Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 11
kar in bata jikina sai da ta gama muka koma dakinta muka zauna ta tambayeni mutanan gidan nace duk suna nan lafiya nan dai muka zauna muna ta hira. 39 WANDA YACE NAMIJI UBA2 Da karfe hudu da kwata Abba ya dawo sai da na tabbata ya kammala da komai sannan na shiga muka gaisa ya shiga tambayata harkar makaranta, da yadda muka fuskanci jarabawa. Nan na nuna masa alhamdu lillahi yace, to Allah ya bada sa'a nace ameen". "Da kika dawo kin ji wani labari?" shiru nayi yayin da na sunkuyar da kaina kasa yaci gaba da cewa. Humaira nasan dai kin ji duk abinda ya faru a lokacin kin amakaranta. To abin da na ke so da ke a nan shine ki tsaya ki sanar dani ainishin abinda yake zuciyarki. Humair ain kika fuskanta zaki ga ina yawan yin wasa dake lokacilokaci to ba wai ina wasa dake bane dan raini ya shiga tsakani, a'a ina yin wasa ne dake kawai dan ki ringa sakin jikinki aa guna ya zamto kina fadamin duk abinda yake damunki. Da farko da naso ace an barki kin dan yi ko da wata ukune, don ki huta sosai, to amma Alhaji Safiyanu ya nunamin matukar damuwarsa akan son a hanzarta yin auren hankalin kowa ya kwanta. Na tabbata an sanar da ke lokacin da aka tsayar ina fatan dai kina ganin bant auye miki hakkin ki ba. Humaira ni dai ta 6angarena na gama miki komai lokaci nake jira. Amma in har akwai abin da kike bukata ki gaggauta sanar dani. Daga karshe, Humaira ina shawartarki da ki riki aurenki tamkar ranki, ki so mijinki kamar yadda za ki so kanki. Ki rik mutuncinshi kamar yadda zaki rike naki mutuncin. Ki mutunta danginsa tamkar naki dangin. Ki tsare masa kanki sosai da sosai ki kiyaye masa dukiyarsa ki boye masa sirrinsa, ki kasance mai tsafta da faranta masa rai. Don Allah Humaira ina rokonki da kada ki zama ballagaza, ki mutun ta aurenki matuka da gaske ki kiyaye wajan magana da wanda ba muharraminki ba. Ba wai ina nufin ki zama mai wulakanta jama'a ba a'a akwai hanyoyin da musulunci ya yarda kayi magana da mutumin daba muharramin ka ba wato musulunci ya yarda ka yi magana da wanda ba muharraminka ba ta hanyar kasuwanci wato wanda siye ko sayarwa ya shiga tsakaninka dashi. Da kuma ta hanyar kare lafiya, wato ka duba ko a dubaka, walau asibiti ko maganin gargajiya koyarwa, bawai sai na karatun Kur'ani ba a'a harma na zamanin muddin za'a karu da shi, wato ya zamto kana koyarwa ko ana koyar da kai sai kuma ta hanyar wa'azantarwa, wato tambaya ga mai wa'azi ko kuma kai a tambayeka sai kuma taimako wajen yaki wato ka taimaki wanda yaki ya galabaitar dashi ko kuma 40 LUBABАН kai a taimakeka to muddin ba wannan mu'amalar bace ta hada ka da mutum ba to duka sauran haramun ce. Dan yanzu zamani ya riga ya juya, ko auren aka yi sai ana taimakawa juna, to amma sai kiga wai yanzu har abota ake yi tsakanin maza da mata, wai sai mace ta kalli wani katon balagaggen ta kirashi abokinta, alhalin kuma ba muharraminta bane, waisu suna ganin ci gaba ne. Dan Allah ni dai ki kiyaye ki tsare mutuncinki, dan hakika kowa kika gani wayayye ne sai dai al'ada da fadar musulunci su danne kuzarinsa. Da naji haka ne na daga kai ahankali nace to Abba, ya kuma maganar aiki, uhm Humaira kenan, kina son yin aikine "a'a Abba na dai tambaya ne kawai" "To Humaira, hakika zamani ya zo mana da cewa in har mace bata aiki ma ba wani abin cinyewa bane. To amma kinsan kuwa da ra'ayinsa ni a nawa ra'ayin in har mace tana da rufin asirinta, gara tayi zamanta a gidanta ta sami ladan aure in kuwa aikin ya zame mata dole, to kuwa babu aikin da ya dace da ita face aikin jinya ko koyarwa shi yasa ma na kawo miki misali da cewa, musulunci ya amince yin magana da wanda ba-muharamin kaba, ta hanyar koyo ko koyarwa. Haka kuma ko ta hanyar duba lafiya, wato a duba ka ko kumı kai ka duba. Ba wai kuma ina nufin sauran ayyukar haramun ne ba a'a hakan dai ya fi mutunci. Dan haka koda nan gaba zaki fahimtar da wata,t o kiyi mata bayani sosai kartace kin jahilceta ko kuma ma ke a jahilceki, me ye jahilci kuwa? Shi jahilci yana tasiri ne akan duk abinda baka sani ba ki tuna da cewa ke kadaice 'ya a gareni, tabbas in har kika tsare mutuncinki, to nawa kika tsare, dan kowanne da kukan gidansu yake yi yana yin ki da maganarki su zasu nuna tarbiyarki ki zama mai tsoron Allah a duk in da kike. Don Allah Humaira kada ki zama mai munafunci a garemu da kuma Ubangijinmu wato kada ki nunawa duniya ke tagarice, amma zuciyarki ba haka bace, abin nufi kada ki zama kyandir, kina haska jama'a amma ke kina kona kanki. Dan kuwa kamun mai ilimi da kamun jahili ko agurin Ubangiji akwai banbanci haka ko gurin aikata 6arna me ilimiz ai iya nuna iliminsa da sanin abu, amma ya yaudari jahili ya aikata aikin asha dashi. Shi jahili shi yake nuna ßatancinsa a fili shi kuwa mai ilimi 6oyewa yake,a mma in ya tashi ya yafi abinda jahilin zai aikata baki ji ana cewa sumu-sumu wutar kai-kai ba wanda turawa ke fadin (green snak on ther green grasess) ba. 41 WANDA YACE NAMIJI UBA2 Dan haka dan Allah ki tsabtace zuciyarki kamar yadda kike nunawa duniya ke tsabtacecciya ce Imaninki shine babbar tsaftarki a musulunci rashinsa kuwa zai iya jawo miki kyamata ga dukkan al'uma ko ba dade ko bajima. Dan Allah ki tsare kanki daga kyashi, dan hakika mai kyashi baya taba ci gaba kuma kis ani ba kyashin mutum sai ya isa kamar yadda ba a zagin mutum sai ya isa kada ki zama mai zagin jama'a wato gulma abin da akasari yanzu yake damun al'umarmu kenan cin naman junanmu. Duk in da aka zauna babu abin yi sai gulma. Allah-Allah ake aga mai rufin asiri asirinsa ya tonu a sami abinyi dan ita kaddara babu in da bata fadawa ke dai ki tsaftace kanki a cikin irin wadannan al'ummar in har kika kiyaye da haka to kuwa zaki sami ribar zaman duniya Allah ya kareki, daga sharrin makiya da mahassada. Duk abin nan kaina a sunkuye yake, duk jikina yayi san yi yayi murmushi yace, to wais ai yaushe zaki zo kiyi mana kwanaki?" nace insha Allahu zan zo yace ko da ya ke ma in bikin ya gabato ai dole ki dawo gida, ko kuwa a gida daya zaku zauna kusha shagalin bikin?" yana magana yana murmushi yayin da na sunkuyarda kaina ina murmushi sama-sama na ke jin wata murya mai kama biyu suna gaisawa da Hajiya Rabi. Da farko na dauka Nasir ne, sai daga bisani na fuskanci muryar Yaya Auwalce, muna cikin tattaunawa da Abba, shima ya shigo gami da sallama sannan ya durkusa ya gaida Aban ya kuma sami guri ya zauna. Abba ya hadamu baki daya yayi mana fada sosai da sosai, fadan zaman aure da zaman duniyar kanta sannan Abba ya zauna damu yana ta hira, sai kace jikokinsa ba 'ya'yansa ba. Bamu ankara ba sai ji muka yi sallamar Hajiya Rabi ta kauraye dakin Abba yace lafiya?" "Dama gani na yi magariba tayi amma babu alamar za ku fito ku yi sallah. Dajin haka gaba dayanmu muka tashi, ni na nufi dakin Hajiya Rabi su kuma suka nufi masallaci, yin sallah". Da muka idar da sallah naci abinci, na tafi dakin Hajiya Iya muna hira nace ai tun dazu na zo akace kin fita makota, wallahi muna dakin Abba muna hira. Nan na zauna muka taba hira da ita ina jin lokacin da su Abba suka dawo daga masallaci, nasan abinci za su ci shi yasa ma ban riga na je ba. Sai da na tababtar da sun gama cin abinci tukunna na yiwa Hajiya Iya sallama na je muka yi sallama da Abba da Hajiya Rabi mun bar gidan da misalin karfe takwas an dare 8:00pm 42 LUBABАН Da muna cikin tafiya ne Yaya Auwal ya ringa yabawa da irin halayyar Abba yace, wallahi Humaira Abba babu ruwansa sai kace ba mahaifinmu ba, ji yadda ya zauna yana hira damu babu abin da ya dameshi. Ba kamar yadda wasu iyayen suke yiwa 'ya'yansu ba kiga da yana tsoron Ubansa kamar Mala'ikan daukan rai, to tun farko an tashi babu shakuwa, kullum daga muzurai sai harara, sam ba sakin fuska, wai kada danka ya rainaka, to ai kuma shi yaran ya taso ba son iyayen ko? To tun farko baka jashi a jiki ba, ka nuna masa ya kaunace ka ba alhalin ko Manzo S.A.W. yana wasa da nasa 'ya'yan tunda har sumbatarsu yake yi ya juyo ya kalleni, yace wallahi muma in har Allah ya bamu 'ya'ya Humaira haka zan ringa yiwa 'ya'yana murmushi na yi ba tare da nace komai ba. Da muka karasa gida ne Yaya Auwal ya bani ledojin da yayomin siyayya don kare da kaya daga kayan ciye-ciye zuwa kayan shafe-shafe wanda bani bama hatta Mama tayi godiya Khadija tace, ke dai yaya kin more wallahi za ki yi auren gida babu ruwanki, da wulakanci, kuma ba za ki ci karo da matsalar kannan miji ba. To kannan nasa mun zama daya ke uwarmu daya shi kuma Ubanmu daya Allah in banda malamin islamiyyarmu yace ba haramun bane da sai in ga kama rbaida ce ba nan dai muka zauna muna ta hira. Da gari ya waye aka maida Khadija makaranta, tun da aka shiga saura sati biyu bikinmu aka shiga shirye-shirye. Daga ni har Yaya Auwal din babu wani mai matsala komai yana tafiya dai-dai kuma hakika iyayenmu sun nuna mana so da kauna matuka. B yau laraba aka tashi da shirin kama amarya,w ato ni kenan. A Tana fadar haka ta daga kai ta kalli Yaya Fahad yayin da tayi murmushit ace yanzu zaka fara fahimtata. A ranar Laraba aka kamani, wato aka sani a lalle a ranar alhamis aka yi min kunshi ranar juma'a aka yi wuni ranar asabar aka daura Aure da safe misalin karfe goma na safen, da yamma muka shirya kayatacciyar walima ta alfarma yayin da kuma a ranar aka kaini gidan Yaya Auwal a matsayin matarshi ta din-din-din kamar yadda yasha fada a wancan lokacin. 43 WANDA YACE NAMIJI UBA2 A lokacin da jama'a suka watse, aka barni daga ni sai halina, sai nayi tunanin in tashi in zagaya gidan don in ga yaddə aka kawata mana shi, dan na ji jama'a da dama suna ta kwada gidan da irin tsarin da aka yi masa, duk da cew anayi kuka sosai da za'a kawoni gidan, amma jin babu kowa daga ni sai halina ya sani na yaye mayafin na shiga zazzagaya gida hakika gidan ya tsaru yanda ya kamata gashi part-part ina cikin zazzagayawa ne naji alamun an shigo gidan cikin sauri na nufi dakin da akamin masauki na zauna, gami da kunshe kaina cikin mayafi Yaya Auwal ne da abokansa suka shigo. Amarsu ta ango naji gaba daya abokan nasa suna ambata, tamkar wadanda suka shirya fadar hakan lokaci daya suka shigo suka zazzauna, amma shi gogan naka sai ya zo ya zauna a kusa dani. Addu'a aka fara gabatarwa sannan nasihu da jawabai suka biyo baya. An jima ana barkwanci a tsakaninmu danni bance dasu komai ba, kawayena kuwa tuni suka yi tafiyarsu, saboda dare ya yi sosai. "Auwal manya duk ka kagu mu fice mu baka guri ko? Wani daga cikin abokansa ya fada su duka suka sa dariya suka tafa, hakan shi ya haddasa min faduwar gaba zuwa can suka yi sallama dani suka ajjemin akwati guda da kuma kudi a kanta, wani daga cikinsu ya zare kudin yace "ya za'a bata kudin siyan baki bayan taki tace la mu komai, magaji shima a cikinsu yake, yayi karaf yace, a'a taci kudinta ai ni ina lura da ita tana ziro kafa tana ta6o angwanta, baku lura da shiba ne sai zabure-zabure yake kunga ai ba maganar da ta wuce wannan. A nan ne yaya Auwal ya kwashe da dariya yace lallai Magaji ka iya sharri. Don Allah ku muyi sallama haka dare fa yi yake yi. Nan ma dariyar suka saka gaba daya, magaji yace ina fatan kun yadda da maganata. Nan dai aka yis allama yaje ya rakasu har kofar gida ya dawo. Abin mamaki sai na tsinci kaina da jin kunyar Yaya Auwal, duk nabi na takure guri daya hakika tun da muke da Yaya Auwal ban taba jin kunyarsa irin ta yauba ya ta so a hankali ya zauna daf dani gami da rike min hannu yana murmushi yace, "To Humaira yaufa addu'ar ta gama ci saura tawa ina fatan kin fahimta. Ta tafasa bance masa ba, yace ahaya baki ce komai ba yanzun nan muka gamu da Alhaji Kabir, yana ta yimin tsiya wai nayi kane-kane na hana Malamina baccin dare yana tamin rokon Allah akan in aureki, dan in kasheshi, to burina ya cika, wai in rikeki sosai in nayi lakwakwakwa har gara taci igiyar to fa 44 LUBABАН bazai bada maganin da za'a fesa mata ba,s ai dai shi ya kwashe igya ya hada ta da igigoyin gidansa ya, kulle. A gaskiya mun jima muna hira dashi yana ta bani shawarwa gaskiya Humaira ki godewa Allah duk dangi kowa sai ya banki yake yi babu mai kusheki, to Allah ya bamu sa'ar zama ameen. A hankali yasa hannu ya zare mayafin dake kaina, yace waike si kace wata bakuwa, amma tsayawa yayi cak cike da matsanancin mamaki, ba komai ne ya daure masa kai ba face ganin hawayen da yayi sharkaf a fuskata, yace, "ya salam Humaira me ke faruwa kuma ya jawoni jikinsa, yana lallashina, kamar wata karamar yarinya yace, haba Humaira bai kamata ace hawaye na fita daga cikin wannan idanuwan ba a dai-dai wannan lokacin da muke kunshe da farin ciki marar musaltuwa ko da yake ban riga nayi tambaya ba shin hawayen na farin ciki ne ko na bakin ciki? A hankali ya kwanta akan cinyata, yana murmushi yace uhm gayamin mana rufe fuskata nayi na kauda kaina gefe guda yasa hannunsa ya rirrike hannuna, yana dariya yace, "Humaira na lura da ke ma kunyata kike ji yayin da ya shiga wasa da gashina bayan ya cire, dan kwalin da ke kaina ya shiga magana a hankali yace, Humaira, amma fa kin san ina onki matuka, kamar yadda nasan kema kina sona sanin kanki ne bana kaunar in ga hankalinki a tashe, to dan me kike son tada min hankali, ya tashi zaune, yayin da ya kwato kansa ta gefen kafadata ya shiga yimin magana sama-sama. Humaira ina sonki, ya kamata ki saki jiki in nuna miki irin son da nake miki a yanzu ki tashi ki yi wanka ko ki ragewa kanki wannan kayan ki zo muci abinci. Ga kazanan da madara na sayo mana ga kuma wani farfesu nan da Hajiya Rabi t abayar tace a kawo mana". A nan ne na daga kaina cikin sauri nace Hajiya Rabi fa kace, kai yanzu har hankalinka ya kwanta da abinda zata yi mana ka tuna da kalamun mana, ana cikin tsaka da bikinfa ta nuna kyashinta da hassadarta a fili. Ganin cewa duk abin da Abba zai min baya wani nemanta sai dai ya aikawa Mama. Saboda lura da take-taken ta dayayi harfa gulmar take yi tana cewa wai an ga biki amma bataga zaman auren ba, ko da yake duk abinda ya faru ga bawa mukaddari ne, to amma fa ita kanta kaddarar addu'a tana sauyata akwai kuma abinda dan adam yake jawowa kansa yace, ai Allah ne ya dora masa kaga yanzu tunda furucinta ya dawo kunnanmu ko zamu ci a tsarge zamuci to kaga duk abinda ya faru akanmu mu muka jawowa kanmu don haka 45 WANDA YACE NAMIJI UBA2 dan Allahı yaya karkaci. Danni ban yadda da ita ba kalli fa kalaman da Kaninta Nasir yayi a kanmu. Tun da Allah ya fisu to muma fa sai mu tashi ya ci gaba da karemu. A nan ne ya ke ce dani kin san ni kuwa da har Allah-Alah nake muzo muci. Ai shi kenan gobe in Allah ya kaimu an ba almajiri "a'a ba za a yi haka ba na fada saboda kasan ba'a san abinda yake ciki ba ba gara ka ba karen ka batun da namane yace to shikenan. Amma na riga na rufe kofa sai dai da safe in Allah ya kaimu. A nan ne ya shiga taimakamin wajen rabani da kayayyakin dake jikina, sai da ya shiga ya kwancen zane nane sai nayis auri na rike saboda kunya yace "a'a Humaira meye haka kuma ai gar aki cire kayan ki saka rigar bacci ko najima sai kamshi kike bama sai kinyi wanka ba, nine dai nake bukatar yin wanka saboda za fi duk nayi gumi. Daga nan ya mike ya shiga bandaki cikakkiyar minti biyar ce ta ishe shi wanka daga shi sai gajeren wando ya fito duk a lokacin ina takure guri guda. A nan ne ya umarceni da in sakko muci abinci, kai tsaye nace dashi na koshi "ai kuwa baki isaba dan kuwa dole kici abincin nan murmushi yace in ba so kike ki galabaitar da muba, ki haddasa mana haihuwar guzuma 'ya kwance uwa kwance. Wata matsananciyar kunya ta kamani dan kuwa na fuskanci in da yasa gaba, gabi. na ya ringa faduwa, to amma ire-iren nasihun da aka ringa yimin lokacin bikin su suka ringa fado min a rai. a A hankali na sako na zauna daf da shi, amma fa duk da haka kaina kasa yake. A hankali muke cin kazar, gami da sassanyan nonon sahanu ahankali yana dan jana da wasa har cikina ya dauka yadda ya kamata. Da kaina na ce dashi na koshi, yace yayi kyau sai da shima ya gama ci sannan ya shiga hilatata da hira gami da 'yan wasanni jan hankali wanda ya taimaka wajen gusar mani da hankali tun ina jin kunyar har ta fara guduwa da kanta. a A hankali ta dago kanta ta kalli Yaya Fahad tace amin afuwa nan bazan iya zaiyane maka yadda muka raya wannan daren ba murmushi yayi yace dalili. Tace duk da cewa na maka alkawarin bazan 6oye maka komai ba, to amma abu biyu ne za su sa in ki gaya maka. Abu na farko shine ina mai matukar jin kunyarka kuma sannan sirrin mune, bai kama ta dan bama tare ba, in kasance mai tona mana sirrinmu, alhalin ako da yaushe Allah yana horarmu da mu kasance masu boye sirrinmu musamman mu mata mu kasance masu boye sirrin mu matuka. 46 LUBABАН A hankali ya lumshe idonsa yana murmushi cikin jin dadi hakika Allah ya hada shi da irin matar da ya ke so. A washegari na tashi cikin mutuwar jiki da kasalar da take barazanar haifar min da ciwan jikin daka iya hanani ko da dora ruwan shayi ne. Dan haka shi da kansa ya shirya mana abinda zamu gabatar wa da cikinmu kuma a wannan ranar wuni nayi ina baki kawaye da 'yan uwa. A gaskiya kowa yana sha'awar yadda muke tafiyar da soyayyarmu ni da yaya Auwal yi nayi bari na barin nan gami da tsantsar biyayyar aure, rashin kiwa wajen gamsar dashi a shimfida kula da dukkan wani motsinsa, tattali da tsantsar tsabta, walau ta tufafi ko ta jiki kin rabuwa da kamshi ako da yaushe su suka taru suka taimaka min har na ringa juya mijina son raina ta yadda nima duk motsin da nayi yasan manufata, in na kawo dauki ne kan kiftawa da bisimilla ya kawo masa daukin haka muka ciga ba da shimfida rayuwarmu muna masu tattalin junanmu kamar kwai. A zahiri muke nuna wa junanmu tsantsar kauna bawai a badini ba mun shimfida so tsantsa a gidanmu, mun kuma shuka gonar soyayya dan haka babu irin soyayyar da bamu nomaba. A hankali ta dago kai ta alli Yaya Fahad, wanda ya kura mata ido, yana faman murmushi, nakika labarin yana kawatar dashi. A gaskiya muna san junanmu, ba kuma mu cuci junanmu wajan nunawa juna kauna ba. Bana mantawa akwai wata rana muna zaune da Yaya Auwal a falon gidanmu yayin da yake zaune a doguwar kujera, ni kuma ina zaune daga kasa a gabanshi. Al'adatace matuka a duk lokacin da muke tare, to fa ina nan ina masa tausa, ko ja masa kafa, domin in inganta irin hirar da muke yi ya lumshe ido ahankali yace. Humaira a gaskiya wutar sonki kullum sai kara ruruwa take a zuciyata. Hakika ina sonki matuka wanda har na yankewa kaina alkawarin babu ni babu karin aure. Allah bai haramtamin kusantar wata matar ba, muddin in matatace, to amma ni na haramtawa kaina. Humaira ko aure na Kara bana tunanin zan iya kwatanta adalci a tsakaninku kinga kuwa ba ma shi da amfanin in kara din ya jawoni jikinshi yana shafani, yayin da muka shiga tsotsar minti, mun jima cikin wannan halin hakika, muna nunawa juna so da kauna wanda a duk lokacin da na tuno irin gata da shagwabanin da yaya Auwal yayi amma daga karshe ya min haka gaskiya hankalina yana matukar tashi. 47 WANDA YACE NAMIJI UBА2 Amma kamar yadda yawancin ma'aikata suka ware ranar Lahadi saboda hutu na musamman ga junansu to fa mu da wuya ka zo a wannan ranar ka same mu saboda mu mun ware wannan ranar rana ce ta sada zumunci, sai mun gama zaga dangin da ya dace muna gaida su daga karshe ya ajjeni a gidansu ko kuma gidanmu. To kuma a ranar sai dare zamu dawo. Dan yawanci a duk inda muka sauka kusan tare muke wuni. Ba ma ace gidan Abba muka sauka ai fa muna tare dashi a dakin Hajiya Iya muna ta hira muna dariya. Dan kuwa tun bayan bikinmu Hajiya Rabi ta rage yi mana fara'a. To kuma wannan ita ya shafa ciwan ido kuwa ai sai hakuri. Dan kuwa ni da Yaya sai dai muce maki gani ya kauda idan shi. Amma fa hakan ya haddasa mana makiya da masu yi mana kyashi. Ganin cewa a kallah mun shafe shekaru da dama amma babu wanda ya taba jin kanmu dashi. sai da na shekara biyu sannan na sami ciki koda yake ban cika biyun ba. Akwai wani zuwa da muka yi gidan Abba a lokacin muna zaune a dakin hajiya Iya ciki ne wata uku manne a marata, babu mai cewa ina da ciki. Hajiya Iya ta kalleni tace ke dai har yanzu shiru to shegen fitina irin tasu ko an sami cikin basu za su kafar da abinsu ba kullum-suna manne da juna kasancewar ta tsufa ba kunyar bace ta isheta ba, Inna biye mata kuwa to sai azo ana aika-aika dan haka sai na yi sauri nace haba dai Hajiya Iya Allah ne dai bai bayar ba, tace tun da kika ce Allah yar nan ai kin kare magana. A lokacin da cikina ya shiga wata na shida sai na fahimci an fara dagoni don haka sai na rage yawan fita kasancewar Khadija ta gama makaranta to takan zo ta taimakamin da aiyuka a gidan shi kuwa Yaya Auwal.shagwabata har ta fara isarshi, to amma babu yadda zai yi dani dole yake biyemin. An nuna kulawa ta musamman a akaina musamman da na shiga wata na tara da lokacin haihuwa ta zo mace Allah ya bani. Na ga so da kauna da kuma kulawa ta musamman dani da yata a gurin yaya Auwal. Da ranar suna ta zo yarinyar ta karbi sunan Fatima sunan mahaifiyarsa kenan da farko mutane sun yi surutu dan da yawa mutane sun yi zatan Safiya za a sa mata wato sunan mahaifiyata, to amma abin da mutane da dama basu fahimta ba shine kowane da da sunansa. Hajiya lya bata sami damar zuwa ganin jaririya ba sai bayan suna da kwana uku saboda yadda jikin nata yake'yawan matsa mata. 48 LUBABAН A lokacin da tazo babu kowa a gidan daga ni sai Khadija kasancewar ranar aikice yaya Auwal yana gurin aikinsa mun jima muna gaisawa. Ta kalli jaririyar tace an kwayi mata aski?" Nace haba dai asiki Khadija tace Hajiya ai yanzu an daina yayin aski. Haka kawai mutum ya askewa dansa kai gashi ya tashi fitowa da sidin ludayi kuma ma gashi baic ika tsawo ba da yawa. A hankali ta saki dan tari tace ai 'yayan yanzu kun yadda sunnar ma'aiki kuma kuna sane tun da fadar Ubangiji bata sauyawa wallahi sam bashid akyau kuma kun sani ba ba ku sani ba kuma abanza da ku aske da kada ku aske alkawarin Allah ne sai kan ya kade tas tun da haka kawai kan zai yi ta kadewa gudun sudin ludayin da ake yi kuwa sai ya sude tas shi yasa sam 'yayan yanzu basu da gashi irin na mutanan da to sam ba'a biyayya da fadar Ubangiji. Ba ga shinan bama nasara sun bata ku duk abin da yake da kyau sun hana ku ayanzu. A hankali cikin dubara suke dulmiyar da ku suke gurbata muku tarbiyarku da dabi'unku. A yanzu fa turawa sun hanaku matse nonon nan na farko wato wanda ake matsewa kafin a bawa mutum yasha alhalin kuma shi yake haifarwa da yara taurin kai shi nonon da likitoci suke ce da ku ya fi lafiya ajikin yara to babu abinda yake hnifarwa face taurir kai sai kiga ya'yan yanzu shegen taurin kai karıar 'ya'yan nasara. Amma in an gaya muku bakwa yadda sai ku ringa cewa ai abubuwan da ne to wallahi harkar da, da kuka watsar da ita ta ke taimakawa wajen watsar da tarbiyar 'ya'yanku mu gashi nan har a yanzu yaro duk girman sa muddin iyayansa na raye ba'a daukan kansu manya komai sai sun tuntube mu, mu magabatansu ku kuwa fa yaro tun yana karamis ai abinda ya ga damar yiz ai yi to meye amfanin hakant abbas da kuna bin hanyoyin da muka bi muka raini namu 'ya'yan, da kuma hanyar da muka bi dasu wajen tarbiyantar da su da ba haka ba. A yanzu 'ya'yan yanzu

Chapter 5 of 11