Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 12
mene ne?" Kaza ta ce, "I, gaskiya ne, ya kamata kuwa ka yi alfahari bisa ga godiyan nan taka. Amma da ka taba ganin mutane sun kama 'yan'uwanka sun yanka, sun fige suna soyawa, yadda na ke ganin kullum suna yi wa dangina, da ran da suka tashi kama ka, bari ta gudu kana fadawa shigifu, in ka balle daga nan ka shiga daji, ko labarin inda ka ke ba a sake ji." Burtu ya yi shiru, ya rasa abin da zai ce wa kaza bisa wannan magana tata. Kaza ta harare shi, ta juya, ta ce, "In za ku yi magana, ku rika tsayawa tukun kuna lura, kuna auna ta tukun kafin ta fito bakinku har wadansu su ji. Ga irin abin da a ke gudu ke nan, mutum ya fadi maganar da bai san kanta ba, bai san gindinta ba, ta zo ta dame shi daga baya. Kai, Allah wadan zaman daji!" Da Ojo ya ji haka ya bushe da dariya, har ya haure ruwan alwallarsa bai sani ba. Da ya gama dariya, ya kare alwalla, ya shiga daki ya yi salla. Da ya gama, sai karuwan nan ta zo ta ce masa, "Maigida, yau ni marmarin shinkafa na ke ji, ita zan dafa, sai a sayo tozo." 55 Zai ce to, sai ya tuna da maganar aku, yana tsammani da ya yarda zai mutu, ga shi kuma ba ya son bata wa matar zuciya, sai ya tuna ba abin da ya fi ransa dadi. Ya san yanzu da ya mutu sai ta fita ta auri wani, shi ta manta da shi. Sai ya ce mata, "An ki, ni yau tuwon dawa za a yi mini, miyar shuwaka." Ta dube shi haka yatsine, ta watsar, ta yi tsaki, ta ce, "In wani ke min da hannun, ba sai ya sa in yi na dawa ba? Ni na shinkafa zan yi, in kama kazarka a yanka in ka ki sawo mini tozo. In ya so, in na yi, ko ka ci, ko kada ka ci, ni ba abin da ya dada ni da kasa." Sai ta tashi ta nufi wajen buhun shinkafa, za ta diba. Ojo ya ga in ya bar ta ta yi abin da ta ke'so, watau shi zai mutu ke nan. Sai ya tafi ya kama ta. Sai kokawa ta kaure kiki kiki. Ojo ya tuna shi namiji ne, ya dauke ta ya kantara da kasa, ya yi ta bugu. Da mutane suka ji kuwwarta tana cewa, "Wayyo Allah, na tuba! Ba na kara yi maka musu, ka ji kaina!" Sai suka rugo, aka zo, aka kwace ta da kyar. Ta yi yaji. Bayan kwana uku Ojo ya bi ta, aka yi rarrashin duniyan nan ta dawo, ta ce in ta koma gidan nan ya zama kabarinta. Ta tashi za ta yi masa halinsu na karuwai, ta tona masa asiri cikin jama'a ya ce ya sake ta. Abinka da mai sule, kafin kwana bakwai ya nemi 'yam mata uku 'yan gaske, aka ba shi. Da ya mila, sai ya ce a sà su lalle gaba daya. Aka sa su, aka yi biki, aka gama. Muka yi zamammu lafiya lau da matan nan nasa, ba sauran mai kuka da wani. Da aku ya kawo nan, ya ga gari bai waye ba, sai ya dubi Musa, ya ce, "Don Allah ka yi kokari ka yiwo abin da kowa zai yaba. Kа tabbata wata dabara taka, da wani tsoro, duk ba su hana makaа mutuwa, domin duk ran da ajali ya yi kira, ko babu ciwo a je. Gama Sarkin Yaki yana zaune lafiyarsa lau, amma ran da ajalinsa yà sauka, sai da ya sayo wa kansa halaka." Musa ya ce, "Ai Sarkin Yaki ya sami lafiya har ya tafi tare da Sarki." Aku ya ce, "Ba Sarkin Yakinku na nan gari na ke magana ba, ina zancen Sarkin Yakin Niraini ne." Musa ya ce, "Ina ne Niraini? Ban taba jih sunan wannan gari ba, balle Sarkin Yakinsu. Me ya sa ya saya wa kansa halaka?" Aku ya ce, "Yanzu kuwa ka ji." 56 In Ajali Ya Yi Kira, Ko Babu Ciwo A Je Wata shekara mutąnen kasar Suraida suka kai yaki kasar Niraini. Mutanen Suraida suka kori na Niraini suka kashe musu jama'a mai yawa. Suna murna za su shiga garin, ashe Sarkin Yakin Niraini ya shirya wadansu dakarai, suka biyo jama'ar Suraida suka yi musu zobe, suka hana su gaba, suka hana su baya. Da wani dakaren Suraida, wai shi Barde, ya ga za a halaka su nan tsaye da yunwa ma kadai, sai ya ce wa 'yan'uwansa, "Ya kamata mu yi kunar bakin wake. Kada mu mutu nan, mu bar wa na baya abin fadi." Suka yarda, suka tasam ma mutanen Niraini. Barde ya fara kaiwa, ya soki wani dan saurayi, ya mace. Mutanen Niraini suka kashe yawancin mutanen Suraida, aka kama Barde, har an fara sassare shi za a kashe, Sarkin Yaki ya ce a kyale shi. Ya sa aka dauke shi aka kai shi gidansa, ya yi ta jiyyarsa ba dare ba rana, kamar dansa. Kullum safe, da ya fara iya magana, sai ya zo ya tambaye shi yaya ya kara ji. Shi kuwa sai ya amsa masa, "Na gode Allah." Yana nan gidansa, ba ya iya tashi har wata guda, sa'an nan ya fara tashi da sanda yana doddogarawa. Sarkin Yaki na binsa, yana-tare shi kada jiri ya kwashe shi ya faďi. Bayan 'yan kwanaki, ya fara tafiya ba sanda. Ran nan yana tattakawa, ya dube shi, ya ce, "Yi tsalle mu gani, in ka iya." Barde ya yunkura kamar zai yi tsalle, sai ya ji ba ya iyawa. Ya dubi Sarkin Yaki, ya ce, "Baba, ai ba na iyawa sai dai an.kara kwana biyu." Bayan kamar kwana bakwai, da Sarkin Yaki ya ga lalle Barde ya warke, sai ya ce ya yi tsalle ya gani. Ya yunkura, ya yi tsalle, ya buga kafa, ya dube shi, ya durkusa ya ce, "Allah ya taimake ka yadda ka taimake ni." Sarkin Yaki ya ce, "Alhamdu lillahi, tun da ka warke!" Sai ya nufi cikin gida, ya dauko masu guda biyu, ya fito da su wajen Barde, ya ce, "Mu je bayan gari yawo, mu shawo iska." Barde ya се, "То." Ya karbi masu ya rike, har suka isa bayan gari. Da isarsu sai Sarkin Yaki ya ce masa, "Zabi daya." Barde ya ce, "Me za mu yi da su?" 57 Sarkin Yaki ya ce, "Kai dai zabi daya, na ce." Ya zabi guda gajere, ya mika masa dogon. Ko da ya karba, sąj ya ce masa ya tsaya nan, shi ya ja da baya kadan su yi yaki. Yaki ko na sosai, ba wasa ba, kowa ya sami dan'uwansa ya kashe. Da Barde ya ji haka, sai ya yar da nasa mashin, ya ja da baya, ya ce, "Subuhana lillahi, Allah ya sawwaka in yi yaki da kai!" Sarkin Yaki ya ce, "Ko kana kasa kana dabo, sai ka yi. Cikin yakin da muka yi da ku watan jiya ina da da, kai ka sa mashi ka tsire shi. Na neme ka kasa da bisa lokacin nan, na rasa, sai daga baya har an yi maka raunuka za a kashe, na gan ka, na ga in na kashe ka sa'an nan ban huce ba, don lokacin nan kusa da matacce ka ke. Saboda haka na ce a kyale ka, na jiyyace ka, sai yanzu da na ga ka warware, ka iya jin zafin da dana ya ji, na ke so in rama masa, ko da ya ke ba shi da rai. Yana kan kokarinsa ka kashe shi, saboda haka ni kuma na ke so in kashe ka bisa kokarinka, ba sa'ad da ka ke ba wąni makami a hannunka ba. Yanzu ko kana so, ko ba ka so, sai ka dauki mashin nan ka taso mini, sa'an nan ni ko in tsire ka." Barde ya yi tubar duniyan nan, ya ki ji, sai ya ce a ransa, "Da ma ni kusan cikin matattų na ke, shi ya kubutad da ni, to, tun da Allah ya nufa, don in kara shan ruwan wata guda ne kadai, aka nufe ni da tsira da fari, ai sai in yi godiya." Ya dauki mashi ya rike. Ko da Sarkin Yaki ya ga ya rika, sai ya zaburo zai tsire shi, yana tsaye yana Kalmar Shahada. Allah mai aikata abin da ya ke so, wallahi, yallabai, kafin ya kawo gare shi, sai kafarsa ta fada cikin wani ramin kurege, mashinsa ya kafe daga baya. Yunkurawan nan da ya ke yi da fushi, sai ya fadi da baya bisa 58 mashin. Nan take ya tsire kansa, bai ko motsa ba. Da Barde ya ga haka, sai ya rungume shi yana kuka. Ya sa hannu a kai, ya shiga gari ya gaya wa Sarki yadda duk aka yi. Aka zo aka iske shi, aka yi ta mamaki, aka rufe shi. To, tun daga ran nan Barde ya dauki alkawari yana kawo wa iyalin Sarkin Yaki abin da za su ci, har ya kan kawo musu awaki su sayar su sayi hatsi, duk dai wai saboda alherin da Sarkin Yaki ya yi masa. Musa ya ce, "Wallahi in ni ne ko kasa ba na bada musu, tun da ya ke ba da niyyar gari ya yi mini alherin ba." Aku ya ce, "Ai ba kai kadai ba, kowa ma ya ji wannan labari haka zai ce." Musa ya yunkura zai tashi, sai ya ji an yi asalatu, ba damar ya fita, kowa ya farka. Da azahar tayi, Waziri ya ga ba zai sami Musa ba, ta ya rude shi da Mahmudu na can na abin kirki, sai ya sake dabara ya rubuto takarda kamar daga Mahmudu, ya aiko tsohuwan nan ta kawo wa Musa. Da ya karanta sai ya ga an ce, "Daga Mahmudu zuwa ga dan'uwana Musa, rabin ransa. Gaisuwa mai yawa da so da yarda. Bayan haka, Musa, yanzu kana da rai har ka yarda aka raba mu ko? To, ga shi jiya na fada wani barde cikin mutanen Sinari, ya yi mini raunuka abin ba ko masaka tsinke. Ga alamar da na ke ji a jikina, ni da ganinka kuma sai Darassalam. Tun da har ka manta da ni, ba ka iya kokarin da za ka zo mu nemi juna gafara ba, to, shi ke nan, ba kome, ni na roke ka gafara. Mutuwa dai ai kowa ka gani za shi ne. Musa! Musa! Tuna zumunci, Musa! Haza wassalam." Da Musa ya karanta wannan takarda $ai hawaye. Tsohuwan nan kuma ta tsuguna ta yi ta yanka maså karya, wai a gidansu (a ke jiyyar Mahmudu). Wannam takardar wai shi ya ba ta hannunsa da nata. Musa duk ya dimauta, mutanen gida suka rasa kansa, suka rasa gindinsa. Da asubar fari, tun bayin nan ba su yi barci ba, sai ya kintsa, ya tafi wajen aku yana kuka, ya nuna masa takardan nan da tsohuwa ta kawo. Aku ya sa tabarau, ya karanta, sai shi kuma ya fashe da kukan karya, ko da ya ke ya 59 san takardar ba Mahmudu ya yiwo ta ba, makirci ne. Sai ya ce wa Musa, "Sai ka yi shiri ka tafi." Musa ya ce, "Ina fa ka ga taflya yanzu, ga bayi can ba su yi barci ba? Da ma abin da ya sa ka ga na zo tun da wuri haka, don in kawo maka takardan nan ne ka gani. In kuma kana da wani labari wanda zai dan faranta mini rai, ka gaya mini tun yanzu, ko na ji dan sanyi-sanyi a zuciya, kada in taho an jima in sun yi barci ka ce za ka tsai da ni, har in zo in makara." Aku ya ce, "Haba, ranka ya dade, in tsai da kai bayan na karanta wannan takarda, mahaukaci ne ni? Tun da dai ka ce kana son in gaya maka wani dan labari wanda zai sa bakin cikinka ya ragu, wannan shi ya fi kome sauki gare ni. Ga kujera nan, zauna, don tsayuwa ba ta da amfani." Musa ya haye kujera ya zauna zugudum. Aku ya yi kaki, ya tofad da yawu, ya fara: 60 Labarin Wadansu Abokai Su Uku Wata rana wadansu samari su uku, abokan juna suka tashi daga garinsu za su wani gari neman aure. Kowane ya yi wankin kayansa, suka yi ado, suka kama hanya. Suna cikin tafiya, sai karamin ya ce, "Ku ci gaba, na iske ku ni zan ratse. Suka wuce, shi kuwa ya ratse, ya rabu da hanya kadan sai ya tarad da wani dan akwati, barayi sun sato ya fadi. Ya duba gabas, ya duba yamma, bai ga kowa ba, ya duka ya dauki akwatin, ya ji da nauyi, ya nemo wani dutse ya fasa. Da fashewarsa sai ya ga kuďi ciki cunkus, sulalla. Ya durkusa, ya sa hannun rigarsa ya kunshe, ya fito da gudu ya bi 'yan'uwansa yana kira. Da suka ji kira, suka tsaya. Ya ce, "Albishirinku!" Suka ce, "Goro." Ya ce, "Kun ga abin da na tsinta." Kowane da ya kyalla ido ya ga kuďi, duk suka yi ta murna, suka koma gefen hanya suka kidaya, suka ga fam ashirin da hudu ne da sisi. Wanda ya tsinto kuďin na kirki ne, saboda haka ya ce, "Sai a raba, kowa ya sami fam takwas takwas, sisin nan kuwa mu sayi abinci da shi mu ci." Da babbansu ya ji haka sai ya сe, "To, madalla, mun gode, Allah ya bar mu tare! Amma abin da ya fi, sai ka tafi gari maza ka sawo mana tuwo da tsire da sisin nan namu. Mu kuwa mu ajiye kuďin, in ka dawo sa'an nan mu raba." Yaron da ya tsinci kudin ya tashi, ya nufi gari da gudu. Da bacewarsa sai babban ya ce, "Abin da ya fi sai mu yi dabara mu karbe kudin nan, mu raba mu biyu, watau fam goma sha biyu biyu ke nan." Daya abokinsa ya ce, "Lalle gaskiyarka. To, yaya za mu yi ke nan?" Babban ya ce, "Ina da dabara. Ga wani maharbi can, mu kirawo shi mu ce ya shiga kogon itacen nan, in an yi magana ya rika amsawa." Suka kira maharbi, suka gaya masa duk abin da su ke so ya yi musu, da abin da su ke so su karbe wa dan'uwansu, har suka ce sa ba shi lada. Da maharbi ya ji batun kudi haka ya yarda. Ya shiga 61 kogon ke nan sai yaron ya komo. Da hango shi, sai suka fara kuka. Ya ce, "Lafiya?" Suka ce, "Ina fa lafiya, itacen nan ya kwace kudi duka!" Yaron ya dubi itace, ya ce, "A'a karya ne, itace da ba ya magana ma, ina ya kai ga sata? Ku dai ku sake shawara." Daga nan sai mutumin da ke cikin itace ya ce, "Wace shawara za a sake? Ni na dauke. Kuma in kana tsammani kai ka fi 'yan'uwanka jaruntaka, to, zo karbi. Matsiyata 'ya'yan zamani, wadanda ko iyayensu ma ba su san girmansu ba, balle wani!" Ko da yaro ya ii haka sai ya garzaya, bai zame ba sai gidan Sarki. Ya gaya masa duk abin daya faru tun daga farko har karshe. Sarki ya ce, "An tasam ma munafunci. Yaya za a ce itaciya ta yi magana? Ina 'yan'uwanka?"" Yaro ya ce, "Suna can gindin itaciya." Waziri ya dubi Sarki, ya ce, "Ranka ya dade, ai sai ka sa ni in tafi in ji in gaskiya ne. Ka san ikon Allah ya fi da haka. Sarki ya ce, "To, sai ka tafi ka gani." Yaro ya shige gaba har gindin itaciyan nan, suka tarad da 'yan'uwansa can suna 'yan koke-koke kamar da gaske. Da ganin Waziri suka ce, "Alhamdu lillahi!" Suka faďi suka yi gaisuwa. Waziri ya dube su, ya ce, "Ku ne itaciya ta kwace muku kuďi?" Suka ce, "1, mu ne, ranka ya dade. Daga mun zauna nan gindinta muna kidayawa, sai muka ga guguwa ta tashi ta murtuke wurin, duk kura ta buce mu, muka rasa inda mu ke. Can an jima sai ta natsa, muka duba kudin da ke gabammu, suka ce dauke mu. Muka shiga tonon kasa, don muna tsammani kura ce ta rufe su, ba mu ga ko kwabo ba. Muka tashi za mu yi fada da juna, don kowa na tsammani dan'uwansa ne ya boye kudin, sa'ad da mu ke ta kammu yayin da guguwa ta buce mu. Da muka fara zage-zage, sai muka ji kamar daga sama an ce, "Kada ku zargi junanku, ni na dauki kuďin. In kuwa kuna jin wata-wata ne ku zo ku kwata. Muka duba babu kowa, sai dai magana mu ke ji na fitowa daga itaciyan nan." Da maharbin nan na cikin itace ya ji haka, sai ya nisa, ya се, "M, wannan dahir ne." Waziri ya dube su, ya ce, "A'a! Ai kuwa ashe da gaske ne." Itaciya ta ce, "Af, da kana tsammani karya ne? Sai ka zo ka kwatam musu."" Ko da Waziri ya ji haka sai ya rike baki, ya ce, "Ki yi mini gafara, ni ba ruwana, aiko ni aka yi." Nan da nan sai ya aika aka fada wa Sarki ya zo da kansa ya gani, domin an ce gani ya kori ji. Can an jima ya tinkaro duk da 62 mutanensa. Da isowarsa Waziri ya ce, "Ranka ya dade, ka ga 'yar itaciyar da a ke markabu kanta." Da maharbi ya ji haka sai ya ce, "Wai, wai, wai, ni ce 'yar itaciya! Kai ne wa tukun da ka ce mini 'yar itaciya? Har dan tsugunin nan naka ka isa zagina? Daga yau ba ka sake duban kamata ka ce mata 'yar itaciya ba!" Da jin haka fa, sai hantar Waziri ta kada, ya fadi ya yi sujada yana ta ahi, yana rokon gafara. Sarki ya tsaya tsayin daka, ya dubi kogon itaciyan nan, ya ga lalle mutum na iya shiga. Ya lura da gindinta kuma ya ga sawun mutum kamar ya hau ta, ya dubi takon nan ya ga dai bai yi daidai da na ko daya daga cikin samarin nan masu kudi ba. Ya tuna tun da ya ke bai taba jin ma wanda ya ji maganar aljannu haka a fili ba. Kai, karewa ma dai tun da Annabi ya kaura aka bar jin irin wannan al'amari. Ko da ya lura da haka sai ya hakikance makirci dai aka kulla, don a cuci yaron nan da ya tsinci kudi. Sai ya dubi Waziri da ke ahi, ya ce, "Kai, tashi! Kwaure ka ke wa sujada?" Ya juya wa itaciyar, ya ce, "Yanzu dai ko ki ba su kudinsu tun da girma da arziki, ko kuwa in sa a kone ki. Da mutum da aljani ni duk wanda ya tasam ma zalunci cikin kasata sai na ga iyakarsa!" Sai itaciyar ta ce, "Kai dai tsaya kan mutane. In ka fada aljannu sai kai a ga iyakarka." Sarki ya dubi mutanen da ke nan, ya ce, "Duk ku saro kirare." Suka ruga nan da nan suka cika gindin itaciyan nan da itatuwa da kirare. Ya ce, "A kawo ashana." Aka mika masa. Ya tasam ma itaciyar zai kunna mata wuta, duk kowa ya rike baki. Maharbi ya ga dai in ya kyale minti biyu, lalle zai halaka. Sai ya yi kara ya се, "Don Allah, ranka ya dade, kada ka sa wutan nan. Ni ba kowa ba ne, mutum ne. Bari in sauko don Allah!"" Nan da nan sai mutum ya tsirgo daga kogo, da kudin rike a hannunsa. Ya fadi ya gai da Sarki, ya tsuguna nan, ya fede masa biri har wutsiya. Sarki da mutanensa suka yi mamakin wannan al'amari. Mutane suka yi ta cewa, "Lalle Sarki shi ma aljani ne." Nan take Sarki ya sa aka yi wa yaran nan biyu azzalumai, da maharbi, bulala hamsin hamsin, ya sa aka kai su gidan kurkuku su yi wata shida shida, ran da za su fito kuma a kewaya da su gari, kowa ya gan su. Ya dauki kudin duka ya ba yaron abinsa. Yaro ya fadi ya yi gaisuwa, ya tashi ya koma gidansu. Sarki kuma ya koma gida. Kullum in an ta da tadi, in ya dubi Waziri, ya tuna da yadda ya yi goho da katon bujensa, sai ya yi ta dariya. Musa ya yi murmushi ya ce, "Ai ba Sarkin nan kadai ba, kowa 63 ya ji wannan labari ya yi dariya. Munafunci dai ba shi da amfani." Aku ya ce, "Ina ka san munafunci ba shi da amfani, tun da ba ka ji labarin Kado ba, da wadansu 'yam fashi guda uku?" Musa ya ce, "Har ya fi wannan daďi? Ban yi tsammani bа. То, yaya suka yi? Fada mini mu ji." Aku ya ce, "Wannan d'in me? Kasa kunne ka ji." 64 Munafuncin Dodo, Ya Kan Ci Mai Shi Wata rana wani bakauye wai shi Kado ya dauki gatarinsa, ya shiga daji zai yiwo itace. Dawan nan kuwa da 'yam fashi, mutanen dan kauyen nan duk sun san da su. Can bakauyen nan ya yi nisa cikin daji, sai ya hango wani abu tsibe yana daukar ido, ya matsa ya ga ko mene ne, sai ya tarad da sulalla ne tsibe. Ya waiwaya baya, ya waiwaya gaba, bai ga kowa ba. Sai ya duka, ya cika aljihun taguwarsa fal, ya saba gatarinsa, ya sheka da gudu ya nufi gida. Ya rabu da wajen da ya debi kudin nan ke nan, sai ya gamu da 'yam fashi su uku. Suka ce masa, "Kai, tsaya! Me ya koro ka?" Kado ya tirje yana kaduwa, yana tsammani kudin nan da ya debo nasu ne. Sai ya ce, "Iye! Ni? Na'am. Mutuwa ce na gani a fili, shi ya sa na ke gudu." 'Yam fashin nan suka yi dariya, suka ce, "Mutuwar da kanta ka gani, ko kuwa maciji dai?" Kado ya ce, "Iye! Ni wallahi mutuwar ce da kanta na gani a can tsibe, shi ya sa ban ko tsaya wurin ba, don kada a ce na gan ta, na sheko da gudu." Da 'yam fashi suka ga lalle ya tsorata da su, sai suka ce masa, "To, mu je, ka kai mu mu gan ta mu ma." Kado ya wuce gaba suna biye, har wajen da kudin nan su ke. Ya ce, "Ga ta! Na rantse da Allah kuwa ban diba ba, kada ku ce ko na ďiba ne." Yana boye-boyen aljihu yana tsammani ajiyarsu ce, shi ya sa ya kara rudewa haka. Da Allah ya sa ba su dubi aljihunsa ba sai suka ce, "To, tafi. In ka fadi kuwa, muna zuwa da dare mu yanka ka." Ko da Kado ya ji haka sai ya ranta cikin na kare, bai zame ba sai gida. Ya kai yana haki, kamar ransa zai fita. Ya boye kud insa, ya kama bakinsa ya tsuke. Da 'yam fashin nan suka ga ya wuce, sai suka yi ta mamakin kudin nan, suka ce, "Watakila wadansu barayi ne suka sato, da suka ga sun yi musu yawa suka zubad da sashi nan. Allah Sarki! " Bakauyen nan fa tsammani ya ke, namu ne. 65 Babbansu ya ce, "Kai, ai ko ya firgita. Yanzu fa ya dade da kaiwa gida." Sauran suka ce, "Haba, tuni. Sa'ad da ya garzayan nan, ai ko mota ba ta kamo shi." Suka bushe da dariya. Sai babban ya dauki sule guda ya ba karamin, ya ce, "Ruga maza kasuwa ka sawo mana abinci mu ci tukun, idanummu su bude, sa'an nan mu san yadda za mu yi kasafin wannan kudi." Karamin ya karba, ya sa riga kamar ba barawo ba, ya yi nadi, ya tafi kasuwa, ya nufi wajen mai tuwo, ya sayo, ya kuma biya mahauta, ya sayo musu tsire ya dora kan tuwon, ya dauko ya nufo daji. Yana kulle-kullen abin da zai aikata da kuďin nan, da nasa ne shi kaďai. Sai ya ga itacen tinya, ya ajiye kayansu, ya ce, "Alhamdu lillahi! Bari in debi ruwan tinya in zuba wa abincin nan, in kai musu. Ni kuwa ko sun ce in ci, sai in ce na ciwo daga kasuwa. Ka ga da sur ci duk sai su mace, ni kuwa in kwashe karfena, in shiga gari in yi ta kece raini." Ya karya tinya ya zuba. Shi kuma ashe kafin ya dawo 'yan'uwansa sun yi shawara da ya zo su kashe shi, su kwashe kudi, su raba su kadai. Suka ce ai haka abin ya fi auki. Can sai wannan karamin ya iso da kayan abinci. Ko da ajewarsa sai suka hau masa da bugu, bai san hawa ba, bai san sauka ba, suka kashe shi. Suka fada abinci da ci, in sun gama sa'an nan su kwashe kudi su san inda suka nufa. Da gama cinye abinci, sai kowanensu ya fara kaduwa, yana faduwa yana tashi, kafin kiftawa da bismilla duk suka kai takarda. Can bayan kamar kwana bakwai sai Kado ya ce a ransa, "Bari in koma wurin nan, in na tarar suna kwashe kudinsu in tsuguna in yi kala, ko Allah ya ba ni dan taro. In kuwa na tarad da su sai in ce na zo ne in gaya musu Sarki zai aiko da dogarai a kama su gobe, abin da ya fi kowa ya yi ta kansa. In ce kuma abin da ya sa na gaya musu don haka, sun ji kaina ne ran nan. Ka ga watakila ma sa ba ni dan sule. Kuďin dai ga su nan tsibe kamar ba su so, ba su da alamar karewa." Da isarsa wurin sai ya tarad da su duk sun mutu. Ya yi juyayin abin da ya kashe su, ya rasa. Da ya lura har kuraye sun ci su, sai ya yi zaton su ne suka kashe su. Ya rasa abin da zai yi don murna. Ya shimfida gwadonsa, ya kwasa. Ya yi 'yan kirare ya dora, don kada a gane, ya kai gida, ya gina rami ya binne. Magariba na yi kuma ya kira dansa, suka tafi suka kwashe saura. Ya zauna ya yi ta cin kudinsa sannu kan hankali, da shi da dansa, ba wanda ya gane. Musa ya bingire da dariya, ya ce, "Allah mai girma! In rabo ya rantse, sai mai shi!" 66 Ya Saurara haka sai ya ji kiran salla, ya ce wa aku, "Wancan kiran sallan fa, na fari ne, ko na biyu?" Aku ya ce, "Sai dai na fari. Amma bari mu ji." Sun yi shiru suna saurare, sai suka ji ladani ya ce, "Assalatu!" Musa ya ce, "Subuhana lillahi, ashe har

Chapter 6 of 12