Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 10
ni? Wato shi. a nufinsa bazawara ya dauke ni bayan ko lalle ba a ta6a samin ba? To amma zan iya cewa ni bazawara ce dan samawa kaina rufin asiri, domin in na ce ni budurwa ce zai gano wani abu nan gaba." "ya kika yi shiru?" Ta ce, 'alhaji ai ni mamaki ka bani domin in ban yi idda ba ai ba zan saurare ka ba ma, bare in kawo ka gidan mu; domin manzon allah (s.a.w.) Ya ce "kar ku yi neman aure cikin idda." 91 46 Kwadi Bari Java Amina 4. Sharuda Ya cc, "sadaka rasululil karim. Wannan haka yake kina da yara ne?" Ta ce, 'wa ni? 'Ya ta daya ce kuma ta rasu."" Ya ce, 'allah sarki allah ya ji kanta." 'Amin." "ko zan iya sanin me ye dalilin rabuwar ki da wancan tsohon mijin naki?" "eh ba wani abu ba ne ya rabu mu ba illa iyayensa da ba sa sona sun takura masa lalai sai ya rabu da ni, shi kuma ya bi umarnin su domin ya faranta musu ya sake ni. Wannan shi ne kawai dalil." Ya ce, "Karewar zama ce. Al in zama ya kare sai ki ga sanadi kadan an rabu. Ba rabonsa ba ce rabo na се. Yanzu dai mu koma kan maganar mu ni fa ba na san a dauki tsawon loakci da wuri na ke son auran nan." "to ai babu wani abu sai a yi da wurin," Ya ce, "yauwa ni yanzu za koma in na sake komowa 2a a san abinda ke cik Ta ce, 'to shi kenan." Ya mike suka yi şallama ya tafi, akan cewa zai komo ranar juma'a wato sauran kwana hudu kenan. Wannan shehakar bashir zai kammala karatunsa na gaba da secondary yayin' da ita kuma maryam take matakin farko a makarantar gaba da secondary din ita ma. Tuni bashir ya fara shirye-shiryen komowa gida babu abin da yake sai doki, dan ya zo ya ga maryam ya take, domin tun daga wayar da ya taba yi mata yake tunanin halin da za ta shiga. Koma ta shiga har ma yake ta faman tunanin kar dai hajiya jamila ta sanar mata 92 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada cewa tsinto ta aka yi, domin shi ya san komai da cewa ba shi da wani wayo lokacin da aka tsinto tan. Mana'a bai wuce shckara goma ba, ko ma yana da wayon to zai iya mance wasu abubuwan in aka yi la'akari da wayan shekarun da aka kwashe wato har shekara goma sha shida. Maryam kam yanzu ta dan sami saukin hajiya jamila ba ta dakura mata sosai, har ma takan dan zauna su,yi hira, kuma takan gaya mata cewa bashir ya kusa dawowa me ya kamata a yi mishi na maraba. Shi ne ta ce ya kamata a yi mishi shirye-shirye masu kayatarwa, ciki ko har da girki. Nan dai suka zauna suna tattauna abin da ya kamata cansai ga abba ya shigo wato alhaji usaini nan ya zauna ana ta faman hira da shi, da kuma shawarwarin abin da za a yi wa bashir, domin faranta masa bashir yaro ne mai biyayya ga iyaye, duk abin da iyayensa suka sa shi ko da ransa bai so ba zai yi dan ya faranta musu shi ya sa alhaji usaini ke matukar son yaron. Abu daya ne za ka umarci bashir ya ki sai maganar maryam in har abin ya sabawa san ransa to ba ko zai yi shi ba, kowa ya san wannan dan haka mutum daya ne yake masa dole akan maryam ya hakura shi ne alhaji hassan, wato mahaifinsa. Domin sanin cewa yana da zafi sosai, amma duk da haka wani sa'in baya yarda da wani abin. Yau ce ranar dawowar bashir dan haka maryam da mama wato hajiya jamila suna ta faman shirye-shirye an gyara gida, an shirya shi ko'ina ya hadu sai kamshi yake tashi. Domin gidan ya turaru da turaruka kun san 93 47 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada sana'ar su ce dama. Bare yanzu idonsu ya bdue sun san sirrin turaruka kala-kala, dan haka ko harabar gidan ka shiga za ka ji kamshi. Sai biyar na yamma bashir ya iso kano, dan haka sai suka shirya tsam, domin tararsa a aiport. Alhaji usaini shi ne zai kai su. Hajiya jamila ta ce har ita za a je tarar dan nata, dan haka sai suka yi kwalliya maryam wani tsadaddan less ta sanya mai ruwan zuma riga da siket da dan kwali. Ya yi mata bala'in kyau sosai. Sai wani dan mayafi irin na 'yan mata da ta yafa shi ma kalar less din. Sannan farin takalmi da jaka kuma ya sha fashion kalar kayan, har abin hannu ga wani kamshi mai dadi da ke tasi a jikinta, gashi dama ta kara girma wato a yanzu ta zama budurwa sosai, ba kamar yadda bashir ya tafi ya bar ta ba. Kyanta ya kara fitowa gashin nan har gadon bayanta, dan ma tana nade shi, domn haramun ne bace ta fito waje da gashin ta. Ko da sili daya ma wasu su gani ko da budurwa wacce in dai baliga cе. Don haka a yi hattara. Maryam ba ta barin gashin ta ya bayyana kuma tama fi yawan amfani da hijabi dan dai wannan karon ta ga damar. sanya mayafi duk da cewa karami ne babu inda surar jikinta ta bayyana, domin hajiya jamila ba ta barin ta wanan kwaliyar banzar. Suna zuwa a daidai lokacin jirgin su bashir ya sauka yayin da fasinjojin ke ta haramar fitowa, su kuma 'yan'uwa na ta zare ido ko za su ga na su. To suma su maryam suna waje suna hange. Can sai suka hango shi ya fito. Ai ko sai suka fara daga masa hannu har ya 94 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada hange su ya nufo inda suke. Wata hadaddiyar shadda ce a jikisna galila ta sha aiki irin aikin nan da ake yinsa har kasa, haka tun daga kafada har hannu. Shaddar dank blue ce ta yi masa kyau sosai. Sam bai san sanya kananun kaya shi ya sa ma mafiya yawan dunkunan sa duk abin da ya danganci yadi ne ko shadda ko na wani abun dai. Yana zuwa ya rungume abba wato alhaji usaini. Sannan ya durkusa ya gaida mama, hajiya jamila. Sannan ya tsaida idonunsa a kan maryam kir ba tare da ya ce komai ba, ahr sai da alhaji usaini ya yi gyaran murya. Sannan cikin jin kunya ya shafa gashin kansa ya sunkuyar da kai ya ce cikin kasa da murya. "maryam an girma.' Ta yi murmushi ta sunkuyar da kai ganin su abba na gurin ta ce, "yaya sannu da zuwa." "yauwa." Sannan suka juya zuwa gurin motar su abin da ya hana alhaji hassan zuwa dan baya gari ne da shi zại zo ya dauke shi Suna kan, hanyar su ta komawa gida hajiya jamila na gaba dralhaji usaini, su ko su maryam na baya suna dan taba fira kadan-kadan, ba tare da su bajiya jamila suna jin hirar su ba, domin suma ta su hirar suke yi. Bashir ya kalli maryam ya yi murmushi, yayin da ita kuma take satar kallon sa, domin kunya ta hana ta kallonsa sosai Sai in ya kalli wani wajen sai ta zura masa ido. Hakika bashir ya hadu karshe, shi ba fari ne can ba, amma yana da dan haske. Sannan kuma yana da dan tsayi, amma ba can ba, gashi da dogon hanci da 95 1 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada manyan ido. A warwaje idanunsa suke tulutulu kuma sun yi wa fuskar kyau sosai ga wani siririn saje da ya ajiye. Sannan ga gashin bakin nan shi ma siriri. Hakorinsa na sama da siririyar wushirya mabaiyaniya sabanin maryam da take da tata wushiryar a tsakiyar hakorin kasa, kuma kowanne ya dace da shi. Gaskiya bashir ba wai boyayyan kyau ne da shi ba. Kallo daya za kai masa ka gano cewa shi kyakkyawa ne, domin mabaiyyanin kyau gare shi. "maryam kin yi shiru ba kya yi mini magana kamar ba ki sanni ba." Cikin alamar zancen bebaye ta nuna masa cewa kunyar su mama da abba take ji. Ya yi murmushi. Har suka je gida idanunsa sun ki aukewa daga kanta. Bayan sun je gida ne suka ci suka sha, suka yi hani'an. Sannan ya tashi ya koma dakinsa wanda dama tuni maryam ta gyara masa. Ya bude ya shiga ya watsa ruwa. Sannan ya dan zauna dan ya huta. Hajiya jamila ta ce, "alhaji in çe ko ka gani da idonka?" Ya ce, 'me fa?" "kai yanzu ba ka lura da irin kallon da yaran nan suke wa junan su ba?" Ya ce, "na gani mana hajiya. To yanzu ya za a yi abin dai da ake gudu shi yake shirin faruwa." 'Wane irin yake shirin faruwa? Ya ma faru." "to yanzu ya za a bullowa lamarin?" 'A to nima wallahi ban sani ba, ka ga kuma alhaji hassan in ya san wannan lamarin mun shiga uku kawai dai mu nuna musu kamar ba mu san komai ba. Sannan 96 3 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada kuma mu gargade su da kar su yarda su nuna wa kan su kauna, domin ba za mu amince ba." Ya ce, "lallai ba ki da hankali ai komai kika gani daga allah ne ni wallahi in har suna san junan su ba zan hana ba, sai dai duk abin da zai yi ya yi. Haba mutum a dinga jin tsoronsa kamar wani mala'ikan mutuwa." Ta ce, "to ni dai babu ruwana wallahi a gaskiya rigima ce wannan tsantsa ba na san abin da zai zo y taba zumuncin ku." Ya ce, "ai daga baya zai gane in ma ya ki in da rabo ai ya je ya mutu a banza, wallahi ni babu abin da ya sha mini kai." 'Allah ya yayyafawa abin ruwan sanyi, a yi shi cikin kwanciyar hankali, ba tare da tashin hankali ba." Ya ce, 'amin, allah dai ya sa haka din." Maryam na daki ta yi jigum tana wassafa irin yadda take ji a game da bashir. "hakika ina. Da a ce shi ma haka zai soni da na more wallahi, sai dai matsala daya alhajin su wato daddy ina tunanin in ya sani ya abin zai kasance? Ni ina mamakin irin wannan kiyayya da daddy yake nuna mini sai ka ce ba 'yar dan'uwansa ba. Wai shi baya ganin irin son da abbana yake wa dansa bashir ne? Why?Shi da ba zai so ta sayar ba, shi ma mai 'ya'ya da yawa aka so na sa bare abba mi kadai ce a gurinsa? Laifin abban ne domin shi yake nuna yana tsoronsa. Ai shi ne babba wannan ai zalunci ne so." Sadaf-sadaf ya shiga ba tare da ta sani ba, ya sanya hannayenta ya rufe mata ido yana murmsuhi. 97 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada Hannu biyu ta sa ta rike hannayensa, domin banbarewa daga idanunta. Ta yi nasarar cire hannun, ta juya ta kalle shi suka yi murmushi. Sannan ta sa hannu ta kare fuskarta. Ya kewayo ya zauna yana fuskantar ta. murya. "why?" ya tambaye ta. Ta ce cikin kasa-kasa da "wallahi kunyarka nake ji shi ya sa ka ga ina ka sa yi maka.........." Kallon da yake mata ne ya sa ta saurin dauke kai. Ya ce, "haba my sweet heart ai bai kamata a ce kina nuna mini irin wannan ba, domin tare muke dama ba wai bakin ganin juna ba ne." "ai ka dade ba ka nan." "okey ashe bakunta ake mini? To daga yau na zama dan gida." Ta sake yin murmushi. 11 Kwanci tashi soyayya ta mika à tsakanin maryam da bashir ta yi nisa, har ta kai kowa ya sani. Shi ma ałhaji hasşan ya fara jin kishin-kishin dan haka, sai ya yi wa alhaji usaini waya ya ce ya zo yana nemansa. Bai dauki lokaci ba kuwa ya je ya same shi, domin jin musabbabin kiran. Bayan sun gaisa ne ya dube shi. "alhaji wani kishin-kishin nake ji wai bashir yana son wannan tsintacciyar yarinyar ko?" Jin wannan magana sai alhaji usaini ya yi tsuru da shi, đomin abin 6oye ya fito sarari. Abin da yake gudu ya faru dan haka ya ga babu mafita. Sai ya fada 98 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada masa gaskiyar lamari. Ai ko nan da nan ya mike da fada. "kar ka soma, na ce maka kar ka soma wallahi ba zai auri 'yar da ba a san asalinta ba." Ya ce, 'alhaji da fa na kowa ne, ni ban ga abin ki a wannan lamari ba. Mace ce fa ba namiji ba, yanzu saboda allah in ba a tausaya mata ba sai yaushe?" "kai dai da kake son tausayawar ka yiyi tata yi, amma ni in nina haifi dana ba zai auri wannan yarinyar ba, dan haka nemar mata miji tun da wuri." Nan take ran alhaji usaini ya baci ya mike gami da haura takalman sa ya mike ya fice abin sa. Bayan ya komo gida sai ya kira bashir bangarensa ya ce masa, "bashir ina son ka samo duk yarinyar da kake so in aura maka, amma ka kyale maryam." Cikin fargaba ya kalle shi ya ce, "abba saboda me ka ce haka?" Ya ce, "mahaifinka ya ce ba za ka aure ta ba, kuma ka san halinsa bai ki a bata a sakamakon haka ba. Shi ya sa na ce ka hakura." 'A gaskiya abba ba zan iya hakura ba, domin ni babu wacce nake so sai maryam.' "bashir na san in na fadi magana ba ka musa mini dan haka yanzu ka yi mini afuwa ka hakura." "to ka fadawa ita maryam din in ta ce ta hakura da ni shi kenan, nima na hakura." Ya ce, 'a'a ai wanan ba magana ba ce, domin ba za ta iya hakura ba. Sai in kai ka fara furta ka hakura." 99 Kwadi Bari Jana "ai ba zan iya ba ne." Amina A. Sharada "ka taimaka bashir dan allah, saboda ba na son in sami sabani da dan'uwana." Tuni idanun bashir ya ciko da hawaye. Ya dube shi zai yi magana, amma ya kasa sai ya mike kawai ya fice yana ta kira, amma ya kasa amsawa ma bare ya dawo. Ganin haka sai ya kyale shi ya ce, "to komai na allah ne nì dai wannan lamari allah ya sa masa ruwan sanyi kar ya yi zafi." Shi bashir bayan ya tashi sai ya nufi dakinsa ya fada kan gado kawai ya saki kukan takaicin abin da zai iya biyo baya, domin shi dai ba zai iya rabuwa da ita ba, ko me za a yi masa dan haka sai ya kulle a ransa in har aka ce za a hana shi shi kuma ba zai yi auran ba. Yana nan kwance shiru, sai ga maryam nan ta shigo ta same shi a kwance bayan ta yi masa sallama ya amsa ta sami guri ta zauna. Shiru kawai ta kasa magana domin ita ma ya fada mata abin da ya fadawa bashir. Kiran sunan sa ta yi ya dago kai suka haďa ido, nan take gaban ta ya fadi, domin idansa ta gani ya yi jawur cikin sauri ta sauke na ta. Ranta ya bace, ta ce, "yaya kai ma ya gaya maka abin da ya gaya mini ne?" Ya ce, "ya fada mini yanzu maryam ya zan ył?" "mu je mu ba wa daddy hakuri mana." "baki san halin sa ba ne maryam ai sai in ya ce ya ki abu to ya ki kenan, sai hakuri." "yau mun shiga uku wai shin bashir ita rayuwa haka take ne? Wai a ce babu yadda za a yi mutum ya dauwama a jin dadi?" 100 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada "ai ba wani abu ne wannan ba jarrabawa ce ta allah in ka yi hakuri to imanin ka ya cika. Wannan yana daya daga cikin shikashikan imani guda shida da sai sun cika sannan imanin ka ya cika, wato wannan shi ne kaddara, duk abin da allah ya kaddara maka sai ka yi hakuri da shi. Wannan rashin yarda ta daddy haka allah ya shirya mana sai mu bi su a sannu har su amince in sun ki ya za a yi ai sai hakuri kwai." "mu hakura da juna kenan bashir?" Ya ce, 'ya za a yi?" 12 Hajiya jamila na zaune sai ga alhaji usaini shi ma ya sami guri ya zauna. Bayan ta yi masa sannu da zuwa, sai ta mike domin kawo masa ruwan sha mai sanyi. Bayan ya sha ruwan ne wanda aka sirya da lemo juice ya aje cup din ya dube ta yace, "hajiya jamila albishirin ki?" "goro." "zan samo miki abokiyar zama...." "wacce irin abokiyar zama kuma alhaji?" "wallahi wata yariya ce na gani zuciyata ta tafi akan yarinyar shi yà sama na ga ya dace in sanar miki, yarinyar tana da kirki ba ruwan ta za ku zauna lafiya." Duk tunaninta a zatonta maryam ce, shi ya sa yake kewaye-kewaye, dan haka sai ta ce, "wai a ina take ne alhaji?" "a gwale take haihuwar ta daya ta fito daga gidan miji, sai ta kama karatu ba ta yi aure ba har sai da ta kammala, amma dai za ki girme mata ba wai babba ce can. 101 1 d b Si 'y Π y Kwadi Bari Jana Amina A. Sharadu ba, za la yi irin talatin da biyu din nan." "oho! Ka ce ba ma budurwa ba cc? To 'yar waye kenan?" ne." "yar lalakawa ce, iyayenta ba wasu masu kudi ba Ta ce, "a gaskiya ya kamata ka auro 'yar manya domin mu goga da ita, in ka auro 'yar talakawa, ai ba zan san matsayina ba, domin na san na fita in ko 'yar masu kudi ce anan zan rabe da irin son da kake mini, domin ina da shi. Ita ma tana da shi, babu wani wanda zai nuna wa wnai tunkaho da abin duniya." Ya ce, "to ai ni ita na gani kuma ta yi mini, dan haka ni ita nake so." "a gaskiya alhaji ka sauya." Ya ce, 'yau zan ga ikon allah wai zamana za ta yi ko zaman ki?" Ta ce, 'zaman ka." "to in ni za ta yi wa zaman to ba zan sauya ba." "to shi kenan ai gata ga gidan nan sai ta zo ta zauna." Ya ce, haba jamila kin ba ni mamaki saboda allah ue ye na tada hakarkari haka?" "wallahi ban ga matar da za a yi wa kishiya ba ta una kishi ba." "shi kenan allah ya sanya alkhairi." "yauwa haka nake so. Shi kenan." Kwanci tashi har an sanya bikin halima. Murna a gurin su su baba abu ba a magana, ita ta zama uwa dan haka komai ita take yi, amma ta ce su je su gano gidan su yalwa, domin dole ne a ba su na su hakkin na iyaye. Haka ran halima bai so ba, domin gudun kar ya je ya gano wani abu da zai sa ya ce ya fasa, domin dai ita tarbiyar ta ce ta 102 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada bashi sha'awa har ya ce yana so kar ya je ya ga gidan na su, kuma baba an ce sune mahaifanta, ba wani abu take tunani ba sai matsalar kannanta da ta uwarta wato yalwa. Yau ce ranar da aka tsayar alhaji usaini zai zo halima ta raka shi gidan su wato can madile kenan, domin ya ga iyayenta saboda an riga an fayyace masa cewa baba abu kanwar uwarta ce. Tana nan tana ta faman-shiri har ta gama ta zauna zaman jiransa. Can da misalin karfe hudu da rabi sai gashi ya zo ya same ta ta gama shiri. Ya ce to su tafi. Ta yi wa baba abu sallama suka tafi abin su. Suna tafe suna hira har suka isa. Sannan ya tsaya ta shiga ciki ta sanarwa yalwa tare suke da wanda za ta aura. Yalwa ta yi murna sosai aka aka kintsa guri. Sannan aka ce ya karaso daga ciki. Nan ya shiga suka gaisa har ya tambayi malam usman. Yalwa tace dazun nan ya' fita masallaci zai komo. Nan dai halima ta gabatar da shi ga yalwa. Sannan ta gabatar da yalwa a gurin sa. Sannan suka shiga hira har malam usman din ya dawo daga masallaci. Malam usman ya tsufa ainun, da sanda ma yake tafiya. Yalwa ta ce, "malam surukin mu ne fa ya zo gaishe mu?" Ya ce, 'a to daga ina?" "har ka mance da wanda zai auri halima?" "at to na ji kuma to bari in zo mu gaisa." Alhaji usaini cikin tausayawa ya ce, 'a'a baba yi zaman ka babra in fito." Ya fito nan suka gaisa. Sannan ya fara yi musu rin nasihar su ta manya. Wato dattawa har wnai lokaci, ya sanya musu albarka. Sannan alhaji usaini ya kawo kudi masu yawa ya basu, suka ki karba. Sai da suka ga ya 103 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada matsa, sannan suka karba. Ita dai yalwa dan dai ta ga baba ya ki karba ne shi ya sa ita ma ta dan wuce ta yin, tana ganin ya karbe sai ita ma ta karbe. Nan suka yi sallama ya tashi akan cewa sai ya komo, domin bayan biki zai komo ya sake gaishe su suka yi musu addu'ar neman zaman lafiya. A hanyar su ta fitowa daga gidan ne sai ga asabe ta zo wucewa da gani a bige take sosai, domin har hada hanya take yi sai ko suka yi kicibis a soron karshe. Cikin sauri ta kalli halima yayin da gaban halima ya yi mummunar faduwa, domin abin da take gudun shi ya faru. Saboda bangazar kafadar alhajin ta yi ta wuce, amma a rashin sani cikin bacin rai alhajin ya ce, 'wannan wace ce?" Kunya ta kama halima sai ta ce, 'wata 'yar makotan mu ce da take zuwa diban ruwa a rijiya in an dauke na famfo." To fa ashe asabe ta jiyo sai ko ta dawo da baya ta danki kwalar halima ta danna mata ashar, "dan haka ta kazar baban ki ni ce 'yar makotan?" Ran halima ya yi mugun 6aci ta ce, 'asabe ni kike zagi?" Ta ce, 'an zage ki ke wace ce? Banza kawai dan za ki auri me kudi shi ne za ki nuna mana wariya har da wani cewa ni ce 'yar makota? To masomin taushiya dawa ke ma ai 'yar talakawan ce banza kawai." Nan da man sai idon halima ya ciko da hawaye, saboda bakin ciki. Tana ganin a lokacin da alhaji usaini yake cewa asabe ta sake ta yana kau da kansa, saboda warin tabar wiwi da ta shawo. Can kuma cikin gida su yalwa ne suka ji asabe na zunduma ashariya a soro sai suka 104 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada taho su ji me yake faruwa. Sai ko suka ga ta cakumi wuyan rigar halima. Alhaji usaini na ta fama da ita akan ta sake ta, amma ta ki. Wai wallahi sai ta fada mata ko waye uban ta tun da ta kawo wannan banza saurayin nata ita 'yar makota ce. Baba ne ya yi salati ya ce, "asabe me yc haka kuma?" Ta ce, 'ba..ba.. Abin da idanka ya gani shi ake yi." 'Sake ta dan iyayen ki, na ce ki saketa mana?" Ta ce, 'wallahi sai ta fadan abin da iyaycna suke ba cewa ta yi da wannan alhajin wai ni 'yar makota ce ba?" Baba ya ce, 'to ai gani ta yi ba ki da nutsuwa shi ya sa ta fada miki haka. Ai da kunya ta ce ke kanwarta ce....... Cikin tsawa ta tari numfashinsa. "to me ye? Ko cewa na yi zani gidanta? Wallahi in kin ga kafa ta a gidan ki ki yanke." Halima ta ce, "nima ba na so ki zo, domin ba ki da tarbiya ko kadan." Ta ce, 'ai ke ma ba tarbiyar ce da ke ba, domin kura ba ta isa ta ce da kare maye ba, gara nima duk iskancina ban taba. Yalwa ta yi kukan kura ta rufe asabe da duka tana tsine mata. Wannan ne ya hana asabe fadar abin da ta yi niya. Har dai aka 6anbare yalwa aka tura ta cikin gida. Sannan alhajin ya ce da halima ta zo' su tafi. Hankalin halima a tashe ta bishi suka tafi, har suka yi nisa ba ta iya magana ba. Kuma ba ta san hukuncin da alhaji usaini zai yanke ba. Sai da ya kai ta har kofar gida. Sannan ya cc, 'to ni zan wuce cikin." Cikin sanyi na kunyar abin da ya faru ta ce, 'to 105 Kwadi Bari Janu alhaji sai yaushe?" tga 1 Sharada Ya ce mata, 'zan dawo gobe da aagriba wato misalin karfe takwas kenan ko?" Ta ce, 'to shi kenan allah ya kai mu." Ta dai amsa ne, amma a tunanin ta ba zai dawo ba. Tana shiga ciki ta sami baba abu na zaune tana yanka dankuna sai ta sami guri ta zauna. Bayan ta gaisheta ne take tambayar ta ya su yalwan? Ta ce suna nan lafiya. "yana gan ki ido ya yi ja lafiya dai?" 'Baba wallahi yau asabe ta ci mini mutunci a gaban bawan allah nan kila ma daga yau shi kenan ya tafi kenan, sai dai a je a kai masa kudinsa." Ta ce, 'to wai me ya hada ku?" Nan take ta kwashe yarda suka yi ta sanar mata tun farko har karshe. Baba abu ta yi salati ta sanar da ubangiji ta ce, 'yanzu halima haka asabe ta koma?" halima ta ce ai baba, asabe ta wuce nan. Ta ce ai shi kenan ba laifin kowa ba ne laifin yalwa ne, ai shi ice tun yana danyc ake lankwasa shi, yanzu kam shirin asabe ai sai allah, domin ta rigaya ta gama fandarewa. Halima ta ce, dan ba ki ji abin da ta dinga cewa ba ne, wai duk iskancinta wai ba ta kai ni ba." "ki ce ma so ta yi ta gaya masa abin da ya faru dan dai yalwan ta kwace ta ne shi yasa?" Kashe gari halima tun takwas take zuba idon ganin alhaji usaini shiru ba-zo ba, duk minti daya sai ta duba agogo, har zuwa karfe tara. A nan ne ta fidda ran zuwansa ta ce, "baba kin ga bai zo ba, dama na ga da wuya in zai dawo." Baba abu ta ce, 'ai ni ma sai da na ayyana haka ai 106 4 Kwadi Bari Jana Amina A. Shurada nan gaba in kika kara samun wani saurayin ba zan kai shi ba, sai an yi auran kwaje in ba haka ba wannan la'anannıyar yarinyar ba za ta bari ki yi auran ba, ta fi so yadda ita ta ki auruwa take zaman sheke ayarta ke ma ki zauna haka. Saboda allah in ba ku yi aure ba sai yaushe?

Chapter 7 of 10