Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
11 / 11
shiri sai ga shi ya shigo da sauri ina zaune bisa kujerar gaban madubi. Humaira am sorry kano zanje yanzu aka aiko maimartaba baban gimbiya bashi da lafya har zaa fidda shi waje shine zan kai su umma suyi masa allah ya kiyaye hanya yanzu haka gasu chan suna jira na. nan da nan halin namu ya motsa wato KISHI wani kallo na fara jefan sa da shi tukun kafin nace "duk gidan ku a rasa direba sai kai?" abin mamaki sai naga kamr ransa ya baci. "haba humaira ina laifi dana ma zo yi maki bankwana da kiji cewar na tafi ba?" yanzu haka na fada maki ga su maimartaba can a waje suna jira na idan ba ke ba wazan wa haka?" ai naga kana ta faman kyarma ne zaka gdan surukai" kema haka ake kyarma idan zaa gidan naki.... maganar ta maqale daga karshe alamr SUBUL DA BAKA yayi. in shirin maida masa sai kawai ya fice, wani gululu ya taso min. Banyi barcin kirki ba ranar, kagara nake ya dawo na amayar masa ta cikina. haka abinci ko ruwa na kasa sha. har yarima ya is aya wulalantani abinda kawai nake nanatawa araina kenan. kwance nake daki naji shigowar sa na mike tsaye tare da rike kugu yana shigowa ko rufe kofa beyi ba na hau masifa daman ance me shiru-shiru be iya fada ba. "da zaka fada min magana kan wata banza na taba aiken ka zo?" ko kuwa na taba aiken ka wajan uwata....." haba humaira wai maganar bata wuce ba?" toh kiyi hakuri ni da wasa na fada."eh din ai da wasan daren ake fadawa wawa magana. "duk naji kiyi hakuri dan allah wai dole sai ka zuna da ni ne?nace bana yi ko dole ne? ya kyakyale da dariya dama na lura sai gumtseta yake yi. Raina ya kara baci wato ya maida ni mahaukaciya sai naga ya fara rawa yana waka 'ashe ana kishina ana kauna ta, a'a lallai yarima taka-taka' Ban san lokacin da nima na kyalkyale da dariya ba,saboda ko waye sai ya dara idan yaga yadda yarima ya dage yana kwasar rwa. ya daina rawar tare da daure fuskar nan irin ta shagwaba. "gaskia ni dai a cigaba da fadan bana so a daina " ni dai na cigaba da murmushi, yana matso yana yar dariya "muguwa na gane ki ashe haka nan ake wani basar wa kaunar yarima tayi katutu a rai?" nayi murmushi "eh din an ji" ya rungumo ni "me aka ajiye min?" ina shirin bashi amsa wayar sa tayi kara ya zura hannu, sai naga ya sake ni da sauri ya latsa tare da sanya handsfree yayi kasa da murya "Allah ya taimake ka" "zancen banza zancen wofi, yanzu nake jin labarin ka raba gida, wannan ai shirme ne lallai ka hanzarta hade matanka waje guda tun kafin raina ya baci,yaushe zaka iya adalci matukar basa tare? anya kai jarumi ne yrima? ba ka iya daidaita matanka?oh allah wadarai a yau nake so ka maida wacce ka ware maza- maza. yana gama fadin haka ya kshe wayar. Gwaram! na koma na zauna tare da dafe kaina . ya kalle ni "kiyi hakuri sai ki tashi mu tafi kar abin yazo da bacin ran sarki" Wayyo ni humaira Wayyo Allah na. Tunda muka fito gbana yake faduwa ni na tabbatar idan aka auna jinina a yanzu ya kai dari biyu da wani abu. har muka isa ina rike da kaina shi dai bai ce komai ba. Komai yana yadda na barshi su rabi suka shigo min da akwatuna na. Nayi tsaye sai zare ido nake ina kyarma ya shigo da sauri. haba humaira duk kin bi kin tada hankalin kan waccen yar iskar. Bai rufe baki ba sai gata "Don ubanki har kina neman raba ni da shi bayan kin samu kin shigo?" Bata rufe baki ba ya wnka mata mari uku a jere,sannan ya kwale belt ya fara tsula mata ta duke kawai tana kuka tana faman karewa. Na rike shi "dan allah ka kyale ta,wayyo ni humaira" na fada ina kuka. bai saurare ni ba na janye shi baya ta sami halin mikewa tsaye ta nuno ni da yatsa "wallahi sai na rama kanki shegiya" zai kara damko ta tayi waje da gudu. tana fita yaranta suka boye saboda duk sunji abinda ya auku. ya kalle ni a fusace "Haka zaki yi mata duk ranar da ta kara zuwa miki ida yar iska" ni dai a sukurkurce na kwana,washe gari ya fita da wuri saboda zai je tiyata. na kulle kaina a daki har kusan karfe daya saura sai da yunwa taci karfina sannan na fito. "Rabi dan Allah kawo min tea" tace "to" tare da juyawa. ni bana sha'awar wani yayi min aiki amma babu yadda na iya saboda masifar gimbiya. Ganinta nayi kamr an jeho ta, nayi saurin mikewa tsaye ban ankaraba ta rufe ni matsiyacin duka na dinga kokarin rugawa amma ta babbake ta hani ni wucewa. Tun ina motsawa har jikina yayi tsami ni dinga rizgar kuka. Sai da ta barni kwance tukun ta fita. Rabi ta shigo dauke da tire duk jikinsu yayi sanyi "Sannu ranki shi dase,sannu!" Dagwayye ta fada lokacin da ta ke kokain daga ni ta maida bisa gado. Rabi ta kalle ni "Wallahi sai kin tashi tsaye gidan nan lallai gimbiya kwararki za ta ci gaba da yi dan bata fi karfin ki bakawai kin sawa ranki tsoro ne" Shiru kawai nayi masu, fuskata tayi jawur saoda duka ga shi gefe daya ya kumbura . Na samu na kurba ruwan tea din sannan na sallame su. karfe udu yarima ya dawo hankalinshi yayi mugun tashi. "Himaira lafiya me ya same ki haka? na langwabar da kaina sai kuka. "Badai fareeda bace ko?" me tayi maki?" nan ta shigo"?Duk ya kidime ya rude, nayi saurin girgiza kai "Faduwa nayi a bandaki silbi ya kwasheni...." Subhanallahi, Rabi,Rabi!! ya daga murya kamr ba shi ba sai gata da gudu "Don me zaku rika wanke toilet ba ku gogewa? maza je ki tsane duk wata lema da ke ciki". sumi-sumi ta wuce. "kin sha magani?" na girgiza kawai saboda jikina ya gama yin tsami. wannan fitina har ina? cikin wata tara amma be hana gimbiya tashin hankali ba. Da Allah ya tashi taimako na sai gashi washe gari ta haihuwa da karfe uku na rana. A yadda su Rabi ke fada min tunda aka ce mata mace ce take kuka har suka bar asibiti. Nayi murmushi saboda ni farin cikina na samu sauki.Abin karin tashin hankali sarki yace a bar yarinya ba ai an kaita fada ba. ni dai ina bangarena, wanda ya shigo maraba wanda be shigo ba bana neman sa. Hidima aka yi sosai an sha shagali ni ma ba'a barni a baya ba, ko leke ban leka bangaran gimbiya ba. yarinya taci sunan Fadimatu Zahra'u. *** ***** ****** Maryam yar uwar yarima ce, jininmu sai ya hade da ita kwarai dan a daki na ma take kwana ita da wasu yan tawagarta. Bayan suna da kwana biyu na aiki rabi gurun su umma ta kai masu abinci, ita kuma dagwayye na baya tana wanki, sai ka gimbiya a harzuke. "Toh munafuka an fada mana kina tsalle kina murna an haifa mace,to dan ubanki matsiyaciya ke ko haihuwar ma baza kiyi ba" Na zaro ido cikin tsoro da mamaki nace "Wa? Ni? Wallahi billahi karya....Ban rufe baki ba naji saukar wani lafiyayyen mari. "Ni zan maki karya shegiya?" na dafe kunci. "Wallahi ban ce ba,haba ya zaayi?" ta kai min harbi a cinya har sai da na tsugunna. "Dan allah gimbiya kiyi min rai.wannan masifa ta ishe ni, wai ya kike son na yi ne? Me zan miki ki kyale ni?" Ta harzuko min "Ina son ki kyale yarima ki fita rayuwarsa ko kuma wallahi na kashe ki na kashe banza" Na rushe da kuka. "Yace bai sakina,bai kyale ni..." "Daure ki akayi da baza ki tafiba makira?" na baki kwana hudu idan ba ki bar gidan nan ba wallahi sai dai uwari ta sake haifo wata mayya kawai". Tana fadar haka ta fice. "Dole na bar gidan nan" na fada a sarari tare da shiga daki ina laluben waya. Ban ga laifin gimbiya ba saboda gaskia ta fada,ba'a daure ni ba, gidan nan dole in kama gabana kwana lafiya yafi. Na dauki waya na latso number Amira, bugu daya ta shiga,ringin biyu ta dauka."Ta yarima ba da kanki a sare" kirarin da take min kenan a kullum da ta dauki wayata,ko da kuwa ita ce ta kirani ina cewa hello zata fadi haka. "Hmm" Na fada kawai. tace ya akayi mutuniyar, hmmm humaiki kimin magana na sani... AMeera guwa xanyi, saboda me?? Nakwashe duk yadda mukayi da gimbiya nasar daita, kinga tunda har tabani zabi gara kawai... Ta kunduma wani zagi lalle humaira agaisheki, wallahi yau nakara tabbatarwa cewa saunace ke, haka zaki zauna tana cutarki, lallai ki kwatarwa kanki yanci tunda wuri, nayi mata me?? Nafada ahankali, kiwanka mata mari kuma ki tabbatar mata kindaina jin tsoronta.. Hmmmmm.... Nafada kawai, au bazaki iyaba kenan?? TO wallahi karki kara kirana akan matsalaki. Idan azaba ta isheki seki nemawa kanki mafita ameera ina gudun kada aga zakewata kituna matsayina da tushena kada naje na debowa kaina masifar dazatafi karfina. Fada zakiyi ne? Nace fada zakiyine? Bata hudo miki dazuwa miki idan yarima baya nan ba? To kidaki shrgiya kuma kiyi shiru muga idan zata fada. Nasaki ajiyan zuciya, to ameera nagode. Zan jarava, nayi agumi, wannan jarabar dayawa take. Atunanina taga banida halin fitane yasa takara dawowa, wannan karan ma tsautsayi nafito kenan bawa dagwaye zanin gado, tana shigowa tamaida kofar baya ta rufe, gabana yafadi, na fella da gudu zan fita ta kofar baya tarigani isowa tana kokarin kullewa, kafin in ankara, ta shako wuyana, tana neman makogwarona, har ga allah bani niyyar fada da gimbiya amma danaga tana neman rabanida raina, bansan sanda na wancajar daita ba abinka dame hakuri nayi zuru!! inna kawai nake tunawa idan gimbiya bata tashiba, nafashe da kuka nashiga uku! ashe surabi da yaran gimbiya suna tsaye kaina bansani ba seda naji daya tace..hakanan zaki tada hankalinki dimin ko kotu akaje bakda lefi, saboda taddaki tayi har gidanki, nayi saurin daga kai. Wallahi nibansan naiya fada haka ba hasalima nibanida abokin fada aduniya. HAba gimbiya munsani aim duka danaji banbarakwai sena daure nace gashi yanxu tajanyomin batacciya, ina fadin haka wayata tafara kuka inadubawa naga yarima, bugun zuciyata ta karu batare dabace kimai ba nakara akunne na hello humaira.. Hum nafada,, kina gidane, huum nafada ahankali. Lafiyarki kalau koh ko akwai abinda farida tamiki? Babu nace atakaice, kin tabbata? Um. To me kika wa mata tayi irin wannab dogon sumar? Sena fashe da kuka ina fadin tsautsayine wlh, itace ta hayemin da fitina taki ta kyakeni, bace mata vanason fada tunda namata alkawarin zan barmata kai kamar yadda ta gargadeni, mtschw, sekuma ya ajiye wayar. Haba ranki yadade dan me zaki tada hankalinki tunda kunfara kwatarwa kanki yanci, walh kidage kiyi maganin gimbiya, aikinmayi kokari. Sannan duk abinda kikewa yarima na kyautatawa karki fa, dole ki rashi ki kwatan wa kanki yanci, Allah ne yabaki babu me kwace miki, mutunciki yasuya miki duk wannan darajar. Shiru kawai nayi ina saurarinsu idan wannan takai aya se wannan ta cabe. Karfe 4 yashigo da kasaitarsa, ina falo yashigo duk nayi firi firi. Kallo 1 yamin yakawar dakai. BAn ruwa insha yafada batareda ya kara kallona ba. Ina bashi yahada da hannayena yajanyoni jikinsa. Wai lafiyarki haka, duk kin wani firgice, meya hadaki da farida amma babason kuka yafada saboda ya lura idanuna sun cika da kwalla. Batareda na boye masa komaiba na zayyana masa jomai daga farko har karshe, yaja dogon tsaki, aidama seda kowa yayi zaton haka. Musamman da sahabi yabada shaidar nan ya kwashe tashi yasa ran maimartaba ya baci yayi min fadan da babu gaira, wai bani adalcine shiyasa, har yau yakasa gane rashin tarbiyyar yarinyar ne, har yana barazanar babu wacce zan rabu da ita cikinku. Dle indaidaita kuzauna lfy, bansan lokacinda nace tabdi ina!! Yayi dariya, kina ganin dawuya ko, nasunkuyar da kai, ai ina hango matsalar ne. Kuma wlh me sauki ce, kinsan meye saukin? Na girgiza ka, kece zaki bi min daita, Allah yaga zuciyata ba nayi miki haka bane da niyyar ina tsoronki kema, nandai baa kano bane balle in nuna miki karfin mulkin sarauta, ita ma a karkashin wata masaraurar take dole tayi biyayya. Nace to. Bani abinci inci, zankoma asibiti. Seda nabari yagama sannan nace ko inzo muje nima indubota. Yayi murumshi, ai harta dawo bazakije ba, kuma ina gargadinki da wannan tausayin kiboye shi koda tadawo kada ki nuna mata dan zata kara samun wata barakar. Amma idan kika shareta lalle zata fara tsorata da alamuranki. Shiru kawai nayi ina mamakin irin wannan zuga ta yarimam shi baze kashe wuta ba sedai ya rura? Nifa anawa tunanin kenan, kullum sauraron dawowarta nake, sgikuma innatanbayeshi yaushe zata dawo seyace min tana can dai, nama amira waya danneman shawarta ga mamakina duk magabar dayace irinta yarima. Haka na santawa sarautar Allah ido ina sauraron dawowarta. kwana2 natashi banajin dadin jikina raina yata baci zuciyata tana zafi, tun bandsmu ba har abin yafara bani tsoro, inyita neman fada dashi amma baya yarda yabiyemin, ina zune afalo naji hayaniyar dawowar gimbiya, banji faduwar gaba ba kamar baya, shuru bata shigo gidana ba kamar yadda nayi tsammani har kwana 4. Ranar jumaa yakama agidanta yake bayan yadawo masallaci yakawo min huduba wadda yake tagomin daita duk sati. Lokacinda yashigo ina wanka seda yajira nafito sannan. Ashe tayi zargin wani abu, bayan yafita nakoma daki ina gyaran wadrobe kawai naga mata, waike dan ubanki me kike nufi ne? Dane kike takama banza talaka? Bansan lokacinda nacire dankwalina nadaure kugu na daura hannu duka2 abinda kike nufi nima shinake nufi kema dan ubanki, tazaro ido cikin mamaki, nikike zagi? Anzageki koda abinda kike ganin zaki iya? To bari infada miki bani tsoronki, ko kifitarmin gida koyauma kiy kwana asibiti, koki bakunci lahira don lallai cikin 2 nan se anyi 1. Sakarai wadda batasan abinda takeyi ba, ke baki zauna lfy ba baki bar wani yazauna lfy ba, a sarautar da kike takama dashi raini da rashin tarbiya ne salon mulkin naku? Ke ko kunya bakiji, agaban baroron dakike mulka mijinki ke dizgaki saboda dakikacinki har dukanki yakeyi amma kinkasa yiwa kanki karatun tanutsu? Ni diyar talakawan dakika raina gashi nazo nakwace fadarki awurin iyayen mijinki dakike taka suna sonki? Kingani riba 2 goma da ashirin, dan haka kirika addua Allah maji rokon bayinsa ne. Nizaki fadawa Allah?? anfada miki farida ko da yadda zakiyi dani ne? Na matsa kusa daita, ina jiranki! Ta girgiza kai, lallai zaki raina kanki ta juya tafita. Na fincikota ta baya kedin banza aisedai ji raina kanki a gidan nan, kuma daga yau zaki gane shirun da nakeyi a baya ba tsoro bane, zaman lfy ne nake neman amma tunda kinkasa ganewa shege kafasa. Sakar min riga tafada tana hararata. Na ingizata baya tareda rufe kofa ta. Nadafe kirhi, oh waini yauke zazzagawa gumbiya masifa tayi shiru? Lalle yau na gano abinda amira da yarima ke nufi, ban fada masa yadda mukayi daita ba danko nuna masa tazo gdan banyi ba. Da marece muna kwance kan gado abinka da lahadi na langabe ina shagwaba. nidai yau sonake muje baya musha iska, zaune yatashi zumbur me? Namaimata ya watsa hannu ok lets go. Cikin raina nace aikaji shi komai turanci idan zaa kashe ni ban iya fassara abinda yake nufi, amma dai nafahimci abinda yake nufi, na umarci abimu dakayan marmari, ni nariga nabashi abaki musamman dana lura tagan gimbiya abude. Shikuwa yana mamaki amma isa da miskilanci yahana ya nuna min. Yana gamawa nace to yagoyani yayi yawo dani cikin lambu, zauyi gardama nafara dira dira ina shagwaba irin na yara idan akaki musu abu. DUK ya rude ya diririce koda ya sureni yayi zagaye 2 dani se yayi cikin gda da gudu, ALlah yatemakeni su rabi duk suna sashensu. SEya kasance duk ranar aikin a lambu muke wuni gashi bayan dakin Gimbiya ne duk abinda yake faruwa tana ji wannan abu yana kona mata zuciya. Da wani yammaci ne su Rabi suka kawo min 'Yar gidan Gimbiya raino in ji Yarima dan na saba da 'yar shi, naji tsoron karba ma saboda kada wani abu ya faru a zarge ni, su Rabi suka ce dani dawani abu yafaru muzamu zama shaida agareki. jn haka yasa na mi,a hannu na amsheta, tun daga ranar kullum se ankawo min ita nima haka nake aikowa daita idan har tayi kuka ban taba yarda naje gidanta ba. ranar da yarima yacemin zeyi tafiya be fada mun inda zeje ba ranar baa kawo hauwau ba na tura rabi wurin yar aikowan karta bari gimbiya taganta taji ko lfy? DUK naji babu dadi musamman daaka kwana 2 ana na 3 ne ina dakin yarima ina gyarawa dayake ranar zan amshi girki, senaji ana kwankwasa kofa, atunanina cikinsu rabine senace shigo mana menene. Ahankali tabude kofan gavana yafadi yau kuma dame tazo don Allah kifita ke bakijin komai kullum masifa ke kawoji gidana amatsayinki na babba?? Ta girgiza kai senaga kwalla sharr duk se jikina yayi sanyi. AHAnkali tafara magana, zuwa nayi inbaki hakuri akan abibda yafaru abaya sannan inmiki bankwana domin nafahimci lalle yarima kaunatace bayayi. Tunkafin na aureshi nake shan wahalarsa gashi har yau ban taba jin wani dadi daga gareshi ... Kai dena fadan haka halinki shiya janyo miki wannar tsanar kuma laifinki ne, tun farko kinfahimci baya sonki kamar yadda ake tilasta aurenki gareshi, memajon kidage da biyayya da kyawawan dabiu se kika nuna ke YAR SARAUTA ce alhalin shima haka gaba da baya yanzu haka dazaki gyara halinki yarima me saukin kaine aidakyarne, domin nitunda ya aureki be karayin kwanciyar aure dani ba, setayi shiru da alamun SUBUL DA BAKA tayi seta bani tausayi saboda yadda duk ta sukurkurce akan nadamar datayi, setaci haba dacewa rashin iya zancena da yadda nake magana cikin gadara yasa yarima yakara tsanata iyayena danake samun sauki awurinsu sun tsanenu, kedin danakeyiwa kinkai karshe. Seta fashe da kuka hakika shaidan ya rivace ni laananne, Allag shiyasa shiyasa na yanke shawarar hakura da yarima dan baze taba sona ba. Injiwa? Nafada, walh inda dagaske kinyi nadama gumbiya yarima ze kaunaceki, nikuma zanyafe miki duniya da lahira nima kiyafe min, tashare hawaye, ga mamakina sebaga ra tashi ta tayani gyaran dakin, dakanki kikeyi ina masu aikin?? nayi murmushi aini da dakin mijina da abincinsa bame tayani, nike gyarawa nayi masa girki da kaina. DAgas? Nace Allah. Lalle zan dunga zuwa daukan course. SAi magariva takoma gidanta. Kamar inva yarima lbr sebati shiru dan ze iya gwasalebi koya karya mata tsari. Washe gari wajen 11 segata da hauwau muna falo muna karin kumallo. Kida tashigo setayi turus shikuma ya daure fuska. Alanar sarautar ta motsa, nati kamar ban lura dasu ba namike ina yar dariya oyoyo hauwau. Nakarbeta tamiko min ita dama ita nakawi miki. Tajuya zata kima sena kamo hannunta Ai tunda kinzo sai munyi karin kumallon zaki tafi. Da alama taji dadin hakan saboda batayi gardama ba shi kuwa wani irin kallo yake yi mana cikin tuhuma da zargi. "Ya akayi, mene ne haka?" Cikin zolaya na kalleshi. "Yo mun shirya da Yayata..." "Mtsss" kawai ya buga tsaki tare da mikewa zai bar wurin. Na sha gabansa "haba Yarima, mutum yayi laifi har ya gane ya tuba amma..." "Kin tabbatar da gaske take, ko sharrin wannan ce kika manta?" Kafin na kara magana ta zube kasa tana rokonsa har da kuka, ni ma sai na kama kukan saboda tausayi. Kai rayuwa abin tsoro ce, Allah ka sa mu dace, amin! Ganin munyi masa rubdugu yasa yace, "shikenan komai ya wuce". Yana fadar haka yayi ficewarsa babu wacce ya tsaya ya lallasa. kusan kwana uku bai dayaye ba, sai da na ringa lallashin sa da ban magana, sannan yake zama muna hira saboda ko girkinta ne kullum da marece tana gidana, har hakan ya zame mana tamkar zaman majalisa. Maimartaba kuwa har kyaututtuka ya aiko mana da su. Da muka tashi zuwa kano tare mukaje da ita har gida ta roki Inna gafara. Zama ya koma mana gwanin dadi, ashe duk neman fadan da nakeyi ciki gareni, mukaje Yarima yayi min scanning sai ga namiji, kullum addu'a ta Allah ya sauke ni lafiya. TAMMAT BI HAMDULILLAHI. nanmuka kawo karshen littafin subul da haka 1,2&3 amadadin Zainab dahiru wauwo ( zeedee)***naku ANaM Dorayi kemuku fat an alkhairi saimunhadu a Novel nagaba Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 11 of 11