Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 11
ko kallonsu banyi ba nace Allah ya ganar daku, wata irin yunwa nakeji na debo kalaci cikin wanda ya rage a bakar leda dankaline da kwai na tafi can baya na zauna inaci kamar daga sama na ganshi wani irin kallo yake min na tausayawa yace donAllah zauna kici kalacin ki na zauna amma na kasa cigaba da ci, a gsky baki kyauta ba dama baki kalaci ba ki hau aiki tun safe sai yanzu kusan karfe daya da kwata? Ya karasa zancen yana duba agogonsa, Nayi dan murmushi wllh na karya tun a gida yanzu ne dai na dan jin yunwa, bai kara mgn ba ya wuce abinsa. Suna zaune shi da gimbiya a saman wasu kujeru na fito da shirina cikin wata kokakkiyar atamfata kafata sanye cikin kodadden silifas da hijabina har kasa na wuce su ina ga yau ce rana ta farko dana taba tafia gida ya bini da kallo harna tsargu, gimbiya ta ware murya ta kirani na taho da sauri na zube gabansu tace yarima yace ku ba'a koya muku bankwana bane? Kafin nayi magana gimbiya ta surfan zagi dama bakice masa zaki tafi ba ko yana bukatar wani abu? Jikina ya dauki rawa yace tayi min bankwana dazu yanzu ne dai batayi min ba (Allah Sarki yarima bai san za'a zageta ba) kana bukatar wani abu ne da zata yi maka? Yace a'a to meye nayi mana wani bankwana keyi tafiyarki, sai naji yana dariya nidai har tuntube nakeyi don sauri ina isa natarar da inna sun shirya cikin kayan da basu da wata nagarta tausayin kanmu ya kamani nace sai ina kuma inna? Tayi murmushi tace ai nayi babban kuskure na manta yau ne ake bikin Harira yar gidan babanku Auwalu raina ya baci amma na kasa nunawa sai nace shine zaku tafi yau baku hakurin gobe? Ta dan harareni suwaye masu aikin abncn idan ba muba? Nace kai Inna har yaushe zaki dinga wahalar da kanki akan wann mutanen da basu san ciwonki ba cinmu da shanmu da suturarmu da uwa uba karatunmu? Ai ba 6angaran dahuwar zan tsaya ba,kinga akwai gyaran kayan miya,yankan albasa,alayahu,fere ka6ewa da sauransu".na ta6e baki kawai.na sauya maganar da cewa,"cikin satin nan naji ana cewa za'a biya mu saboda haka gaskiya inna har dunkuna sai munyi". Kuruci dangin hauka,in ba hamaira ba yaushe ana ta ciki za ai ta tsumma?Allah dai yakawo albashin lfy,biyan bashi dai shine farko idan Allah yaso". Nace,"Amin". Na fiddo abincin da nazo dashi,suka ci suka yi kat,sannan ta mike,"kiyi kokari ki lega gurin 'yanmatan kafin lokacin islamiyyar". Da kai kawai na amsa mata. Ta yi murmushi,"mgn ku,a ta kulle?" Na dai yi shiru."Don Allah kada kije kiyi wannan miskilancin cikin jama'a,ki saki jiki wani abun daurewa ake yi". Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 Subul da Baka 1 page 2 Posted by ANaM Dorayi on 06:04 AM, 21-May-15 Under: Subul da Baka * Na dai yi murmushi kawai ta fita tana fadin."Hali zanan dutse".na dan watsa ruwa sannan na fiddo wasu riga da siket a sosassen leshi wanda akalla zai yi shekaru 4,yana 1 daga cikin na ganin sarki wanda nake takama da shi. Na yayyyafa masa ruuwa tare da bigewa saboda cikwikwiyewar ta tashi.farin gyale duk. Ya tashi saboda tsufa na yafa,sannan nasaka takalmin robata na zuwa biki,ko suna ruwan hoda. Na fito tare da jawo kofar gidan nadan sanya tsinken kara da dan icce gurin hancin na kulle kamar yadda muke idan zamu fita tare da kudurtar insha Allah da an biya mu kudi zan sawo mana kwado. Tafe nake kaina a kasa na wuce gungun samari kusan 5,kwanar karshe da zan bita kai ni kofar gidan nayi karo da wata majalisar. Na dan gifta kadan na ji wani yace,"kai yarinya har yarinya amma ba galihu".karaf naji wani ya amshe,irinsu kuma sai shegen girman kai na banza, waccan yarinyar ita ake yiwa kirari da danwake kafi ubanka,a unguwarsu gidansu na dan nesa da na su ibrahim balarabe,an ce girman kan tsiya gareta saboda..." Maganar tayimin nisa,ban karasa jinta ba na shige gidan kawai inda sabo na saba da irin wadannan maganganun bakin samari,shi yasa bana mai da kai.dalili kuwa shine ina yawan yin samari da farko,amma duk wanda zai zo sai ya yi amfani da talaucinmu ya nemi yi mini maganar banza,korar karen da nakeyi musu ne yasa suke yi mini shaidar mai kashin tsiya,kuma girman kan tsiya gareni,sannan danwake ce ni. Na kan yi mamaki,TALAUCI HAUKA NE? Ina ganin tsira da mutumcin 'ya mace shi ne babban arzikin duniya da lahira. A nawa fa tunanin. Kamar duk lokacin da hidima ta tashi a kullum muna raku6e gefe,haka ma wannan lokacin.zaune nake kusa wasu tsofaffin maroka ina kallon kowa yadda ake shagali bare wanda bai hada komai dasu ba,ya fi ni sakewa da gata saboda BABU.... ,Babu wacce ba ta ganni ba,amma ko kallon arziki har aka kira la'asar ko ruwa na shiga nace,"yaya harira sai Allah ya kaimu". Tayi watsi kamar ba taji ba,na kara maimaitawa,ta daka mini tsawa,"naji". Na juya cikin abokanta naji wata ta ce "kin sallame su?" Ta ce,"wa?" Ta nuno ni da yatsa,"ba 'yar marokan can ba ce?" Na dan juyo dan kallon wacce ta yi maganar. Ta yatsina fuska, "wai 'yar uwarmu ce". Dayar na zaune da waya a hannunta tana latsawa tun shigowata ta kyalkyace da dariya,tare da fadin,"shegiya harira,wato wai ma ne?" Gaba daya dakin ya dauki shewarsu,ni dai na yi waje ina mai takaicin irin wannan salon wulakancin,a ce duk sabga da salon irin wanda za ayi mana? Dama waecan karon an kira inna da 'yar aikin gida. A tunanina zan tarar da su inna su ma sun dawo saboda zuwansu Aisha islamiyyar,sai na ga cewa ba su dawo ba. Na dauki littatatfaina da hijabi bayan na gama sallah na fito... Shekara 2 da suka wuce nayi saukar alkur'ani,yanxu ta 2 zanyi,wacce nake hadda,ga shi na gama littattafai da dama kamar su;ZADUl MUSLIM,HAKKUL MUBIN,KHAMSUNA HADITH,HUSNUL MUSLIM,BULUGUL MARAM...kai za su kai 12 yanzu wasu sabbi muka shiga irin su,ma'anar addu'a da fassarorinta,tarihin Annabawa da kissoshinsu,da sauransu. Acan na tarar da su sumayya suka ce daga gidan bikin suka taho,inna sai anjima na kada kai kawai cikin raina nace ba ta gama bautar ba ko? A gida muka tarar da ita bayan mun tashi da nairarmu 300,wacce aka bada sadaka wani bawan Allah ne ya kawo.tun a hanya na siyo mana taliyar leda daya,naira 110.magin 20,gishirin 10 sai mai na 20 kwanti. Na san muna da dan sauran busassen tattasai muka rago 150,su Aisha sai tsalle ake yi gobe za a yi kalacin koko har da kosai. Ba karamin dadi wannan labari ya yiwa inna ba,na ba Aisha ta siyo mini icce na 20 ashanar 5. Nan da nan na dora dafadukat taliya.saboda rashin kamawar iccen ya sanya ana kiran isha'I na sauke. Bayan munyi sallah na zuzzubawa kowa na gyara wurin na kauda duk kayan da na yi amfani da su,sannan ni ma na karasa saman tabarma nan waje farin wata ya haske ko'ina. Lomar farko almajiri yayi sallama da robarsa a hannu nayi saurin hadewa da hanzari don samun damar amsa masa sallamar. "Ance ana magana da humaira". Wani gululu ya taso mini, dama na hango tsayuwar mutum jikin katangarmu tunda karamace,nasan cikin 'yan iskan samarin nan ne saboda yau na wuce majalisa da yawa,shi yasa ban ciki son zuwa gidan baba Auwalu ba,unguwar da hanyarta kamar nan aka tara samarin KANO! Ko motsi nakasa yi har yaron ya fita da amsar inna,wato. Tana zuwa". Na fi minti 5 a haka cikin nuna fushi inna tace. Baki da halin zuwa kika sa nayi karya?.Raina ya kara 6aci,wani abu sai iyaye,shin inna ta manta da cewar abinci nake ci? ko kuwa nice na ce ta byr da amsa? "sai kin gama shawara Zaki tashi?"Ta katse ni tana fada . Na mike kawai ba tare da nace komai ba. "wnn miskilancin? wnn miskilancin?? Allah ya rabaki da shi Humaira, ace duk aikin duniya babu mai miki wuya sai MAGANA? "Na dan yi murmushi lkcn da na sako hijabi, maganar taso bani dariya, Inna kenan. Na fada a raina. Wani kamshi ya doki hancina, kamshi mai kwantar da zcy da tarwatsa tunani zuwa wuri guda . tsaye yake ya jingina da katangar hnnynsa goye a kirji. Na kasa klln fuskar na dan jingina ni ma dan nesa dashi kadan muna fuskantar juna. Ya yi magana shiru! har kusan 25mins a kiyasina. Tun Ina daurewa har tsayuwar ta fara gundurata, km da alama ni kadai yake kallo. Gaba da gabanta, na fada a zuci, Inna da mutanen gari na kirana MISKILA, yau ga wnd ya shafeni. A tunanina shi yazo ba tare da na gayyatoshi ba. Wasa sabon aji hr ana neman kusan 40mins haushi ya turnikeni, wnn wulakanci da yawa yake, amma zan ba shi 20mins nan gaba, matukar bai yi magana ba to zanyi tfyta. "Kai zo nan".Tattausar muryarsa ta katsen lkcn da ya kira wani almajiri.Tsoro, fargaba da kuma razana duk a ckn wdnn 'yan sakanni suka shige ni, na dago Kai tare da kallonshi. Tuni ya maida kallonsa ga yaron, har ya karaso. Ya ce "shiga ciki ka ce YARIMA ya ce yana son shigowa ya gaisa da inna". Na sunkuyar da kai ckn jin kunya, da kyar na kalato klm 3, "wlh ban San kai ne ba..."Yaron ya fito, "Ta ce, ka shiga".Ba tare da ya kalle ni ba, ya gitta ta gabana tare da wucewa ciki, sai a lkcn na lura hnnynsa akwai leda baka. Simi-simi ckn faduwar gaba na rashin kyautatawata na bi bayansa... ,Aisha,sumayya duk sunyi barci anan inda muke zaune inna ta bashi tabarma ita kuma ta dan tsugunna a kofar daki. Na dinga addu'ar Allah ya sanya su sumayya basu zubda taliyar ba,saboda fararen kayansa karsu nadi manja?."Mun same ku lfy? Ya fada a hankali,sai ka ji zaka san irin su magana na basu wuya. Inna tace lfy kalau,ya kuke? Lafiya ya fada a gajarce. Na koma kusa da inna na tsugunna ni ma. Sai dayayi 'yan mintuna 2 kafin ya ce,ya jikin? Tace "Alhmdllh". Ya bude ledar ya fiddo magunguna. Ga wadannan. Ya mika mata 1 wannan kuma 1 ne kwal zaki shanye a daren nan. Sai wadannan sau uku-uku guda 2 kowanne kullum. Mamaki ya kamani,ashe yana bayani?shi kawai nake kallo. Ya fiddo wani abu a gaban aljihunsa. Sai wannan allura ce idan ba zaki damu ba zan yi miki ita yanzu ta kwana 3 ce yau,gobe,sai kuma jibi a hannu akeyi". Na kara yi masa kallo 'likitane ? Na tambayi kaina,dama 'ya'yansarauta na karatu?shin yarima TAUSAYI gare shi ko kuwa KIRKI? "Me zai hana yarima,wlh ayi mini ina so,na kuma gode,Allah ya biya".inna ta fada. Ya taso hr kusa da ita, abn mamaki sai naga ya rage tsawo. Yana gamawa ya dan kalleta ckn murmushi, " Inna da zafi? " Ckn -yar dariya ta girgiza kai. Ya mike tsaye yana fadin. " Don Allah a sha maganin akan ka'ida.Mu kwana lfy".Ya juya abinda. Na yi saurin mikewa na bi bayansa tun kafin inna ta gargadeni. Har ckn Lungu na bishi nufina sai zai shiga mota snn na bashi hkr, amma sai na ga ya dan tsaya are da juyo wa. "Za ki bi ni ne?" Na yi turus! Ba motsi. "Idan Zaki bi ni ne, to mu tafi. idan kuwa ba Zaki bi ni ba ne koma gida".Ya nuna mini hny da yatsa. Na yi wani dummy!!! kunya ta kamani ainun, shin mai zan kira hkn da ya yi mini, dizgi ko wulakanci? Ya dawo baya, "mu je!!"Da sauri na juya hr bakin kofa ya Kai ni ba tare da wani abu ba, ya juya kawai abinsa. "wnn Yaro Humaira Allah ya dasa masa tausayinmu".Maganar da Inna ta tare ni da ita ke nan. Na yi murmushi kawai. "Tunda yazo ashe abin na damunsa, wlh mun gode, Allah ya nuna mana aurensa da Gimbiya".Na ce,"Ameen".Ckn rai. Kasa cin taliyata na yi, na rufewa su Aisha da safe su dumama. Yau na dan makara sbd lkcn da na isa kusan 7.30 hr ta gota. Na tarar da 'yan aikin safe an tara su a falo maza da mata. Gabana ya fadi, ko a gabansu zai koreni? Nima na yi hanzarin shigowa tare da samun wuri na durkusa. Sanye yake cikin shiga ta alfarma,wata rantsatsiyar alkyabba ce ya saka ciki kana hango kayan sakin da ya zuba kansa da hula irin ta sarakai,yau ya fito a matsayinsa na (PRINCE)wato yarima mai jiran gado a kowane lokaci. Gabana ya fadi lokacin da muka hada ido nayi saurin saukar da kaina kasa.yau mulkin yake ji,ya dago hannu,dogarin sa dake tsaye yace. "Yarima na amsa gaisuwarki". Duk muka sunkuyar da kai alamar godiya. Ya dan gyara murya. Dogari ya yi saurin cewa. "Magana ta 2 kowa ya nutsu inji yariman gimbiya". A tausashe yace,Na hana zuwan maza cikin gidan nan iyakarku waje,saboda aikin cikin gida na mata ne. Ina sane da ta6arar da ake aikatawa". Nan da nan mutane na ido ya raina fata. Ya kara da cewa.""ma'aikatan abinci Ina son daga yau a kara yawan abin da ake ba ni, ya na yi min kadan".Duk suka amsa da, "An gama yarima " ya mike tare da shigewa ciki, kowa ya tashi tare da kama tsaginsa. Na gama da ko'ina snn na shiga ciki, yana zaune dirshan saman kafet da takardu baje a Kasa, shigowata wayarsa ta fara kuka. Ganin ya kanga a kunne yasa na shige kewaye kafin na karasa shima ya gama na Kai gaisuwa tare da ban hkr. Aiki nake yi, amma Ina jin hirar tasa wadda na tabbatar da mahaifiyarsa yake yi, sbd jin ya ambaci MAMEE. "kun tashi lfy?"Ya kara narkar da murya yana shagwaba ya ce, "Ni kam Klum Mamee... wlh har yanzu bana jin sonta. ,Don Allah a nemar mini afuwa gurin mai martaba a janye auran nan. Da yake ba na jin abinda ta ke cewa,ya kara shagwa6ewa har ina mamakin kato dashi da shagwa6a. "Mamee HAMEED din ki ne fa,don Allah ki taimaka,wallahi ba ta da kunya.kullum sai ta kai karata ga sarki. Na jinjina kai tare da maimaita sunan 'HAMEED'wato sunansa ke nan. Ni dai mamee kiyi wani abu,bana so!!! What? Ya fada da karfi,wallahi mutuwa zan yi ko na gudu na bar muku kasarku...o.k... O.k,to shi kenan,mom ina jira fa". Yayi murmushi,bye love you!!" Tare da ajiye wayar. Ya koma ta baya ya kwanta tare da rufe idanunsa duka,hannayensa yayi filo da su ba tare da ya motsa ba. Na dawo wurin kansa daga nesa na durkusa. "Brk da asuba". Da sauri ya bude idanunsa, sun yi jawur ga su tubarkalla ya dallo mini su tare da maidawa ya rufe.Na daure na cije sbd ni ce Kasa, na ce." Yrm !!!"Da sauri ya tashi zaune yana mai kara shigar da kallonshi gare ni. Na yi Kasa da kai, na kara yin yaki wajen furta klmr. "Don Allah ka yi hkr jiya..."sai kuma mgnr ta makale ta Kasa fitowa. Ya jinjina kai,"Uhum? "Alamar na ci gaba yana saurare. "Ban San cewar kai ne ba wlh, a tunanina irin samarin unguwarmu ne da ke damuna". Ya daga kafadu tare da watsa hnn yana tabe baki alamar bai damuba. ,Na tashi kawai na fita tare da hado kalaci. Yanayin yadda ya ke cin abincin ya bani dariya a cikin rai,mutum sai ka ce mace,wallahi ko macce ta yi yangar yarima tayi kokari,sai yatsina yake yi abin har ya zamar masa jiki. Ya ture kayan har zan dauka yace,zauna ki ci a nan! Na dafe kaina,wannan mutumin na neman haddasa mini fitinar Gimbiya,ga shi ba a yi masa gardama. Na dan cusa kwan da dankalin tare da satar kallonsa. Na ce, na koshi". Ya kada kai kawai. Har nakai bakin kofa ya ce idan kin juye ki dawo". Nace to. Kawai na fice da sauri. Wata wayar na tarar yanayi sa'adda na dawo,amma yanayin wannan ya tabbatar mini abokinsa ne. Na yi tsaye na jingina da bango kaina a kas har ya gama. Dakin ya dauki shiru na wani lokaci. ,"Humaira".Ya kira sunana a hnkl. Na yi saurin dago kaina.ya shigar da idonsa sosai ckn nawa."Magana tana yi miki wahala ko?"Na girgiza alamar a'a. ya yi murmushi, ckn KASAITA ya ce. "Bata yi miki? Na daga kai alamar, 'eh'.Murmushi ya kara yi ya ce."To bani lbr..."Da sauri na kalleshi ya daga min gira yana bin fuskata da kallo. ana sunkuyar da kaina Kasa Ina wasa da 'yan yatsun hnn. Zuwa can na dago ido, ashe ni din yake kallo.Muka yi arba da juna ya kara saka mini murmushi, nayi saurin dauke kai. "Humaira ". Ya kara kirana a karo na 2.Na dago Kai ban yrd mun hada ido ba.yace,miskilancinki da jan aji har ya fi na 'ya'yan SARAUTA,da ana sauyi yau da kin koma GIMBIYA,ita kuma na mayar da ita BAIWA ta zama barorinki kamar yadda kika zamanto a cikin nata a yanxu. Gabana yafadi matuka. Ba zaki yi mini magana ba?.Nace zan yi. Yanayin yadda na fadi maganar ya sanya shi fahimtar gab nake da yi masa kuka. "Kin takura ko? Ya fada... Nayi shiru ina kallon babban yatsan kafata, Humaira! Gabana ya kara faduwa wai me yakeji idan ya ambaci sunana? Ko kuwa duk salon wulakancin ne zai ta takura min? Jin ya taso yasa nayi saurin dagowa kwalla ta taran min nace yanzu zan baka wllh yallabai lbrn nake hadawa....amma saida ya matso gabana gashi gab dani kamshinsa yana dokar hancina jikina ya dau kyarma addu'a nake Allah ya karemu daga sharrin shaidan ya sunkuya dab da fuskata yace kina da sarauta? Nace a'a to meya sanya kin cika TAKAMA? Nace kayi hakuri.Yace to bani lbr koda tarihinki ne yau sai naga miskilanci irin naki... Yace gaba na fiki rashin son mgn da miskilanci tunda na ajiye girman kai harna tambayeki dole ki gaya min har gidan ku naje amma kika kasa tambayata dalilin zuwana. Ya dalli bakina oyya am waiting.... Na kalleshi idona taf da kwalla nace ai kaga gidanmu ko? Ya kanne ido daya yace ban kula ba sbd duk na gama tsorata dashi... Mu kenan babanmu ya rasu ya barmu 6yrs kenan muna da yan'uwa da yawa a nan garin. Ya kalleni kin gama? Nace umm yace to saura ni na dago da sauri saura kadan mu hada fuska sbd ya dan duko, donAllah ka matsa na fada ina fidda kwalla. Baki so? Ya fada cikin maraitacciyar murya. Na ce,"eh". Sai ya koma saman gado ya zauna. "Ki shiga kowaye ki wanke fuskarki,kada ki fita a haka,ko kuwa ba komai ? Na yi hanyar fita. Zan wanke a kicin. Zaune nake dirshin ina tunani ban ga wurin aiki a nan ba,saboda idan haka halin yarima yake lallai shima yana layin 'yan unguwarmu. Har na tafi gida bai kara sanya ni a ido ba,duk tsanarshi tashiga zuciya ta.Da daddare na yiwa inna karyar barci zan yi da wuri don haka lokacin da ya zo da daddare yiwa inna allura sai ta ce ya shigo kawai. Ina jinsu ya share wuri ya yi zaune inna na yi masa labarai wanda shi ne ke mata tamboyoyin,sun dade kafin ya tafi. Da safe na yi shiri kamar na tafi na zame gidan su Amira na yi mata karyar daga can nake ba ni da lafiya shi ne aka ba ni izini ga shi inna ba ta nan tana gidan yini,ni kuma sai anjima zamu tafi party sai 2 na koma gida. Da daddare yazo,inna ta fada masa muna wurin walima. Washegari na wuce gurin walima abina. Wasa wasa sai da nayi kwanaki 4 banje ba,kullum ba ya tadda ni sai yau. Ina alwalar magriba na ga mutum a tsakar gida yana sallama. Gabana ya yanke ya fadi,tuni inna ta kabbara sallah. "Wurinki na zo. Ya fada tare da juyawa ya fita waje. Na zuro hijabi na kalli inna,na ce "inna yarima ke kirana a waje". Tayi gyaran murya,wanda na gane umarni ne ta bani na je din. Na sameshi waje ya harde hannayensa yana tsaye. Barka da isowa. Na fada a hankali. Ya kalle ni,zuwa na yi bada hakuri da neman afuwa,ina kuma biko don Allah a koma aiki na tuba idan halina ne kuma zan kara. Nayi shiru kawai ina mamakin mutum mai GIRMA matsayi yazo bani hakuri. Allah ya baki hakuri ya kuma huci zuciyarki Humaira, acikin raina nace yana kaunar sunan nan nawa. Kin jahilceni Humaira zuciyarki tana gaya miki karya lalai da kinsan waye yarima da baki shiga rudani haka ba but am sorry pls, shiyasa nakeson ki sami sakewa cos shiru shirun naki is too much kada ki sami wata cutar amma na daina kiyi hakuri 'bakomai' itace kalmar dana fizgo daga bakina na fada yayi murmushi to acikin abnd ya faru meya bata miki rai dani? Nayi shiru donAllah kiyi min magana ko sai munyi sallah? Da sauri na daga kai, to kawo min buta, na tsya ya gama alwalar yaceDako min tabarma nayi ta anan".Na zaro ido Ina murmushi har bakina ya dan bude kadan, sbd ya bani dariya, na ce."Gafa masallaci can".Na nuna masa da yatsa.Ya sosa keya kawai ya wuce yana murmushi.Na rasa abinda zan cewa inna akan zuwan Yrm, abin ka da wnd yasan hali sai kawai ta share ni.Ana karasa sllr isha'i ya dawo, na dakko tbrm a kusa da katangar tana kallon dakin inna, sbd bani son ta ji hirar har ta ganoni. Na leka nace "shigo ciki yallabai". Karshen tbrmr na zauna nesa kadan shi kuma ya zauna bisa daga farko. Ba tare da ya kalle ni ba ya ce, "kin fi sha'awar zama hakane, ko kuwa kina ckn takura?"nayi saurin kai guwoyina Kasa.ma'ana na durkusa. Ya dago Kai.... Ke nake sauraro,ko sai kin gama jan ajin? Na yi shiru saboda na rasa ta inda zan fara masa. Ya kuran ido wataKe nake sauraro... Nayi shiru sbd narasa ta ina zan soma yu kuran ido ga wata me haske kamar lantarki.. Uhm....uhmm...u hmmm..daman... Kai wani kaya sai amale wasu na fama da magana wasu kuma wahala take musu duk maganar nan bata wuce kalma uku ko hudu ba sbd iyakar zancenki kenan idan mutum ya matsa amma kin kasa furtawa, kinga dare yana karayi kada ki jawo min wata masifar bana son yawan korafi, nayi kasa da kai nakara rage murya nace kasan aikina yana da hadari kuma ance inda duk mace da namiji suka kebance na ukun su shedanne kuma gashi naga....... Kinga me? Nayi shiru bakiji? Ya maimaita.Uhm me kikace? Duk daya san ban yi magana ba. Ganin ka taso daga kan gado yasanya na tsorata, nafada kamr zanyi kuka yadan matso kan tabarmar tare da juyowa ya fuskanceni sosai ta hanyar jingina da bango, ya sassauta muryar nan tasa mai taushi "saurara kada kiyi kuka inna zata zargeki kota sani?" Nayi saurin girgiza kai yayi murmushi don Allah ina neman alfarma a dinga ce min e ko a'a tunda basu da tsayi kinji? Nace to da kyar, kiyi hkri bazan kara ba shikenan? Na sunkuyar dakai kawai naji kunya ko bakiyi bane? Nace nayi. Ina jin sautin murmushinsa ya kalleni inaso ki fahimceni zan fada gsky ba don na kare kaina ba wllh Humaira ko Qur'ani kika dauko zan dafa na rantse, duk me ya kawo haka na tambayi kaina, na girgiza kai, zaki amince dani? Na girgiza kai to wllh Humaira ban taba yin zina ba na rantse da Allah a turai nayi karatuna saida nayi 9yrs amma budurwata 1 itama hi hello ne tsakaninmu muna gama karatu muka rabu dama ita take damuna lokcn dana dawo kuma na tarar an hadani da Fareeda wato gimbiya a matsayin wacce zan aura ba don kuma ina sonta ba ganin ina kaukauce wa alamarin yasa aka yi min wannan kofar ragon,ga shi zuwan bai wani amfani ba domin ya kara min tsanarta maimakon na ji sonta. Wallahi ba ta cikin tsarin macen da nake son aure,ko mun dace? Nace,uhm. Ya kalle ni,nayi saurin daukar da kai. Uhm fa kika ce? Nayi murmushi. Magana zaki yi,domin shawara na zo mu yi ko ban isa ba? Kai isa mana,amma kayi hakuri zan yi tunani". Yanayin yadda ya tabbatar min da maganar ba karamin dadi tayi masa ba. Zuwa yaushe?"Jibi. Na fada. Yace, A'a,zan jira ki gobe da safe idan kin zo. Na yi shiru kawai ko ba zakizo ba? Nace ,insha Allah zan zo". ,yayi murmushi wai ke baki iya karrama bako bane humaira ko dan ruwa? Narasa inda zansa kaina kamr na tsaga kasa na shige don kunya, zan mike yace a'a zauna saida na roka Allah ko kin kawo bazan sha ba. Nasan dama barazana ce ba zai iya shan ruwan gidanmu ba kamr ya karanci hrt dina naji yace gobe ki tanadar min fura mai dadi na sha kinji? Nace uhm! Sbd tunanin bazai iya cin abncnmu ba yasa ko ruwa bana bashi. Ya mike zan wuce naga inna ta shiga ciki watakila ma tayi bacci ko bakya bacci da wuri? Inayi fada tare da mikewar nima, yar gayu' kalmar ta tsaya min arai ina ce yan gayu sune masu hira ba bacci da wuri ba? Muna kaiwa bakin motar nace Allah bamu alhair da sauri yace kezonan! Kibari na bashi fitila mana ko kinason fadawa kwata ne? Da rana ma mutum bai tsira ba balle dare wann lungun naku(kai yarima a hakan dai!) Ya mikon wayarsa na zare ido ki haska gobe kya taho min da ita, na juya baka gajiya zo humaira na tsaya batare dana juya ba ya karaso gabana natsani gardama donAllah ki daina ungo wayar nan ko wllh in yarda, jin ya rantse yasa na karba hannuna yana rawa jikina yana kyarma kirjina naci gaba da faduwa, kinji dadi? ,Nace uhm amma cikin raina fal haushi maimakon yabarni na koma sai cewa yayi zomuje mota nai miki kyauta ko bakya so? Maganar gsky idan haka halin yarima yake to banaso sbd banason yawan takura dayawan tambaya (kunji kinibabbiya) ace duk maganar da mukayi saiya nemi na bashi amsa kamr yasan zuciyata saiya dan duko yace kona dameki? Na bata fuska kabarshi kawai bakyaso? Na kalleshi cikin takaici na wuce wajen motar kawai sbd na tabbatar yarima mutum irin mai naci ya biyoni lalala! Ashe kin iya harara haka irin wann harar ai saikisa na kasa bacci a yau. Maganar tashi tayi min tsaye naita luguiguitata cikin kwakwalwata. Abin takaici sai naga ya fiddo da cakulet kwaya 1 ya mikomin harga Allah bansan sanda nayi dariya ba wacce har yaga hakorana shin ko dai yarima auta ne? Shima ya kara kura min ido yana murmushin nan nasa na kasaita mai kunshe da nishadi marar misaltuwa yace. "I can't express my feelings bcos of this beautiful laughing thank U so muc!" Duk cikin wann dogon turancin da yayi thank u din kawai na fahimta, na juya kawai jikina ya bani kallona yake bai tafin ba har na kai karshe layi zansha kwana na juya sai naga ya dago min hannu yana dariya. Inna na zaune na shiga tace yau kam ya dade lfy ko? Na zauna nace inna yarima na bani tsoro, tsoro kamar yaya Humaira? ,Wai inna shawara yazo na bashi akan gimbiya fareeda wai shi baya sonta, inna ta zare ido baya sonta humaira? Haka yace inna. Naci gaba da bata lbr da irin yawan tambayoyin da yake min. Zan baki shawara 1 goben ki gaya masa yayi biyayya da iyayensa shine kawai mafita don bazasu sashi hanyar dasuka san bata da amfani ba ita kuma gimbiya a matsayinsa na namiji shi zai nuna mata yanda yakeson tayi sbd mu mata muna da rauni da karamar kwakwalwa duk zurfin iliminmu kuwa. Nayi murmushi nace amma inna ngd da wann shawarar wllh dama narasa me zance masa. Ki yi wa kanki godiya da kin yi shiru kinga ai ba zan sani ba bare na ba ki shawarar. Shi yasa ake son duk abin da yaro zai yi ya shawarce magabatansa. Na langwa6ar da akai ina fadinada mata irin abubuwan da yake yi min. Ta yi murmushi

Chapter 3 of 11