ka zo. In da rana ne ko, ba ruwanka da ita. Ka
kuma amince, ba kayan aljannu ne ka ke sata ba, balle ma ka ce
za ka ji tsoro. Kai dai ban da dibar abin da ya fi fam guda
kullum."
Ya dubi masassaki ya ce, "Fara daga yau." Masassaki ya duka
ya kidaya fam guda, suka fito. Malam Dogo ya ce, "Garam, kulle
dutsen kudi!" Dutse ya koma ya rufe.
Malam Dogo ya dubi masassaki ya ce, "To, sai mu yi ban
kwana, ni zan wuce." Suka yi sallama. Malam Dogo ya wuce,
masassaki ya komo gida yana tsalle-tsalle don murna. Ya kwashe
duk labari ya gaya wa matar, amma bai gaya mata abin da za a се
da dutsen ya bude ba. Suka yi ta murna.
Gari na wayewa, ko da magariba ta yi
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 12