Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 11
har sau biyu,sannan ta kalle ni. Kin san abin da ake nufi da HADUWAR JINI? Na girgiza kai ta kara murmusawa. ,Abin da akae nufi shine,kauna ta cikin jini,haka kawai Allah ya hada bayinsa cikin hikima tasa. Ma'ana yarima Allah ya hada jininku ba don komai ba,saboda hakan Allah ya rubuto. Wallahi ina mai tabbatar miki,da yana tausaya mana ne kawai na farko yafi karfinmu nesa ba kusa ba. Tsarinmu da shi ya sha bamban da sa.kuma ya fahimci hakan. Shawara daya zan baki. Kiyi kokarin inga ba shi amsa gamsasshiya a duk lokacin da yayi miki tambaya,hakan zai sanya ya daina damunki tunda halinsa ne.Yarima ba yaro bane don akalla zaiyi 38yrs ke kuwa duka fa yanzu kike 15 kawai daiya dauke a kanwarsa ko yar cikinsa a tunani. Jin tayi shiru nace to inna yace gobe zai dawo na dama masa fura, fura? Ta tambaya tana kallona nace uhm tayi tagumi to bamusan abnd Allah zaiyi goben ba na mika mata wayarsa daya bani aro ta karba itama hannunta yana kyarma don kyaunta ga wani kamshi da yake fita ta juyata ta kara juyata Allah sarki humaira yaron nan tausayi gareshi adana masa zuwa safiya na amsa ita kuma ta juya ta fara bacci ni kuma yau baccin sama-sama ne sbd kamshin yarima daya addabeni (kuji mayya lol) kamshin da yake a jikin wayarsa harta hanneyana ma kamshin sukeyi. Saina tsinci kaina cikin faduwar gaba ina tunanin irin halayensa. Tun daga kofar shiga falon na fara fahimtar yau gidan babu lfy kowa ka gani yayi tsuru-tsuru yana zare idanuwa ba mazan ba ba matan ba kowa yana cikin fargaba. Jikina ya dauki rawa don bana kaunar tashin hnkli a dunia. Takun farko dazan shiga cikin falon najiyo muryar gimbiya tana balbala masifa abnd kunnena ya jiyemin saura kadan fitsari ya zubo min nayi saurin komawa ta kicin tare da lafewa a jkin bango ina saurare. Duk abnd kake takama dashi nima ina takama dashi yanda kake dan sarauta haka nima ubana yake sarki na gaji da wann cin kashin da kake min tun zuwanka! Kullum da irin salon wulakanci da rainin wayon da zaka 6illo min da su kana kunyata ni a gaban BARORI nah! Ya zama dole ka amsa min tambayar nan INA KAKE ZUWA KULLUM CIKIN DARE? Na tambaye ka jiya bayan ka dawo kace min bacci ka ke ji. Yo yanzu kuma fa? Da kai nake kayi banza dani,ko za kayimin izgilanci ne da kasaitar da ake yi maka kirari da shi? To ka tuna cewa,nan ba masarautarku bace,don'yan magana na cewa,sarki a gidan wani sarkin sunansa BAWA....Ba za kayi magana ba? Lallai zaka amsa kira a fada yanzun nan,idan ka raina ni ina ganin sarki yafi karfin raini a wurinka. Ta banko kofa,tuni kowa ya kama aikin karya kada ta gane ana sauraronta. Na makale wayar a siket dina,kada ma wani ya gani. Kallo daya zaka yi min ka gane ina cikin tashin hankali. Aiki kawai nake amma Allah Allah nake ta dawo a aiko kiran yarima fada nayi amfani da wann damar na hamzarta kammala tare da ajiye masa wayarsa koda a karkashen carpet ne tunda ba mai shiga dakin saini amma shiru kakeji. Rabi ta kalleni na tsaye kawai ta matso. Gimbiya fa batasan baki zoba kwana 2 sbd haka kadaki bari ta gane kiyi hamzarin kammala aikinki kinga yau za'a bamu albashinmu tana cikin fushi kada a kiramu baki kammala ba. Gaba kawai nayi zuwa daki dama can kadai ya rage da bandaki ina tura kofar na ganshi kwance idanunsa jawur kamar wuta. Kamar dama ni yake jira yayi saurin tashi zaune ya tura kofar tare da kullewa da mukulli nayi saurin kallonsa har lokacin idanunsa jawur suke fuskarsa murtuk kamar zai fashi... ya karaso gabana ya kalleni kamar zai fashe da kuka idanun sun kara ja na sunkuyar da kaina ya kankantar da murya kamar zaiyi kuka. Humaira banason gimbiya na tsaneta wllh... Nayi saurin kallonsa ya bude min idanu sun kara rikicewa cikin matsanancin bakin ciki yaci gaba da cewa ni fareeda zata kira BAWA sbd nazo gidansu na zauna? DonAllah ki taimakeni menene shawara? Kwankwasa kofa mukaji na kalleshi cikin tashin hankali tare da saurin fiddo da wayarsa na mika masa ya karba sannan ya dan ware murya yace waye? Dogari ne Allah ya taimakeka, lfy? Ya bukata a fusace yace Allah ya taimaki yarima. Sarki ke nemanka fada karfe 12 na rana.ya kalle ni cikin wani yanayi sannan yace. Allah ya nuna mana. Hannuna ya kamo muka zauna bakin gado. Na kyale shi ganin kamar hankalinsa ya dan gushe saboda 6acin rai. Ya kalle ni,ni kuma na dan zame hannuna. Humaira ya zan yi da fareeda?kayi hakuri kuma kayi biyayya ga mahaifinka, Allah yana nan. Ya tallabo fuskata ya kara yi min kallo sosai,na dauke kaina. Ya kara yin kasa da murya. Nayi hakuri shine tunaninki? Nayi dan murmushi,bayan wuya sai dadi yarima,sannan ka daina fitar daren tunda bata so,dole ka rinka gujewa 6acin ranta matukar kana son kwanciyar hankali. Kinga kalle ni". Ya fada... ,Na kalleshi a kaikace ya nuna min saitin zuciyarsa,wani abu ya tasayan nan kamar dutse gaskiya guduwa zan yi,bana zama a kashe... Na kyalkyalce da dariya,sai kawai naga ya sakko kasa ya zauna gabana tare da tsire ni da ido. Dariya mana baki ko?ya fada kamar zai yi kuka. Nace,to don Allah ko ni yarinya yanzu nace zan gudu? Baki sani ba ne wallahi da gaske nake. Na zaro ido,don Allah kayi hakuri kada ka 6ata ran mahaifinka. Yayi shiru,sai kawai ya ba ni tausayi to shi wa ya ke so?na dube shi a tsanake tare da ambaton sunansa.yayi saurin dubana. Na ba ka shawara? Ya daga kai yanayin yadda ya yi kamar yaron goye, sai ya bani dariya. Nayi murmushi. Idan kun je fada ka kama bakinka,kada kace zaka maida magana saboda gudun yin SUBUL DA BAKA,ka fadi abin da zai janyo wata matsalar da tashin hankali. Murmushi kawai yayi. Tashi ki kawo min karin kumallo na. Na mike na tarar lokacin suka gamasaukewa,don haka sai da na jira tukunna.... Kafin na kai masa ya wanke kewaye tare da gyara dakin. Na rasa abin da zance masa,amma faduwar gabana ta karu. Ina ajiye farantin wayar nayin kara. Dariya na ga yana yi kafin ya kara wayar a kunne. Haba Alhaji nayi fushi,ka jira dawowata zaka kwana yau don ubanka! Hakan ya fahintar dani abokinsa ne. Ya ce,kana ta wannnan albishirinka?...ina ganin Allah ya amshi addu'ata...I FOUND A LITTLE BABY THAT I DREAMT ALWAYS TO BECOME MY BELOVED" ya kyalkyale da dariya kamar bashine ya gama fushi yanzu ba yace. "AM TELLING YOU. Ya dan saci kallona. Uhm! I CAN'T EXPRESS BUT JUST EXACTLY I DESCRIBED. Bana fahimatar turancin,amma sai kawai naji cewar na tsargu da hirar. Ya kara cewa. Wlh abokina HUNDRED PERCENT. Na mike zan bar dakin,yayi saurin nuna min hannu alamar na zauna ya na fadin. DO YOU KNOW WHAT? Na gama kamuwa billahillazi saboda JUST 3 DAYS bamu hadu ba sai ga zazza6i...ka dai bari zan kira ka anjima,akwai STORIES A LOT. Yana gama fadin haka ya ajiye wayar. Ya kalle ni yana murmushi idanunsa sun washe sauran dan jan kadan. Taho 'yar kanwata muyi karin kumallo kin ji? Ko baki gode da aikin da na yi miki ba? Na yai murmushi, Na gode,amma...maganar ta makale saboda sauyin da na gani a fuskarsa... Haka na dinga cusa wainar kwan sbd kallon daya tsareni dashi yana karin kumallon duk ya samu nutsuwa, baki son kallo ko? Na daga kai Eh wllh, yayi murmushi kiyi hakuri zaki saba dashi bansan sanda nace kallon? Ya kurbi ruwan zafi kawai bai bani amsa ba wai ke ya maganar karatunki? Babu nace babu fa kikace ke bakison ilimine? Nayi murmushi kusan hakan. sbd me? Ina ganin bacan alhairin yake ba, istihara kikayi ne? Nayi murmushi ina mmkin yanda baya gajiya da tambaya. Gimbiya Humaira ya fada yana murmushi idanunsa kyar akaina nayi saurin kallonsa. Sbd yanda naji sunan banbarakwai. Aka buga kofa waye? Rabi tace Humaira tazo muje karbar albashinmu idan ta gama. Nayi saurin mikewa ya kalleni da Allah zauna na karyar da wuya na kalleshi yayi murmushi a dawo lfy jeki. Kayan fa? Idan kin dawo kya kwashe ko baza'a bamu salala ba? Nayi murnushi duk na dauka wasa yake zan baka mana nawa? Ya tambaya duk yanda kake so yayi murmushi rabi zaki bani harda aikin da nayi miki yau. Nace to. ,Duk zatona Gimbiya ce za ta raba kudin ashe wasu ne daban. Muka bi layi nice ta 2n karshe,ga shi biyan baya sauri shi yasa muka dauki lokaci mai tsawo,har ku san karfe 1 saura. Ban tarar da shiba,amma na tarar da 'yar guntuwar takarda gefen faranti wanda ya rubuta da manyan baki cewar 'KIN AMSO? TO KI AJIYE MIN NAWA KARKASHIN FILO. hakan kuma aka yi,na ajiye na fito. Da dubu 7200 na isa gida,saboda na biya basussuka sauran kudin icce da maggi kawai ya rage,su kuma ko su Aisha na aika. Inna tayi murmushi da na gama yi mata bayani tace. Gwadaki yayi kawai yaga cewa,kina da rowa? yanxu bada 50 a sawo masa furar sai nonon ma na 50 ko yagot zaa sanya?"Yadda ki ka ka gani inna. Na fada. Tace. A hada masa duka,kin san maza akwai son din dadi. Yau kam har balangu muka ci da lemon kwalba. Ana gama sallar isha'I ya iso,yace na yi masa iso wurin inna. Bayan sun gaisa yace, don Allah inna ina son Aisha da sumayya da kuma humaira suyi min rakiya wani wuri. Jin an ambaci su Aisha yasa inna cewa Allah ya kiyaye yarima,mun fa gode. Ni kuwa saura kadan na kurma ihu don takaici. Ba wai rakiyar nake ji ba tambayoyinsa da son maganarsa ke damuna. Muka fito fuskata a daure su Aisha sai tsalle suke yi don rashin sanin ciwan kai. Muka shiga motar nan naji wani tsam!karo na 2 dana ta6a shiga karamar mota,ranar da ya sawo wa inna magani sai yau... Wani daddadan kamshi (not clear)na dai daure duk wurin sai kallona suke yi,ban san me suke cewa ba kamar suna wani yare. Ana cikin sharcewa ana gyarawa suka shigo,naji takaici. Shi kuwa kamr mutuwar tsaye yayi bakin kofa zuwa can ya tako kusa dani,tare da sunkuyowa yace. Masha Allah. A hankali. Abin dariya abin haushi,sai naga mata na faman barbaza gashi nayi hakuri ta gama kawai tana sakar min kai na hade shi wuri guda,na cushe kamar yadda nake yi. Tayi saurin cewa. OH SORRY YOU NEED HOSE WIFE? Ko kallon sakarai ban yi ba, nayi gaba kawai abina. Su sumayya kuwa kowacce hannu cike da kayan zaki ana washe baki. Maimakon muyi gida,sai naga ya karya kwan,shagon da muka shiga sai dana tsorata don ganin duniyar dake ciki. Ya sami kujera 2 ya zauna tare da miko min dayar na zauna. Ya dubi sumayya da Aisha dake tsaye yacekunga kekunan can? Sukace eh yace to kowacce ta turo guda 1 ku zagaya duk abnd kukeso ku dauko ku zuba aciki. Yaro! Yaro! Wani takaicin sai yaro wllh bai ida rufe baki ba su ka kwasa da gudu sukayi gaba na dubeshi nace mekake nufi? Yace shopping zanyi musu, danAllah meyasa kakemin haka? Kinason sanin dalili? Nayi shiru cike da takaicin na tambayeshi ya tambayeni yayi murmushi konayi miki bayani a yanzu bazaki gane ba. Kamr nace masa sbd mahaukaciya ya daukeni ko? Amma sai nace kaga kai kake haddasawa kanka fitina da rashin kwanciyar hankalin gimbiya. Yayi dariya ba wani abu lokaci ne zanyi magana yace waike baki kunshi ne? Shiru kawai nayi sbd bani da amsar bashi. Samarinki nawa Humaira? Ashirin na fada, ya kyalkyale da dariya har nayi mmki yace ashe kin iya gatse? Wllh idan muna tare sai naji kamar na saceki na gudu. Nace eyeh? Ya dubeni da sauri nan da nan na fahimci SUBUL DA BAKA yayi idanuna jajur nace me nayi maka zaka sace ni ka gudu? Yanzu kai.... Ke! Ya matso da kujerarsa wllh wasa nake nan da nan ya hau yan kame-kamen furta kalmar. Daga nesa na hango lodin kaya na yo kanmu ba ka hango masu tura kayan saboda tsoran da suke yi. Ni tsorata manayi,tunanina kayan ne suka turo kansu. Sai kawai na ga su Aisha na mike tare da salati. Me ke damunku su.. Ya taso babu ruwanki. Waje na fita na tsaya bakin mota ina jiransu kawai. Maza 4 suka rako su kowanne hannunsa da kartin ledoji. Har muka isa gida bance komai ba,nayi gaba abina,shi ya jido kayan kafin ya shiga. Na gama fadawa inna komai. A tsakar gida ta ta fito tana salatin wadannan himilin kaya,yana tsaye shi kuma ya goya hannayensa duka a kirji. haba yarima har yaushe zaka biye haukan yaro? Inna kada ke maki ga laifinsu,wlh ni na sanya su ko humaira? Shiru kawai nayi. Ya kara yin kasa da murya... Amma inna ayi hakuri. Nan da nan inna ta gaza cewa komai,sai kawai ta shiga daki tana yi masa godiya. Ya kalleni ni,dauko min furar ko baki dama ba? Na wuce kawai na kyale shi. Zaune yake saman tabarma. Kofar daki na ajiye kwanon na yi tsaye. Ya dube ni kawai,sannan ya fara shan furar. Ga mamakina sai na ga uya shanye duka ya mike tar da matsawa kofar daki. Inna na bar ku lfy. Tayi saurin cewa. Allah yabamu alheri yarima an fa gode. Su Aisha murya zauu!Aka ce yaya yarima sai gobe. Yace Allah ya huta gajiya kunji? Yaya dube ni,yace. Mu je!!! Kamar kada nabi shi,haka na daure muka isa bakin motar. Ya jingina bayansa a motar tare da fuskanto ni yana kallona. Ya zura hannu a aljihu ya fiddo ambulan ruwan kasa mai fadi,ga tudu yace. Ungo kudinki ni wasa nake yi miki. Na sunkuyar da kai kawai. Kin ji? Nadai yi shiru. Ki kar6a nace dare na kara yi kin san halin Gimbiya,ana can an dake lamba... Allah ka dauka. Nace dashi. Wallahi wasa nake yi,kar6i kudin babu inda zan je dasu. Jin ya rantse yasa na mika hannu,sai kawai ya fizgo ni na fada kirjinsa,nan da nan na ji wani irin abin duniya mai wuyar fassarawa. Ya rikr ni gam!nayi kwance a saman kirjinsa. Wai fushin na mene ne? Ya fada tare da sunkuyowa saitin fuskata.... ,Sai kawai na tsinci kaina da sunne kai a jikinsa. Ya dago ni yana kallona fuskata. Na runtse idona ni kaina na rasa kunyar ta mecece. Kunya ta kuma ake ji? WONDERFULL ya fada. Ni dai ka sake ni ban so. Na fada murya na rawa. Cewa zaki yi na kyale ki ba wai na sake ki ba,wannan kalmar bata har abada tsakaninmu. Idan kina son na kyale ki kuma sai kin fada min fushin da kike yi tun fitarmu. Ba fushi nake ba. To mene ne? Yadda yayi maganar ya kara jefa ni cikin yanayi. Gida zani. Na fada da kyar. Zan raka ki yau,kada ki damu. Ya fada tare da kara riko ni. Wannan abu yayi min yawa. Na fada a zuci. Ga shi sam haka kawai na kasa kallonsa,da kyar nace. Wannan fa haramunne. To naji,amma idan na sake ki kada ki matsa kin ji? Na ce to. Yana sakina na yunkura zan kwasa da gudu,yayi saurin maida ni jikinsa yana fadin. Ashe kina da wayo? To ai ni... Nayi shiru. Sai kawai na sanya kuka. Yayi shiru,zuwa can ya sake ni yana fadin. Kina rugawa zan biki. Na tsaya cak! Goge hawayen,goge su. Sai kuma yayi shiru. Baki so ko? Nace uhm. To na bari muje na raka ki gida. Zan je kawai. Ke dai mu tafi,ai ba roko ki ka yiba,ni na sa kaina. ,Har tuntu6e nake yi don sauri,jikina ya yi min wani iri. Zuciyata ta tsaya wuri 1 cak!yayi saurin shan gabana. Kin kagara ki rabu dani ne? Nayi shiru kawai. Wai wannan snkui sunkui da kan na mene ne? Muryarsa na kara dagula min lissafi,na ce. Ba komai. Humaira kenan,wlh miskilancinki na burgeni. Da akwai namiji gidan nnan yau da a nan zan kwana a dakinsa. Tsoro ya kamani,anya yarima baya da ta6in hankali?kamar wanda ya shiga zuciyata,sai ji nayi yace. Ke ni idan muna tare rasa hankalina nake yi. Abin nan yafi karfin kwalkwalwata,sai kawai na hau addu'o'in tsari a zuciyata da kyar ya kyale ni kamar zai bi ni cikin gidan. Hakan ya kara lalata kwalkwalwata tare da tunzura zuciyata zuwa wani babin tunani. Labule kawai na daga na fara ce da inna. Inna!inna! Yarima yana bani tsoro. Tsaye ta mike. Abin tsoro ne humaira,domin na karanto inda ya dosa. Na mika mata ambulan. Kudin dana bashi ne ya maido. Tace daman na fada miki jaraba ki yayi. Ta hankada filo kawai ta ajiye. Kinga kaya?nayi shiru,tace gaba da cewa. Kaya ne wani abun ma ban san ko mene ne ba. Na kwanta kawai. Inna kyale su sa cinye tunda su suka debo. Idan akwai wanda ba'a ci ciki fa? Nace A'a to ,Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Ina ta fada. Shiru nayi maganganun nadawomin cikin wani irin yanayi tare da kwanciya danayi a jikinsa. Nan da nan tsikar jikina ta tashi. Fasalinsa ya fado min,na lumshe ido,sai gefin asuba bacci ya sace ni,kiran sallar farko na farka. Na tsinci kaina da kosawa gari ya waye na tafo aiki. Karfe 6 saura muka fiddo kayan nan don kara dubawa ni da inna,bayan mun karasa lazimi. Ko madara tafi guda 10,wasu abubuwan kam mun kasa gane su balantana mu san yadda ake amfani dasu. Ta dube ni,idan yazo kya tambayar mana shi yadda suke,idan muna iya amfani dasu toh!idan kuma ba ma iyawa lillahi warasulihi gara ya mayar a bashi kudinsa da yayi asaraa,ko yakika gani? Nace gaskiya kam,sannan da alam dinki zai mana tunda har ga teloli muka je fa. Tace,su Aisaha sun fadan. Kinga kudinmu sun kara auki ke kadai zaki yi sauran musha shagali. Na karasa maganar ina murmushi. Sai mu yi sana'a kada mu ajiye haka nan,kinsan zara bata barin dami. dauko mana su nan in tisa ko naji sanyi,hadi da sauran suna cikinjakar filo. Sai da na hure kyandir din kafin na tashi,saboda hasken daya gauraye ko'ina wato gari ya waye. Na fara mika mata na ciki ambulan din ni kuma ina tisa canjin da suka kwana. Humaira!!! Inna ta kira ni da karfi,wanda yayi sanadiyar tashin Aisha da sumayya. Tsaye na mike ganin bandir din 'yan dubu- dubu a hannunta ina zare idanu cikin tsoro. Karkarwa da hannuna ke yi ya taimaka wa bandir din faduwa kasa. Munfi mintuna 10 muna musayar kalllo kafin tace. ,Akwai abin da yaron nan ke nufi humaira,lallai kudin nan koma masa zasu yi,domin sun fi karfinmu. Idan kin je ki ce inna na son ganinsa a yau din nan,wannan alamari yafi karfin tunainmu. Kasa ce mata komai nayi,na shiga shiryawa domin na ji an yi sanarwar karfe 7 saura mintuna 13 a rediyon inna. Har na bar gidan inna ba ta daina sambatu ba,tana faman mita. Na isa kan lokaci kamar kullum,na shiga gyaran falo,amma cikin yau ya fi na kullum saboda sauya tsarin da nayi. Wanda yana 1 daga cikin gargadin da Gimbiya ta yi min,cewar duk. Bayan sati 1 sai na yi hakan. Su kuma 'yan aikin rana duk bayan sati 2. Lokacin dana kammala ina goge 10 har da ku san kwata,motsin fitowarsa naji tare da kamshin turarensa da ke fadar min gaba a duk lokacin dana shaka. Kamar kullum hadin baki,sai ga Gimbiya ta shigo da irin nata kamshin nan da nan falon ya hade ya gauraye da wani irin daddadan kamshi. Na bada gaisuwa ga kowannnesu ba tare daba kalli 1 daga ciki ba,sannan na ci gaba da aikina. Ina jiyo sautin murmushinta,lokacin da tace. Barka da safiya. Ban ji ya amsa ba,amma wata kila yayi mata da fuska,nasan kasaitarsa. "Na zo yin karin kumallo da yarima,tunda ni an ankasa zuwa har yau ayi dani, nayi gayyatar cin abninci har na gaji. Kai kuma ka. Kasa gayya tatat,shine yau ni nazo. Bai dai yi mgn ba,ta kara cewa. Da za'a taimakamin yau kadai da na fita da kai unguwa. Lokacin ne yayi mgn da wata 'yar shakakkar murya. Yau bani da lokaci,sai dai wani. Dama nasan haka zakace,wai yarima wannan halin ko inkulan da kake nuna min na menene?ta katse shi da fadar hakan cikin nuna tsananin 6acin rai. "Humaira zoki bani kalaci. Ya sauya mgnr yana mai kara kallona.nayi saurin dauke kaina saboda ganin irin kallon da yake yi min. Na ajiye kayan,ta kalle ni cikin fushi. Je ki kawai,zan yi SERVING dinsa. Ya dube ni,zauna ki bani abinci humaira. Hankalina ya tashi saboda ganin yana neman haddasa min fitina da tashin hankali,wanda zai haifar min da rashin zaman lfy. Rai a 6ace ta kalle shi,tuni ya maida hankalinsa gare ni. Haba yarima,me yasa kake neman gwasale ni a duk lokacin dana ke kokarin nuna gwaninta a wurinka? Shekeke ya kalle ta cikin izgili yacekarya ki ke,dan da baki baza borori a kaina ba... Ni kake karyatawa a gaban BAIWATA? Shin zuwa kika yi neman tashin hankali da neman rigima,ko kuwa gaisuwa ce kika kawomin da gaske? Ya fada yana mai kare mata kallon raini. Ta sassauta murya,tace. Zuwa nayi in faranta maka rai saboda... To ki bi abinda nakeso,bana son shisshigi,nan sashena ne ina da ikon yin duk abin da naga dama a harkokkin gidan,sai ki bari ranar da naje inda kike irin duk yadda kike so shi zan bar kiki aiwatar. Ya na gama fadin haka yace. Zo ki bani BREAK humaira. Jin Gimbiya tayi shiru yasa na dukusa ina zuzzuba masa,sanan ita ma na hada mata tayi min wani mugun kallo,kafin tace. ,Sanya ki nayi? Shi kenan ya janyo min abinda nake gudu! wammamn mgn ita kawai nake maimaitawa a raina,kamar nayi ta kurma ihu. Ta daka min tsawa. Ki kayi wa mutane tsaye munafukla,wuce ko na harfe ki da kafa,mai kama da aljannu!!! Wannan kalma tayi min zafi,sai kawai naji kwalla sahr! Shi ma ya fusata yayi mata tsawa. Tsawar danaji har cikin raina,saboda na san fitina kawai zai kara janyo min,yace. Kiranki nayi,ko na aika miki da katin gayyata?don me zaki zo ki haddasa min fitina? A hanzarce ta dube shi daidai lokacin na bar falon,amma duk da haka ban daina jin amon muryarsa ba,yana balbala mata masifa. Daga jin muryar kasan kuka take son yi. Yarima zan hadddasa maka fitina da BAIWA? Mene alakarka da ita?shi yasa na lura kana yi mata wani kallo na daban? Ke!kada ki kullan sharri... Ta mike tsaye tana fadin. Lallai zan dauki mataki a kan wannan,domin bazan ta6a daukar rai ni ba. Na juyo karar buga kofa alamar ta fita na rushe da wani irin kuka. Ba motsin dana ji kawai ba,turarensa maya ganar dani cewe shine ya shigo. Kukan na mene ne?saura kadan na dauko ta6arya na kwada masa don takaicin wannan tambayar ta rainin hankali da ya wurgo min. Zaki yi WASTING hawayinki a wofi, domin ita ba Allah bace da zaki damu kanki daon tana ganin kin yi mata laifi.saboda hauka da tsabar son kai ta mance ni ne mai laifin,ko kuwa fib karfi take son nunawa?kizo muje muyi kalacin kada yunwa... Na dora hannu saman kai na kurma ihu,ina fadin. Ni kam kana neman haddasa min fitina alhalin ni din ba wata bace,iyayena ba wasu bane dazu su kare min. Da sauri ya bar kicin din ganin alamar su Rabi na da niyyar zagayowa ta baya. A rude suke,kuma a kaidime gaba daya har da mutuminsu suka hada baki. Lafiya 'yar fulani?sai a yau na san wannan suna ashe haka suke fadamin idan bana nan,ko suna kwatancena. Na dago kaina jage- jage da hawaye. Don Allah rabi ku yafe min abinda nayi muku iya zaman da muka yi,karshin zaman gidan nan yayi. Ta dube ni kamar ita ma zata yi kuka tace. Wallahi muba kiyi mana komai ba yaushe ma mgn ta hada mu ballantana ki 6ata mana rai?laifin me kikayi wa yariman? Zanyi mgn ya shigo duk suka tsorata tare da ja baya suna kame-kame. Humaira zo ina son ganinki. Ya na fadin haka ya juya. Rabi ta matso tace tashi kije watakila yafe miki zai yinaga kamar yana tausaya miki. Ni ba zan jeba. Duk suka zabura da fadin. Kin yafe aikin ne? Nace,Ai yazama dole,saboda wacece ma keyi domin ta ita ya hada min gwarmai(rigima) a wurinta. Bamu gane ba. Inji harira. Na fada musu badakalar da ka yi yanzu a falo,duk suka hada baki suna INALILLAHi. Yau ke kin bani. Allah ya tsare ki da shiga wakafi don da wuya idan baki yi yariba. Na rushe da kuka cikin wata irin kidima. Zubairu yayi dan tsaki tare dayin kasa da murya. Ba zata yi tari ba,domin yarima SON HUMAIRA yake yi!!! Duk muka kwalala masa idanu cikin firgita abinka ga dan duniya sai yayi murmushi yace ,Wallahi na fahimmace haka tun ba yau ba. Saboda haka kada kiyi wa kanki salalar tsiya,arziki ne ke binki. Ya kara yin kasa da murya. Don Allah humaira kin san ya mu cikin barorinki?mu kam daman Gimbiya...tishe kunnuwa na nayi tare da fasa wata irin kara. Yarima muka gani tare da dka musu wata irin tsawa yana mai korarsu,wai sune ke kara tsoratani. Ina kallonsu ta bayan taga sun la6e. Shi kuma ya fara magana a hankali. Rigimar Gimbiya humaira yawa gareta kullum da abin da zata tsiri. Fitar nan da nayi wurin mahaifinta ta kai ni kara,wai na fifita ki a kanta,kin ga duk ta zubar da kimata wurin iyayenta. Yanzu hak na baro tana mgn da mahaifina,ban san abin da zatace masa ba,ta 6ata ni gurin nawa. Ta durkuso,sannan yaci gaba kiyi min mgn na sami saukin abin da nake ji azuciyar ann koda kuwa ba mai bdadi bane. Kada kiyi fushi dani a lokacin da nake bukatar taimakonki. Lokacin ne daba ni da wani gata sai wanda kika bani a matasayina na marayan Allah. Kamar na shake yarima nake ji,sai kawai na kara fashewa da kuka. Yau ni HAMEED na gata kaina! Sai kawai ya fice. Na duke ina shawarar na tafi yanzu ko kuwa na bari loacin ya cika? Ban karasa yanke hukunciba naji an fizge ni. Na dago kai sai kawai naga yarima ya rike hannuna. Dukewa kawai nayi ban dagi ba,sai da naga mun shiga sashen Gimbiya kawai sai na kara maida kaina kasa. Shin dukanta zai yi?cin mutunci ko kuwa? Ganin mun doshi dakin kwananta ya samya nayi hanzarin kallon shi. Naku ANaM Dorayi Amadadin Zainab Dahiru Wauw nakecewa muhadu a kashi na 2 Subul da baka 2 page 1 Posted by ANaM Dorayi on 07:10 AM, 21-May-15 Under: Subul da Baka Kwance take rub da ciki da gani tana cikin damuwa mukayi sa'a ba kowa da gani korarsu tayi. Ya jefar dani gefe ya isa bakin gadon tare da tallafota ya tada ta zaune kallon da take masa me dauke da mmiki, sha'awa tare da tambayoyi masu yawa ya durkusa gabanta yace fareda ki gafarci yarinyar nan ta tsorata da fushinki ki yafe mata domin kaunar da muke yiwa juna. Kallo daya zakayi mata kasan ta fara rasa hnklnta don hk tayi saurin kallona tace na yafe miki Humaira dama bakiyi min komai ba, idona shabe-shabe da hawaye saiga murmushi ya subuce min. Ta maida kallonta gareshi dahra tym din bai tashi dg durkusonta da yayi ba saima kallonta da yake yana smiling na tuba nima a gafarce ni amaryata kuma gimbiyata... Ban jira amsar da zata bashi ba nayi waje tare da karayin godiya da goge hawayena kowa ni yake kallo sbd ta gabansu muka wuce, banga su rabi ba don hk na wuce dakin kwanansu don na gyara gashi lokcn ya kusa. Ko rabi banyi ba ya shigo har kewayen na kalleshi tare da banko min harara kinsan Allah yau saina kai kararki ga inna na gaji da irin salon rigimarki wllh. Na mulmula maganar tare da lailayata kafin nace rigima ta wuce irn naka kuma kafin ka kaini kara nizan fara kaika In Shaa Allah. Haka kikace? To bari

Chapter 4 of 11