yake ji sabdoa
abinda ya faru hakika da dai-dai da rana daya nasan Yaya Auwal
zai min haka, da ban yadda dashi na sake dashi ba kaini a nan ma
har dana sanin aurensa na yi na yi bakin cikin haihuwa dashi a
lokacin dan tsananin kishi da haushinsa da nake ji inda ca aka yi ma
'ya'yan sun mace, kuma ya sakeni zan so hakan.
69
WANDA YACE NAMIJI UBA2
A gaskiya Yaya Fahad ina da tsananin kishi yadda baka zato maganganun da yawanci kawayena suka ringa gaya min sait a fara tasiri akaina, na tsani inji mace, tana da aure amma tana zagin namiji, wata ma har mijin da take aure. To amma a lokacin sai naji ba zagi ba in za'a tsine su ma, to nice kan gaba hakika kalmar nan
da yawanci mu mata muke amfani da ita wato wanda yace namiji
uba zai mutu maraya nan take tayi tasiri a kaina hakika sai yanzu na
gane dalilin da yasa mata suke rike da ita tamkar kalmar kur'ani.
A gaskiya duk matar da zata rike Namiji, tayi takama dashi ta
riki banza, dan duk yadda kake zaune dashi zuciya daya, shi ba
haka bane a zuciyarsa, komai yake kawo haka? oho.
A zahiri na yadda da kalaman nan da suka yi tasiri a zuakatan
mata da dama a cikin al'umarmu wato ta yadda suke amfani da ita
wajen zagin maza san ransu, ba tare da kowanne irin tunani ba
kalmomin kuwa sune da yawa, kasan ita hausa yawa ne da ita kowa
da karin maganarsa da ya ga ya dace ya fada akan maza wasu suna
cewa: WANDA YACE NAMIJI UBANE, MAZA BASU DA
TABBAS, NAMIJI BA DAN GOYO BANE, MAZA RUMFAR
KARA. Da dai sauransu.
A askiya duk sai naji maganganun na sun dace dasu. Fahad ya
kalle ta yace, "to shin zaki iya min bayaninsu daya bayan daya,
wato dalilin da yasa ku mata kuke amfani da wadannan kalmomin
don ku fc.fi abinda ranku ke so ga da namiji duk girmansa duk
tsufansa, ko kuma duk yarintarshi? Hakika zan iya maka bayani
dai-dai gwargwado ko kuma in ce dakai bisa abinda ni na sani ko
kuma na fahimta.
Abinda yasa mata suke amfani da wannan kalmar ta duk
wanda yace namiji Uba ne zai mutu maraya shine. Duk abinda zaka
yi da namji duk irin jin dadin da kuke yi dashi duk irin alkawarin da
zai maka kai duk dai abinda zai maka sai kaga daga karshe yaje ya
karo aure. Alhalin yabar mace ta sake sosai, har tan abawa makiya
haushi ta sakar masa ragamarta da komai da komai, amma sai kaga daga karshe ya kwaso mata wacce bata isa bama ta hada kishi da ita
ba ko yarinya kowacce ta girme ka koma wata nakashashiyar murmushi kawai yayi yace uhm ci gaba.
70
LUBABAН
Amma kalmar nan ta maza basu da tabbas maza suna yawan
amfani da ita ga wasu mazan sakamakwan tsabar rashin mutuncin
da suke shirya musu, wato sai kaga namiji in zai aurcka, ya nuna
maka babu yakai karya iri-iri kamar zai hadiyeka dan so kuma ya
nuna maka shi mutumin kirki ne ya nuna maka cewa shi mai kula
da gida ne da sauransu shi dai burinsa yaga cewa, ka aureshi amma
da zarar kaje gidan sai kaga komai ya canza. Allah ya sama kayiw
ata lafiyalau a gidan wasu kuma suna binka a hankalihar sai sun ga
ka sami cki to fa sun san ka gama kafuwa sai su shiga shuka maka
rashin mutunci iri-iri.
Amma shi namijin da ake kiransa ba dan goyo bane, shine
yayi dai-dai da kalmar da mata suke amfani da ita, wato da suke
cewa baka shaidar namiji, marassa kunyar ma har su kara da cewa
ko da Ubanka ne, kada kayi shaidar shi zai iya nuna maka shi
mutumin kirki ne ya shigo yana muzurai da sauransu. Amma in
kaga yadda yake hudawa kadangarun bariki kunne yana saka musu
dan kunnen gwal zaka sha mamaki.
Amma kalmar maza RUMFAR KARA shi ne sai ka sami
namiji ka sakar masa komai naka ta dauro ma ka sai da kadarorinka
ka bashi dan a taimaki juna, amma lokacin da ya fara samu, sai ya
yayeka ya barka kuen na kadaka.
"Amma kin birgeni hakika kin san laifukan maza. To shin-su
kuma mata meye nasu laifin? "haba su mata meye laifinsu, ka taba
jin ance mace ba 'yar goyo bace, ko kuma mace bata da tabbas?
Kaga kuwa ai mu mata namu da sauki, dukt siya dai ai mace a
karkashin mijin ta take". Dariya ya saka yace, "amma lallai kin
birgeni, bisa kalamanki, amma fa bazan iya yadda da hakan ba zan
fi yadda da ke idan dai kika ce dani baki san halinku na mata ba, kin
fi rike na mazan. To da ance dake ni zan gaya miki goma naku
dukda cewa ke kwaya hudu kika fada. Kuma da za'ace za'a sami
macen da bata da wadannan halaye to da hakika ta juya namiji son
ranta, ba tare da taci karo da laifin ko daya ba daga cikin irin
laifukan da kika zana na da namiji to amma yanzu karasa bani
labarinki tukunna.
A hankali ta daga kanta ta kalli Yaya Fahad sanan tace.
71
WANDA YACE NAMIJI UBA2
A lokacin da na cika sati daya a asibiti sai aka sallarne mu
zuwa gida tun da muka koma na daukewa Yaya Auwal wuta saboda
ni kadaice nasan abinda nake ji a zuciyata gashi ina da wani irin hali bana kaunar bayyanawa kowa sirrin aurena ina mai jin kunyar
in fito in sanar da kawayena ko makotana, saboda sauda yawa, su suke kawomin labarin halayyar maza, amma ni sai in yi tsalle in се
ni miji na daban ne a cikin maza.
Amma sai gashi rana daya ya kunyatani ya tozartani waini
Yaya Auwal zaiwa kishiya hakika maza basu da tabas. A hankali na
ringa jin tsanar Yaya Auwal na shiga raina na tsane shi tsan amai
tsanani wacce tafi ta da da na yi masa sam naji gidan yayi min zafi
ina zaune a dakin kan gado na daga kaina sama ina tunanin irin
hukuncin da ya dace in dauka sai ga Yaya Auwal ya shigo. Na daga
kaina a hankali na kalleshi, yayin da na tattarashi na watsar sannan
na saki tsaki wanda yayi dai-dai da faduwar gabana. Hakika na san
matsayin matar da takewa mijinta tsaki dan ko a zuwan da Annabi
yayi Isra'l da Mi'iraji da ya kai ziyara gidan wuta yayi karo da
wasu mata da aka zazzago harshenta aka kuma nadeta dashi ana
gana mata azaba da ya tambayi laifin da tayi sai aka ce tsaki ta yiwa
mijinta kai dole mu mata mufi yawa a wuta sabosa sam kanmu yayi
yawa. Ni dai nan take na sinkuyar da kaina kasa duk jikina yayi san
yi matuka.
Amma me lokacin da kishin ya kara turnukoni sai ma na
manta da dukw ata azabar Ubangiji da nake tunani shi dai a sanyaye
ya zauna kusa dani yace "dan Allah in tambaye ki mana? Banza
myi dashi bance dashi komai ba. 'Na dai riga nasan kina jina dan
haka bana bukatar izininki, sai dai zan so ace kin bani amsa. Wai
dan Allah me na yi miki kika tsaneni, tsana mai tsanani haka? A
dai-dai lokacin da ni kuma Allah yake dada cusa min sonki a raina.
Amma tabbas Yaya yama rainamin hankali dan me ba zai
zabgamin mari ba, in san marina yayi da hannu in sosa. Da irin
wannan dukan zuciyar da yayi mini". Ya ci gaba da cewa ek baki
barni na sanar da ke gundarin abin ba, amma tashi daya duk kin bi
kin dugun zuma tunanir ki, kin kuma hargitsa na kowa. Sanin kanki
ne ina matukar sonki, don haka karin aurena ba yana nufin
wargajewar soyayyar mu ba kin san Allah ni tausayin yarinyar ma
72
LUBABАН
nake ji kawai tausaya mata nake, shi yasa zan amince da tayinta,
domin in ceto rayuwarta dan bamu san hannun wanda namu 'ya'yan
za su fada ba.
A gaskiya kin ban mamami dan ni ina ganin kaf duniyar nan
babu 'ya macen da nake ganin zan aurota in wulakantaki saboda ita.
Barantana wannan da zan aura da bata kama Kafar kafarki ba haba
dan Allah ki kwantar da hankalinki ina fatan kin gane.
A gaskiya Humaira matakin da kika dauka sam bai dace ba
asalima babu adalci a cikinsa. Humaira sanin kanki ne in har akwai
abinda na tsana a rayuwata bai wuce bacin ranki ba. To danme ke
ba zaki guji duk wani abu daka iya haddasamin 6acin nawa ran ba.
A gaskiya abinda kike yi bashi da amfani sam-sam kuma babu wata
hanya da zai amfanemu baki daya. Sanin kanki auren nan bani nasa
kaina ba sani aka yi yarinyar nan ita ta fara aikowa tana sona, kuma
ni ban ma san hakan zata kasan ce ba" E ai dama ku maza har abada
bakwa neman mace ku aura sai dai in ita yarinyar ta zabeku. Ato ni
dai ina sanar dake ne ban kuma damu da ki yarda ko kada ki yarda
ba.
A lokacin da ta aikoma ba ki ji haushin da najiba saboda ni
kwata-kwata yarinyar bata layina bama ta cikin tsarin irin matan da
nake lissafawa zan iya zama dasu, koda ban same ki ba. Baran tana
wannan kyauta da Allah ya yi min na mace daya da daya kamarki
yayin da ya dago kai ya kalleni ni kuma na akwar da kaina gefe
guda. Wallahi ba wai cika baki ba, kema dai ai kin santa sam bata
da wani diri ko fasali irin na mata da ya kamata ace wani da namiji
ya ganta yace zaia ura, wannan ai dole ma ta rasa mashin-shini. Ga
uban shekaru falka. To da in auri wannan a budurwa ba gara in auri
bazawara ba in san bazawarar na aùra ba.
Ana cikin haka kwatsam sai Allah ya hada mahaifina da
mahaifinta, sanadi kuwa itace siyasa yayin da ni sam na ma manta
da ita a rayuwata. Lokacin da Alhaji ya aikeni gun mahaifinta kallo
daya ta yi min ta gane ni yayin da ni sai da tayi min bayani ma
sannan na gane ta. Saboda shekara daya fa kenan, amma tsufanta ya
fito sosai, ga uban muni da ta kara. Tunda ga lokacin sai tabi ta
zakemin. Daga karshe ina ta sanar da mahaifinta, shi kuma ya yiwa
73
WANDA YACE NAMIJI UBA2
mahaifina magana shi ne fa ban san yadda suka kulla maganar su ba
kawai sai ji nayi ance wai an yi min mata.
Amma za ki sha mamaki in nace miki duk da cewa har sun sa
rana amma Abban ki da Mamam basu san maganar nan ba saboda
ya rasa hanyar da zai bi ya sanar dasu, w allahi Humair ani nace ba
zan yi aure yanzu ba to amma sun matsamin. Daga karshema uban
yarinyakiran ayayi ya ringa rokona akan dan Allah in rufa masa asirikada in bashi kunya dan har ya gama sanar da jama'a shi kuma
Alhajina har ya kama min gidan haya inda zamu zauna.
A gaskiya ni kaina ban san yadda zan yi ba amma ni a ganina
yarinyar babu wani daga kai da zata yi miki, kinga dai bata fiki gata
ba kuma duk gatanda za'a nuna mata ba'a nuna mata wanda a ka
nuna miki ba to mai zai dame ki yarinyar nan bata fiki kyauba, bata
fiki komai ba, to me ne zai dame ki a kanta.
A yanda Yaya Auwal ya nunamin a takaice dai auren dole za a
yi masa kai sam wannan tsarin nasa ba abin yadda bane. A dai-dai
lokacin da na tuna da irin shawarwarin da yawancin kawayena suke
gaya min. Demin sun sha gaya min cewa, duk lokacin da namiji ya
shiga neman aure, ya shiga tsatstsara matarshi kenan da karya da
gaskiya. Hakika hakan abin yake a raina nace to ni da yazo yake
nuna min cewa matsa masa aka yi akan ya aureta, ni waya san
abinda yaje yace.
A zah.ri babu mamaki ma zuwa yayi yace da yarinyar ni ladan
noma aka bashi ni, ko nima din yace mata hadin iyaye ne. Hakika
namiji ga abin yadda bane kuma ma har yaushe za'a ce za a yiwa
namiji auren dole. Yadda yanzu zamanin nan ya juya macen ma ta
daina yadda da auren dole balle namiji. Tabbas na yadda da cewa
tsarin ne irin na da namiji, kamata yayi kawai in shareshi dan
hausawa ma sunce duk wanda yaje ya zagi wani a gabanka, to kuwa
kaima zai je ya zage ka.
Amma abin lura a nan shine, ta yaya za'a yi yace Alhaji shi zai
tursasa masa akan wai ni a yimin kishiya hakika wannan da sake.
Ai 'yaya ne dashi yaya Auwal din dan me ba zai matsa masa akan
ya mallaki gidan kanshi ba. A'a sai dai ya nuna masa hanyar kara
aure asalima shi kansa yayan ko sana'ar kirki bashi da ita motar ma
gata ga kamarta, muna zaman rufin asirinmu amma ya tashi ya
74
S
1
2
D
LUBABАН
nemo aure, yace tilasta masa aka yi, wannan ma ai zance ne. To ma
wai shin wacece ita yarinyar da zai aura, in ma dai yana sa rai da
siyasar Alhajin ce wato in yana nufin siyarsar da Alhaji ne yake yi
yake tunanin zai sami wani abu har yake tunanin aure, to Alhajin yn
fadi in ga ta tsiya.
A nan ne ya katseni da tunanina yace, wallahi Humaira da kin
san yarinyar da baki tada hankalinki a kanta ba. Ni fa ba wani santa
nake sosai ba wallahi ko an yi auren ma sakinta zan yi. A nan ne na
dago kai na kalleshi hakika lallai Yaya Auwal ma ya raina min
hankali kwata-kwata ya rainan wayona. "Ba ta wata bace illah
SUMAYYA YAR GIDAN ALHAJI BATURE.
Ai da yasan abinda zai faru hakika da bai sanar dani ba.
Masifa, Bala'i, zaza'i su kawai naji suna fita daga bakina, mai
makon in ambaci Innalillahi wa inna ilaihir raji'un, kamar yadda
musulunci ya koyar damu hakika na amince tsananin kishi yana iya
fitar da mutum daga cikin hayyacinshi.
Auwalu na ambata cikin bacin rai da dacin rai, hakika kayi
kadan wallahi sai dai ka za6I daya tsakanin ni da kuma ita karasa
wacce zaka auro min a matsay'n kishi ya sai wannan gogaggiyar da
idonta ya gama budewa. Asalima ta fini ilimi kai kanka iliminku
daya haba wallahi da sake, an bawa mai kaza kai, daga kai har ita
kun girmeni, wato don kusani a tsakiya kuyi ta cuta ta kama rasa
wacce zaka auro min saiw annan mummunar matar marar mutunci
tsohuwar guzuma, wacce mutane da dama suke zarginta da yawaceyawacen banzan ta to wallahi ba zata taba sabuwa ba bindiga a
ruwa.
A gaskiya sai dai ka za6I daya tsakanin Humaira da Sumayya.
Sinkuyar da kai yayi ya rasa abinda zai ce dani zuwa can ya dago
kai ahankali yace, Humaira idan ki kenan kike kirana da Auwalu
kai tsąye, to amma f aki tuna da cewa aljanata tana karkashin kafar
mahaifana, to ta yaya za'ayi ki fadi haka amma fa kin san dai aure
Kaddara ne ko?.
Alal hakika nasan da haka, to amma ni ban dauki aure a
Kaddara ba, dan me zaka ga yarinya kaji kana sonta ka zurfafa sonta
a zuciyarka har Allah ya biya maka bukatarka sannan ka ce wai
Kaddara ce. Ni abin da na daukesu a kaddara shine danka ya fada
75
WANDA YACE NAMIJI UBA2
wuta ko mota ta kaďe shi. Gidanka ya kama da wuta ko ruwa ya
cinye shi ka haifi gurgu ko makaho ko kuwa kuturu ko gurgu, fa
dawa rijiya da sauransu, it akanta asara duka aikin kaddara take shi
ya sa ma Allah yace ka yadda da kaddar amai kyau da marar kyau.
Amma a gaskiya ba zai yiwu ka sa aurenka a ciki ba, in banda
haka ai da musulunci bai yadda da kayi istihara akan aure ba, dan
kaga kyanshi ko rashin kyansa. Ni gaskiya na kása kaddara a abu
biyu ni a iya fahimtata kaddara ta Ubangiji da ake cewa a yadda da
kaddara itace, ka yadda da abinda Allah ya kadarta wato Allah yayi
duniya ya kuma yi lashira ya kuma yi sama yayi kasa ya kuma yi
halittocinsa iri-iri wadanda suka dace da zaman gurin. A sama ya
halicci Malaʼiku. A kasa ya halicci bil adama, ya kuma hada da
dabbobi da tsintsaye, tsutsotsi da kwari, yayida bbar gida da dabbar
dawa yayi na ruwa yayi kan kasa. Da akwai halittun da za su rayu
akan kasa akwai kuma haittun da za su zauna aruwa, kai da duk
wani abu da Allah ya halitta. Haka kuma akwai wuta akwai aljanna.
Ga kuma littafan da ya sauka rda maganganun da yayi to ana so duk
mutum mumini ya yadda da wannan haka kuma shi yayi aljan.
Akwai kuma Kaddara t amutum da dan Adam zai raya a ransa,
ya kuma karfafa san abin, Allah kuma ya bashi ikon yi sanin
kankane Yaya Auwal Bature shi ya yi jirgi na kasa ko na sama ko
kuma jirgin ruwa. Haka su suka kirkiri mota ko kake, da Babur ya
kuma yi hanyar mota don ta ji dadin murza tayunta. To amma Allah
shi ya basu ikon yi ka duba kaddara irin ta mutum da yayi talabijin,
aka yi bidiyo ga kuma talfon ga wutar lantarki, amma duk kaddara
ce ta mutum Allah dai shi ya basu ikon yi.
A lokuta da dama jama'a na jahiltar kansu sai su aikata abu
suce kaddara ce wasu ma sai su sakankance ga ibadarsu, su ce in
Allah ya kaddara su 'yan uwatane za su shiga wuta in kuma Allah
yayi su 'yan Aljanna ne za su shiga a gaskiya wannan duk kuskure
ne babba. Allah da ya halicci wuta da Aljanna ai kuma sai ya bawa
mutum za6I bai kuma bamu a cukurkude ba, wato bai samu a duhu
ba komai sai yayi mana shi dalla-dalla, fadan dillih wato ya sanar
dakai hanyoyin da zaka bi dan shiga Aljanna ya kuma sanar damu
hanyoyin da zamu bi don shiga wuta.
76
LUBABAН
A sanan kuma dangane ga tsara rayuwarmu, wata tana ga
Ubangiji, wata kuma tana garemu.A yau mutum yana tasa Allah na
tashi akwai mutumin da zai tashi da kafafuwa daga karshe ya
gurgunce ko ya tashi da idonsa daga karshe ya makance, wannan
duk kaddara ce. Amma fa mutum ba zai je ya zabawa kansa matar
banza ba, yace kaddara in haka ne ai Allah ya hore mu da mu auri
mace ta gari, domin 'ya'ya yanmu su dace da uwa tagari. Akwai
abinda yake bashi da amfani a kanka, ka kuma zafafa san shi a
zuciyarka, har ka hada da rokon Allah in Allah ya soka da
rahamarsa yayi ta kawo maka wasu hanyoyin dan ka farga kasan
babu alkhairi a tare da kai to amma in ka zurfafa rokonsa da son
abin sai ya biya maka bukatarka kaga duk halin da ka shiga ba za
kace shi ya dora maka ba. Haka kuma akwai abinda yake alkhairi a
gare ka ana nuna maka kana gudu, saboda kai kana hangen wani
abu na daban, sai abin ya wuce kace dama Allah bai kaddara zan
samu ba, alhalin ya baka kai ka gujeshi, hakika addu'a tana canja
kaddara, marar kyaut a koma mai kyau kuma tana canja mai kyau
zuwa marar kyau.
Amma Yaya Auwal abin lura anan shine don me mutum baya
hawa tsakiyar titunan mota ya shiga tafiya ta tsakiyarsu, yace in
Allah ya kaddara za'a kaďeshi za'a kađe shi, in kuwa Allah bai yi
za'a kade shi ba ba za'a kade shi ba? sannan kuma me yasa mutum
ba zai hau bene hawa uku ba ya ga in ya biyo ta matattakala zai bata
lokaci kawai bari ya diro in Allah yayi zai karye zai karye in kuma
ba zai karye ba ba zai karye ba? To dan me yasa mutane ba su yin
haka a'a sai mutum ya tafi ya nemo aure da kafarsa sannan ya roki
Allah ya biya masa bukatarshi sannan a kirawo kalmar da kaddara?
A gaskiya a sake tunani.
Amma gaskiya kin bani mamaki Humaira kada fa zafin kishi
yasa ki kauce hanya kina sane da cewa komai yana da sila, ita kuwa
silar nan Allah ne yake kaddara ta shifa aure ha6o ne, mudun lokaci
yayi sai an yi da mutuwa da haihuwa da kuma aure basa wuce
lokacinsu kin manta sai kiga mutum tun daga Landan ya zo Afrika
yayi aure ya koma saboda dama can Allah ya kaddara matar sace. A
gaskiya ni duk bayanin ki na yadda da wasu amma wasu ban yadda
da su ba in banda haka ya mutanan da suke yi su da daukan matan
77
WANDA YACE NAMIJI UBA2
ake a basu ba tare da sun je sun nema ba to in banda kaddar aya
za'ayi haka Humaira ki tsaya ki nutsu, bana san imaninki ya wuce
saboda kishi.
A hankali ta daga kai ta kalli Yaya Fahad tace, yaya in gaskiya
yar Allah ce ni kai na nasan aure kaddara ce. To amma kishi shi ya
sani wannan zubar kamar kanya to amma duk da haka yana da kyau
a duba batuna. To amma bazan gayawa mata haka ba saboda
yawancinmu bamu da nutsuwa, da cikakken tunani, dan haka sai ya
bawa mata da dama wata kofa ta shuka rashin mutunci suce, ai
Humaira tace Aure ba kaddara bace, a'a Humaira ma ta sani takewa
tayi saboda na taba cin karo da wacce ta taba gaya min haka. То
amma a lokacin ban yadda ba sai yanzu. Dakishin ya taso min har
nima nake adar da hakan.
A hankali ya kalleta yayi murmushi yace, Gaskiya fa da yawan
ku mata kuna sane da abu kuke takewa saboda kishi. Yanzu ki duba
misalin zuwa maka ai dai tana daya daga cikin shika-shikan
musulunci to amma ki duba ki gani sai kiga me kudin yana ta
daukar niyya har ya biya amma wani abu ya zo ya hana shi zuwa
kuma kiga wanda bashi da ko kwabo yaje wanna.n duk ba kaddara
bane ato ku dai mata ku iya bakin ku kada za fin kishi ya kwashe
imaninku "uhm ci gaba wallahi na matsu in ji dalilin da yasa kika
gudo zuwa nan wannan ma ba kaddara bace ba to Allah ya yi zan
aure ki ne shi yasa ina fatan kin yadda da maganar Hausawan nan
da suke cewa matar mutum kabarinsa.
A lokacin dana gama soki burutsuna, murmushi yayi yace to
su kuma matan da suke gani suce suna son namiji wasu har su hada
da asiri dan su auri mutumfa, shi kuma me zaki ce a kai nace ai
wannan sai dai in Allah yayi dama can matarshi ce in banda haka in
zata shekara tana sirinta, asirinta ba zai taba sawa a aureta ba, kuma
ki duba ki gani hatta sakin aure lokaci ne sai kiga wasu suna wani
irin zama kashe kansune kawai ba sa yi, amma suna tare, saboda
Allah bai kaddara rabuwa ba wasu kuwa suna cikin zaman jin dadi
kamar sa hadiye juna sai sabanin da bai kai ya kawo ba ya haddasa
dalilin saki saboda Allah ya kaddara lokacin za'a rabu. Sakima
kenan da Allah ya kirashi da halak, amma halak din da baya so.
78
LUBABАН
A gaskiya Humaira kiyi tunani kuma da kike cewa wai sai dai
in zabi daya ko ke ko ita to wannan kuma ya rage naki ke ya dace ki
yanke hukunci, tun da ni nawa iyayen sun riga sun gabatar min da
tasu dokar babu kuma yadda zan yi in tsallaketa. Don duk abuna ba
zan iya sauya su ba mace fa?
A nan ne fa na dugunzuma rain aya masifar baci, na dawo
tamkar mahaukaciya na ringa zage-zage, nace aini gar ain rabu da
kai daman can ba zaman Allah da Annabi kuke yi da muba daga kai
har Alhajin, wallahi sai Allah ya sakamin macuta kawai sai da kabi
ka kalallame mahaifina ya saki jiki da kai shine daga karshe zaka ci
amanata ai nasan in ma auren za ka yi to kuwa da kudin ubana za ka
yi shi shi Alhajin da kake takama dashi me gareshi, siyasa ta
tatukeshi gashi kuma bai ci ba. Ba dole ya lallaßa ya jona maka 'yar
gwamna ba, ko ya ringa samun kwangila.
Aini wallahi ba'a burge niba in banda haka da a zabo maka
yarinya danya sharaf mana ba wai tsohuwar da tayi kwanti aba har
ma ta rankwafa saboda tsufa alhamdu lillahi ai dai bata fini da
komai ba in dan kudin siyasa ce ai aikin banza ne gasu haram daidaine masu aikata gaskiya shi kuwa wannan gwamnan babu abindı
zai yi in ba cuta ba daga shi har jama'arsu. Dan ba za su taba yin
abinda Gwamna Shekarau zai yi ba gwamna mai adalci da sanin ya
kamata kafa hujjojinsa akan islama kai gaba daya jam'iyyarma
babu na banza har suka sauka kowa yabansu yake yi babu mai
zaginsu amma me uban Sumayya zai yi tun yanzu shi Azzalumi ne
yana ruguza zaman aure na dadaddun masoya balle ace ya hau
mulki.
A nan ne ya kwashe da dariya hakika da da farko na lura dashi
ransa ya dugunzuma matuka kuma hakika hankalinsa ya masifar
tashi, sakamakon gore-goren da na yi masa to amma ina fadar
wannan kalmar ya tabbatar ba'a cikin hayyacina nake ba, wanda har
ya sakida riya. To amma da ya ji naci gaba da yi masa bakaken
maganganu na fitar hankali,s ai shima bacin rai ya fitar dashi daga
cikin hayyacinsa.
A lokacin ne fa na kalli tsabar idan Yaya nace dashi daman
nasan Alhaji shi yayiwa Mama asiri don karta zauna a gidan
79
WANDA YACE NAMIJI UBA2
Abbana ya ga gara ya aureta ya kuma rungumeni hannu biyu don ku
samu ku hau dukiyarsa ta Allah ba taku ba azzalumai.
A nan ne fa ransa ya baci matuka ban ankara ba sai ji nayi ya
saka rmin wani wawan marin da ya nemi tafiya da raina to mai ya
rage ma don a kalla marin ya tafi da lumtashina na dan lokaci a
kalla minti talatin na yi