Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 12
sa an tsire shi, in gari ya waye. Ai cewa aka yi su kama barayi, ba a ce musu su kashe ba. Duk mu tsaya, in ya so in za su kashe mu ne su kashe mu duka, tun da dai suka raba mu da dan'uwammu. In ko suka kashe mu, ai lalle sur ma a kashe su, don mu ma Musulmi ne, ba kafirai ba." Da 'Yan Gadin nan suka ji haka fa, sai suka yi tsammani sun kashe mutumin nan ne. Saboda haka suka fara shawarar su gudu, kada a gan su. Suna cikin shawarar inda za su bi, sai suka ji barawon nan na kwance, ya fara kakarin mutuwa, yana shakuwa kikaf kikaf. Can sai ya ja wani kakari mai karfi, ya yi shiru. Sauran barayin suka buga salati baki daya, suka ce, "Ya cika." Ko da 'Yan Gadi suka ji haka, ba su tsaya su gama shawarwarinsu ba, sai kowa ya ce in ba ka yi ba ni wuri. Kazunzumi da jin tif tif tif na 'Yan Gadi suna gudu, sai ya tashi ya shiga gaba, sauran na biye har gida. Da zuwa suka sami ruwa mai sanyi, suka kyankyama. Ka san na gaya maka kafin su debi rogon nan sai da suka ci daya daga cikinsu tukuna. Abinka da kayan zalunci, ko da suka sha ruwan nan sai danyen rogon nan da suka ci ya taso, ya murde su, kowane ya yi ta murde-murde abinsa, yana nishi. Kafin asalatu cikunansu suka haye tim, sai amai sai zawo, gari bai waye ba, sai da duka suka hauri arewa. Da safe da aka tarad da su kowane cikin nan ya kumbura kamar salka. Ga su kace-kace cikin amai da zawo. Rogo na fita har ta hanci. Aka duba sako aka ga kwanduna cike da danyen rogo, sai aka hakikance danyen rogo suka yi wa cin yunwa, ya halaka su. Aka yi 'yan koke-koke, aka yi musu jana'iza, aka kare. 20 Garin nan ya faye yawa, 'Yan Gadin nan ba su san wannan abin ya auku ba. Da suka gamu da hantsi sai guda ya ce, "Shin wa ku ke tsammani ya harbi mutumin nan ne na jiya? Ni dai na tabbata ba ni ba ne." Na biyu ya ce, "Balle fa ni da na ke biye da ku daga baya." Na uku ya dubi na fari, ya ce, "Amma ko da ku ke neman ku maka mini laifi, ai ku kuka ce in harba." Na fari ya ce, "I, gaskiya ne, amma ai kai ka san abin da na ke nufi. Ka harba ta ketare kansa, ba ka same shi ba." Na uku ya ce, "Ni ma tsammani na ke koli na harba ta. Ina mamakin yadda ta same shi. Kaddara dai ce ta tarad da ajali kusa." Sauran suka ce, "Gaskiya ne, sai dai mu yi kurum, kada mu tona kammu." Daga'ran nan duk sa'ad da biyu daga cikinsu suka gamu sai su ta da taďin, su rika kokari su lika wa wanda ba ya nan laifin. Suka zauna kan hakanan dari dari har iyakar ransu, suna tsammani a gane su yau, a gane su gobe, ba su ji magana ba. Suna son su tambaya, suna jin tsoron kada son iyawa ta tona su. Musa ya ce, "Wadannan 'Yan Gadi sun kuwa isa sakarkaru." Aku ya ce, "Su ma ai suna da hankali bisa ga wani Bahaushe wanda ya tafi fatauci cikin kasar Yarbawa." Musa ya ce, "Har ya fi wadannan sakarci? Haba, wanda ya fi wadannan sakarci, ai sai yanka." Aku ya ce, "Bari ka ji gogan naka, ka san ko cikin Hausawa akwai Yausawa." 21 Sauna Kira Mana Shashasha, In Ka Ga Sakarai Ku Taho Tare Wata rana wani Bahaushe wai shi Wawa za shi fatauci, sai ya bi ta kasar Yarbawa, Wawa ba ya jin Yarbanci, mutanen da ya tarar a wannan gari su kuma ba su jin Hausa. Amma duk da wannan Wawa bai lura ba. Yana cikin tafiya, ya kawo kofar gari, sai ya ga wani katon garken shanu fari fat suna kiwo. Wawa ya yi mamakin wanda ke da wadannan shanu masu yawa haka, sai ya tambayi wani mutum nan kofa ya gaya masa ko shanun wane ne wadannan. Mutumin ya amsa da Yarbanci, ya ce, "Ni baı ji ba." Wawa da ya ji haka tsammani ya ke "Ni ban ji ba" shi ne mutumin da ke da shanun. Don haka ya ce, "Ni-ban-ji-ba lalle yana da sukuni." Ya wuce ya shiga gari, sai ya kai ga wani babban gida. Ya daga kai, ya ga lalle gidan nan ya amsa sunansa, sai ya ce wa wani yaro da ke nan kofar zidar, "Don Allah, samari, wa ke da wannan babban gida haka?" 22 Yaron ba ya jin Hausa, shi kuma sai ya ce a cikin harshensa "Ni ban ji ba." Da Wawa ya ji haka, sai ya ce, "Kai, ba shakka Ni-ban-ji-ba ba wanda ya fi shi sule garin nan. Wannan irin gida sai ka ce na Sarki. Da ganin wannan ai ko ba a gaya maka ba ka san wurin nan sule ya zauna da gindinsa." Ya haura takalmansa ya wuce faram, faram, faram, faram, har bakin kogin garin. Yana zuwa sai ya tarad da wani jirgi ya zo, ana ta fid da kaya daga cikinsa. Wawa ya dubi kaya, ya ce, "Oi! Wannan jirgi ya yiwo kaya!" Ya dubi wani nan kusa gare shi, ya ce, "Dan'uwa, duk ko kayan nan na mutum guda ne?" Shi Bayarabe bai ji abin da ya ce ba, sai ya dube shi, ya ce, "Ni ban ji ba." Da Wawa ya ji haka sai ya rike baki, ya ce, "Masu gari! Hakika Ni-ban-ji-ba ya huce haushinsa. Ina ma Allah zai sa in gamu da wannan mutum, ko wajen adonsa ma in more ma idona!" Sai ya zauna ya huta, ya debi ruwa ya sha, ya kama hanya zai wuce. Ya kai kofar gari ke nan, sai ya ga wani matacce an dauko shi, za a kai shi a rufe, wadansu na ta kuka. Wawa ya tsaya yana dubansu. Tausayi ya kama shi, ya matsa wajen wata tsohuwa, ya ce mata, "Wane ne wannan ya riga mu gidan gaskiya?" Tsohuwa ba ta ji Hausa ba, sai ta dube shi, ta ce, "Ni ban ji ba."" Wawa da ya ji haka sai ya dafe kai, ya ce, "Allah mai girma! Ka san kowa samun nan na duniya ya ruda, ya shiga uku. Don Allah dubi abin da Ni-ban-ji-ba ya tara. Ga shi yanzu ya zama sai labari, kamar dadai duniya ba a halicce shi ba! Cikin duk abin nan da ya tara, dubi dan kyallen da za a kai shi da shi. Tun da ya ke al'amarin nan haka ya ke, to, ni yanzu me ya ruda ni har da na rabo da gida don rashin wadar zuci? Ga shi Allah bai hana mini abin da zan ci ba. Watau ba dai abin da ya fid da ni gida sai in sami abin alfahari in kara sabo. Mhm, Allah ya kiyashe mu da aikin Shaidan! Na gode Allah da ya kawo ni nan na sami gargadi daga al'amarin Ni-ban-ji-ba. Ba sauran abin da ya fi, sai in koma garimmu, in dangana da abin da Allah ke ba ni wajen 'yar gonata. Da ma an ce, "Gani ga wani ya isa tsoron Allah." Musa ya tashi, har ya bude zauren farko, sai ya ji bayi sun farka. Sai ya kuta, ya koma. Da Waziri ya ga kwana biyu sun wuce, kowace safiya bayin 23 nan da ya sa suka dawo sai su ce ba wanda ya ko leko zauren, har abin ya dame shi, ya ce, "A'a! Da ko na yi tsammanin zai fito, yaya haka! Amma ba kome, kada ku fasa aikinku, na san dabara." Ya kira wata tsohuwar baiwarsa, ya bayyana mata abin da ya ke so duka game da Musa, ya ce mata in ta yi kokarin ta taimake shi har ta sa Musa ya fito waje, zai ba ta fam goma, ya kuma 'yanta ta. Ya kawo sule goma, ya fara ba ta ta lasa. Tsohuwa ta ce, "Ta kwana gidan Sauki." Magariba na yi, sai ta shiga gidan Sarki da kayan talla, ta kaikaici idon mutane ta yahuto Musa waje guda, ta ce, "Mahmudu ya aiko ni, ya ce a gaya maka wai kai haka za ka yarda ka lalace cikin mata? Ya ce a gaya maka fa duniya ba ta auren raggo." Musa ya matsa kusa da tsohuwa, ya ce, "Don Allah iya, yana can yana ta yaki ko?" Tsohuwa ta ce, "Haba! Yanzu sansanimmu akwai wanda a ke magana irin Mahmudu? Ni ma fa can na ke sansani, mu ke yi musu abinci. Mahmudu ya shaku da ni, ya aiko ni gare ka." Musa ya ce, "Koma maza ki gaya masa, gobe in Allah ya so ya gan ni." Tsohuwa ta koma. Da dare ya yi, Musa ya saurara ya ji barci ya kwashe bayin nan, sai ya shigo damaru, ya zo wurin aku, ya ce, "Ka ji Mahmudu na can sansani yana ta abin kirki, ni za ka sa in lalace nan cikin mata." Aku ya ce, "Yallabai, ina ruwana? Ni ban hana ka ba. Yaya barde kamarka zai ce za shi wurin yaki a hana shi? Tun da ya ke niyyarka ka yi abin da zai faranta wa tsohonka rai ne, ai kowane 24 hadari ka shiga Allah ya fisshe ka, yadda ya fid da Auta dan Sarkin noma daga namun jeji." Musa ya ce, "Wane rigima ta kai shi ga fadawa hannun namun jeji?" Aku ya karba: 25 Labarin Auta Dan Sarkin Noma Da Namun Jeji Wata rana wani manomi ya ce wa dansa Auta kullum ya san yadda zai yi ya harbo musu abin da za su yi miya. Auta yа сe. "To." Kowace rana sai ya je daji, yau in ya harbo zomo, gobe ya harbo batsiya ko gada. Kullum haka har ran nan bai samo ba, uban ya yi ta yi masa fada har ya ba shi kashi. Yana cikin haka, ran nan har namomin daji suka gaji da kisa, suka kai kara gun zaki, Sarkinsu. Zaki ya ce, "To, yaya za mu yi? Kun sani fa Allah abin tsoro ne, mutum ma abin tsoro ne." Sai kura ta ce, "Ai, ranka ya dade, babu wata dabara sai mu yi kokari mu kawo maka yaron nan, kai kuwa ka yi abin da ka ga dama da shi." Sauran dabbobi suka ce, "Ai kuwa haka ne, abin da kura ta ce shi ne gaskiya." Suka sallami Sarki, suka watse. Ran nan yaron yana yawon harbi sai ya ci karo da dila ya ja baka zai harbe shi, sai dila ya ce, "Tsaya! Na ce ko abinci ka ke so? Zo in kai ka inda za ka hųta da wahala." Auta yana tsammani gaskiya ne. Ya bi shi, suka mika har wani katon kogo inda zakin nan ya ke mulki. Da shigarsu dila ya ce ya ajiye bakansa daga waje don kada a ce shi maharbi ne. Suka shiga, sai dila ya komo da baya ya boye bakan yaron. Suka tarad da zaki a zaune, duk ga namomin daji sun kewaye shi, ana fadanci. Dila ya fadi, ya yi gaisuwa. Kura ta dubi yaron nan, ta ce, "Kai, ba ka gai da Sarki?" Auta ya ce, "Ke, me ya sha miki kai? Ke kika aiko ni?" Ya duka ya yi gaisuwa. Da suka zauna, zaki ya dubi dila, ya се, "Shi ne wannan da ya dame ku?" Kura ta amshe ta ce, "Shi ne, ranka ya dade. Kuzajje mai kaі kamar kodago!" Zaki ya ce ma Auta, "Kai samari, me ya sa ka ke kashe mana 'yan'uwa?"" Kafin ya amsa tambayar Sarki sai kura ta ce, "Ranka ya dade, raina mu dai ya yi, dubi jikinsa, dan nema, jemamme!" Auta ya durkusa, ya ce, "Ranka ya dade, shin kai ne Sarki, ko kuwa kura?" 26 Da zaki ya ji hàka, sai ya yi fushi da kura, ya ce. "Kada in sake jin kin yi magana a nan. Faďi jawabinka, samari." Auta ya sake durkusawa, ya ce, "Dattijan garimmu suka ce in zo in rika kashe ku, don mu ga idan abubuwan da kura ke fadi na labarinka gaskiya ne." Zaki ya ce, "Me kura ke faďi na labarina?" Auta ya ce, "Mu da nufimmu mu fid da Sarkimmu na mutane, don ba shi da hakuri, mu nada ka, ka yi mulkin dabbobi kuk da mutane baki daya, mu gama kammu mu bi ka, duk abin da ka ce mu yi, mu yi, abin da ba ka so mu bari. To, muna cikin wannan shawara sai ran nan kura ta shigo gari ta ce ka aiko ta, wai ba abin da ke tsakanimmu da kai sai kisa. Muka sake tambayarta, ta ce duk Sarakunan duniyan nan babu azzalumi irinka. Wai da an yi maka dan laifi kadan sai ka ce a kashe mutum. Saboda haka aka ce in rika kashe ku, mu gani ko ka sa a kashe ni. In ka sa an kashe ni, lalle maganar kura gaskiya ce. In kuwa ka yafe ni, kura ta zama makaryaciya." Zaki ya dubi kura, ya buga mata tsawa ya ce, "Wa ya aike ki ga mutane?" 27 Ta zabura, zawo na fita, ta ce, "Karya ya ke yi, ban taba shiga gari ba." Auta ya ce, "Wa ke maki karyar, zaki da kansa? Kin manta har muka ba ki kujera kika zauna, don girmamawar Sarki da kika се ya aiko ki?" Za ta yi magana zaki ya zabura, ya sa gaba ya banke ta, duk namun daji suka hau mata, mai yaga na yi, mai cizo na yi, har suka kashe ta. Zaki ya sallami yaron nan. Ya ba shi kaya mai yawa irin wanda su ke kwacewa daga fatake. Yaro ya yi godiya, ya ce zai je ya gaya wa mutanen gari abin da ya auku. Wannan shi ya sa ko yaushe in ka ga zaki a daji ka durkusa, ka ce, "Ranka ya dade," ba zai cuce ka ba. Musa ya duba haka, sai ya ga gari ya waye. Bai ko tsaya ba ya ji ko labarin ya kare, ko bai kare ba, sai ya yi tsaki, ya juya ya shiga gida. Yinin ran nan duk ya ki ko zuwa wurin aku, har magariba ta yi. Bayin Sarki suka ci abinci suka zauna hira, sai can barci ya kwashe su. Da Musa ya ji alamar bayi sun yi barci sai ya tasam ma wajen aku. Da hango shi sai aku ya bushe da dariya. Musa ya dube shi, ya ce,'Me ka ke wa dariya haka, kai kadai kamar mahaukaci?" Aku ya ce, "Ai ba ka san abin da aka yi ba jiya da dare. Shigarka ke da wuya, sai na ji bayin can naka na babban zaure suna hira, Sarkin Gida na yi musa tatsuniya. Da na ga ba na jin barci, ni kuma na tafi in taya su. Da Sarkin Gida ya kare tatsuniyoyinsa, ni kuma na ba su labarin. wani bakauye da wadansu 'yam birni." Musa ya ce, "Ashe Sarkin Gida tsofai-tsofai da shi nan, har ya iya tatsuniyoyi?" Labarin me ka tarar yana yi musu?" Aku ya ce, "Ba wani labari mai dadi ba ne, tun ina yaro na san shi. Kokawa da aka yi cikin labarin ne, in na tuna ta ke ba ni dariya." Musa ya ce, "Yaya suka yi?" Aku ya ce: 28 Labarin Sahoro Da Sahorama Wai akwai wani saurayi ne wanda a ke kira Sahoro. Kullum bá ya tabuka wani aiki sai ya kora akuyarsa, ya kai ta bakin rafi ta yi kiwo, da maraice ya kwanto ta. Nonon akuyan nan shi ne abincinsa, ko ya sayar ya sayi wani abu, ko ya sha hakanan. In akuyar ta yaye kuwa, sai ya sayar da ita, ya sayi wata mai da. To, ba abin da ya miskile shi sai kiwon akuyan nan. Kullum ya dawo gida sai ya ce, "Wash, ba shakka kiwon akuya ba aikin da ya sha kansa kan wahala! Haba, lokacin nan yanzu akwai abin da ya fi mutum ya sami inuwa mai sanyi, ya kishingida, ya yi ta barci? Amma ba dama, dole ne mutum ya bi ta, in ko ya ki, ta fada wata gona ta shirga barna a ci mutum tara, ko kuwa ta ki dawowa kura ta sami kalaci. Kai, ya kamata dai in tuna yadda zan sanyaya wa raina daga wannan azaba. Rai fa an ce dangin goro ne, ban iska ya ke so." Yana nan kullum yana zulumin wahalar kiwo, sai ran nan ya ce, "Ah! Na san dabara, ba abin da ya fi sai in auri Sahorama. Ga ta da akuya daya ita kuma tana kiwo, ka ga in na aure ta sai ta rika gamawa da tawa, ni ko in samu in rika taba dan kailula." Sai ya nemi Sahorama aure. Iyayenta suka ce, "Am ba ka. Dа ma da Tukura da Bako duk Umbutawa ne." Aka yi aure, ta tare, ta shiga hidimar kiwon awakinsu biyu. Don ba su da wani abinci sai wanda suka samu daga gare su. Sahoro ya yi ta shara barci a natse. Ba a dade ba kuma Sahoroma ta ce wa Sahoro, "Maigida, ni fa na gaji da wannan irin wahala, kudaje na cizona, ina tuntube. Don Allah, dubi jikina. Da na zo nan gidanka ina sheki, duk yanzu na fara kirci don cizon kudaje. Kai, ba na yarda in tsofad da kaina tun ina gabar kuruciya, sai mu sake dabara." Sahoro ya ce, "Wannan batu naki ba makankara. Ni ma fa na ga kin fara baki, ni ko dubi yadda na fara ajiye taiba. To, yaya zan yi da su?" Sahorama ta ce, "Sai mu ba Dabo, ya ba mu amiya guda, mu ajiye a bayan gida, in zuma ta shiga ta yi saka, mu rika diba muna 29 samun abinci. Ka ga ba ruwammu da kiwonsu, balle mu wahala." Sahoro ya ce, "Kai, ai ko kin samo dabara, ga shi kuma ko ba a faďi ba zuma ta fi nono dadi." Sai ya sa matar ta je ta yi magana da Dabo. Ya yarda da musayar, don ya ga da riba. Ya ba su amiya guda, suka yi ta samun zuma daga ciki suna sha. Suka sami wani gora suka cika, suka rataye. Sahoro dai in ya kwanta tun da dare, ba ya tashi sai rana ta take. Ya kan ce wai tashi da wuri shi kan hana gira tofo, kuma ya kan sa dundumi. Ran nan ya farka daga barci da rana tsaka, sai ya ga matarsa ta dauko goran zuman nan, za ta diba ta yi musu gari su sha. Sai haushi ya kama shi, ya ce, "Ku fa mata barnarku ta fi ku! Dubi goran zuman nan har ya kusa karewa. Watau zuman nan ta kare ne, har za ki fara dibar ta gora? Abin da na ga ya fi sai mu sayar da goran zuman nan mu sayi kaji da zakaru, su rika yi mana kwai suna kyankyashewa." Sahorama ta ce, "In ko haka ne sai mu sami wani yaro wanda zai rika zuba musu ruwa da hatsi. Ni dai ba na iya wannan jidali kullum kwanan duniya." Sahoro ya ce, "Lalle kiwon kaji wahala ne ja wur. Yaran yanzu kuwa kowa ya san su a kan ragwanci. Yanzu ko, ko mun yayo wani yaro don ya rika lura da kajin, in mun saya sai ki ga wasa ya dauke masa hankali, ba ya wani abin kirki." Sahorama ta ce, "Ko wane yaro muka dauko in ya ki yin aiki sai in dauki sandan nan" (ta sa hannu ta dauki wani guntun itace), "in sheme shi, tau a kai!" Sai ta kwantara wa gora ice, Gora ya fashe, 'yar zumar da su ke takama da ita ta tsiyaye. Sahoro ya ce, "Shi ke nan, ta faru ta kare, an yi wa mai dami 30 daya sata! Da kajin da za mu saya, da yaron da za mu dauko, duk ga su nan sun malale a kasa. Amma dai na isa barka, da sakainan nan da ta yi tsalle ba ta fada mini a kafa ba." Ya dubi matar, ya ce, "Sa hannu, kwashe wannan da ke gudu kasa kafin kasa ta shanye, don mu sami na farawa, kada yunwa ta sa in gintse barcina tun ban koshi da shi ba." Sahorama ta shiga sa hannu tana kwashe zuma, tana zuba dan abin da ta samu cikin wata kwarya, tana lashe rabi tana ba mijin labari tana cewa, "Abin nan fa da na yi yanzu amfanimmu zai yi nan gaba. Don na taba jin wata rana an gayyaci kunkuru wajen aure, don rashin saurinsa da ya tashi bai kai gidan ba sai bayan watanni. Da ya isa ya tarar ana sunan dan amaryar da ya zo bikinta ta haifa. Da aka gaya masa ya ce, "Ba kome, sauri shi ke haihuwar nawa!" Sahoro na kwance bisa gado yana kallonta, tana ta shan zuma da wayo, tana zuba masa surutun banza. Sai haushi ya kama shi, ya ce mata, "Wane labarin banza ki ke ba ni haka, ba kai ba gindi? Wayon a ci an kori kare daga gindin kanya! Ga shi ragwancinki ya jawo mini asara, wai ba ki iya kiwon kaji biyu sai kin nemi yaro. Mutuniyar banza, sullutuwa!" Sahorama ta ce, "Kai ne mutumin banza, wanda in ya kwanta da magariba ba ya tashi sai gari ya waye da rana tsaka!" Sahoro yana dai daga kwance ya ce, "Wa ki ke zagi, Sahorama? Ka ga lalatacciyar banza, Kafira!" Sahorama ta ce, "An je an zage ka, kai dai ne Kafiri, ba ni ba. In kai da ne, ba shege ba, ka gina rami ka tsattsage ni!" Sai zuciya ta turnuke Sahoro, ya tashi daga kwance ya sauko, ya tarad da matar, sai kokawa kici kici, kica kica. Can Sahoro ya gaji, ya ga bai ka da matar ba, sai ita ke neman tandara shi da kasa. Sai ya ce mata, "To, sakan ni, kin kayar. Na ce ko iyakarta ke nan?" Sahorama ta ce, "Af! To, in sake ka, ni in fadi?" Musa ya ce. "Lalle ne wannan kokawa tana da ban dariya. To, kai gogan da ka je, wane labari ka ce ka ba su na bakauye da wadansu 'yam birni?" Aku ya ce, "Wannan shi ma yana da ban dariya." 31 Labarin Wani Bakauye Da Wadansu 'Yam Birni Wata rana wadansu 'yam birni na zaune, sai ga wani bakauye tafe, yana janye da jakinsa zai kai kasuwa ya sayar. A gaban bakauyen nan kuwa akwai wani dan hoto, shi kuma za shi kasuwar ya yi wasa. Ana tafe ana yi masa kidi, yana jefa garma yana cafewa. Da 'yam birnin nan suka lura da bakauye, sai suka ga ya bude baki yana ta kallon dan hoto, bai kula da ko jakin da ya ke ja ba. Daga nan sai wani daga cikinsu ya ce, "Yanzu fa ba ku sani ba, karbe wa muzin nan jakinsa bai sayi wuri ba, in ina so." Saura suka ce, "In ba kurarinka ba yanzu, yaya za ka yi? А buge dai ba ka iya buge shi ka karba, yanzu ko ba dare ba, balle ka ce ka sace." Sai dan birnin nan ya tashi ya bi bayan bakauye, saura na biye da shi sululu. Ya matsa, ya kwance igiyar da ke wuyan jaki ya daura wuyansa, ya mika wa 'yan'uwansa jakin, suka koro. Gagon naka tun da dai ya ke jin tsauri-tsauri a hannunsa, sai ya yi ta tafiya baki bude, yana kallon dan hoto. 32 daya sata! Da kajin da za mu saya, da yaron da za mu dauko, duk ga su nan sun malale a kasa. Amma dai na isa barka, da sakainan nan da ta yi tsalle ba ta fada mini a kafa ba." Ya dubi matar, ya ce, "Sa hannu, kwashe wannan da ke gudu kasa kafin kasa ta shanye, don mu sami na farawa, kada yunwa ta sa in gintse barcina tun ban koshi da shi ba." Sahorama ta shiga sa hannu tana kwashe zuma, tana zuba dan abin da ta samu cikin wata kwarya, tana lashe rabi tana ba mijin labari tana cewa, "Abin nan fa da na yi yanzu amfanimmu zai yi nan gaba. Don na taba jin wata rana an gayyaci kunkuru wajen aure, don rashin saurinsa da ya tashi bai kai gidan ba sai bayan watanni. Da ya isa ya tarar ana sunan dan amaryar da ya zo bikinta ta haifa. Da aka gaya masa ya ce, "Ba kome, sauri shi ke haihuwar nawa!" Sahoro na kwance bisa gado yana kallonta, tana ta shan zuma da wayo, tana zuba masa surutun banza. Sai haushi ya kama shi, ya ce mata, "Wane labarin banza ki ke ba ni haka, ba kai ba gindi? Wayon a ci an kori kare daga gindin kanya! Ga shi ragwancinki ya jawo mini asara, wai ba ki iya kiwon kaji biyu sai kin nemi yaro. Mutuniyar banza, sullutuwa!" Sahorama ta ce, "Kai ne mutumin banza, wanda in ya kwanta da magariba ba ya tashi sai gari ya waye da rana tsaka!" Sahoro yana dai daga kwance ya ce, "Wa ki ke zagi, Sahorama? Ka ga lalatacciyar banza, Kafira!" Sahorama ta ce, "An je an zage ka, kai dai ne Kafiri, ba ni ba. In kai da ne, ba shege ba, ka gina rami ka tsattsage ni!" Sai zuciya ta turnuke Sahoro, ya tashi daga kwance ya sauko, ya tarad da matar, sai kokawa kici kici, kica kica. Can Sahoro ya gaji, ya ga bai ka da matar ba, sai ita ke neman tandara shi da kasa. Sai ya ce mata, "To, sakan ni, kin kayar. Na ce ko iyakarta ke.nan?" Sahorama ta ce, "Af! To, in sake ka, ni in fadi?" Musa ya ce. "Lalle ne wannan kokawa tana da ban dariya. То, kai gogan da ka je, wane labari ka ce ka ba su na bakauye da wadansu 'yam birni?" Aku ya ce, "Wannan shi ma yana da ban dariya." 31 Labarin Wani Bakauye Da Wadansu 'Yam Birni Wata rana wadansu 'yam birni na zaune, sai ga wani bakauye tafe, yana janye da jakinsa zai kai kasuwa ya sayar. A gaban bakauyen nan kuwa akwai wani dan hoto, shi kuma za shi kasuwar ya yi wasa. Ana tafe ana yi masa kidi, yana jefa garma yana cafewa. Da 'yam birnin nan suka lura da bakauye, sai suka ga ya bude baki yana ta kallon dan hoto, bai

Chapter 3 of 12