Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 10
ta ce, "hadawa bashir da maryam nake yi." Ita kuwa hajiya rukayya ba ta yi musu ba sai ta hada musu. Suka koma falo suna ci har ma ta ce ai wannan dama kara dankwan zumunci ne, su kuma suka koma can wani dan matsakaicin falo suka zauna suna сі, nan suka bar yaransu suna ci suna hirar su. Tsawar alhaji hassan ce ta firgita su kamar wanda ya ga gobara. Cikin. tsabar kidima suka tashi a guje domin ba su fahimci abin da yake cewa. Su kuma su hajiya suna zuwa falon sai suka yi turus wai ashe duk wannan fadan dan an hadawa. maryam da bashir abinci ne. Nan da nan ya fige maryam guri daya ya yar, sannan ya tashi bashir. Shi kuma bashir ganin haka sai ya ce baya cin abincin. Ai ko shi ne sanadin fadan yana cewa da hajiya jamila. 'Kin cuce ni wallahi kin cuce ni ni, saboda me za su kyale su har su shaku." Hajiya cikin bacin rai tą ce, 'wai alhaji me ya sa kake irin wannan abu ne? Ita yarinyar nan ba ka san irin baiwar da.allah ya yi mata ba, ya za ka bi ka tsani yarinya sai ka ce ba mutum ba? A gaskiya irin wannan babu kyau ka ga fa yarinyar nan tana sane da duk abin da ake yi........" "dakata malam an yi sai ki yi abin da za ki yi." in ji alhaji hassan. "wallahi akan yarinyar nan zan iya batawa da kowa, saboda haka maza a fitar mini ita daga gida, ai ban san ma da ita aka zo ba." 61 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada ana hayaniya. Cikin sauri alhaji usaini ya shigo, domin ya jiyo Ya same su ya ce, 'su waye ne? Me ye haka ne?" faru. Ya Take juya hajiya rukayya ta sanar masa da abin da ya tana ya kalli maryam ta rungume hajiya jamila girgiza kuka tana cewa, 'zo mu tafi gida mama." sai ya saki ka kai hada kawai ya cewa hajiya rukayya, "to ke me ya nasa." musu abincin? Ai sai ki warewa kowa "wallahi ban san zai yi fada haka ba, da ban hada musu ba, amma irin wannan ai ba kyau ya za a yi ka wannan, debi karan tsana ka zubawa yarinya karama kamar saboda allah?" mini Ya ce cikin fushi, "kin ga rukayya kar ki kara yi katsalandan a cikin harkokina ni ina da hujjar ta ta tsanar wannan yarinya dan haka kar ki kara yi mini wata magana a kanta." ta ce, "to shi kenan alhaji, amma na ga ai kai ba jahili ba re da iliminka bai dace a ce ka na irin wannan ba." Ya ce, 'na dai gaya miki dan haka sai ki zabi na zaba kodai ki daina shiga sabga ta kan maganar yarinyar nan ko kuma in s36a miki." Cikin fushi ta ce, "in dai akan wannan yarinyar ne na daina magana insha allahu daga yau." Haka suka gama yininsu suka tafi. Su hajiya jamila na ta faman mamakin alhaji hassan. Ta ce a ranta, "ai wannan gara ma da allah ya sa ba shi ne mijina ba da ba zai bari in dauko yarinyar nan in rike ba." 62 a Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada 6 Al'amarin halima kuwa bayan ta bar jaririyar ta tafi gida gudun kar a ganta a gane abin da ta yi sai ta bi wata 6arauniyar haniya wacce za ta iya kai ta gida, ta yadda babu mai iyay ganinta. Ta ko yi kicibis da wani famfo shi kadai a wajen; sai ta wanke jikinta. Sannan ta wuce gida. Yalwa nà zaune tana ganin shigowarta sai ta mike zumbur. mata. ba "kin haihu?" Ta gyada kai cikin fargabar abin da za ta -ce "ina yarinyar take?" 'Na kashe kamar yadda kika umarce ni." 'In ce ko dai kin tabbatar babu wanda ya ganki/" "na tabbata babu wanda ya ganni, domin gurin kowa." "yauwa shi kenan mun rabu da kaya, sai kuma allah ya kiyaye gaba kar kwadayi ya kara jan mu mu sake afkawa a cikin nadama. Au! Me kika haifa?" "mace na haifa, amma suna kama da jamilu." 'To me ye na wani suna kama ina ruwanki da kamar ta su? Ke in har kina da hankali ma har kya wani kula da kamannin ta? Yaran da ya nuna bai san mu ba, ko dai ba ki kashe ba ne?" "na kashe mana." "a to in kika barta kin shiga uku in aka gane, domin ke za a rike babu ruwana." "ai ba wanda ya gani." 63 Kwadi Bari Jána Amina A. Sharada Cikin dole take maganar, domin jikinta ba dadi. Allah-allah take ta je ta kwanta ta huta. Sai yalwa ta lura da yadda take jan jikin nata sai ta ce, "je ki ki yi wanka ga ruwan zafi nan akan murhu, da zafi sosai idan kin yi wankan sannan ki kwanta." ta ce to. Bayan ta yo wankan ta sanya kaya sai ta shiga daki ta kwanta lamo tana tunanin 'yar ta da ta bari tana cewa a ranta. "ko yanzu tana nan tana kukan, ko an sami mai daukar ta? Oho. Kila ma yanzu ta mutu." tana wannan tunanin sai hawaye ya zubo mata ta fara kuka a 6oye dan kar ta jiyo ta. Tana cikin kukan ne sai ga yalwa ta shigo, nan da na sai ta goge hawayenta. Bayan yalwa ta shiga ne ta zauna ta dube ta ta ce, "halima ni yanzu abin da na ga yafi sai ki tattara kayan ki ki koma can gwale gurin kanwata abu mai danki ko kya sami miji a can, kin ga anan babu wanda zai aure `ki da wannan abin kunyar kin san halin kauyen nan namu ga surutu da zagi kuma ko da a ce wani ya fito neman auranki ba za a bar shi ba sai zoge shi. Don haka ki koma can ki yi zaman ki kin ji?" Ta ce, "nima yalwa sai da na ayyana a haka na ga kamar ba za ki aminc eba, shi ya sa ban gaya miki ba." Ta ce, "dane me ba zan amince ba, bayan na san irin halin da ake ciki? Yanzu dai abin da za a yi ki shirya ki tafi tun kafin jama'a su san cewa kin haihu kin ga sai a ce tun tafiyarki ba ki komo ba." 'To, amma sai dai da daddare in na dan ji kwarin 64 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada jikina, domin yanzu ba zan iya zuwa ko'ina ba." "ai dama sai da daran kya je yanzu zan sa asabe ta hada miki kayan ki tun da ba za ki iya hadawa ba." Tana gama fadar haka sai ta kirawo asabe ta ce, "zo ki hadawa halima kayanta a nan dakin in ya so sai ki kai mata bakin titi da dare, sai ta tafi." Asabe ta ce, "yalwa ina za ta je." "gidan abu za ta can gwala ta zauna." Sai asabe cikin tausayawa ta ce, 'a gaskiya halima ke kika yi sake tun farko ai ni wallahi ba ma zan taba bari ciki ya shiga jikina ba tun yaushe muke tare da usman mai gyaran babur kin taba ganin wani abu ya faru tsakanin mu? Sai ke kawai ki saki jikin........." yalwa ta katse ta ta hanyar tsawa ta ce, 'wato dan uban ki ke ma iskancin za ki yi har kike wani tutiya da usman mai gyaran babur? To ina kudin da yake ba ki?" duka. "kashewa nake yi." Ai jin cewa tana kashewa sai yalwa ta bita da "wato almubazzaranci za ki dinga yi babu adani ko?" Nan da nan sai mamaki ya kama halima wato yalwa ba ta yi bakin cikin abin da asabe ta fada ba sai bakin cikin kudin da ba ta kawo mata? Ta ce lallai yalwa ba ta saduda ba, kawai abin da za ta yi sai ta bar musu gidan su ta daina bakin ciki, domin gidan ba gidan zama ba ne, in har suna tare da yalwa za ta iya jefa ta wata hanyar kan san kudinta. Dare na yi yalwa ta bawa asabe kayan halima a 65 Kwadi Buri Jana Amina A. Sharada boye ta fita zuwa can bakin titi ta tarar mata adaidaita sahu ya kawo wasu mata ya aje su har kofar gida ta kawo su. Halima ta yi sallama da mutanen gida har da babanta shi ma ya yi farin cikin komawarta can gwalen, kuma ya yi mata fada sosai akan kar ta sake shashanci irin na da ta zamo mai kamun kai. Sannan ya sanya mata albarka. Suka yi sallama hawaye na zuba a idon halima ba dan komai ba sai dan tausayin babanta, wanda a kullum girma kara kama shi yake yi, kuma ga shi kullum gidan ba kwanciyar hankali sai kara 6ata masa rai ake yi. Tana zuwa gidan baba abu ta yi sallama, safiya 'yar gidan baba abu na ganin halima sai ta tashi da gudu ta taryo ta, ta rungume tana tsallen murna. Baba abu ta leko da sauri tana ganin ta ta ce, 'wa zan gani a gidan nan? Lallai ma halima sai yau?" Halima ta shiga daga ciki ta zauna. Sannan ta gaida baba abu. Baba abu ta ce, "yanzu da daddaran nan in çe ko dai kalau ko yalwa ta yi tsiyar ne?" Ta ce, 'a'a lafiya kalau sun ce ma in gaishe ki." "ina amsawa?" Sannan ta dubi halima ta ce, 'wai yana ganki haka ina cikin kuma?" Nan take halima ta kwashe abin da ya faru da haihuwarta ta gayawa baba abu da kuma yadda ta bar 'yar da rai dama shawarar da suka yanke da yalwa cewar ta komo gurin ta ko ta samu mijin aure duk ta sanar mata. Nan da nan baba abu ranta ya yi matukar baci ta ce wai me ya sa yalwa take haka ne? Kullum sai rashin 66 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada mutuncinta ne yake karuwa? Ya za a yi a jefar da dan mutum sukutum, saboda allah? Haba halima ke ma kin yi wauta anan." Ta ce, 'baba wallahi yalwa ce ta ce kar in komo mata gida da jaririn ita cewa ta yi ma in kashe ni ce dai na ga ba zan iya ba shi ne na ajiye na taho na bar ta a can." "don ubanki da ta gaya miki ki yar ba sai ki gudu gidana da jaririyar ba? Ai ko ni na rike ai 'ya ba ita ce da laifi ba iyayen ta ne masu laifi." Nan da nan sai halima ta ji kaunar baba abu ta kara shigar mata rai, domin nuna cewa tana san 'yar da ta haifa. Sai ta fara da ta sani da ta kawo mata 'yar tun farko. Baba abu ko har yanzu fada take yi. "halima kin yi wauta wallahi sai ka ce akan ki aka fara? An sani wannan abu babu dadi, to amma tun da ya faru ya za a yi ai sai dai kawai a kiyayi gaba, amma ba kya yarda da sukutum kamar dabba ba. Kai ko dabba ba za ta yi abin da kika yi yanzu ba, wallahi yanzu in ba wani ikon allah ba ke ba 'yar nan har abada, kai wannan bakin ciki da yawa yake." Halima cikin shashshekar kuka ta ce, "baba ko cigiya za a yi a ji ko wani ya tsince ta?" "dan hauka, wato ki tonawa kan ki asiri kenan ki janyo mana dauri domin wannan abu da kika yi ya zama dole ya zama sarri in ba haka ba kin shiga uku har da mu." Safiya ta ce, 'wallahi abin dai aunty halima babu dadi, to amma komai mukaddari ne haka allah ya so." 67 Kwadi Bari Jana Amina A, Sharada Baba abu ta ce, "tashi ki kai mata jakar daki sai ki hado mata abinci ta ci tukunna zuwa da safe mu ga me ya kamata ta yi game da wankan jegon in ba haka ba ai sai ta kumbure ko ta yi wankan ko kuma ta sha magani. Kai gara ma maganin domin wankan tonan asiri ne." Haka dai halima ta ci gaba da zama gidan baba abu ta yi bulbul da ita da yake babu wani abin da yake damun ta kyanta ya kara fitowa, domin tun da ta sami ciki take cikin bacin rai ga shi ta yi duhu. To yanzu babu wani abun da yake damunta sai dai ta wanke goma ta tsoma biyar, dan aikin gidan ba wani mai yawa ba ne, kuma su biyu suke yi wato ita da safiya. Ga shi safiya na koya mata karatun alkur'ani mai girma, har ta yi nisa. Baba abu ta ce, "in kin yi arba'in zan saki a makarantar gidan galadima ki yi karatunki na firamare da sakandire, domin wannan abu da ya faru ma da rashin ilimin in da a ce da ilimin wani abu ma ba zai faru ba." Halima ta yi ta faman murna jin cewa za a sanya ta a makarantar boko, domin tana da sha'awar ta yi ilimin ita ma. Watan ta biyu a gidan baba abu ta shiga makarantar gidan galadima har shekara shida. Sannan ta yi jarabawa ta ci gaba da secondary duk a can ga shi kuma tana da kwazo sosai. Kuma duk abin da ya kamata a saya da ma sauran matsalolin makaranta baba abu се mai yi, domin kuwa baba abu tana da sana'ar ta ta dinki da saka har ya kasance ta yi suna a gwale, duk inda ka ce kana neman gidan abu mai dinki za a kai ka. Baya ga 68 Kwadi Bari Juna Amina A. Sharada kwarewar ta akan dinkin har ma dinkin 'yan makarantar nursery take yi a kawo mata kwangilar hukuma makarantar ta biya ta. Sannan ga shi tana da satifiket na kungiyar mata manoma, domin tana dan taba noman rani da damina kuma ta yi noma sosai dan haka baba abu ba wata mai wadata ba ce, amma akwai rufin asiri sosai. Sannan mai gidan ta ya rasu, 'ya'yanta biyu kacal wato ta fari sunan ta saudat tana aure a tukuntawa, 'ya'yanta uku wato akwai ummi ta farin, sai sadik mai bin ta. Sai kuma kabir mai sunan baban alhaji dahiru mijin ta. Tana sana'ar sayar da lemon kwalba wato mineral. Sannan kuma tana kulla so6o. Tana kuma yin cake da cincin da dubulan da alkaki wato dai ita ma sana'arta take sosai. Kun san an ce ba a maraya sai rago shi ya sa rashin mahaifinsu bai sa sun shiga matsala sosai ba, domin suna da sa'anarsu ta rufin asiri. Ita kuma safiya ta kusa gama makarantar sakandire dan haka auranta za ta yi, dama tana da tsohon saurayinta tun tana primary ga shi yanzu suna tare, har secondary in ta gama za a yi mata auran ta domin har an. sa musu rana. Duk sanda halima ta sami dogon hutu takan je gidan su, domin ta gaida iyayenta wato su yalwa da malam usman abin takaici har yanzu babu abin da ya sauya a gidan nan game da nutsuwa kullum in halima ta je da abin bacin ran da za ta tarar a yanzu haka su auwalu sun maida kan su kamar sarakunan arna, ban da shaye-shaye da neman matan banza ba abin da suke yi sai ka ce karnuka sata ko kamar beraye. Tun suna sace 69 Kwadi Bari Jana Amina dSharada kajin dane mutane da agwagi yanzu ta kai su su bi dare su Ssacı akuyay ko tunkuya su sayarwa da mahauci ya ba su dan abin da bai taka kara ya karya ba Yanzu sun sn tolitisZ SO 59 !ln 2nI JgUS buwayi gari kowa sai allah wadai yake yi da wannan Yrа sx yalwa is202, Asabe воa kam ba miji, domin tabshiga hanyarபயம் banzą, ga எம் shi ta gandame duk wanda ka gan su tare fo Ба eure De ya kawo shi ba zuwa ya yi ya hole ya lalnn SWEDUயர் wadannan abubuwan su suke damun halima har a 0 a 7zo gidan. Ga yalwa da malam usman sun kara Isul ullum karfi na dada karewa, ga babu wani mataimakı sai allah olsw sdк поl ab s62 16'ns2 am піх виma halima ce ta yi shirin la tsaf za ta gaida Yau su yalwa, Sai baba abu tata bab ta kayan miyada su 0961 shinkafa danya kwana uku ta ce ta kai musu. Sannan ta 162 6VEL E ЕU 30 DS E2 0 saya musu goro da su sabulu da omo, domin ba komai yanzu sai wahala. Tun da ita kuma ta sha kwanar gidan take jin tashin kidan zamani kamar wani hotel. To amma Was BM B da yake ba a raba matasan samari da wannan ba ta damu полог в ba Kai tsaye ta shiga cikin gidan domin ita da kanta kai 18 st musu abin da baba abu ta bayar a kawo musu. Ta shiga 48 ம shagon gidan domin ta sanar musu ta zo. Me za ta gani? Hayakin tabar wiwi ne ya yi dan karamin gajimare a saman dakin. Sai da ta toshe hanci, ta dan jima sannan EDidanta ya gane mata wasu 'yan mata su biyu bisa gado kowacce daga ita sai shimi iya gwiwa suna busa hayaki. A nan ta gane cewa yawan da suka yi shi ya sa har hayakin ya zama tamkar girgije a dakin. Kuma kowacce kanta bisa Kirjin sauryain ta. Warin tabar wiwin ne ya sa ta saurin fita daga dakin ba tare da ta iya cewa komai ba. タン 70 Kwadi Bari Janа Amina A. Sharada 'Yan matan nan suka ce da su auwalu, kai wannan wacce ajawowa ce take sa mana ido. Suka ce wallahi wata aunty din mu ce ai duk abin da muke yi a gunta muka samu. Ai ko sai 'yan amtan nan suka kece da shewa da ihu suna cewa, "sai aunty." Cikin bacín rai ta shiga cikin gidan tana ta faman fada. Sai ko ta yi kicibis da asabe ta ci kwalliya ża ta fita, sai ta tsaya da baki a sake tana kallonta ta sanya wasu damammun riga da siket na atamfa wadanda suka matseta sosai. Tsagar siket din ta kai kwarin gwiwarta ta baya. Kanta babu dan kwali ta yi karin gashi an.yi mata kalba kanana sun zubo har bayan ta. Bakin ta da kan idonta duk ta fante da janbaki ruwan toka ga wani ta kalmi mai shegen tsini wanda ya kara mata tsayi. Dinkin rigar kuwa iya cibiya, gashi da gani sai da ta dauke numfashi sannan ta sa su har sike din. Kallo daya za ka yi mata ka zaci ba musulma ba ce. Halima ta yi karfin hali ta ce, "ke kuma ina za ki haka?" "fati za ni?" 'Amma ki rasa kayan da za ki sa ki je fatin sai wadannan? Haba asabe don allah ki dinga sanya kayan kirki." "kai halima yanzu me ye laifin wadannan kayan? Ai sune suturar duk wacce kanta ya waye, amma wacce kanta bai waye ba ita take sanya manyan kaya. Ina nake iya sanya wannan kayan." ta kama less din jikin halima. 'Sai ka ce wata jakadiya ai wannán sai ku." Ta juya ta na cewa, 'na tafi in kwana za ki yi in 71 } Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada na dawo ma gaske, domin ina zaton sai kusan daya na dare zan shigo yau." Cikin bacin rai halima ta finciko ta ta baya tana cewa, "ke yanzu ba a isa a gaya miki ki ji ba? To koma ki cire wadannan kayan ki sanya na kirki in ba haka ba yanzu ranki ya baci kin ji ko?" Asabe ta kalleta a yatsine ta ce, 'kin yi haliman nan ni da allah cika mini wayan riga kar ki yamutsa mini guga ke lokacin da kika yi ta ki holewar waya sami kí ido? Sai nis za ki takurawa wai ke ga ustaziya to karatun na ki na ga ai na bayan an gama holewa ne, kuma yanzun ma ba a hanaki ba, dadin ma rashin dabara ne da wayewar kai shi ya sa kika dauki cikin, amma yanzu da kina yi amfani da magani ai babu abin da zai same ki ga shi ni yanzu ina ta sha'anina ba wani abu." Tana gama maganar ta sai ta yi waje abin ta ta bar halima nan tsaye cikin bakin rai sororo. Sai ta yi ciki da gudu tana kuka. Ta sami yalwa'a zaune ta ce, "yalwa muddin ba za ki dinga tsawatarwa yaran nan ba zan daina zuwa gidan nan, domin ba zan zo ina ganin irin wannan takaicin ba." Yalwa ta ce, "me kuma suka yi miki uwar korafin tsiya ke dai ba dama ki zo ki ga yaran nan sai ki dinga tonan su da fada, to muddin bab ki ja girman ki ba za su raina ki a banza.". To ashe duk abin da suke yi a kunnan malam usman ne yana daga dan dakinsa a kwance da ke bashi da lafiya shi ya sa baya magana, to amma jin yadda suka yi da kuma abin da yalwa ta ce sai ya sa baki ya kira 72 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada halima. Ta zo ta tsugunna bayan ta gaishe shi ta kuma cc, "baba abu na yi maka sannu da jiki." ya ce yana amsawa in ta je ta gaida ita. Ta ce to za ta ji da kyau. Sannan ya ce, "abin da ya sa na yi kiran ki shi ne duk abind a kuke yi ina jin ku, dan haka nake so in gaya miki daga yau in har kin zo gidan nan kika ga suna yin wani abu to kar ki kuma yi musu fada kar ki sake yi wa kowa magana kowa ya gyara halinsa, kyale su kowa duniya za ta gyara shi, gani suke yi fadan da ake muşu kamar ba san su ake yi ba shi ya sa." Ta ce, 'to baba waye ma zai musu fadan duk fadin unguwar nan? Dama kai kadai ne, kai din ma kuma in ka yi ba sa ji." ya ce, "wannan mahaukaciyar uwar ta ku ai ba san a yi musu fadan take yi ba, in ta ji ana yi musu fada sai ta ce wai an takura musu. Ke dai ki tayani addu'a musamman akan asabe, domin ita mace ce gara su maza ne." 'baba ai ba gara su din in riga an san halin su wa zai ba su 'yr su su aura? Ka san dai ana ganin kashi da rana ba za a bari a taka ba?" su." Ya ce, "wannan haka yake allah dai ya shirya 'Amin." Sannan ya ce, "wai ni halima yau she za ki yi aure ne kin ga fa ko asabe ta isa aure tuni, bare ke halima." "baba zan yi ne kai dai ka yi ta yi mini addu'a domin ina so in sami nutsatstse mai hankali wanda in mun yi auran zai rike ni da daraja ba wanda zai koro ni 73 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada nan da nan ba, ka san tun da abin nan ya faru ba kowa ne zai iya jurewa ya kyaleni a gidan sa ba, in har ya sami wannan labarin kila za su iya koro ni ka ga kuwa in na sami mai hankali zai iya hakuri ya bar ni domin na san zancen duniya baya 6oya komai jimawa wata rana sai zanan nan ya fito." 'Haka ne allah ya kawo na gari." 'Amin baba." Ya ce, "kin gama karatun ne?" Ta ce, 'e to na kusa dai ina gama secondary, to amma in dai ban sami mijin ba zan ci gaba da karatuna ko diploma in samu na yi, in samu wani dan aikin." Ya ce, 'to shi kenan allah ya taimaka." ta се, 'amin baba." 7 Alhaji hassan ne zaune a falon alhaji usaini gefe kuma hajiya jamila ce da alhaji usaini da kuma bashir sun yi kasake suna sauraron abin da alhaji hassan ke cewa; 'Abin da ya kawo ni ina so ka bani bashir zan kai shi misira ya yi karatunsa a can, domin can, nake bukata in kai shi." Babu ko musu alhaji usaini ya ce, "to shi kenan alhaji ai wannan babu komai zai tafi." Daga ganin fuskar bashir ka san cewa sam bai so wanna tafiya ba, dan dai yana matukar tsoron uban ne sai ya amince bisa dole. Alhaji usaini ya tambaye shi, "yaushe za a yi tafiyar?" Ya ce, "ai ya gama komai gobe-goben-nan ma 74 Kwadi Buri Jana zai zo a tafi." Amina A. Sharada "to shi kenan allah ya kai mu." Sannan ya tashi ya fice suka raka shi har bakin motarsa wato bashir da alhajin. Hajiya jamila na shiga cikin dakin sai ta sami maryam tsuru a rakube a jikin bango ta ce, "au ke kuma me ki ke yi anan? Ai ya tafi sai ki fito." Ta mike jiki na rawa ta ce, 'umma ina na ji ana cewa bashir za shi?" Ta ce, 'bashir misra za shi karatu in ji abbansa." tana jin haka sai ta dafe kirji ta fice da gudu ta bar hajiya jamila a tsaye, ta yi 6angaren bashir. Hajiya jamila ta ce, "oho! Ni jamila wadannan yara sun shaku da juna ga shi alhaji hassan sai sa musu birki yake ta faman yi to yanzu ya za a yi? Ai sai hakuri." Ita kuwa maryam na shiga dakin bashir sai ta same shi zaune a gefen gado ya yi tagumi kawai yana tunani sai ta ce masa, "yaya bashir wai misira za ka je?" Ya daga kai kawai ya kalleta, sai ya kasa ba ta amsa, domin yana ganin idon ta duk ya cicciko da hawaye. Sai ta ce, 'yaya yanzu ba yarda za a yi a hakura da wannan tafiyar?" "to ya za a yi maryam tun da ya ce sai na je ai sai na je kin san halinsa." Tana jin abin da ya ce sai ta durkushe kasa ta saki kuka. Ya ce, 'ki yi shiru maryam kar abban nan gidan ya zo ya ganki ki na kuka in ya tambave ki me za ki ce masa?" Ta ce cikin shashshekar kuka, 'a gaskiya yaya 75 Kwadi Bari Jana Amina A. Sharada mun riga mun shaku to sai yaushe za ka komo?" Ya ce, 'ni kaina ba so nake in tafi in barki ba sai dai dan babu yarda zan yi ne." lokaci. Nan dai suka yi ta tattauna lamarin har wani Can kuma hajiya jamila ce zaune a falon alhaji usaini suna hira. Inda hajiyar ki cewa alhaji, 'anya kuwa ba wata soyayya tsakanin yaran nan?" Ya ce, "suwa kenan?" "bashir da maryam mana." "kai haba me kika gani?" Ta ce, 'to ai gani

Chapter 5 of 10