Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 11
komai Yaya sirrin mufa. Yace sirrinmu to waya ke ji? mu biyu ne fa. E ni dai don Allah ka yi shiru cikin sauri na kammala da komai na shiga wanka cikakken minti biyar na fito naje can yara kwalliyata ta gani ta fada saboda nasan gidan mu zani amma duk da haka ban wani kure adaka ba. "Zaiyana irin wannan kwalliya haka sai kace za mu yi zaman gida". "To ai kai kaji Yaya Auwal in nayi kwalliyar ka furta in ma ban yi ba ka furta ka dai san gidanmu zani ba gidan biki ba, to naji zo muyi muci abinci ko ma tafi muna kammala cin abincin muka fice daga gidan kai ka rantse irin fitar Ango da amaryan nan ne. Zahiri ban ji ba dadi da muka je muka tarar Abba har ya fita, to arnma babu komai tun da wuni na zo. Bayan mun gama gaisawa da Hajiya Rabi ne take tambayata yara tace in Nur din ko basa nan wallahi duk suna gurin mama, har Iftisan din kaddai in ce an yaye ta e yau kwananta uku da yaye". "Shine ba a gaya mana ba, to Allah ya rataya. Nace Ameen. ta Zan je gurin hajiya Iya in gaidata" To ai tana can akwance". "Bata da alfiya ne?" ko ku sa tana dai hutawa ne na je na tarar da ita bayan mun gaisa ne muka zauna muna ta hira. Ina yaran kuma? Iya tambaya, wallahi duk suna gidan Alhaji, ke 'yar nan har da mai shan nonon". "Iya ai na yayeta", "haba dai 'yar wata shidan Allah Hajiya Iya ita taki shan nonon da kanta shi ne na yayeta, saboda in yi ciwon nonon gaba daya in huta". To ai shi kenan Allah ya kyauta in dai baka mutu ba to kuwa baka gaji da ganin abubuwa ba in banda zamani yaushe yaro zai yaye kansa to Allah ya kyauta. Zahirin gaskiya 'ya'yan yanzu kora da hali kukewa 'ya'yanku. Nasa dariya nace kamar yaya Hajiya Iya "oho kuma”. Zama nayi muna ta hira da ita nace wai ni ina Mary ne? tunda na zo ban ganta ba" Ina jin sun fita da wannan dan dan sauda yawa tare suke fita 'yar nan ai uwar nan taki ta dawo da halin nata irin na da shi 59 WANDA YACE NAMIJI UBA2 yasa aka ce ba'a yaban kuturu sai ya girma da yatsa shi kuwa mai hali baya fasa halinsa". "Zahirin gaskiya nima Hajiya Iya abinda na lura dashi kenan taje dan kanta Allah dai ya zaba masa abinda ya fi alkhairi in Allah ya yaye masa wahala sai kaga lokaci daya kamar an yi saka an yanke, Allah dai ya kyauta shi dai Abba haka Allah ya shirya masa rayuwarsa "uhm ke dai 'ya rnan bari, kullum dai addu'a nake masa Allah ya zaba masa abinda ya fi alkhairi ameen. Zuwa can da yamma likis sannan Abba ya dawo mun jima muna hira, shima ya ringa nuna min rashin jin dadinsa na shiga harkar siyasa nace to Abba ya za'ayi kasan duk abinda Allah yayi mutum zai yi sai yayi sai dai mu taya shi addu'ar Allah ya zaba masa abinda ya fi alkhairi. Zaman da muka yi da Abbane muna hira yas ana fahimci, abinda siyasa ryanzu ta ke ciki. Tabbas dole su nuna rashin jin dadinsu ni duk ciki abinda na tsanama bai wuce yin harka da 'yan daba ba wai a yanzu ya zama dole ace in har kana harkar siyasa to kuwa, sai ka ajiye ‘yan daba saboda su ka reka daga ta addancin makiya to Allah ya kyauta. Zu'va can Yaya Auwal ya zo shima mun jima mana hira dashi daga kaishe muka yi sallama ya kawo kudi mai yawa ya bani yac e na sayawa 'yar yaye alawa. R ranar litinin muka yi sallama da Yaya Auwal ya dauki Akayansa na sati daya ya nufi makaranta mun rabu cikin tashin hankali da jimami amma kafin ya tafi sai da aka dawo min da yara da kuma Khaidija da da farko mama bata yadda ba tace ya duk za'a dauke mata 'yan matan a barta da mazan to amma da kyar Alhaji ya shawo kanta ta amince ta dawo, kasancewar ta gama karatunta sai islamiyya da take yi kawai, sai ya zamto koda yaushe muna tare. A lokacin da Yaya Auwal ya dawo weekend, sai itama Khadijan ta tafi gida yin nata week end din, domin ta bamu fili musha iska. Dan saban dan taya bera 6ari harda yaran ta tafi. Tun da yammacin ranar də yaya ya dawo ya nemi ya hanani sakat, kai ka rantse mun shekara bamu ga juna ba. Girkima kusan tare muka shige shi dana gama ne na samu na gabatar da sallar insha'i daga 60 LUBABAАН nan kuma na shiga wanka ai da na fito ko shafa mai ban barni nayi ba barantana saka kaya baya ga body sprey dana fesa da farko naso in ja masa aji to amma me da na fuskanci kwata-kwata ba ya cikin hayyacinsa, sai kawai na sakar masa kan bori ya hau kada inje garin jan ajin in kwasarwa kaina nauyi mai wuyar saukewa wato zunubi. A zahiri nasan Yaya Auwal ya shiga damuwar da ba zata musaltu ba yayin da ni kuma na wujijjiga a wannan daren, wanda har sai da na dawo ina bawa Yayana hakuri, akan ya hakura haka dan hausawa na cewa ciwo ne mai shiga lokaci daya sauki kuwa sai a hankali dan na lura dashi wannan ciwon daya shigeshi ba mai jin saukin wuri bane. Da kyar ya kyaleni na koma gefe ina huci yayin da shi kuma ya zauna gefan gado yana mai da lumfashi dai-dai yana mai shafa kai da hannu bibbiyu, kansa sinkuye a kasa tamkar mai tunani zahirin gaskiya ba zan iya wanka ba a wannan lokacin dan ina jima sai na shiga ruwan zafi, irin na masu jego, to amma ya zame min dole in daura Alwallah tunkan in kwanta bacci kamar yadda manzo (SAW) ya koyar damu. A safiyar ranar sai na tsinci kaina da jin kunyar Yaya, sai kace wata sabuwar Amarya saboda tun da muke, ba mu taba rabuwa ko da kwana daya ba, a tsawan shekarun da muka yi to sai yanzu a ranar yaya yace ai kuwa ya bar kwanan makaranta, Allah ya gyara. A gaskiya ni kaina naji dadin hakan, dan kuwa hankalina ya fi kwanciya, gani da zargi na innanaha, ba kuwa komai bane ya kawo haka sait sananin kishi, ni kaina nasan mijina ba mai yawace ya wace bane, to amma sha'anin shaidan ako da yaushe in banda kitsekitse babu abinda nake yi. A lokacin da zaßen siyasa ya gabato Alhaji ya tsaya a dan majalisa aka shiga gaganiyar zabe akan dole dagani har Yaya Auwal din muka dugunzuma harkar siyasa. Gwamnan da aka tsayar na jam'iyar L.Y.B. ba karamin kauna ya nunawa Alhaji ba dan haka muma aminci ya shiga tsakaninmu da mutan gidan. Wata yarinya ko ince babba koda yake a yanzu girman ya hau kaina itac ebabbar yar gidan Alhaji bature wato mai jiran kujerar Gwamna a lokacin mai suna Sumaiyya ta nuna matukar kauna ga 'ya'yana wanda hakan yasa daga ni har yaya Auwal din muka saki jiki sosai da ita kasan ance maí da wawa gata da wayo. Tun da harta gama 61 WANDA YACE NAMIJI UBA2 digirinta na biyu yanzu ta shgia digiri na uku. Dan hakа wayayyiyace sosai, sai dai akwai muni to amma wayewarta ita take boye muninta kuma babu lefi dirarriyace. A duk lokacin da take da lokaci to kuwa tana gidana tare da 'ya'yana. Tana bani girma na na cewa ni matar aure ce kamar yadda nake bata girmanta a matsayint ana wacce ta girmeni sosai. Dan kam in da tayi aure lokacin da 'yan da suke yi da sai ince ta haifeni. Saboda ance wacce aka yi goyansu tare kwanan nan aka aurar da 'yarta ta fari. Ita kanta kannanta da yawa duk sun yi aure, harma kannant amaza daga wansu sun yi aure. A lokacin da harkoki suka yiwa Alhaji yawa sai ya rage bawa Yaya Auwal kudi shi kuma yana jin kunyar tambayar Abba kudi saboda a yanzu kusan ince Alhaji ya janyeshi, saboda yawan aikensa da ya ke yi dan haka sai na shiga bashi kayan kwaldina yana sayarwa yana biyawa kansa wasu bukatun na gida, da kuma na makaranta. Hatta tangarayena sai da na sayar dasu na sayi irin wanda ake yayi a lokacin 'yan kadan sauran kudin kuwa na dankawa Yaya Auwal shima ya shiga hidimarsa da su. Badan komai nayi haka ba sai dan nasan shima in har ya sami kudinsa bashi da wani tunani sai ni da 'ya'yansa. Akwai Munirat, wata makociyata da muka bala'in shakuwa da ita, a gaskiya kaf makotana, ba bu wacce muke shiri da ita kamar ta sai kuma wata da ake kira Saddika, to ita mutuncin namu samasama ne saboda tana da yawan surutu ita kanta bata boye sirrin kanta ba balle na wani ni kuwa ina da wani hali na tsani in yadda da mutum ya zo yaci amanata. A gaskiya in na yadda da kai na yadda da kai kenan zuciya daya, ba kuma na shayin in gaya maka duk abin da ke raina, sai dan abin da ba'a rasa ba. Sai dai da zarar kaci amanata sau daya to kuwa ni dakai har abada babu kuma abinda zaka taba min ka birgeni kai ko zaka sadaukar da kanka saboda ni, zan kalli abin a munafinci ne kawai saboda ako da yaushe kamin abu zan kawo wani zatan na daban. Ta daga kai ta kalli yaya Fahad tayi murmushi tace ako da yaushe ina sakin baki wajan sanar da kai halayyata ina gaya maka ne Yaya dan ku fahimce ni saboda ku baku sanni ba. 62 LUBABAН A yawanci lokuta in muka hadu da mata ana hira akan kokarin nunamin cewa na muji ba abin yadda bane, amma ni na kan dauki maganar a shirme da kuma tsabar jahilci. Duk matar da naji ta ambaci wannan kalmar kuwa nakan ji raina ya masifar baci matuka, w ato in naji mace tana fadin duk WANDA YACE NAMIJI UBA NE ZAI MUTU MARAYA. A zahiri ni ban yadda da wannan kalmar da mushimmaci ba, naga dai ni shekarata wajan nawa a dakin miji amma babu wanda ma ya taba jin kanmu, kowa ya banmu yake yi yayin da makiya suke jin haushi. A lokacin gidana kusan zama yayi gidan kare maza. Saboda duk wacce naji zata zagi namiji nakan hanzarta karewa. Akwai wasu ma da suke cewa dani wai ni mace ce a fili amma a zuci zuciyar maza ce dani, in raina ma ya so ya baci sai inga ai daman duk wanda zai zam amai fadin gaskiya sai an nemi a bata shi mutumin banzane za ka ga duk inda yayi ana son shi duniyar ce ta zama haka duk abinda ka yi a zage yake. A yawancin lokuta Sadika takan yawan bani shawara, wacce a lokacin na dauketa gurguwar shawara. Dan takan min fada akan in daina yawan sakin jiki da mijina zūciya daya, dan ta fahimci duk abin da na samu kan in tuna dan cikina na tuna mijina, kuma hakika hakane wai duk sanda ya sami kudin kansa aure zai yo. To amma ni kallan mai zuga nake mata, dan kuwa yaya Auwal yasha ce dani bashi babu aure har abada, kuma hakika na amince sam a lokacin na manta da kalmar nan da hausaw akan cewa kana taka Allah na tashi. Amma Yaya Fahad za ka ga ban faye maganar kawayena ko abokan Yaya ba, to a gaskiya ina da kawaye sosai, kamar yadda shima yake da abokai sosai, sai dai ina baka labarin rayuwata ne kawai, in da aboki ko kawa suka yi tasiri a labarina ba mamaki kaji na ambato su. A gaskiya in har nace zan yawaita kawo hirarrakin abinda ya faru a tsakanina da kawayena ko tsakanin Yaya Auwal da abokansa to kuwa zamu dade ban gama baka labarin ba wanda har hakan zai jawo kosawarka duk da cewa yanzun ma na isheka da surutu, to amma na kusa gamawa. 63 WANDA YACE NAMIJI UBA2 A nanne yayi murmushi yace haba Humaira ta Yaya labarin ki zai gudureni alhalin abinda nake so kenan kuma ni kaina ina ta daukar darasi a ciki. Duk da haka yaya Fahad kasancewar shi dan Adam ajizi ne, da ace ku da yawa nake bawa wannan labarin sai wani yaji ya gaji da surutai na, shi dai burinsa yaji dalilin da na gudo. Amma da zan sanar dashi yaji dadin zancen ko kuma ya gama jin dalilin, sai kuma ya shiga jin haushin ta yadda ban sanar dashi tushen labarin ba wani kuwa jima zai yi duk shirme ne. Akwai wani yammaci ina zaune a falon gidanmu sai ga Yaya Auwal rai a bace, kallo daya na masa nasan ya shiga matsanancin tashin hankali. Dan haka a dole na 6oye nawa farin cikin da nake ciki dan kuwa kunshe nake da matsananciyar murna wato Abba ne ya aikomin da cewa bana ya biya mana makka ni da Yaya to amma ganin halin da yaya yake ciki sai na boye murnar tawa, dan ban san abinda yaya Auwal din yake ciki ba. A sanyaye na karasa gabanshi cikin sanyin murya, tamkar mai nuna nadama ga wani aikin da tayi nayi masa sannu da zuwa fuskarsa kadaran kadahan ya dan boye bacin ransa ya amsamin to amma ni nasan boye bacin ransa yayi. Naje na kawo masa ruwa mai sanyi da wani lemon tumatur da nayiw ato tomotoas juns, wanda yasha kayan kamshi da file bo na bashi, bacin rai yaso ya hanashi sha, to amma nan da nan na shiga yi masa kissa da shshsafa gami da dubarun kissarmu irin ta mace ina bashi lemon a baki a haka har na samu ya dansha da yawa. A nan ne naga ya dan jin gina da jikin kujera, ya rufe idonsa ya saki ajiyar zuciya a hankali. Ban matsanta da yawan tambayar sa ba a lokacin sai kawai na shiga 6ablle masa maballin dake wuyansa na sakar masa fankar falon na dan kauce na bashi guri. A lokacin da na fito sai nan da nan na tura yara gidan Munirat, ni kuma na shige dakina, na je gaban mudubi na kara gyara fuskata, na shafa turaren da nasan yayana Auwal na san kamshinsa, na cire kayan jikina na saka kananan kaya dan sauda yawa yaya Auwal yafi nuna sanshi ga wannan shizar na kara feshe jikina da turare mafi soyuwa a zuciyar Yayana sanan na biya ta dakin girki na kwashi farantin kayan abincinshi na shiga falon. 64 LUBABАН A lokacin dana shiga cikin hanzari da kidima ya dago kansa, wanda babu tantama nasan kamshin turarenne ya dokeshi, murmushi na sakar masa a hankali, gami da kada ido sama-sama fuskata na kunshe da alamun taya shi jimamin abinda ke damunsa. Cikin hanzari ya maidamin martanin murmushina yayin da cikin doki ya tashi ya tare ni nan da nan zuciyata tayi sanyi, hakika nasan nayi nasara wajan fatattakar 6acin ran da ya nemi ya mamaye masa zuciya. A lokacin da muka ajje kayan abincin ban yi aune ba sai ji nayi Yaya Auwal ya rungumeni ya kuma kankameni sosai dan yadda ya matse kirjina a nashi sai da naji alamun dukan kirjinshi ajikina mun jima a tsayen yana rungume dani, gami da shashshafata yadda ransa ke so, yayin da ni kuma ban kawo wani yinkurin saka masa cikas a la'amarin saba saukar dumaman man hawayen da naji a jikina shi ya hanzartamin daga kaina, Yaya Auwall ne ke faman zubar dashi ya salam na ambata yayin dana dan zame daga jikinshi shi kuma ya wuce jikin bango ya dake shi gami da kifa kai ahankali. A nan ne na ruko hannunshi a hankali na zaunar dashi adoguwar kujerar dake nan falon na zauna kusa dashi, sai da na tabbatar jikina ya mannu da nashi sannan'na dubeshi a hankali nace dashi. "Yaya ina fatan kana nan da sanin kaddara har yanzu ina fatan kuma ka gamsu da hakan haba Yaya ka yi tunani fa komai yayi zafi maganinsa Allah. Allah shi kewa bawa maganin komai, kai kuwa Yaya maiz ai tada maka zuciya haka ya nemi gusar da kai daga tunaninka ina ganin ka fauwalawa Allah ya fi wannan dogon tunanin da ka iya haddasa maka wani 6acin ran na daban shin wai mai ya tada maka hankali haka. Alhaji ne kake ganin zai shiga tashin hankali, ko kuwa? Ko kuma siyasar ce ta fita kanka wallahi yaya in har na ganinka cikin bacin rai hakan ba karamin dugun zumanin tunanina yake yi ba dan Allah koma meye ka fauwalawa Allah. Amma in har da halin in sani, dan Allah ina san ka sanar dani in kuwa maganar bata dace a gaya min ba, to dan Allah ka ware, ka kuma kwantar da hankalinka ka fauwalawa Allah. Ka yawaita ambatan innalillahi wa inna ilaihir raji'un ka kuma yawaita istingifari, itace maganin yayewar kowane bala'i. 65 D a ki in Бa ti ka y WANDA YACE NAMIJI UBA2 Anan ma sakin ajiyar zuciya yayi sannan ya jawoni a hankali ya dora bisa kirjinshi yana shaf akaina yace. A gaskiya Humaira bazan iya boye miki ba ya kamata in sanar dake ainishin abinda ke faruwa. Tun da wannan abu an dade ana yinsa nayi kokarin in 6oye miki saboda halin da naga kina ciki,w ato karamin cikin nan da kike dashi ina ga kamar tayar miki da hankali a wannan lokacin ba karamin tashin hankali bane. Humaira sanin kankine kin san ina sanki so ba na wasaba, ina kuma kaunarki, kauna mai tsanani. Hakika, ina mai gudun bacin ranki a ko da yaushe ko ba haka ba. A nan ne yayi shiru gamida girgiz akai, ya kwantar da bayansa a jikin kujera yana girgiza kai cikin takaici, wasu hawaye masu dumi suka zubo a kumatunsa. A gaskiya na tausayawa Yaya Auwal, nasa hannu na goge masa hawayen yayin da na isar da bakina anasa bakin muka shiga tsotsa minti, na dan lokaci kalilan, nayi masa hakane dan in kara kwantar masa da hankali. Nace yaya ina kara gaya maka da kabi a hankali kada wani ciwon ya sarkake, shin Abba ne ya mutu ko Alhaji ko kuwa Mama, kai koma waye ya mutu dan Allah ka gayamin". "No Humaira babu maganar mutrwa a nan". "To zaben da akayine aka fadi sakamakon basu ci ba ko kuwa? Ko kusa ba haka bane Humaira ai fadar sakamakoma sai nan da kwana ukus annan sun kara daddalewa. Anma dai Yaya koma mene ne bai kamata ka tsaya kana jamin raiba kaga nima in ada wani labari mai dadi, da nake san sanar da kai, to amma na fasa. A nan ne ya dago kansa idonsa cike da hawaye, yana murmushin karfin hali yace, Humaira ki sanar dani ROL naki labarin insha Allah zan sanar dake nawa cikin gaggawa". "Alkawari yace ya dauka "Abba ne ya aikomin cewa ya biya mana kudin maka ni da kai, kaga insha Allah bana damu za'a sauke farali. Ga mamakina sai naga ya saki wani murmushi mai hade da hawaye baki daya. Ya jawoni ya kara matse kaina sosai a kirjinshi, sannan yace dani. "Amma wallahi na ji dadi matuka, Allahya saka da alkhairi Humaira gobe zan turo Manu ya kaiki ki yiwa Abba godiya, dan nì bazan iya zuwa ba saboda ina jin kunyarsa matuka". "Kasan kuwa dama kwanan nan da najeni sai da yayimin wannan tambayar yake 66 LUBABAН cewa wai kwana biyu baya ganinka, ko laifi yayi har yake cowa dan ka daina zuwakayi masa aiki ai ko gaisawa kajo ayi tunda shi kansa ya san abubuwa sun maka yawa. Amma Yaya ai dai yanzu an gama zaben ya kamata ace ka samu kaje kun gaisa, maganar jin kunyarsa ma ai bata taso ba yace muje mu fadi sunan da ya dace ma abawa masu yin takardar gida dan yana son ya dankamin wannan gidan ya dago kai a hankali ya kalleni yace, Humaira duk wannan bata taso ba zan sanar dake wata magana amma ina san kimin alkawarin ba zaki tada hankalinki ba ki tsaya ki nutsu kiji abinda zan sanar dake Har yanzu kaina kwace yake bisa kirjinsa yayin da ya shiga shashshafani, ya fara magana kamar haka: Alhaji yasha kirana kan wata magana a watannin baya da suka wuce yana sanar dani wata magana, da naki amincewa wanda har ya nuna 6acin ransa sosai da kyar Mama ta shawo kansa ya hakura, har ya fara yimin magana. Amma ita kanta bata san abinda yake hadamu ba. Amma sauda yaw ain taji musu ya kauraye tsakaninmu takan shigowa tasa santamu, amma cikin ikon Allah bata taba tambayata Jalilin hakan ba ban dai sani ba ko tana tamtayar Alhajin. A gaskiya na fahimci Alhaji kunyar Mama yake ji na kuma san ba zai iya tunkarar ta da wanan maganar ba, balle uwa uba ya tunkari Abba da ita. Alhaji ya yi min abinda babu yadda zan yi tunda mahaifina ne. To amma daga karshe na fuskanci shi kansa dole aka sashi, bawai yin kansa bane kuma uwa uba siyasa na neman sauya masa akida kwata-kwata kuma wallahi Humaira jikina yana bani cewa da kyar ne in zaici kuma wallahi in dai har ya fadi to sai dai muce Allah ya kyauta. A gaskiya an dade ana ruwa kasa na shanyewa kuma gero ya dade da fitowa, to ya kamata a fitar masa da kai yau. A hankali na shiga shafa kirjinshi, na kura masa ido na dan lokaci, na ce "Yaya ka sanar dani ainishin abinda ke faruwa ni ina ganin wannan zagayeyeniyar kawai 6ata lokaci ne ka gayamin yayin da na kura masa ido kallo ido cikin ido nace" uhm ina sauraranka me ke faruwa ne. 67 WANDA YACE NAMIJI UBA2 A gaskiya nayi mamakin yadda na ga nan take wani gumi ya keto masa, kan kace meye wannan jikinsa ya fara jikewa da ruwan gumin. A hankali ya buda baki yace Humaira AURE ZAN YI. Innalillahi wa inna ilaihirraji'un me kuma kunnuwana suke jiye min ayau hakika da Yaya cakamin wuka ya yi na mutu da nafi so da wannan bakin labari da bani da abinda zan kwatantashi da shi. Amma ban iya cewa dashi komai ba sai kawai na tsame jikina tsam daga jikinshi na mike tsaye da nufin barin falon saboda ni ban ma san abinda zance da shi ba. TO amma me ga mamakina sai na tsinci kaina idona ya rufe gaba daya ban fasa tafiyar ba ina kokarin in fice daga falon ba tare da tabbacin ina zan dosa ba rangaji naji ina yi wanda babu tantama jiri ne ke daukata. Ban ankaraba sai naji nayi waniw awan karo da bango gagaram nant ake na dauke wuta wanda ban farkaba sai a asibiti, shima ina kyautata zatan kulawace ta musamman da na samu gami da taimaka wani azababban ciwon ciki da ya shiga murda min, tamkar wacce ake shirin kwashewa kayan cikin. A lokacin dana farkama ban fara furta komai ba sai cikina. Hakika cikina ya mikar dar.i daga dogon suman da nayi kankace wannan Yaya Auwal yayi dirar mikiya a gabana, carab ya café hannuna,w anda yayi dai-dai da fitar wani azababban ruwa mai bala'in dumi daga jikina amma babu shakka ba fitsari bane, dan kuwa babu wani yinkurin yinshi da nayi karan da naji Yaya Auwal ya saka shi ya tabbatar min da cewa babu lafiya. A nan ne naga wata Nos ta shigo aguje, tace yeeh! Kasancewar Arniyace babu bakin salati, ko da yake musimin ma kara rya fara yi kafin salatin ya biyo baya wanda a gaskiya musulunci bai horar damu haka ba musulunci ya koyar damu cewa ya kamata duk wani bawa mumini mai Imani ya kasance ya rike wata kalma ta alkhairi a asararsa abin nufi ya zamana ya rike yawan fadar Innalillahi, ko ayatul kursiyyu, ko dai wata addu'ar a duk lokacin da yaci karo da abinda bashi da kyau ko mai kyau saboda ance in har ka rike abu ya zama sarar ka koda salati ne to a duk lokacin da Mala'ikan daukar rai ya zo maka abinda ka saba fada zaka ambata ko da tashinka aka yi daga kabari. 68 LUBABAН Amma in har ka saba da ashar, ko ihu to kuwa da shiz aka tashi yayin da aka tashe ka a kabari, ko kuma Mala'ikun daukan rai ya zo maka hakika saurin rabka ihu ko kwa ashar, a lokacin gamuwa da abin tsoro ko kuma na alkhairi bashi da amfani saboda bawa bai san tayaya Mala'ika zai zo masa ba. Abin nufi a nan bai san da wacce irin siffa zai zo masa ba. A lokacin da ta yi ihun, itama waje tayi sai gata tazo da likita wanda sai a lokacin na fuskanci ainishin abinda ya faru gareni, sakamakon ambatar blood din da na ji yayi, hakan kuma ya tabbatar min da cewa, nayi barin cikina dan kimanin wata uku, idan ma da kari baifi 'yan kwanaki ba. A gaskiya ni kaina, nayi bakin cikin abkuwar hakan. Hakika tsananin faduwar gaban da nayi ne a lokacin da Yaya Auwal ya sanar dani labarin aurensa shi ya haddasa min 6arin cikina, da nake tattalinsa a lokacin duk da cewa na dan same shi da wuri, to amma ina san abuna sosai, kamar cikin fari. To amma babu abinda zan yi a kai, tun da haka Allah ya kaddaromin. A gaskiya na sha wahala sosai a lokacin kwanana uku a asibitin, yayin da 'yan dubiya suka ringa zuwa Sumayya tazo dubani ita da Kannanta a lokcin dauke da kaya niki-niki, wanda a lokacin nayi matukar farin ciki da zuwan nata har suka tafi yaya. Auwal bai zo ba. A lokacin da ya zone na shiga yi masa bayanin zuwan su Sumayyar, na kuma nuna masa kayan da suka kawo min. Halin ko in kula daya nuna, sai ya nemi dasa min wani zargi na daban to meye dalilin haka. Amma ban tambaya ba bai kuma furt awani kalami dangane da maganar zuwan ta ba. A nan dai muka zauna muna 'yar magana dukda cewa mun kasa sakin jiki da juna saboda ni ina jin haushin irin halin dayake shirin sani shi kuwa ban gamsu da abinda yake nuna min ba shin fushin barin dana yi masa yake yi ko kuwa kunyata

Chapter 7 of 11