Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 10
А kalla ke kan ki za ki yi talatin da biyu, ita kuma ina zaton shekarunta ashirn da takwas, kuma ba arabi ba boko gara ke ma kina makaranta har ma kin gama, ga shi yanzu kina aikinki to ita fa? Gfa safiya 'yarta ta fari ajinta biyu a makarantar gaba da firamare." Ta ce, 'to ai ni wannan abu baba ban san irin sa ba, wai nì na komo nan din ga shi a nan din ma abu na neman gagara." Ta ce, "ba komai allah zai kawo miki naki rabon da izininsa, ke dai ki lazamci addu'a domin takobin mumuni ce, kuma sannan ki dinga yawaita istigifari, saboda abin da kika aikata a baya kya sami wani rangwamin." Ai wannan magana sai ta tuno mata cewa akwai wata magana da suka yi da malam idi cewa ta zo bayan ta haihu zai yi mata bulala tamanin da ake wa duk wata budurwa wacce ta yi zina. Nan take ta ayyana gobe za ta je domin ta sauke wa kanta nauyi ta huta ma ranta tun da dai aure in ta yi shi kenan. Tana cikin wannan tunani ne sai ta ji an ce wai ta zo in ji alhaji usaini. Ai nan da nan ta mike tana rawar jiki ta dubi agogo goma saura kwata, har baba- abu ta soma barci, sai ta tashe ta ce, 'baba alhaji ne fa ya zo." "a daran nan?" "kila wani abu ne ya tare shi kin san shi baya san ya yi alkawari ya fasa." 107 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada "to shi kenan je ki sai kin dawo." ta ce to. Cikin doki ta fice, to amma tana zuwa da ta ga yana motarsa bai fito ba ma sai jikinta ya yi sanyi ta zaga gurin da yake ta yi masa sallama ya amsa, gami da zuge glass din bangaren sa. Sannan ay ce, "shigo mu tafi?" Ta ce, 'alhaji ina za mu je a wannan daren?" "unguwa za ki raka ni." Ta ce, 'to bari in je in tambayi baba abu tukunna." 'a'a ai ba zama za mu yi ba, yanzu za mu dawo in mun dawo kuma sauke ki zan yi ki shiga gida in juya." Ta ce, 'to shi kenan mu je." Ta shiga ya ja suka bar layin suka hau titi. Kallon sa kawai take har suka isa wani kyakkyawan gida kato. Suna shiga ya yi parking ya fito. Sannan ita ma ta fito ta tsaya tana kallonsa wani fangare ya nufa. Sannan ya ce ta shigo ita ma tabi bayansa. Suna shiga ani katon falo kyakkyawa suka sami guri suka zauna a wasu kyawawan kujeru, wadanda suke yi da'ira a tsakiyar falon. Alhaji ya dubi halima ya yi murmushi ya cе, 'Ki nada bukatar in mun yi auren in aje ki a wannan gidan?" Ta ce, "me zai hana alhaji." "to shi kenan nan za ki zauna shi ya sa ma na kawo ki ki ga guri, domin nan da sati za a daura mana aure." Cikin dadı da murna zuciyar ta fari tas, amma sai ta boye ba ta nuna masa ba.-Ya mike ya matso kusa da ita ya ce, 'ya kamata mu dan ji dumin juna kafin zuwan ranar." Cikin mamaki ta matsa can nesa ta ce, 'haba alhaji kana sane fa da cewa wannan abu haramun ne ta ya ya zan 108 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada amince?" Ya ce, 'ai ba wani abu za a yi ba kawai ki dan bani hadin kai na minti biyu." Cikin shashshekar kuka ta ce, 'alhaji ban san haka kake ba, in da a ce na san haka kake da ba zan biyo ka ba. To amma shi kenan na gode maida ni gida in kuma ka ki zan tafi ko a kafa ne?" Shiru kawai ya yi ya zuba mata ido yana kallonta har ta yi shiru. Sannan ya ce, "kin ki ni ko? To na gode shi kenan je ki." Cikin sauri ta mike za ta fita, sai ya yi kiran sunan ta, 'halima." ta amsa, amma ba ta waigo ba, domin idanunta cike yake da kwalla. Ya ce, "yanzu halima tafiya za ki yi??" "to ya kake so in yi maka? Ni wannan bukata taka ba sana'a ta ba ce, ka ga kuwa sai in tafi in ya so sai kai ma ka hakura da auran allah sai ya baka wacce ta fi ni, amma ka ba ni mamaki a yadda na ganka da girma da daraja da mutunci da kamala ina murna allah ya bani kamilin miji sai gashi abun bakin çiki wai kai kake furta mini kalmar da ban taba zaton jin ta a bakinka a aynzu ba." Ta ci gaba. 'Ba komai haka allah ya so ni na tafi." Ya ce, 'a'a tsaya in maida ke gida." "ka bar shi kawai zan sami abin hawa a bakin titi." ta fice abin ta sai da ta kai bakin gate sai ta ga ba za ta iya budewa ba, sai ta koma ta ce, "ka zo ka buďe mini in fita." ya yi murmsuhi ya ce, 'halima kenan abin da ya sa na kyale ki har kika fita dan na ga kin dau zafi ne, amma ba dan haka ba zan sanar da ke dalilina na furta miki wannan 109 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharadu magana ba, amma yanzu in kin yi mini izini ki zauna in fada miki." Ta ce, 'ka ga sha daya ta kusa yanzu in har babab ta leka ba ta ganni ba za ta nemi inda nake in ko tá ga ba na area mu sai ta tuhume ni inda na je, gara ka maida ni in ya so ka fada mini a can kofar gidan mu." "to shi kenan mu je in kai ke." ta ce to. Bayan sun iso ne ya tsaya ta fita. Sannan ya rakota har ksua da kofa. Sannan ya tsaya ya ce, "halima." ta amsa gami da kallonsa cikin ido dan jin abin da zai ce sai ya ce, 'alima ina sonki ina kaunarki wallahi wannan abin da na y! miki na yi miki ne kawai dan na gwda ki in ga halin ki, domin a gaskiya na tsargu da abin da kanwarki ta fada, to amma tun da ba halinki ba ne shi kenan zan turo a daura mana aure ranar asabar din nan mai zuwa." Halima ta ce, "shi kenan allah ya kai mu." Suka yi sallama akan zai dawo gobe in sha allahu. Haka dai suka rabu tana mamakin abin da ya yi mata, to amma kalaminsa sun sa ta hakura a kan dole domin in ma ta ki auran nasa ba ta san wanda zai zo kuma ba. Kashe gari halima sammako ta yi ta ce za ta je can gidan su wato medilee baba abu ta-ce in ce ko lafiya? Tа се lafiya kalau. Ta ce mata shi kenan ki gaishe su. Ta ce to. Ta kama hanya ta tafi. Da zuwa ko gidan ma ba ta nufa ba sai gidan malam idi na layin su ta same shi yana karatu a zaure ta sanar masa cewa ta zo-ne akan batun wannan hukunci da suka taba magana cewa sai an yanke mata hukuncin bulala tamanin ne za ta fita daga fushin ubangiji dangane da abin da suka aikata. Ya ce to shi kenan kin ko yi sa'a yanzu ba kowa sai ai miki bulalar ki ki tafi ba tare 110 Kwadi Buri Jana Amina 4. Sharada da sanin wani ba ma tun da don allah kika yi. To babu wanda zai sani, sai shi din da kika ya yi domin sa, Haka ma in da ba ki zo ba yana sane da ke sai kin je kin same shi. Nan da nan ya yi mata bulalar ta tamanin kamar yadda shari'a ta tanadar. Ai ko nan'da nan jikinta ya rikice domin sai da ta sume. Bayan ta farfado ya ce za ta iya zuwa gida ko sai an kai ta? Ta ce ba za ta iya zuwa ba. Ya sa mai adaidaita sahun kofar gidan sa ya dauke ta, domin maida ita gida. Ta ce a kai ta gwale kar a kai ta gidan yalwa, domin in an kai ta gidan yalwa za ta fara babatu har gari kowa ya sani, kuma zancen dyniya baya buya zai iya zuwa kunan alhaji usaini. Nan da nan aka kai ta har kofar gidan baba abu. Tana shiga baba abu ta ganta ta ce cikin fargaba. "lafiya halima?" "lafiya kalau." "ina fa lafiya kin tafi kalau kin dawo jiki duk jini?" Ta ce cikin jin ciwo, 'wallahi baba ba wani abu ne ya same ni ba zuwa na yi aka wanke ni bisa ga laifina na zina." Ta ce, "kamar ya ya?" "hukuncin bulalar aka yi mini." "allahu akbar shi kenan kin hutawa kan ki. Allah ya kiyaye gaba ya kara rufa man asirt." 'Amin baba." Sannan baba ta ce, "to yanzu abin da ya gama a yi shi ne ki zo mu je in kai ki asibiti a baki magunguna shi kenan." ta ce'to. Ta bude bayan ta ta ce, 'baba dubi baya na ki gani." 111 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada baba ta duba ta ce, "kai! Kai!! Kai!!! Ai duk bayan a fashe yake." 'Wallahi ni na san irin azabar da nake ji." "to ke ko bulala tamanin ai da yawa ko goma ce ma mutum ai zai dandana, bare tamanin in ce ko dage karinsa ya dinga yi kamar ya sami jaki?" "oho! Ni dai a lokacin da na fara jin zafin sai na cikuwikuye zanina na cusa a bakina dan kar in yi kara ta janyo hankalin jama'a a san abin da nake ciki. A gaskiya baba ba karamin karfin hali na yi ba." 'Ai shi kenan allah ya kiyaye gaba ga dukkan alamu wanda ya yi haka ai ba shi da niyar komawa ga sake aikata wani sabon makamancin wannan." "wallahi kuwa." Sun je asibiti an yi mata allurai da magunguna suka komo gida. Baba abu ta ce ai yau in al aji ya zo za ki iya fita kuwa? Ta ce kayya baba ba zan iya fita ba." ta ce to ya ya za a yi kenan? Ta ce kawai sai in ce masa ba ni da lafiya. Ta ce ai kin san shi cewa zai yi ki zo yay kai ki asibiti. Ta ce ai sai in ce masa na je asibitin. Ta ce to shi kenan. Haka ko aka yi bayan ya zo ne aka shaída masa ba ta da lafiya, sai ya shiga har ciki, domin ya duba ta. Yanzu ya same ta a kwance ya tambaya ta me yà same ta. Ta fada masa cewar wato zazzabi ne sai ya ce to su je asibiti. Sai ta ce ai ta je har ta sayi magunguna ta sha. Ya ce ina katin? Nan sai jikinta ya yi sanyi. Haka dai ta fito da shi ta nuna masa sai ya ga an saka mata babin liman wato duka ne kuma magungunan ma na maganin taruwar jini ne da kuma gajiya da dai sauran su. Cikin sauri ya kalleta ya kara 112 Kwadi Bari Jana Aminu A. Sharada kallon sunan mai katin ya kuma tabbatar ita ce sai ya ce, 'Halima ai duka ne wa ya yi miki wannan danyan aikin?" ta yi shiru hawaye na zuba mata dan fargabar abin da zai biyo baya ya ce cikin tsawa, 'ina magana kina jina wai waye ya yi miki wannan abin?" Nan da nan baba abu ta amshe. "waye ko ban da kanin mahaifinta?" Ya ce, "waye kenan mahaifin nata me ya hada su har ya yi mata wannan mummunan dukan haka?" Ta ce, "wai saboda ta ce ba ta son mijin da ya kawo mata har gida ya zo ya dake ta." Ya ce, 'amma kuka kyale shi?" 'A'a alhaji kanin ubanta ne fa uwa daya uba daya to me zance?" 'Ai wannan zalunci ne a ina yake da zama?" "a kauye yake." "to shi kenan ya yi na farko ya yi na karshe, na ce aure kuma babu fashe. Ai zaluncin ya yi yawa yanzu su mahaifan nata suna kallo?" "to me za su ce masa magana ai tana gurin yarinya ita kuma ta.ce kai take so ka ga ba shi da magana sai dai dukan." "a to ya dai yi na farko ya yi na karshe domin wallahi ko uban ta ne ya yi mata wannan dukan sai na yi kararsa, an bi mata hakkinta." "kai dai a bar maganar, daurin aure kuma babu fashi sai an yi." Ya ce, 'yauwa shi kenan. To ni zan tafi, amma sai na kai ta wani asibiti tukunna." "to alhaji ai ba komai." 113 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada Sannan ta yunkura da kyar baba ta kama mata suka fita har gurin motarsa. Sannan bayan ta shiga ya kai ta asibiti aka aunata sosai aka ba ta wasu magunguna masu kyau. Sannan ya maido ta gida ya wuce abinsa. An dai yi biki sosai abin gwanin ban sha'awa kowa na san barka. Baba abu ba ta yi gayya a can unguwarsu halima ba, gudun kar wani ya tona asirin 6oye sai ji suka yi halima ta yi aure wadanda aka gayya ta sai surukan goggo hanne domin ita ta tsufa sosai, 'ya'yan basa barinta fita ko'ina. Domin kafarta na mata ciwo kun san jikin girma. Bayan an gama biki tsaf kowa ya fashe sai alhaji usaini ya kira matarsa hajiya jamila ya tara su a dakinsa har amarya halima. Ya fara musu nasihar su zauna da junansu lafiya ban da yawan rigingimu, domin shi ba mai san tashin hankali ba ne. Hajiya jamila ta e, "ai ba komai alhaji sai kai ma ka dinga kamantawa, domin in gida ya gyaru daga namiji ne, in ma ya bace to shi ne in har mu mutum yana kamanta gaskiya ba wai sa rai ba babu ta yadda za a yi wasu fitintinu su dinga kunno kai cikin gidansa." Ya ce to ya dauki alkawari zai daidai ta na sa bangaren, domin ganin an sami zaman lafiya da kwanciyar hankali. Tun da aka yi bikin, sai hajiya jamila ta kara jan maryam a jiki, ta nuna mata so fiye da da, domin ta kwabi alhaji cewa kar ya soma nunawa halima maryam ba 'yar ta ba ce, 'yar tsintuwa ce. Kuma ya amince da hakan dan ya sami zaman lafiya. Suna zaman su lafiya, sai dai hajiya jamila mace ce 114 コ Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada mai shegen san girman kan tsiya. Sannan kuma ga gadara ko juyin miya ba ta bari maryam ta yi, wa halima aunty take cewa halima, amma sai cewa ta yi me ye wani aunty in za ki ce halima ki ce, banza uwar iyayen tsiya. Ta cе, "haba umma in na ce halima ai abbana ba zai ji dadi ba, kin ga aunty da nake kiranta ba karamin dadi yake ji ba." "a to dama tun da ke ubanki ne ai sai ki faranta masa, ni ki munana mini: To wallahi daga aunty babu kari, kin ji ko?" "to umma." Halima komai a daddare take yinsa a cikin gidan, domin kuwa hajiya jamila ta fita iko akan komai, ku makullin store yana hannunta, sai ta tambaye ta. Sannan ta ba ta, kuma kafin ma ta ba ta sai ta san me za ta yi, domin wai irin su 'ya'yana marasa abu hannu sunan da matsala in sun auri mai kudi za su dinga satar abinci suna kaiwa iyayen su. Ko abinci halima za ta yi sai ta tambayi hajiya jamila wane iri za ta girka, ga shi dai akwai masu aiki a gidan; amma sai hajiya jamila ta hana su yi wa halima aiki wai ai ita ta saba da aikin wahala a gida su kyale ta ta yi da kanta. Da yake masu aikin gidan nan kaf tsoran hajiya jamila suke yi mazan su da matan su ba sa yi wa halima aikin komai. Ita ke yin abin ta a gidan, ta yi abincin kuma ta rabawa masu aikin da masu gadin suna mike da kafa. Alhaji usaini nasa ake masa, amma sai hajiya jamila in girkin halima ne ta sa ta ta hada nasa da na mutanen gidan sai kuma ta kwauranta mata magi da nama sai ka ji girkin kamar an wanke kai, babu mai iya ci sai a zube shi a jabejabe a cikin gidan. Shi kansa alhajin baya iya ci sai duk ranar girkin halima ya tafi can rasturant ya ci abinci bai san 115 Kwadi Buri Jana Amina A. Sharada dalilin rashin dadin abincin ba, kuma ya san dal masu girkin nan dai daya ne ba bambanci. To amma baya magana ita ko halima sai in abin ya dame ta sai ta shige daki ta yi ta faman kuka. Kuma wani abin allah jininsu ya hadu da maryam a kullum ta ga halima cikin wannan hali sai hankalinta ya tash, ta faki idan uwar ta shiga Bangaran haliman ta dinga rarrashinta tana cewa, 'Aunty wai ke da waye? Aunty don allah ki yi hakuri ba na san in ga kina cikin kunci." Sai halima ta ce mata ba komai. Ita ma halima tana matukar son maryam. Sáu da yawa alhaji usaini da sa'adiyya yake kiran halima, amma hajiya jamila dubu take ce mata, har ma bakinta ya saba da dubun, ita ma halîman amsawa take dan ba yarda za ta yi. Tana zaune ta yi jigum sai alhaji usaini ya shigo ya same ta a zaune ya ce, "wai ni sadiyya me yake damun ki ne kin bi duk kin rame a kullum sai in gan ki kin yi jigum kina tunani?" sai ta ce ba koami. Ya ce a'a akwai dalili. Tа ce wallahi babu wani abu. Ya ce to na fi san ki dinga sakin ranki ai bai kamata a dinga zuwa ana samun ki cikin wannan hali ba. In ba ke ce da da girki ba, babu yadda za a yi ta tunkari 6angaran alhaji, amma in ita ce da girki hajiya jamila na can har sai lokacin barci sannan da kyar tana cika tana batsewa ta baro dakin. Da halima ta ga haka sai ta daina shiga sai in shi ya yi mata magana ako da yaushe tana dakinta, wani lokaci suna tare da maryam suna hira shi ne hajiya jamila ta ce wai maryam munafarci take zuwa yi dakin dubu, dan haka ta daina. Halima ta yi ta mamakin hajiya jamila ta ce in ban da abin hajiya ai mai san danka 116 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada tunanin in hajiya jamila ta sani to ta shiga uku. Kwanci tashi yau watan halima biyar da auran duk cikin 'yan'uwanta babu mai zuwa, sai baba abu kawai, domin gudun, kar su lawan su je su gano gidan su dinga zuwa har su sa a korota, shi ya sa ba wanda ya sake ya nuna musu gidan. Kowacce shawara ce da baba abu suke kulawa har halin da take ciki a game da hajiya jamila ta sanar mata. Baba abu ta ce, sai hakuri halima da sannu abin zai dinga saki, kin san halin mai gidan ki in kika fara kai masa kara ke zai bawa rashin gaskiya ki yi hakuri har idansa ya nuna masa. Ta ce to shi kenan baba. Yau wata uku kenan da samun cikin halima tana so ta fada tana fargabar abin da zai biyo baya game da hajiya jamila. Shiru ta yi ta ce a ranta cikin dai dan duma ne yado yake in ya bayyana sa gani, amma ba zan fada abu ya zame mini dan gyauto ba. Kwanci tashi sai halima ta fara laulayi ita ce yawan amai, ga yawan kwanciya, ga shi ba ta san shiga kitchen saboda kamshin dahuwa wahala yake ba ta. Sannu a hankali har dai alhaji ya gano cewa ba ta da lafiya sai ya ce ta shirya'ya kaita asibiti. Ta shirya suka tafi. Da za su fita sai da ya ce ta biya ta sanarwa hajiya zai je asibiti dan kar su fita bai san sun fita ba, sai da ta gama gaya mata sai ta dako tsalle. "yana ina alhajin?" 'Ga shi can yana jirana a mota." Ta yi saurin fita ta same shi. Ta ce, 'alhaji ai da kamata ya yi ka kai ta kyamis (chemist) yaushe har sai kun wani je asibiti?" "ai da ma ba asibiti za mu je ba kyamis za mu ya rufe kofar motar ya ja suka tafi abin le Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada tunanin in hajiya jamila ta sani to ta shiga uku. Kwanci tashi yau watan halima biyar da auran duk cikin 'yan'uwanta babu mai zuwa, sai baba abu kawai, domin gudun, kar su lawan su je su gano gidan su dinga zuwa har su sa a korota, shi ya sa ba wanda ya sake ya nuna musu gidan. Kowacce shawara ce da baba abu suke kulawa har halin da take ciki a game da hajiya jamila ta sanar mata. Baba abu ta ce, sai hakuri halima da sannu abin zai dinga saki, kin san halin mai gidan ki in kika fara kai masa kara ke zai bawa rashin gaskiya ki yi hakuri har idansa ya nuna masa. Ta ce to shi kenan baba. Yau wata uku kenan da samun cikin halima tana so ta fada tana fargabar abin da zai biyo baya game da hajiya jamila. Shiru ta yi ta ce a ranta cikin dai dan duma ne yado yake in ya bayyana sa gani, amma ba zan fada abu ya zame mini dan gyauto ba. Kwanci tashi sai halima ta fara laulayi ita ce yawan amai, ga yawan kwanciya, ga shi ba ta san shiga kitchen saboda kamshin dahuwa wahala yake ba ta. Sannu a hankali har dai alhaji ya gano cewa ba ta da lafiya sai ya ce ta shirya 'ya kaita asibiti. Ta shirya suka tafi. Da za su fita sai da ya ce ta biya ta sanarwa hajiya zai je asibiti dan kar su fita bai san sun fita ba, sai da ta gama gaya mata sai ta dako tsalle. "yana ina alhajin?" 'Ga shi can yana jirana a mota." Ta yi saurin fita ta same shi. Ta ce, 'alhaji ai da kamata ya yi ka kai ta kyamis (chemist) yaushe har sai kun wani je asibiti?" "ai da ma ba asibiti za mu je ba kyamis za mu je." ya rufe kofar motar ya ja suka tafi abin su, yana mita. 118 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada 'Kai hajiya akwai ta da bakin kishi, to me ye dan an je asibitin? Ta fiye neman husuma a yi magana ta tayar wa da mutane hakarkari da hayaniya." Halima ta yi murmushi ta ce, 'alhaji ni fa ina son in gaya ma wani abu ina tunanin in hajiya ta sani ban san abin da za ta yi ba." Ya ce, 'mene ne?" 'Ciki fa gare ni wata uku........" Ai sauran kiris kan motar ya kwace daga hannunsa. Allah ya kiyaye, ya ce cikin rawar baki, "ciki halima?" "hakika." Ina ai komawa ya yi gefe ya tsaida motar ya juyo ya zura mata ido kawai ya ma rasa me zai ce, domin abin ba zato. Sai ta ce, 'alhaji ka gode wa allah bisa wannan baiwa da babban rabo da ya baka." Cikin tsananin farin ciki mara misaltuwa alhaji ya yi shiru kawai sai ga hawaye na gudu a fuskarsa. Ya daga hannunsa sama domin yin addu'a ta godiya ga ubangiji mai kowa mai komai kamar haka. "subhannallahi walhamdullillahi allahu akbar." Wannan tana daya daga cikin addu'ar da in farin ciki ya same ka ko bakin ciki za ka fade ta. Ya dubi halima ya ce, 'tun da nake a duniya ban taa jin abin da ya faranta mini rai kamar yau ba, wallahi kin yi mini albishir da ba zan taba mantawa da ke ba." Sadiya kanta sunkuye tana murmushin farin ciki mijinta ya yi murna kamar bai taba haihuwa ba. Sai ta dan dago kai ta kalle shi. "amma fa ina tsoran hajiya wallahi." "ki cire duk wani shakku ko tsoro ai wannan abu 119 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada yin allah ne babu wanda ya isa ya hana yin allah." 'Haka ne." Kwanci tashi hajiya jamila ba ta san maganar ciki ba, sai gani take abu na tsiri tun tana kin yin magana har dai ta kasa hakuri. Rannan suna zaune da alhaji ranar girkinta sai kawai ta ce masa, "wai ni alhaji dubu ko ciki gare ta ne?" Ya ce, "me kika gani?" "ni gani nake kamar cikin tana girma kuma sai ta dinga wasu abubuwa irin na masu ciki kamar zubda yawu." ba." "kila cikin gare ta kin san ta da kunya ba za ta fada Ai nan da nan sai gaban hajiya jamila ya fadi ta ce, "ta6dijan! Yanzu ya zan yi?" "to ya ko za ki yi? Ai komai nufin allah ne."" "alhaji ka ga fa yarinyar nan ba tawa ba ce, kai ma ka sani, ga shi kai ka haihu ni ba ni da da kenan matsalar haihuwar ba a gareka take ba a kaina take ko?" Nan da nan sai tausayin ta ya kama shi ya ce, "iyi akan ki take sai dai kawai mu yi miki addu'a allah ya ba ki ke ma." Nan da nan sai ta fashe da kuka ta ce, 'shi kenan yanzu dubu za ta zama 'yar gaban goshi tun da har ta sami karuwa da kai." "a'a ba haka ba ne ai kowaoce da halinta za ta zauna kin ga ke ce uwar gidana da a ce ke wata mai wayo ce sai ki yi zaman ku lafiya ba sauran wasu fitintunu kin ga zan sami nutsuwa nima ai duk abin da aka samu na mu ne ba ki daya. Hajiya jamila dan ki fan sadiya.ne, dan sadiya 120 Kwadi Bari Jana dan ki ne?" "ba sai za ta bari ba." Amina A. Sharada "bari kai. To wai ke za ki nuna mata bake kika haifi maryam ba ne?" "haba ai ni kai nake ji." "to ki nuna mata cewa maryam 'yar ki ce kar ki fasa kin ga ko da za ta yi miki wani hali irin na ku na mata ta san cewa ke ma kin haihu a gidan." "to shi kenan." 13 Al'amarin soyayyar maryam da bashir na nan sai abin da ya karu, domin dai ba sa iya rufa kwana biyu ba su ga junan su ba. Duk da cewa gida daya suke tare abbansu ya yi ya yi su hakurewa juna sun ki su amince. Ya gaji ya hakura ya zuba musu ido, domin dai ya san da wuya wannan abu ya dorc. Alhaji usaini na

Chapter 8 of 10