na yi duk sun damu akan
maganar tafiyar nan ta bshir. Maryam fa har da kuka,
wai ita ba ta san tafiyarsa."
Ya ce, "to ai ko in haka ne wallahi sun daukar
mana jidali domin in ba wani ikon ailah ba, aure a
tsakanin su ba zai taba yiwuwa ba, ya ma za ai alhaji ya
yarda ke in ya ji wannan zancen ai mun shiga uku, a
zafin rai irin nasa ma ya ce an daina zumuncin."
Ta.ce, 'lallai kam ni ai sai ma na fi kowa laifi
domin ni zai ce ina hada su."
"ai abin ma ba mai yiwuwa ba ne gara a yi
hakuri kawai."
Ta ce, 'to ai shi kenan."
Da sassafe suka shirya tafiyar, dan haka da duku-·
duku alhaji usaini ya dauki bashir domin kai shi gidan
su. Ya ko yi sa'a shi ma alhajin ya fito suka ranka ya
zuwa airport, domin jirgin shida da rabi za su bi. Bayan
sun tashi ne ya komo gida ya samu maryam ta tashi ba ta
76
t
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
ga bashir ba, tana ta faman kuka. Hajiya jamila ta yi
rarrashin duniyar nan, amma ta ki ji sai ya ce, "ki yi
hakuri maryam in kika gama karatun ki na gaba da
primary zan kai ki can ki yi karatun ki na gaba da
secondary, domin ki samu kwanciyar hankali."
Ta ce cikin kuka, "ni dai sai dai ka kai ni gurin
bashir."
"kin san halin mahaifin bashir yanzu in na kai ki can
mun shiga uku ko za ki je haka?" haka ta gyada kai
alamar eh. Ya ce, 'a'a na dai yi miki alkawarin kai ki
london din."
Hajiya jamila ta jata a jiki tana cewa, 'iye 'yar
gatan abban ba wallahi abban nan na ki yana shagwaба
ki sosai. Haba london sukutum ai wannan tare za mu."
Ya ce, "eh a je da ke din kawai shi kenan."
Daga cikin kawayen hajiya jamila akwai wata
mata mai suna hajiya sa'a, sun hadi ne ta harkar
cinikayyarsu da hajiya rukayya wato business din
turaruka na wuta da na ruwa da ke gidan alhaji hassan
ba sakin fuska a gurin sa sai ta likewa hajiya jamila, har
suka shaku sosai da sosai, har ya zamana hajiya jamila
ba ta boyewa hajiya sa'a sirrin ta anan shegen tsegumin
ta har ta labarta mata cewa ba ita ta haifi maryam ba, to
dama ita hajiya sa'a ba ta da aure, kuma tana ganin irin
riguntsumin daular dadin da hajiya jamila ke ci a gidan
alhaji usaini ya tsonewa hajiya sa'a ido, dan haka take ta
neman hanyar da za ta samu ta janyo hankalinsa zuwa
gare ta, amma ta kasa. Dan haka sai ta yi tunanin sai fa
da makirci, wasu sun sata ta yi a baya, bare ita da kanta
77
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
tana so ta yi wa kanta da kanta. Ta jima tana neman
hanyar da za ta bi ta shawo kan lamarin, amma ta rasa
sai can wata dabara ta fado mata.
Sallam ta yi gidan hajiya jamila cikin murna ta
tashi ta tarye ta suka zuana a falo suna hira. Ba su jima
ba ko sai ga alhaji nan ya dawo da shigowarsa maryam
ta mike da tsalle ta nufi inda yake ta rungume shi, shi
kuma yana murna ya ba ta jakar hannun shi suka yi
sama. Hajiya sa'a ta dubi hajiya jamila ta ga hankalinta
na kan su sai murmushi take yi cike da farin ciki. Sai ko
nan da nan kishi ya turnuke ta. Ta dube ta ta ce, "janila
wannan wacce irin sangartcciyar 'ya ce haka ke ko kina
kallon ta?"
Ta ce, "me ta yi hajiya sa'a?"
"wato ba ki gama abin da ta yi ba ko? Yanzu
saboda allah baligar 'ya kamar wannan ta dunga
rungume namiji ba kuma muharramin ta ba, ba komai
ba/"
'Wai wa kike nufi ne ban gane ba?"
"wannan budurwar ta gabanki ko muharramar
alhajin ki се?"
'Wai wane irin zan ce kike yi mini ne?"
'Za ki gane, amma ba a bakina ba sai lokacin da
wani abu ya faru tukunna. Ana baki kina kin karba nawa
muka gani an yi a gaban mu? Hajiya kulu 'ya bayan ta
girma mijin ya aura, ta koma kashima ya fi hajiya kulu
daraja a gidan nan. Haka ma hajiya laure ya kasance
karshe rabuwa suka yi. Haka allah ya ji karai hajiya ai
ita wannan ma bacin rai ne ya kashe ta kamar ke din nan
78
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
kin tsinci yarinya tana karama kin rike ta ta girma kamar
dai maryam din nan sai kawai bayan an matsawa
yarinya ta fidda miji sai ta ce alhaji aka ce wanne alhaji
ta ce na nan gidan. Ai ko da yake shi ma munafuki ne
sai ya ce ai wai allah bai haramta ba. To ya zo ya aure
yarinyar nan daga karshe sai da ta zo duk 'ya'yan da
yarinyar nan ta haifa ba sa ko shiga dakin hajiya ai, wai
kar ta kashe mata yara tana bakin ciki ta haihu dan ita ba
ta taba haihuwa ba."
Hajiya jamila ta ce, "ai 'yar iskar yarinyar ba ita
ta raina ta tun tana karama ba?"
Ta ce, "kamar kina zaune, to ai karshe bakin ciki
ne ya kashe ta ga shi nan tana ta cin duniya, ita da yaran
ta a bagas."
Hajiya jamila ta yi shiru tana mamakin wannan
abu sai ta ce, "allah ya kyauta."
'amin." sannan suka yi sallama ta fice.
Tun daga rannan sai hajiya jamila ta fara juya
zancen nan a ranta tana so ta kauda shi ya na komo mata
sabo. Sai ta dinga zuba ido ta gani wai ko abin da hajiya
sa'a ta fada zai faru da gaske. Kawai sai ta dinga jin
haushin yadda maryam take nananewa alhaji sai ta fara
nuna kishinta.
Rannan alhaji na falo a zaune yana cin abinci
maryam na kusa da shi tana ta yi masa shagwa6a, domin
ita a zatonta sune suka haife ta. Sai ga hajiya jamila nan
tana gani sai ta daure fuska ta ce mata, "wai ke me ye
haka ne sai ki dinga wani nannane masa wai yaushe za
ki san kin girma ne?"
79
a
a
11
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
Sai ta mike cikin jin kunya ta matsa daga can ma
da taga ba fuska gurin hajiya jamila sai ta yi waje kawai
ko kadan ba ta kawo komai a ranta ba, domin ta dauka
dai ta na san ta dinga hana ta nanikar sa ne, domin ta
girma. Shi ma alhajin bai dauki komai ba, domin bai san
komai a kai ba.
Maryam yanzu ba kamar da ba, domin duk
abubuwa sun fara sauyawa mata a gidan, domin in ta yi
irin tahowar nan za ta rungume hajiya jamila in dawo
daga unguwa sai ta ingije ta guri daya ta ce mata ke
matsa can mara mutunci ke ba ki da kunya ne? Sai
jikinta ya yi sanyi ta koma ta zauna. In kuma tana
zaunan ta dinga tunani kenan wai ko wani laifi ta yi wa
hajiyar ne take mata haka. Shi kuwa can alhaji a
kowanne lokaci sai ya ga hajiya jamil na daure wa
maryam fuska, kuma ba ta so ta dinga rabar sa, bai dai
ce komai ba, ya dai zuba mata ido kawai domin bai san
abin da take nufi ba.
Rannan maryam na zaune a dakin hajiya jamila
sai kawai alhaji ya zo wucdewa sai ya ji tana cewa,
"na gaya miki kar ki kara ganin kin shiga dakin
alhaji in dai ba ina nan ba, ko kuma nina aike ki."
Ta ce, "to."
Kawai abin ya yi mata wani banbarakwai. Shi
kuma ya na jin haka sai ya kasa daurewa sai ya shiga
maryam na na ganin ya shiga sai ta fice. Tana fita sai ya
zauna ya dubi hajiya ya ce, "wai hajiya jamila me kike
nufi da yarinyar nan ne?"
Ta ce, "me ka gani?"
80
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
'Ai gani na yi kin sa mata tsanani a kai na wai shin kin mata irin alkawarin da keka dauka ne na
wannan yarinyar?"
"to alhaji saboda allah ina akwai alkawari ya za a
yi kawai yarinya ta girma, amma sai ka dinga janta a jiki
kana wani shafarta?"
Cikin sauri ya ce, "auzubillahi haba jamila yanzu
ko wani kika ji zai mini wannan zargin a kya hana bare
ke da kan ki kuma?" ya yi tsaki ya fita ransa a басе.
Maryam kam na zaune ranta a bace tana tunanin
abin da ta ji a bakin hajiya jamila, wato ummanta. Ta cе
a ranta, "wai me ya sami umma ne?"
Nan da nan sai hawaye daga nan sai kuka, ta yi
ta kuka kamar ba za ta daina ba. Sai can jamilar ta yi
kiranta domin ta kai wa abban ta abincin sa. Ta karba ta
kai masa nasa. Ta na direwa sai ta yo baya da sauri dan
kar ta tsaya ma ya sa ta wani aikin hajiya ta zargi wai
abu a tsakani. Haka ta dinga yi masa in ta gan shi ya
shigo sanmu kawai take masa ta koma daki. Shi kuma sai
ya fara zargin ko wani abu ta ce mata, dan haka ya ce
zan yi maganin ta ne tun da haka take so aure zan nema
ba shi kenan ba, a da ba ni da niyar kara aure, to amma
tun da ta biyo'mini da wannan hanyar sai ta yi
mamakina mara kunya.
8
Bashir na can misira yana ta karatu, babu abin da
yake damunsa sai abu daya. Wannan abu kuwa shi ne
tunanin maryam, domin shi a yanzu in ban da tunanin ta
ba abin da yake yi, gashi bashi da lambarta dan haka sai
81
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
ya yi wa abban sa karamin waya wato alhaji usaini ya ce, "abba dan allah ka bani lambar maryam yau."
To da dai kamar ba zai bayar ba. Sai ya tuno
maryam na halin kunci sakamakon uzzurawar hajiya
amila shi ne fa ya sake tunani ya bashi, domin ta haka
he za ta sami damar kwanciyar hankali, domin shi bashir
wani ne gurin iya lallashe shi.
Samun lambar maryam ke da wuya sai ya buga
nata a lokacin tana daki ta ci kuka ta koshi. Tana jin an
pugo ba ta san kowaye ba, sai ta daga. Jin cewa bashir
he ai sai murna, amma duk da haka sai da ya fahimci
bin da take ciki. Nan da nan ya tambaye ta ko lafiya, Ta
te masa lafiya lau. Ya ce a'a da sake a kwai abin da yake
lamun ki.
Ta ce, 'wallahi ba komai."
"to shi kenan in ba ki gaya mini ba zan daina
ugo miki waya kuma in kashe tawa."
Tana jin haka sai ta ce, 'kai dai dama umma ce a
ullum sai ta yi mini fada shi ne ni kuma ba na
p.........." yana gama jin haka sai ya katse wayar, ashe
mman ya bugawa tana dauka ya ce, "umma bashir ne."
Ta ce, "au bashír kuma lafiya?"
Da dai ya ji za ta yi dogon bayani sai ya katse ta
a cewa, "umma wai me maryam take miki ne?"
Ta ce, "me ta ce na yi mata?"
'Cewa ta yi kina fushi da ita."
"ni karya take yi mini."
Daga ji maganar ba ta shige shi ba, dan haka sai
a ce, "to umma ki yi hakuri don allah in ma wani abu ta
82
U
Kwadi Bari Jana
yi miki ki yi hakuri."
'to shi kenan ya wuce."
"to na gode umma."
Amina A, Sharada
Sannan ya sake buguwa maryam waya ya cc,
'maryam in kin san kina mata wani laifi ne to ki daina,
domin kuwa ba na son in dinga jikin ki cikin takura."
Ta ce, 'to ni me na ke yí mata? Wallahi ba
komai."
ce to.
Ya ce, "akwai dalili dai ke dai kiyaye kawai." ta
9
Halima yanzu ta gama makarantarta ta gaba da
sakandire har ta kama aikin koyarwa a primary tana
daukar albashin farko sai baba abu ta ce ta je ta kawai
iyayenta ko rabi ne. Ta yi, ta yi baba abu ta karbi
albashin, amma ta ki karba, domin tausayawa halin da
baban ta yake ciki na rashin ido da rashin cikakkiyar
lafiya. Ta hada kudin ta, domin a yi masa aikin idon.
Nan da nan aka yo masa. Yalwa ce a gurinsa da ya ke
sai da ya kwana. Sannan suka tafi gida. Suna zuwa gida
suka samu lawandi ya sha giya ya yi, mankas abin shi,
duk ya fada kwata ya daddauje jikinsa. Sai yara ne ke
bin sa suna cewa ya yi marisa ya sha kafso.
A maimakon yalwa ta ga wannan abin ranta ya ci
sai haushin yaran ta ji. Nan take ta fara zage-zage tana
kunkunduma wa yara zagi cikin takaici halima ta bar ta
a gurin ta komo gida ran ta a 6ace. Can jimawa sai ga su
shi ko dama malam usman gida ya taho bai ma tsaya ba,
halima ce ta dan tsaya kafin daga baya ta komo gida. Ita
83
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
ma yalwa kuma ta sawo shi a gaba tana ta 6abatun fada
har cikin gida.
"kai ma duk da kai wallahi dan lawandi na се
maka in za ka sha a bar nan ka dinga shan daidai
gwargwado, amma kai ba ka jin magana. To ai gashi nan
ka tarawa kan ka jama'a."
Ran halima ya kara baci, jin irin kalaman da
suke fitowa daga bakin ta. Sai da ta bari yalwan ta daina
fadan ta nutsu. Sannan ta sami yalwan zaune a dakinta
ita ma ta shiga ta zauna. Sannan ta ce,
"yalwa a gaskiya abin da kike yi a kan yaran nan
bashi da kyau ki duba ki ga irin shaidancin da yake yi
amma maimakon shi ki ji haushin sa sai haushin yaran
gari kike ji. A gaskiya wannan ba tsari ba ne ai kamar
kin ce ya je ya kra aikatawa ne. Duk tsiya da kina yi
musu fada da haka ba ta faru ba. Wai a ce mai rai
kullum sai ka ce dabba? Yara gaba daya babu na gari sai
ka ce aikin baki? To ni dai gaskiya yalwa in har irin
a
wannan za ta ci gaba da kasancewa ba zan kara zuwa ba,
wallahi allah da a ce na yi aure dauke baba zan yi in har
muku gidan ga ki ga yaran nan sai su yi yadda suke so,
amma ya ma za a yi a ce duk unguwa ana ganin su suna
shaidanci ke ko a jikin ki. Ni dai ba zan iya jure wannan
abin ba."
•Yalwa ta ce cikin fada, 'amma dai ba ni na ingiza
yaran nan na ce su je su dinga şata ko shaye-shaye ba
ko? Sha'anin rayuwa ne in allah bai shirya maka zuri'a
ba babu aydda za ka yi."
Ta ce, 'a'a yalwa wannan ta neman shiri ba laifin
84
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
kowa ba ne laifin ki ne domin tun da ke kika sangartar
da su har suka zama tamkar marasa galihu a gari. Dubi
yadda lawan ya shawo barasa ba ya kwasowa kansa
gayyar yara. Ina jin 'yan majalisar kofar gidan mallam
idi suna ta faman magana wasu na cewa allah ya shirye
shi, wasu kuwa sai faman zagin sa suke har yalwan kin
ga irin wannan babu dadı. Yalwa yanzu saboda allah ba
kya gudun kar ki mutu ki rasa mai miki addu'a? Yanzu
suna cikin wannan halin ta a za su tuna da ke su yi miki
addu'a wadanda sallar ma ba ta dame su ba. Kina kallon
rannan ma fa da na zo na kwana na sami auwal mai dan
bankalin ma kenan kusan tara na safe ko sallar asuba bai
yi ba, dana ce me ya sa bai yi sallar ba cewa ya yi wai
shi ya gaji. Wai mutum ya yi ta faman dungurawa wai
shi in ya yi sallar duk ga6obinsa ciwo suke yi.
Yanzu saboda allah mai muke zo yi duniyar?
Wai a ce duk ball din da suke ba su gaji ba, sai sallah ce
za ta sa su gaji. Sai su yi awa uku suna dukan ballamma
ba su nuna gajiyawa ba; sai sallah. Sallar da duka-duka
in sun dade su yi rabin awa kafin a idar. Yalwa duniyar
nan fa ba ma tabbata ba ce, in mu ne yau ba mu ne gobe
ba. Mutum yana can yana haukan sa bai san lokacin da
allah zai karbi ransa ba, shi kenan sai abin da ka aikata.
In ka yi khairan ka ga khairan, in sharran ka yi shi za ka
gami. Duk abin da ka aikata shi za ka girba. Dan haka
yalwa kisa ida akan yaran nan an san sun riga sun sangar
ce, amma ya kama ta a ce ki na yi musu addu'a da kuma
fadan baki. Ubangiji shi ne mai shiryarwa in ya so zai
shirya duk wanda ya so, amma zama haka cikin irin
85.
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
wannan halin ba babu inda zai kai mu sai 6ata."
Jin wannan nasiha ta ta ashe duk a kunnan lawan
takc yi, dan haka yana jin ta gama sai kawai bazato ba
tsammani sai kawai suka ji ya ce, "allahu akbar lallai yau mun gamu da malama." sai ya fito sanye da
doguwar farar riga jalla biya da hula irin tashi kafiya naci din nan fara da wani tsohon carbi kato a wuya. Wai
masallaci zai je ya yi sallah a lokacin sha biyu na rana ta
yi. Ya sake ficewa. Halima ta ce, "allah ya shirya man
azuri'a, domin arzikin annabi muhammad (s.aw.) Da
alkur'ani."
yalwa wacce jiki a yanzu ya yi sanyi ta ce, "amin. To ai
ni kin kashe mini jiki ma halima dadin neman ilimin
kenan kin ga kin yi karatun ki, amma muna nan muna ta
bauma-hauma dama wani abu ai dan ba ka da ilimi ne
shi ya sa ake yinsa in akwai ilimi wani abu ai ba za a yi
ba. Ga shi yanzu tsufa ya riske mu, babu wani ilimin
kirki."
Halima ta ce, "ai yanzu ma ba ki makara ba
gemu ai baya hana ilimi akwai makarantu da aka bude
domin manya sai ki shiga ki dinga zuwa ga su baba abu
sun kusa sauka ita gidan gidan gadalima take zuwa."
Yalwa ta ce, "yanzu abun da girmanta karatu
take zuwa?"
"ai na gaya miki gemu baya hana ilimi shi ya sa
na ce ki daure ki shiga."
Ta ce, 'to zan shiga. A kwai wata makaranta da
yaran nan dan gidan jummai mai kuli ya bude na ji an
ce matan aure ne suke zuwa bayan isha'i. Sannan su taso
86
Kwadi Bari Jana
karfe goma."
Amina A. Sharada
Ta ce, 'yauwa to kin gani sai ke ma ki shiga bara
in je in gani in yana nan sai in saya miki form din."
cike."
Ta ce, "me ye kuma form?"
'takardar shiga makarantar ce da za a saya a
"to je ki ki gani in yana nan, domin shi ma
makarantar yake zuwa."
"ai na gan shi dazu ya wuce mu har ya gaida
baba da jiki."
'Au! To ashe wannan yaran shi ne?"
"shi ne mana."
'Ai yaron ya girma sosai, shi ya sa ban shaida shi
ba. Ikon allah koma shi ne mai korar yaran nan ne dazu
da suke bin lawandi?"
"ina ga shi ne."
'Ke shi ne ma ba koriyar riga ce a jikinsa ba?"
"eh shi ne fa mai koriyar shadda."
Yaran yana da hankali. Lallai zan yi kokarin
zuwa makarantar nan.
10
Alhaji usaini kam yanzu neman aure yake
tukuru, domin ya yi ko hajiya jamila ta sassauta wa
maryam abin da take mata a kullum. Shi kenan cikin ban
baki kar hajiya jamila ta kuskure ta sanar wa maryam
cewa ba su ne iyayenta ba, amma ita nema take ta tona
abin wai ai so yake ta sakankance ya aure ta. Ai ba
almuharramarsa ba ce. Maryam har yanzu ba ta gane
halin da ake ciki ba, ita a zatonta wani liafi ta yi wa
87
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
ummanta, wanda ya ba tạ haushi. To amma kuma har
yau ba ta san wanne laifi ba ne shi ne ta ke ta faman
tunanin abin duk ta bi ta rame ta rasa yadda za ta yi,
gashi ita ba ta da wata wacce suke hulda ita a gidan su
sai gidan su bashir. Can kuma ba sakewa saboda alhaji
hassan ko sha'awar zuwa gidan ma ba ta yi dan haka ko
yaushe tana zaune a gida ko ďaki, ko kuma a falo sai in
alhaji usaini ya ganta sai tausayi ya kama shi ya се,
amma hajiya ta dauki tsarar banza haka kawai ana zaune
lafiya ta dauko wani lamari na daban mara tushe bare
asali ta kawo shi gidan, dubi yadda yarinyar nan ta rame,
saboda damuwa a kullum ba ta da kwanciyar hankali.
Wallahi da a ce gambo na nan sai ya kai ta gidan sa ya
ajiyeta domin ta fi samun nutsuwa a can.
Yau halima ta koma daga aiki wato makarantar
da take koyarwa sai ta yi tsaye a bakin titi tana jiran
motar da za ta hau wato in ta hau motar asibiti za ta kai
ta can bitinariya in ta sauka sai ta wuce gidan su. Amma
ta fi awa a tsaye ba mota,, bini-bini sai ta duba agogo.
Can sai ta ga wata bakar jeep ta yi parking a gabanta
kallo daya ta yi mata ta dauke kai, domin a zaton ta
akwai abin da ya tsayar da mai motar. A sannu a hankali
glass din motar'ya suaka wani kamshin dadi gami da
ni'imtaccen sanyin ac ya buso fuskar ta a hankali ta dago
kai suka yi ido hudu da wani hadaddan alhaji, fari tas da
shi, ga kwarjini da kamala. Suna haďa ido sai ya saki
murmushi. Sannan ya ce,
"ba tafiya za ki yi ba ne? Zo mu tafi mana."
Ta ce cikin sunkuyar da kai, 'ai gani na yi motar
88
Kwadi Bari Jana
ba ta haya ba ce shi ya sa."
Amina A. Sharada
'ai rage miki hanya zan yi na ga ana wuyar
mota."
"haba alhaji yanzu da kimar ka da girman ka da
darajarka ka tsaya
Daukan talaka kamar ni."
'Ai abin san rai ne domin tun da idona ya ganki
na ji ina matukar kaunar ki."
Ta ce, "to na gode da kaunar ka gare ni, amma je
ka kawai."
'Saboda me ba kya so ki zo mu je in kai ki?"
Ta ce, 'haba alhaji in jama'ar unguwar mu suka
ganni an kawo ni da mota kamar wannan wacce fassara
za a yi mini kenan?"
Ya ce, 'ai wato shi kamannin mutumin banza ma
ai ya fita da ban kin ga dai ban san ki ba, amma ina dora
ido kan ki sai na ji nan da nan zuciya ta ta harba
begenki."
Ta ce, "to sai ka bi a sannu."
"to dai yanzu yi mini kwatancen gidan na ku."
"to shi kenan nan." ta yi masa kwatance ya kuma
fahimta. Sannan suka yi sallama akan cewa sai jibi zai
zo ta ce to allah ya kawo ka. Ya ce 'amin. Sannan ya
mika mata kudi masu yawa. Kememe ta ki karba. Ya yi
ya yi, amma sam ta ki karba, Haka ya hakura ya tfi,
amma ya karbi lambar wayar ta, kuma ya ba ta tasa.
Sannan ya tafi, bayan ya tambayi sunanta ta gaya masa
cewa sunan ta halima, shi kuma ya ce sunansa alhaji
usaini.
89
45
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
Halima na zuwa gida ta sanarwa baba abu abin
da ya faru, ta yi murna domin wannan shi ne karo na
farko da halima ta ta6a kawo saurayi gidan su tan
komowarta gidan baba abu ta yi fadan har ta gaji ta bari.
To sai yau sai ga shi kwatsam ta zo mata da maganar.
Kwana biyun kuwa da misalin hudu da rabi na
yamma sai ga alhaji usaini ya zo ya aika wani yaro a yi
masa sallama da ita. Nan da nan kuwa ta shirya ta fito.
Tana ganinsa sai ta ce, 'au ashe kana tafe?"
Ya ce, "me zai hana tun da na yi miki alkawari
kyan alkawari ai cikawa, kuma masu hikimar magana
sun ce mai san dan tsuntsu shi ke binsa da jifa."
Ta yi murmushi ta koma ciki ta dauko masa irin
farar kujerar nan ta ba shi daya ya zauna ita ma ta zauna
a bisa daya. Sannan suka gaisa. Ya dube ta ya yi
murmushi ya ce, 'wallahi tun da na rabu da ke ban kara
samun sukuni ba, duk abin da nake yi hankalina na
wajen ki; domin tunanin yadda za ki karbi maganar da
na zo da ita. Wato ni ba wani abu ne ya kawo ni ba sai
maganar aure, domin ni tun da na dora ido kan ki na ji
ina da sha'awar ki zama mai dakina, domin bayan son ki
da nake yi to na yaba da hankalin ki da tsarin tarbiyarki,
shi ya sa na ga ya dace ki kasance mai dakina.""
Murmushi kawai ta yi, amma cikin zuciyarta ban
da bugun uku-uku babu abin da take yi. Fargabar irin
halin da take ciki da kuma irin tarbiyar gidan su, babu
yadda za a yi ya aure ta ba tare da ya san asalin iyayenta
ba. To amma ba komai take ji ba illa rashin tarbiyr gidan
in har ya gani zai iya cewa ya fasa, dan haka ta fara
90
Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada
tunanin ta goce masa kawai ya tafi ta huta. To amma,
kuma in ta yi haka ba za ta yi aurc kenan ba, domin duk
irin mijin da ya zo dole ya san gidan ainihin iyayenta.
"halima! Halima!! Ya kika yi shiru, tunanin me
kike yi haka?" in ji alhaji usaini. Cikin sauri ta daga kai
ta yi murmushi.
"ba komai."
stli nd Ya ce, "ai na fuskanci baki da san magana sośai, gashi kuma ni mutum ne mai san a sani a gaba ana ta yi
mini hira." ta yi murmushi.
"alhaji an ai in dai hira ce to an gamu da ita,
domin nima ina da srutu."
Ya yi dariya.
"an ya kuwa za ki` yi magana? Kai da wuya." ta
yi dariya, sannan ya ce, "to mu koma kan zancen mu ban
ji kin ba ni amsa ba, koani ya rigani?"
Ta ce, "babu wanda ya riga ka."
'To amma dai ina fatan kin cika idda ko?"
Nan da nan sa gabanta ya fadi. Ta ce, "wai shin
alhajin nan a me ya dauke