Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da Ubansa ya san da cikinsa ba balle ya san da shi. To ta ina zai san da shi bayan ita kanta ba zata ce ga fuskar Uban ba, bata tab’a saninsa ba balle ta san sanda ya kusanceta abu guda ta sani cikin nasa ne kamar yarda ta ji a bakin wasu mutane da ba zata ce su waye ba. Ta lumshe ido zuciyarta na cigaba da dukan tara-tara ko sunan Mutumin ta tuna sai ta ji tashin hankalinta ya hauhawa balle kai tsaye ta danganta shi da Uban Jaheed. Motsin da ta ji yana kusanto d’akinta ne ya sata saurin mayar da fuskar haukanta ta yarda ba zaka tab’a zaton ita d’in mai hankali ba ce. Najwa ce ta shigo da kwanon abincinta Na dare flask mai kyau d’an madaidaici sai dogon jug da aka zubo mata kunun aya a ciki. Murmushi take sakar mata da alama shak’uwa a tsakaninsu ta zauna daf da ita tana furta “Allah yasa dai Nene ta yi sallah?” Maimaita maganar Najwan ta yi ha’de da waftar kwanon hannunta kai tsaye ta fara cin abincin cikin alamu na rashin nutsuwa. Najwa tana kallonta ta wafce kwanon Kafin cikin kwanciyar murya ta ce “Baki fa’da ba?” Itama ta maimaita Najwa ta ce Bismillahirrahmanirraheem.” Itama ta maimaita sannan Najwan ta mik’a mata kwanon abincin bayan ta saka ta wanke hannunta a y’ar robar da ta shigo da ita. Sosai ta ci abincin kafin ta sha kunun ayar. Najwa ta kunna mata kallo suka zauna suna kallon sau tari a irin wannan lokacin Najwa ce take zame mata abokiyar hira yarinyar ta d’auko nagarta da kyawun halayen iyayenta. Bata raina na gaba da ita sam sab’anin su Najma. Suna zaune suna kallon Najwa na tsefe mata kanta. 𝕬𝕬~~Kamar yarda Haidar ya yi alk’awari bayan an idar da Sallahr magriba da kansa ya ja Jaheed zuwa wajen Baffa don gaya masa ance Jaheed d’in ya turo. Shiru Baffa ya yi bayan jin mai ya kawo su, tashin hankalin da yake zuciyarsa bai b’uya a kan fuskarsa ba duk da k’ok’arin aikata hakan da ya yi. Har wata zufa ce take zubo masa. Shiru ya bak’unci wajen kowa da nazarin da yake a ransa. B’angaren Jaheed tausayin kansa ne ya kama shi ganin kamar ba zai nasara ba a yarda alamun Baffan Suka nuna. Tsawon mintuna kafin Baffa ya d’ago yana sakin ajiyar zuciya ya ce “Za’a je In sha Allah, Ina fatan wannan karan ya zamo na k’arshe da zamu je neman aure idan ba su baka ba In sha Allah a cikin zuri’ata zan baka Mata.” Gaban Jaheed ya wani irin bugawa tsoro ya d’an shige shi ba don komai ba sai don ya san tunda Baffa ya ce haka ba kowa yake nufi a cikin zuri’artasa ba sai Najma ko Nasma su ne y’an mata Najwa bata isa aure ba idan kuwa haka ne akwai babbar matsala shin Baffa bai san tsanar da yaran suka masa bane, ba kuma sa ganinsa da gashi sai dai zai ji kunya k’warai da gaske ba zai iya Ingice kyautar Baffan nasa ba. Mutumin da shine jigon rayuwarsa, nakamashin dukkan wasu nasarori da ya cimma a rayuwa. “Zamu je gobe In sha Allah bayan sallahr magriba sai ka bani numberr mahaifin yarinyar na sanar masa.” D’aga kai kawai Jaheed ya yi yana fatan wannan karan ya dace da auren Khairi kafin Baffan ya gingimo masa auren Najma ko Nasma da suke masa kallon wulak’antaccen Bawa mara galihu. Jiki a sanyaye suka mik’e suka bar wajen Baffan, shima nasa jikin a sanyaye ya bi bayan su da kallo tausayin Jaheed d’in yana sake mamayar zuciyarsa, tabbas da yana da iko da ya mayar da Jaheed jininsa d’ansa na halak malak ba d’an rik’o ba. Sallama Jaheed ya yi da Haidar ya fa’da nasu b’angaren inda d’akunan samarin gidan suke. Gwiwarsa a salub’e take kamar yarda gangar jikinsa ta zama salaf ba k’warin ko sisi. Yana karya kwanar lungun da zai sada shi da B’angarensu suka kusa gabza karo da ita tana ta sauri zata isa wajen saurayinta. Wani irin banzan tsaki ta ja masa kafin ta zabga masa harara cikin mayalwatan idanun ta ta kuma tsartar da miyau tana furta “Nonsense.” Cak Jaheed ya tsaya yana jin kamar ya zabga mata mari sai dai fuskar Baffa yake ganowa kawai a cikin tata fuskar don haka ya kasa samun nutsuwar marin nata ya cije leb’ensa kawai ya wuce yana jin sanda ta sake furucin “D’AN MAHAUKACIYA KAWAI.” Da d’an k’arfi ta yi maganar don haka maganar ta shiga cikin kunnuwansa direct. Yana jure dukkan wulak’ancinta amma baya bari ta k’etare iyaka ta tab’a masa mahaifiya don haka bai san sanda ya isa gabanta ba cikin taku d’aya ya yiwa hannunta wani irin fincika ya ha’data da bango. Idanunsa tuni suka sauya kala don tsananin tashin hankali k’ok’arin k’wacewa take amma hakan ya gagara saboda rik’on da ya yi mata mai tsauri ne. Cikin dakushewar murya ya ce “Repeat your words.” Runtse idanunta ta yi tana jin wani irin bugu a k’irjinta da gaske ta razana da kalamansa sai dai girman kanta da tasirin idanunta ya hanata barin ta bayyana hakan akan fuskarta ta jure zafin rik’on tana kallon cikin idanunsa ta sake furta “K’arya na yi? Ba mahaukaci…..” kafin ta k’arasa ya kai yatsa ya murje leb’enta da k’arfin gaske har sai da ta saki fitsari a wando bai Kuma saki leb’en ba ya furta “Gwara ni tawa Uwar mahaukaciya ce, taki Uwar kuwa mushirika ce waccece ta fi illa?” Ya wancakalar da ita gefe yana murza hannunsa ya ce “Kika sake furta kalmar b’atanci ga mahaifyata zaki ga abinda zan miki Wallahi, I won’t tolerate this kind of nonsense anymore.” Ya wuce ya barta a tsaye tana bin bayansa da kallo cikin tsananin mamakin tsaurin idanunsa. Huci ta saki da k’arfin gaske tana jin zuciyarta na sake rub’anya tsanarsa a fili ta furta “Mu zuba ni da kai.” Ta gyara rolling d’inta tana jin haushin jam bakin da ya goge mata duk da tsayin lokacin da ta d’auka wajen shafa shi duk don ta yiwa gwarzon zuciyarta kwalliya sai ga shi mutumin data tsana yau har da rab’ar jikinta ya kuma Mutstsike jan bakin. Ga mayen k’amshin turarensa da ya zauna ra’dam a hancinta. Ko da ta dawo daga zancen ranta a b’ace ta fa’da sassan su tana shiga kuma direct d’akinsu ta fa’da ta shige toilet kayan jikinta da suka mak’ale da k’amshin turarensa ta fara zare wa da sauri tana cillasu cikin washing machine, kafin ta sakarwa kanta shower da k’arfin gaske. Ta hau mitstsika jikinta. Takaicinta d’aya yarda jikinta ya ha’du da nasa ji take da da hali da ta cire fatar bakinta da hannunsa ya tab’a idan ba tunaninta bane ya gaya mata k’arya sai take ganin kamar k’irjinsa ma ya tab’a nata. Da sauri Najma ta runtse ido tana furta “Allah ya isa.” Wasu hawaye na bak’in ciki suna zubowa daga idanunta. Ta dad’e tsaye cikin shower d’in kafin ta hak’ura ta zura rigar wanka ta fice tana tsane gashinta da yake d’igar da ruwa. Kayan barci kawai ta zura wando iya gwiwa da y’ar b’ingilar riga da armless ta fice parlourn dama sam bata saba suturce jikinta ba. A cikin kujerar da ke kallon Mahmeey ta zauna fuskarta a tsume tana duban Nasma da itama ta zuba mata nata idanun. Mahmeey ta ce “Wai me ya faru kin fita da walwala kin dawo rai a b’ace? Ba yau kika ce zaki gaya masa ya turo ba?” Mayar da gashin kanta baya ta yi tana furta “Na gaya masa Mahmeey ya kuma yi murna.” Mahmeey ta ce “To me ya b’ata miki rai?” Tsaki ta ja sosai kafin ta ce “Ni da wannan banzan ne, Mahmeey na tsane shi Wallahi bana son na bu’de ido na gansa a gidan nan, yau don na kira uwarsa mahaukaciya shine wai ya kalleni yana furta gwara shi Uwarsa mahaukaciya ba mushirka ba ki ji fa,har ya samu courage d’in gaya min haka? Wallahi duk Baffa ne ya jawo mana da ya daidaita matsayin sa da namu shi yasa yake ganin mu kai d’aya da shi, da ya mayar da shi driver Ai da ba haka ba.” Fuskar Mahmeey a ha’de take dubanta ta ce “Ni ya cewa Mushirika? Cabd’i jam, amma kuwa wallahi ya d’ebo ruwan dafa kansa, ba kuma mamaki a wannan karan k’arshen zamansa ne yazo a gidan nan zai san ya shigo gonata, ki yi shirunki wannan fa’dan ba naki bane nawa ne.” Najma ta saki ajiyar zuciya tana furta “Wallahi Mahmeey wannan karan kada ki bar shi ya samu nutsuwa ko ka’dan ko sharri ne ki masa ya bar gidan nan.” Mahmeey ta cije bakinta kawai ba tare da ta furta komai ba ta ce “Yanzu za’a fara wasan ki bar ni da shi.” _________ Kashegari kuwa Baffa ya isa k’ofar gidan Alhaji Ahmad Jari. Mahaifin Khairiyya shi da Aminansa guda biyu da k’annensa guda biya. Jin wanda yake nemansa yasa Alhaji Ahmad Jari fitowa da wuri don dama ya shiryawa zuwansu tun kuma da Khairi ta gaya masa d’an Alhaji Ilu Mai fata ne yake sonta ya ji da’di a ransa don ba wanda bai san Baffa da irin alherinsa a gari ba don haka dole ka so ha’da zuri’a da shi. Ba wai don arziki ba sai don zamowarsa mutum Karimi mai nagartattun halaye ababen so da koyi. A babban sitroom d’insa ya masa masauki, suka zube bisa faffad’ar daddumar da take parlourn cikin farin ciki da walwala suke amsa gaisuwar juna fuskarsu d’auke da mad’aukakin murmushi. Aka gaisa sosai kafin a fara abinda ya tarasu. Baffa ne ya ce “Ka san me yake tafe da mu?” Alhaji Ahmad ya ce “Sosai kuwa, Khairi ta gaya min d’an wajenka ne yake son ta da aure na yi matuk’ar farin ciki da jin haka don ha’da zuri’a da kai abin a Ai ne a kuma yi murna. Don haka babu ja na ba shi auren Khairi.” Baffa ya yi shiru yana sake d’agowa tsoro da fargaba suna shigarsa lokaci guda baya son ya gayawa mahaifin Khairi ba shi ya haifi Jaheed ba, yana kuma gudun b’oye masa gudun kada ya ji labari daga baya ya d’auke shi mutumin banza, yanayin da yaga farin cikin Ahmad Jari ya san zai karya Masa gwiwa a lokacin da ya ji ba shine mahaifin Jaheed ba, asalima ba a san waye mahaifinsa ba. Murya a raunane ya ce “Amma akwai abinda nake so na gaya maka, ina son Kuma ka saka a ranka k’addararsa ce a haka kuma bawa ba ya wuce k’addararsa shima da za’a nemi shawararsa ba zai so ya zamo a haka ba zai zab’i kyakykyawar rayuwa irin ta kowa, maganar aure ba wasa bane don haka ba’a son k’unbiya k’unbiya a cikinta Ba ni na haifi Jaheed ba………. (Kin shirya mallakar naki? To hanzarta biya kafin free pages su k’are 500 ne kacal special kuma 1K (a tura miki har gida) Tura kai tsaye ta wannan account d’in 2118666253 UBA Sai ki tura shaidar biya ta wannan numberr 08033748387. Nagode. JIKAR NASHE CE✍🏽 KUDIRAR ALLAH. 4. NAZEEFAH SABO NASHE 08033748387. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION. ……. Baffa ya cigaba da bayani da furta “Tabbas iya gaskiyar kenan sai dai ina rok’onka ka zama mai adalci kada ka hana shi auren y’arka dalilin laifin da ba nasa ba… tsintar mahaifiyarsa na yi da shi a hannunta kuma bata da hankalin da za’a gane shin Jaheed d’in halattacen d’a ne ko wanda k’addara ta fa’dawa….” Wani irin kallo Alhaji Ahmad yake jifansa da shi, ya manta da duk wani girma na baffan murya a shak’e ya dakatar da Baffan da furta “Ba zan ba shi auren y’ata ba Wallahi, ai kai ma kana da y’ay’a ka je ka bashi mana idan har da gaske Imanin naka ya kai har haka, ta yaya zan d’auki y’ata in Bawa yaron da ba a san asalinsa ba, bayan rashin asali ma mahaifiyarsa ma bata da cikakken hankalin da nan gaba za’a gane wanene asalin Uban yaron idan ma akwai shi? Mahaukaciya kowa yana iya saduwa da ita a lokacin da yaga dama kaga kuwa maganar asali babu ita, don haka am sorry to say ba zan ba shi auren y’a ba.” Shiru Baffa ya yi hankalinsa a tashe ransa kuma ya jagule jin abinda Alhaji Ahmad ya ce. Sakin ajiyar zuciya kawai ya yi ba tare da ya sake furta komai ba ya mik’e a zafafe zuciyarsa na sake k’arfafa masa ya aiwatar da shawarar da take ba shi. Abokan tafiyarsa ma Nasu jikin a salub’e suka Bi bayansa, ba su ga laifin Alhaji Ahmad ba ba kowa ne zai iya bawa Jaheed auren y’a ba sai mai Imanin gaske, idan kuma ba b’ata suka yi ba wannan shine karo na biyar da suke zuwa nemawa Jaheed d’in aure ana Hana shi kuma ko su ne abinda zasu aikata d’in kenan. Tunda suka fara tafiya a mota Baffa ya kasa furta komai ba abinda zuciyarsa take tuna masa sai maganar Alhaji Ahmad da ya ce shi mai ya hana ya bashi auren y’arsa. Wannan ya zauna daram a zuciyarsa yana ganin kuma Lokaci ya yi da ya kamata ya gwada k’wanjinsa koda kuwa hakan na nufin abubuwa da Dama. Yarda Jaheed da Haidar suka ga jikin Baffa a sanyaye duk da k’ok’arin b’oye musu da yake hakan ya sanyaya gwiwarsu hankalin Jaheed ya sake tashi matuk’a ainun fargabar da yake ciki ta sake hauhawa, tun Baffan bai ce komai ba ya bawa kansa amsa da kansa. BA NASARA. Shine abinda zuciyarsa take jaddada masa don haka bai buk’aci jin cewar Baffan ba ya mik’e jikinsa a salub’e zai bar wajen. Baffan bai hana shi ba don shi kansa ba shi da k’warin gwiwar da zai masa bayani. Haidar ya ha’diye wani abu da ya tsaya masa a wuya tausayin Jaheed na sake kama shi kafin ya kalli Baffa ya ce “Babu nasara ko Baffa?” D’aga masa kai ya yi kawai ya kuma yi masa alama da ya wuce kawai baya son surutu. A cikin gida Umma ma ta kasa zaune ta kasa tsaye so yake kawai Baffa ya shigo ya sanar da ita wannan karan an dace. Najwa ma shiga d’ari fita d’ari sai ta shigo ta ce Umma Baffan ya shigo?” Umma ta girgiza mata kai tana furta “Bai shigo ba Najee ina ji a jikina wannan karan ma ba nasara.” Najee ta zauna turus a kujera tana fatan kada Maganar Umma ta tabbata tausayin Jaheed ne a ranta sosai tana jin da ta isa aure ba abinda zai hana ta ce Baffanta ya aura mata Jaheed. Ba gani yake ba don haka duk inda ya samu yake jefar k’afarsa cikin tashin hankali da rashin nutsuwar zuciya, k’afafunsa sun yi rauni sosai kamar yarda zuciyarsa ta raunata ji ya yi kawai ya yi karo da abu da sauri ya ja baya yana runtse idanunsa sanin laifinsa ne yasa ya ce “Am sorry.” Wani irin tsaki ta sakar masa wanda ya fusata zuciyarsa ba shiri abinka da wanda zuciyar tasa take a fusace. “Sorry for your self d’an mahaukaciya kawai ko haukan Uwartaka ya fara shafarka ne don yanayin ka ya nuna mahaukaci sabon kam….” Kafin ta kai k’arashen zancen ta ji an zabga mata kyakykyawan marin da ya d’auke ganinta na wani d’an lokaci Jaheed ya d’ago raunatattun idanunsa yana kallon Wanda ya yi marin Baffa ya gani a tsaye ransa a matuk’ar b’ace har huci yake ya nuna Najma da yatsa ya ce “Ashe baki da tarbiyya Najma kalar rashin arzikin da kuke masa kenan? Daman ina jin labari sai ga shi yau na gani da ido na…” muryarsa har rawa take don b’acin rai kamar yarda k’walla ta taru a k’asan idanunsa yana mamakin ace wai y’arsa ta cikinsa itace take irin wannan bak’in halin kamar rainon sabon gari. “Kalleshi ki ba shi hak’uri kuma ina tabbatar miki zan baki mamaki Wallahi.” Ganin yarda zuciyar Baffan take a harzik’e yasa ta kalli Jaheed cikin rashin dad’in rai da rashin sukuni ta ce “Ka yi hak’uri” kalmar da ta fa’deta cikin jin haushi da kuma sake k’ullatar Jaheed a zuciyarta ta ayyana ko mu da’de ko mu jima sai ta rama marin da yasa Baffa ya yi mata. Baffa ya zabga mata harara kafin ya ja hannun Jaheed suka shige daman biyo sahunsa ya yi ganin yarda yake tafiya kamar zai kifa sai ya tarar da Najma na masa wannan tijarar. Najma ta bi bayan su da mugun kallo kafin ta datse leb’enta tana furta mu je zuwa shege wulak’antaccen bawa. Baffa ya zaunar da shi a babban falon su na samari yana kallonsa cike da tausayawa ya ce “Baba son ka sakawa kanka damuwa Jaheed, in dai maganr aure ce ina son ka sakawa ranka wannan karan matsalarka ta zo k’arshe da ikon Allah, ka sani ko wani bawa da irin k’addararsa kuma Allah yana jarraba bawa ne don ya gwada mizanin Imaninsa In sha Allah nan gaba zaka yi dariya zaka yi farin ciki ina son ka jure ka daure ba wai don Ubangiji baya sonka ne ya yi yo ka a haka ba, ba mamaki akwai hikima da aya da Allah yake son ya nuna da hakan so nake ka jure ka sakawa kanka Jarimta kamar yarda ka saba kada ka karya zuciyarka ka sawa kanka ciwo a banza a wofi.” Shiru Jaheed ya yi sai dai wannan karan ya kasa rik’e hawayensa tuni hawayen suka fara zuba ba kakkautawa jikinsa har rawa yake ga wani zazzafan zazzab’i da ya rufeshi lokaci guda. Baffa tsoro ya kamashi da sauri ya kira likita yana tsoron kada ciwo mai girma ya kama Jaheed d’in. Kafin zuwan likitan jikin Jaheed ya sake rikicewa kakkarwa kawai yake. Baffa ya rufeshi da bargo yana zubar da hawaye yana fatan Jaheed d’in ya samu lafiya don ya samu damar aiwatar da burinsa da kuma k’udirin da yake zuciyarsa cikin lokaci k’ank’ani. Ganin Jaheed d’in yana shirin sume wa yasa ya kalli Sadik ya ce “Maza shiga gida ka kira Ummanka ka ce tazo ina nan Boys quaters.” Sadik ya fita a guje don isar da sak’on ya bar Baffa na sake danna kiran likitan don ya gaya masa ya yi saurin zuwa akwai gagarumar matsala. Umma hankalinta tashe ta zunduma hijabinta ta fito a guje Najee na bayanta itama nata hankalin a tashe. Jin abinda Sadik ya ce wai Ya Jaheed ya suma. Nene na tsaye a bakin k’ofarta ta ji kuma abinda aka ce wannan karan ta manta da haukan ta ta fita da sauri tana fatan kada wani abu ya samu Jaheed d’in. Najwa na juyo ta ganta a bayansu don haka ta dawo ta ja hannunta suka nufi Boys quaters d’in. Tsoron tonuwar asirinta yasa bayan sun isa Boys quaters d’in ta mayar da asalin fuskarta ta hauka tana dubansu d’aya bayan d’aya. Kan Jaheed na saman k’afar Baffa yana shafa masa ruwa idanunsa a k’afe suke. Salati Umma tasa tana furta me ya faru da shi Baffa?” Hannu ya d’aga mata idanunsa akan na Nenne da take tsaye nata idanun a waje tana addu’a a zuciyarta. “Matsala aka samu sun hana shi auren da muka je nema masa abinda ya jawo masa shiga halin da yake ciki kenan.” Umma ta ce Hasbunallah. Ji suka yi itama Nenne ta ce Hasbunallah ta maimaita abinda Umma ta ce ba kuma tunanin komai ta dawo ta zauna a kusa da Jaheed d’in idanunta ta zube a kansa ko kiftawa bata yi. A zahiri fuskar haukace a tare da ita sai dai a ba’dini tsoron rasa Jaheed shine abinda yake girgiza mata zuciya kada shekarun da ta d’auka tana hauka don cikar wani burinta ya zama a banza. Ashe ba zata d’au fansar zaluncin da aka mata ba? Ashe ba zata ga ranar da zata sada Jaheed da mahaifinsa ba ta kuma sanar da shi jininsa ne kamar yarda ta baro abokin haihuwarsa wato Hussaininsa a can don ya zame mata shaida ko don nan gaba. Can ta baro shi bata san a wace rayuwa yake ba bata sani ba Mahaifinsa ya karb’eshi a matsayin d’a ko kuma ya yi watangaririya da rayuwarsa? Ko kuma ma ya mutu? Kullum da tunanin da take barci ta tashi da kenan.. tausayin yaranta guda biyu gwara Jaheed yana tara da ita amma Hussaininsa fa da ta bari a k’ofar Fada cikin dukan ruwan sama? Ya rayu? Ya mutu? Shine abinda bata sani ba, ta san dai ta rubuta takarda da zata nuna shi d’in Jinin Sarkin gabas ne ta saka a cikin kayansa bayan ta gaya musu ta wa d’anta suna da Muhammad Murad! Ta kuma sanar da su shi d’in Jinin Sarkin Gabas ne ba tare da Mahaifin su ya san da cikinsu ba ko kuma ya tab’a ganin Uwarsu ko da kuwa a cikin mafarki balle a farke! Shigowar likita ce yasa ta farka daga wancan tunanin da ta tafi lokaci guda ta sauke idanunta tana matsawa daga kusa da Jaheed d’in ha’de da zare idanunta gudun fallasuwar sirrinta a zuciyarta take addu’ar Allah ya bawa Jaheed lafiya wata rana ta sada shi da danginsa koda hakan na nufin k’arshen rayuwarta ne. Aune aunen likita ya tabbatar da raunin Zuciyar Jaheed da hauhawar jininsa don haka ya masa allurai masu k’arfi da zasu samar masa da nutsuwa ya kuma buk’aci a bar shi ya samu hutun In sha Allah everything will be alright. Ya fa’da yana kallon Baffan. Ganin barci mai nauyi ya d’aukeshi yasa suka fice daga d’akin. Jikinsu a sanyaye da fatan samuwar lafiyar Jaheed d’in. Ranar Juma’a ne duk hakan ta faru a ranar kuma bayan an sakko daga babban masallachi Baffan ya buk’aci mutane su tsaya zasu taya shi d’aura auren d’ansa. Aka kuwa tsaya cikin dandazon jama’ar Baffan ya mik’awa waliyyin amaryar Jaheed sadakinsa ha’de da bada Umarnin a d’aura auren……. To fa! Ko wa Baffa ya aurawa Jaheed a cikin y’ay’ansa Najma? Nasma? Ko yarinya Najwa? Ina jiran amsar ku… JIKAR NASHE✍🏽 Don biyan littafin nan kai tsaye danna numberr account d’in nan 2118666253 UBA don free pages ya kusa k’arewa. Tafiyar dai mai nisan zango ce kamar yarda rikici da soyayyar da take cikin littafin sun girmama. Ina tsoron kada a yi babu ke hanzarta biya ki danno min shaidar biya ta wannan numberr 08033748387. JIKAR NASHE TAKU CE! KUDIRAR ALLAH.. Page 5. NAZEEFAH SABO NASHE. 08033748387. Tuni mai sanarwa ya fara kwararato a loud speaker yana sanar da AN DAURA AUREN AISHA ILU MAI FATA WATO NAJMA DA MUHAMMAD MUJAHEED MAI FATA. Ras gaban Haidar da yake waje ya fa’di yana tunanin anya kuwa Baffa ya san me ya aikata? Ya san k’iyayyar da ke tsakanin Najma da Jaheed kuwa kiyayyar da take jin kamar ta soke shi da wuk’a ta huta da ganinsa, da Baffa ya nemi shawararsa da kai tsaye zai gaya masa ya ba shi Najwa sai ya raineta a gidansa. Ya ciji yatsa tausayin Jaheed yana kama shi irin tozarci da rashin mutuncin da Najma zata masa a duk sanda ta ji labarin an aura masa ita. Ya saki ajiyar zuciya kawai yana fatan Allah yasa hakan ya zama alheri garesu baki d’aya. Cikin gidan basu san me yake faruwa ba, kamar yarda labari bai isar musu ba. Jaheed na cikin d’akinsa a kwance duk da jikin da sauk’i sai dai har yanzu zuciyarsa ba da’di ji yake banda k’arfin Imanin da yake togaceshi daga aikata kisa da ba abinda zai hana shi kashe kansa ya huta da wannan takaicin duniyar da yake ciki. A kai a kai yake ganin missed call d’in Khairi sai dai ya kasa d’agawa a duk sanda kuma zai ga missed call d’inta sai ya ji hankalinsa ya ninka na baya tashi. Hawaye yake zubar wa sosai kamar yarda ra’da’din zuciyarsa yake sake rub’anya. Ba zai iya irga adadin kiran ba kamar yarda itama Khairin bata gaji da kiran nasa ba da tura masa text messages mai bayyana tashin hankalin da take ciki ba. Bai bu’de message d’in ba saboda ya san duk abinda message d’in ya k’unsa ba zai wuce bayyana rashin nutsuwa da tashin hankalin da zuciyarta take ciki ba, kamar yarda tasa ma take ciki. Gidan tsit sakamakon masallachin juma’a r da jama’ar gidan da hadiman gidan suka tafi.

Chapter 3 of 16