An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
D’AND’ANO DAGA KUDIRAR ALLAH.
LITTAFIN NAZEEFAH SABO NASHE.
PAID BOOK IDAN KIN SHIRYA
SIYA
TURA KUDIN KAI TSAYE A
ACCOUNT
NUMBERR NAN. 2118666253 UBA
KI TURA
SHAIDAR BIYA TA 08033748387.
Ta Yaya zai zama jinina alhali ni na san bayan matana ban tab’a kusantar wata mace ba?” Ya furta kai tsaye yana kallon likitan da sakamakon gwajin yake hannunsa. Likitan yana jinjina kai ya sake furta “Tabbas Jaheed jininka don gwajin k’wayar halittarku da komai ya tabbatar kai ne mahaifinsa kafin a kai ga haka ma ko Kamanninku da suka zamo kwabo da kwabo sun tabbatar da Hakan koda Ba’a yi gwajin ba.”
Shiru na tsawon lokaci d’akin ya d’auka kowa da irin tunanin da yake a ransa ya kasa yarjewa zuciyarsa shine Mahaifin Jaheed duk da k’wararan shaidu. Abinda ya sani ko da wasa bayan matansa na aure na Sunna bai tab’a rik’ewa wata mace hannu ba, idan kuwa ya tabbata Jaheed d’ansa ne ta yaya ya samar da cikin nasa a jikin wacce aka kira mahaifiyarsa da ko a mafarki bai tab’a ganin mai kama da ita ba TABBAS AKWAI LAUJE CIKIN NAD’i. Mahaifiyar Jaheed ma Zata iya zama abar tuhuma da zargi. Kai tsaye zai iya cewa hakan zai iya zama K’UDIRAR ALLAH….
K’UDIRAR ALLAH.
Page. 1
NAZEEFAH SABO NASHE.✍🏽
08033748387.
******
Idanunsa ya Lumshe a hankali Bayan ya gama kallon fuskarta da take d’auke da Tsananin farin ciki, da alama sak’on da mahaifinta ya bayar ta isar masa shine abinda ya saka ta tarin farin ciki da annashuwa.
Bata sani ba shi sak’on yazo masa a hagunce da ta ta fassarar madadin farin ciki kwatankwacin nata, nasa hankalin tashi ya yi ya kuma shiga irin wancan yanayin da yake riskar kansa a duk sanda budurwa zata gaya masa sak’on mahaifinta ya ce ya turo. Ya bu’de tattausan idanunsa masu tsananin kyau da haiba ya zuba mata su, k’walla ce kwance a saman idanun wanda k’arfin zuciya da taurin rai yasa ya kasa sakin su su zubo. Namijin gaske ne da yake iya b’oye rauni da gazawar zuciyarsa a lokuta da dama, duk da matsalar da yake ciki ya ci
A koka mata koda kuwa kuka ne mai kuwa da kururuwa. K’addarace mai girman gaske take watangaririya da rayuwarsa, irin k’addarar da kai tsaye mutum zai ce dama Allah bai haliccesaba matuk’ar bai jajirce akan doron Imaninsa ba, da sanin cewa Allahn ne dai shine yake jarrabarsa don ya auna nauyin mizanin sa. Ya gani shin bawansa zai iya yarda da k’addarar har ma ya rungumeta a yarda ta zo masa. Hawayen da Khairi ta gani cikin idanunsa su suka k’arya mata gwiwa har nata farin cikin ya zagwanye ya bi iska. Cikin mabayyanin tashin hankali ta ce “Me ya faru Hubby? Kada dai maganar Abba ce ta b’ata maka rai baka shirya aurena bane?” Ya girgiza kai yana k’ok’arin togace tashin hankalinsa ya ce “Na shirya Habibteey, sai dai ke da kan ki tun a farkon fari na sanar da ke wanene ni? Abinda nake tsoro idan Har ke kin amince kina tunanin Abba za su amince idan suka yi bincike a kaina suka gano ni ba kowa bane face d’an mahaukaciya da bata san inda kanta yake ba, balle ta gano waye ya mata ciki har ta samar dani?” Khairi shiru ta yi zuciyatta itama tana tsallen tashin hankalin. Tuni ta manta da wannan matsalar ta JAHEED sai yanzu da ya farkar da ita, tabbas ita ta san waye mahaifinta mutum ne mai zafin gaske mai kafaffiyar Ak’ida wanda ba’a tab’a tankwara zuciyarsa idan har ya gano wanene JAHEED ko zata mutu ba zai bari ta aure shi ba, ita kuwa a yarda take jin soyayyarsa a zuciyarta zata iya aurensa da amincewar mahaifinta ko babu.
Don haka ta saki ajiyar zuciya tana kallon JAHEED cike da tausayin yanayin k’addararsa da ba laifinsa bane asali ma da za’a tambayeshi zab’i ba zai yarda yazo duniya ta wannan hanyar ba. Murya cike da rauni ta saki ajiyar zuciya hawayen da ta kasa b’oyonsu suka fara karakaina a kan k’uncinta bata san sanda ta kama hannun JAHEED ba ta ce “Ba mai raba
Mu JAHEED ko suna so ko basa so sai na aureka. Da sonka Allah ya halicceni na tabbata ina jin kai ne maha’din rayuwata, ruwa da iska ina tare da kai am always your’s.” Ta fa’da tana saka fuskarta a cikin tafin hannun JAHEED d’in tana sakin kuka mai k’arfin gaske mai saka tausayi a zuciyar mai sauraro. Shiru JAHEED ya yi yana sauraran kukan nata da yake raunata zuciyarsa yana jin shima kamar ya saki nasa kukan, sai dai dakiya da k’arfin zuciyarsa ya hana shi aikata hakan. Madadin hakan wani irin ciwo da bugu zuciyarsa take yi kamar yarda ta saba a lokuta da dama idan haka ta faru da shi. Sau hu’du yana neman aure sau hu’dun kuma ana hanasa dalilin rashin asali da cikakken tushe yana ji yana gani yake rasa abinda zuciyarsa take so da Muradi. Khairi itace budurwa ta biyar da yaso yana ji kuma a jikinsa wannan shine zai zama ganin da zai mata na k’arshe. Shikkenan shi haka rayuwarsa ta zo a juye irin tasa k’addarar kenan mai zafi da wuyar sha’ani. Kalaman Khairin da take sake kwararo masa mai nuni da tsananin soyayyar da take masa basu k’arfafa masa gwiwa ba, don suma wa’dancan Matan ba abinda basu ce masa ba k’arshe bisa tilas suka rabu bai sake jin d’uriyarsu ba.
Ya janye fuskar Khairin daga tafukan hannunsa yana kallon hawayen da take zubar wa yana jin zafin zubar su kamar dalma a zuciayrsa. “Ki yi shiru Khairi ni na san tabbas a wannan karan ma banda sa’a, kuma In sha Allah daga kanki ba zan sake soyayya ba zan yi hak’uri haka Allah ya k’addaro min.” Kuka ta saka sosai tana sake k’arfafa masa gwiwar ya turo neman aurenta In sha Allah zata yi addu’a tana ji kuma a jikinta wannan karan Abbanta zai amince ya ba shi aurenta.” Ya yi shiru yana nazarin idanun Khairin soyayyar Khairi mai girma ce a zuciyarsa zai iya cewa bai tab’a tsintar kansa a kwatankwacin soyayya irin ta Khairi ba. So yake mata irin son da ake kira Pure love, wanda shi da kansa ba zai ce ga dalilin da yasa yake son Khairi ba. Tun bayan da ya ha’du da ita bai sake samun nutsatstsen barci ba kullum itace a cikin barcinsa da tunaninsa. Kamar yarda kullum zuciyarsa take cikin fargaba da rauni akan kada a zo gab’ar da zai rasa Khairi, baya jin a wannan karan zai iya jurewa. Ya saki ajiyar zuciya yana jan siraran yatsunta ya sake murza zoben sa da yake hannunta da nata da yake hannunsa wanda suka kira zoben Alk’awari. Allah yasa mfarkinsu ya zama gaske yau ya gan su a matsayin ma’aurata shi da Khaireey bai san wace irin godiya zai wa Allah ba, tabbas zai iya yin azimi sittin don murnar auren Khaireey. “Shikkenan Habibteey ki je gida, zan je na yi magana da Baffa, za’a turo idan Allah yasa an dace shikkenan idan kuma ba’a dace ba ina rokonki ki yi hak’uri mu rik’e k’addararmu.” Da sauri Khaireey ta girgiza kai “No JAHEED I can’t ba zan iya rayuwa ba tare da kai ba JAHEED love. Idan bai yarda ba mu gudu kawai mu yi auren mu.” JAHEED ya saki murmushi wanda yake bayyana ciwon da zuciyarsa take masa ya d’aga mata kai kawai ba wai don ya amince da tunaninta da ya kira shirme ba sai don son ya
Kwantar mata da hankali. Ya ce “Okay maza ki je gida, ki yi mafarkin JAHEED mafarki mai kyau kin ji Khaireey, ki yi mafarki na ina kissing those sweetable lips.” Ya fa’da yana k’urawa lab’banta da suke fusgar hankalinsa ido. Da sauri Khaireey ta runtse idanunta ta fice da Motar da gudu. JAHEED ya saki raunataccen murmushinsa kafin ya lumshe ido hawayen da yake ta killacewa suka samu damar silalo masa. Tabbas soyayyar Khaireey daban ce a zuciyarsa tunda har ya tsiyayar mata da k’walla. Da k’yar ya samu ya ja motarsa a hankali ya har harabar gidan zuciayrsa na ayyana masa ba mamaki ban kwana ya yi da Khaireeynsa.
_
Yarda yake tuk’in cikin rashin nutsuwa shi da kansa bai yi tsammanin zai iya sa gidan da ake rik’onsa lafiya saboda yarda zuciyarsa ta rasa sukuni ko ka’dan. Mai gadi ya bu’de masa gate ya yi parking a wajen da aka tanada don ajiye motoci. Nan d’in shine gidansu gidan da tun yana jariri anan ya taso shi da mahaifiyarsa bai san kowa ba sai mai gidan shi ya ba shi duk wata kulawa da shi da Uwar gidansa da yake jin ta tamkar mahaifiyarsa tunda ita ta raineshi har kawo yanzu da ya kai munzalin aure. Ba zai ce baya fuskantar k’alubale a zamantakewar gidan ba a’a yana samu daga b’angaren Matar gidan ta biyu dama y’ay’anta gaba d’aya da suka d’au karan tsana suka d’ora masa shi da mahaifiyarsa da suke tunanin Akwai dalili mai girma da Baffa yasa yake kula da Mahaukaciyar, duk a zuciyar Baffa bakomai illa son cika umarnin Manzon Allah da kuma tausayi da jin k’ai irin na duk wani managarcin d’an Adam. Sam Baffa baya banbanta shi da yaransa na cikinsa k’aunarsa yake kamar y’ay’an da ya tsuguna ya haifa, idan banda Anty da take kwaza ba Baffan bane ya haifeshi ba wanda zai gane idan ba fa’da maka aka yi ba.
Ya dad’e cikin motar saboda yarda gabbansa suke cikin rashin kuzari da raunin zuciya. Kafin ya d’auke kwantacciyar k’walla da take idanunsa ya saki ajiya zuciya a hankali ya bu’de motar ya fito yana zuro k’afarsa. Idanunsa suka fa’da cikin na Haidar da ya sakar masa murmushi don nufo motar ya yi da ya gaji da jiran Jaheed d’in. Haidar tare suka taso shima d’an Umma ne ita kuma ta rainesu kamar y’an biyu, bata banbanta su ko a wajen kayan sawa har abada ba zai manta karamci Umma a kansa ba. Haidar ya d’an daki kafa’darsa yana furta “Mutumin daga ina?” Jaheed ya saki ajiyar zuciya ya ce “Daga wajen Khaireey.” Murmushi Haidar ya yi yana furta “Na Khaireey ba da kanka a sare, amma naga mood d’inka is not good me ya faru?” Jaheed ya d’an dube shi kamar ba zai ce komai ba sai kuma ya tuna yarda suke da Haidar basa iya b’oyewa junansu damuwa kamar dai y’an biyun zahiri. Ya saki ajiyar zuciya ya ce “Abbanta ya bani umarnin na fito neman aurenta idan da gaske nake yi.” Haidar shiru ya yi shima hankalin sa na d’an tashi yana tsoron afkuwar rashin nasara kamar yarda wa’dancan neman aurarrakin suka dinga lalacewa, an kuma rasa makirin da yake zuwa dangin Y’an matan ya kwatsa musu asalin Jaheed. Tun lokacin da shi Haidar ya yi nasa auren Jaheed d’in yake ta walagigin neman aure amma an rasa dacewa saboda waccan gundumemiyar matsalar. Jaheed ya dubi Haidar da ya lula duniyar tunani ya ce “Ina ji soyayya ta da Khaireey itama ta zo k’arshe kamar yarda wa’dancan ma suka wuce
Kamar ba a yi su ba, amma ban tab’a jin haushin rasa budurwa ba kamar yarda yanzu zuciyata take cike da rauni da k’unci na rasa Khaireey da zan yi a karo na biyar, Ina son Khaireey Haidar.” Haidar ya ‘dago idanunsa da suka ka’da suka yi jajir ya zuba akan Jaheed shi d’in zuciyarsa ta raunata matuk’a ainun saboda tausayin halin da d’an uwansa yake ciki. Tabbas da ace Najwa ta girma ta isa aure ba abinda zai hana shi aurawa Jaheed, tunda itace k’anwarsa da suke ciki d’aya da ita yake iko kaf gidan ita ka’dai ce mace a cikin y’ay’an Umma su biyar, sai dai she is too young shekarunta 14 only. Su kuma wad’ancan fitsararrun da suke Uba d’aya Nasma Da Najma dama ba a zancensu don sun raina Jaheed d’in matuk’ar raini sun tsani ko bu’de ido su yi su gan shi a gidan. Gudun kada ya sake raunata Zuciyar Jaheed d’in sai ya dafa shi. Ya CE “Kada ka karaya mana Bro, In sha Allah Lokaci yazo da kaima zaka angwance ina jin hakan a jikina just pray Nima kuma Zan taya ka. Sannan mu samu Baffa mu sanar masa In sha Allah za’a dace, fatan mu kada Allah ya bawa makirin da yake zuwa ya rusa maka maganar aure dama a wannan karan.” Jaheed ya d’aga kai yana furta “Ameen” ba wai don har a zuciyarsa yana saka rai zai samu Khaireey ba sai dai dole zai bi shawarar Haidar don basu tab’a k’in yiwa juna Biyayya akan shawara ba.
Daidai lokacin rantsatstisyar motar bak’a wuluk ta shigo cikin gidan a mugun speed, ga wani ki’da mai k’arfin gaske an ware a cikin motar. Sauti yake bayarwa sosai. Haidar take ransa ya b’aci don ya san ba kowa bace sai Najma itace mai wannan banzar d’abi’ar yarinya kamar rainon kafirai, ba Kuma laifin kowa bane sai na Uwarta data ke d’aure mata k’ugu. Jaheed kuwa ji ya yi kamar zata tarwatsa kan sa don a rayuwarsa baya son hayaniya shi mutum ne very cool bai Kuma son shiga shirgin kowa.
Wawan parking ta yi a gefensu, ta fito cikin takun k’asaita da nuna isa na isassun mata. Idanunta sanye da bak’in shade da ya k’ara mata rantsatstsen kyan da take alfahari da shi. Ta cikin glass d’in take jifan Jaheed da wani wulak’antaccen kallo ta isa ta gefensu zata wuce. Murya a ciki ta ce “Ya Haidar barka da yamma.” A ciki ya amsa tana shirin shigewa ya kira sunan ta a tsawace, cak ta tsaya ba tare da ta juyo ba duk da suna shakkar Yaya Haidar ‘din da fa’dansa amma ba zata nuna a gaban mutanen da ta tsana ba. “Ni ka’dai kika gani a wajen?” Ta juyo a zafafe tana kallon sa kafin ta ce “Kai ka’dai ne ya wajaba na gaisa da kai.” Mamaki bai bar Haidar ya mata magana ba, tsananin mamakin gadara da tsaurin idon ta. Kunyar Jaheed ce ma ta kama shi, da sam bai nuna ya san me suke ba danna wayar sa kawai yake, duk da maganar yarinyar ta doki dodon kunnensa kuma ta yi masa zafi matuk’a sai dai bisa tilas ya shanye don ba yau ya fara karb’ar wulak’ancinta da rashin mutuncinta ba ya Riga ya saba da ita da y’ar uwarta da ma uwarsu gaba d’aya basa ganin k’ima da mutuncinsa duk da dama shi d’in ya sani a wajen mutane ba shi da wata k’ima balle daraja irinsu da aka haifa a titi rashin Uba ya kan janyo musu tsana da wulak’anci daga wajen jama’ar da ba su kai su ba ma balle su taka k’afarsu, balle ita wannan da yake ganin karanta ya kai tsaiko, a k’ark’ashin Ubanta yake, cin sa da shansa tun yana zanin goyo Ubanta ne ya d’auke su shi ya samar masa da nagartaccen ilimin da yake tunk’aho da shi a yanzu. Don haka ba zai damu ba so samu ne shine zai zama mai gaisheta da nuna ladabi a wajenta abinda suke so kenan, shi kuma ya kasa musu girman kansa da fa’din ransa da yake jin sa kamar basarake ya kasa yarda ya amince wa zuciyarsa ya Zauna a taka shi. Ya yarda shi shege ne mara gata mara galihu amma bai amince shi d’in mara daraja bane, yana kallon kansa a wani mutum mai daraja ta farko a cikin mutane, don haka ba zai tab’a k’ask’antar da kan sa ba. Haidar ya saki ajiyar zuciya yana kallon Jaheed da ko a fuskarsa bai nuna damuwa da abinda Najma ta masa ba, madadin haka ma wani k’ayataccen murmushi ne kwance a kan kyakykyawar fuskarsa mai d’auke da zagayyen saje. Cikin sakakkiyar murya ya ce “Yaushe ka ke ganin ya dace na samu Baffa da maganar?” Haidar ya saki ajiyar zuciya shima ya nuna bakomai d’in kamar yarda Jaheed ya bagarar ya ce “Ko yau da Magriba sai mu same shi mu ji abinda zai ce.” Jaheed ya diro daga kan motarsa yana mik’a masa hannu ya ce “Allah ya kai mu, ka gaisar min da yara na da madam, ace da d’an rigimata wannan week end Zan zo na kai su park.” Haidar shima murmushin ya yi ya mik’a masa hannu yana jinjina zuciya irin ta Jaheed mai k’ok’arin nuna komai ba komai ba duk tsananin b’acin ran da yake ciki ba dai ka gan shi a kan fuskar sa ba, sau tari har mamakin hakan Haidar yake yi. Ya saki ajiyar zuciya yana fad’awa motarsa don ya isa gida da wuri don yaga yamma ta yi.
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/EZyeAwHEGGhJz1pRBmmale
K’UDIRAR ALLAH.
Page. 1
NAZEEFAH SABO NASHE.✍🏽
08033748387.
******
Idanunsa ya Lumshe a hankali Bayan ya gama kallon fuskarta da take d’auke da Tsananin farin ciki, da alama sak’on da mahaifinta ya bayar ta isar masa shine abinda ya saka ta tarin farin ciki da annashuwa.
Bata sani ba shi sak’on yazo masa a hagunce da ta ta fassarar madadin farin ciki kwatankwacin nata, nasa hankalin tashi ya yi ya kuma shiga irin wancan yanayin da yake riskar kansa a duk sanda budurwa zata gaya masa sak’on mahaifinta ya ce ya turo. Ya bu’de tattausan idanunsa masu tsananin kyau da haiba ya zuba mata su, k’walla ce kwance a saman idanun wanda k’arfin zuciya da taurin rai yasa ya kasa sakin su su zubo. Namijin gaske ne da yake iya b’oye rauni da gazawar zuciyarsa a lokuta da dama, duk da matsalar da yake ciki ya ci
A koka mata koda kuwa kuka ne mai kuwa da kururuwa. K’addarace mai girman gaske take watangaririya da rayuwarsa, irin k’addarar da kai tsaye mutum zai ce dama Allah bai haliccesaba matuk’ar bai jajirce akan doron Imaninsa ba, da sanin cewa Allahn ne dai shine yake jarrabarsa don ya auna nauyin mizanin sa. Ya gani shin bawansa zai iya yarda da k’addarar har ma ya rungumeta a yarda ta zo masa. Hawayen da Khairi ta gani cikin idanunsa su suka k’arya mata gwiwa har nata farin cikin ya zagwanye ya bi iska. Cikin mabayyanin tashin hankali ta ce “Me ya faru Hubby? Kada dai maganar Abba ce ta b’ata maka rai baka shirya aurena bane?” Ya girgiza kai yana k’ok’arin togace tashin hankalinsa ya ce “Na shirya Habibteey, sai dai ke da kan ki tun a farkon fari na sanar da ke wanene ni? Abinda nake tsoro idan Har ke kin amince kina tunanin Abba za su amince idan suka yi bincike a kaina suka gano ni ba kowa bane face d’an mahaukaciya da bata san inda kanta yake ba, balle ta gano waye ya mata ciki har ta samar dani?” Khairi shiru ta yi zuciyatta itama tana tsallen tashin hankalin. Tuni ta manta da wannan matsalar ta JAHEED sai yanzu da ya farkar da ita, tabbas ita ta san waye mahaifinta mutum ne mai zafin gaske mai kafaffiyar Ak’ida wanda ba’a tab’a tankwara zuciyarsa idan har ya gano wanene JAHEED ko zata mutu ba zai bari ta aure shi ba, ita kuwa a yarda take jin soyayyarsa a zuciyarta zata iya aurensa da amincewar mahaifinta ko babu.
Don haka ta saki ajiyar zuciya tana kallon JAHEED cike da tausayin yanayin k’addararsa da ba laifinsa bane asali ma da za’a tambayeshi zab’i ba zai yarda yazo duniya ta wannan hanyar ba. Murya cike da rauni ta saki ajiyar zuciya hawayen da ta kasa b’oyonsu suka fara karakaina a kan k’uncinta bata san sanda ta kama hannun JAHEED ba ta ce “Ba mai raba
Mu JAHEED ko suna so ko basa so sai na aureka. Da sonka Allah ya halicceni na tabbata ina jin kai ne maha’din rayuwata, ruwa da iska ina tare da kai am always your’s.” Ta fa’da tana saka fuskarta a cikin tafin hannun JAHEED d’in tana sakin kuka mai k’arfin gaske mai saka tausayi a zuciyar mai sauraro. Shiru JAHEED ya yi yana sauraran kukan nata da yake raunata zuciyarsa yana jin shima kamar ya saki nasa kukan, sai dai dakiya da k’arfin zuciyarsa ya hana shi aikata hakan. Madadin hakan wani irin ciwo da bugu zuciyarsa take yi kamar yarda ta saba a lokuta da dama idan haka ta faru da shi. Sau hu’du yana neman aure sau hu’dun kuma ana hanasa dalilin rashin asali da cikakken tushe yana ji yana gani yake rasa abinda zuciyarsa take so da Muradi. Khairi itace budurwa ta biyar da yaso yana ji kuma a jikinsa wannan shine zai zama ganin da zai mata na k’arshe. Shikkenan shi haka rayuwarsa ta zo a juye irin tasa k’addarar kenan mai zafi da wuyar sha’ani. Kalaman Khairin da take sake kwararo masa mai nuni da tsananin soyayyar da take masa basu k’arfafa masa gwiwa ba, don suma wa’dancan Matan ba abinda basu ce masa ba k’arshe bisa tilas suka rabu bai sake jin d’uriyarsu ba.
Ya janye fuskar Khairin daga tafukan hannunsa yana kallon hawayen da take zubar wa yana jin zafin zubar su kamar dalma a zuciayrsa. “Ki yi shiru Khairi ni na san tabbas a wannan karan ma banda sa’a, kuma In sha Allah daga kanki ba zan sake soyayya ba zan yi hak’uri haka Allah ya k’addaro min.” Kuka ta saka sosai tana sake k’arfafa masa gwiwar ya turo neman aurenta In sha Allah zata yi addu’a tana ji kuma a jikinta wannan karan Abbanta zai amince ya ba shi aurenta.” Ya yi shiru yana nazarin idanun Khairin soyayyar Khairi mai
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 1 Chapter of 16