Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 10
amsa, Zama Goggo tayi sanan tace       Bari shi yazo idan tsoron ta yake mu ba tsoron ta muke ba,ta turo shi yaron yazo ayi musu aure.       Zai dai fi Goggo,tunda yarinyar nan ba tsoron baccin ran mu take ba, duk kwanakin da na d auka bana mata magana a banza, yau tana fita sai da ta tsaya a wajen sa.          innullahi wainna illaihi rajiun. Ummi ta fad a tare da d ora hannu akanta,wanan wane irin mai sa ido ne yake mata wanan mummuna binciken?       ba kyajin Goggo tazo ne, ko ita zata shigo ta gaisheki rik ak iyya?.        Hajiya ta fad a daga nan tsakar gidan  kaya nake cirewa.   Ummi tafad a a ranta tana cewa kamar Hajiya ce yar Goggo sabida yan da halin su yazo d aya.      jiki ba k wari ta gama cire kayan sanan ta canja zuwa riga da wando kasancewar yanayi zafi da ake fama dashi, haka ta fito tsakar gidan kamar mara laka a jiki,daga nesa ta tsugunna k asa tare da cewa      Goggo sannu da zuwa,ina wuni.  ke za ai wa sannu,uhm uwar masoya. Googo tafad a tana tab e baki,kallon ta Ummi tayi a ranta tana cewa wanan tsohowa da kinibibi take, kitchen Ummi tashiga ta zuba abinci, tana cikin ci Abba yashigo gidan sakamakon kira da Goggo tasa Hajiya tayi masa, sai da suka gaisa da Hajiya sanan tace         Kaga Kamalu a matsayina na mahaufiyar ina baka Umarni akan cewa maza maza yarinyar nan tafito da miji ayi mata aure,domin bazan zauna ka zuba mata ido ba tunda ta zab i kule kule maza.          aure kuma Goggo duka duka yaushe Ummin ta ta girma.     Abba yabata amsa cikin tausasawa   to indai bazaka yi mata aure ba inaso a yanzu a gabana ka haramta mata kula kowanne namiji,fita indai ba muhimmiya bace.     daman wanan shine plan d in da suka shirya da Hajiya     gyada kai Abba yayi sanan yace    toh Goggo. Ummi ce ta tareshi da cewa    a ah Abba nazab i ayi mun auren. kallon ta sukayi gaba d ayan su, Hajiya cikin t sananin tashin hankali tace       Ubanki Ummi nan zaki zo kiyi mana maganar banza.        Hajiya akan kuce zaku rabanj da Yaya Mukhtar gwanda kuyimun auren kawai.       Au har yazama yayanki? wace uwar ce ta haifa masa ke?.      Abba ne ya katse Hajiya da cewa   Saliha me kikeyi hakane?. sanan ya juya ga Ummi yace        kinsan abinda kike fad a kuwa?,Aure ba abu bane na wasa Ummi, sanan ba a kowane mataki ake yiwa yarinyar aure ba,bikiga yayarki Nafisa ba, saidai ta kammala diploma a k aramar jami ah,sanan akayi mata aure,kuma bikiga wanda ta aura ba?, mutumin arziki duk sanadiyar tayi ilimi ne.            Abba nima a yanzu nayi ilimi fiya da mata da yawa,kuma idan cigaba da karatu ne ana cigaba ko a gidan aure ne.        Ubanki Ummi shegiyar yarinyar da rashin kunya.      Goggo ta kat se su      to Goggo ina laifin yarinya anan da yahuce na Ubanta da bai tashi ya kwakwad e ta ba.     Hajiya ta fad a ta na makawa Abba da Ummi harara          Ummi ba yanzu za ayi miki aure ba,ki maida hankali akan karatun ki, Allah yayi miki albarka. cewar Abba yana niyar tashi      A ah Abba dan allah ni dai ayimun. tabbas lamarin Ummi yafara bawa Abba mamaki,dagaske dai auren take so!      Abba kayi shiru dan Allah. kallon Ummin yayi sanan ya kalli Goggo da Hajiya       Ummi kice masa yazo ya sameni. daga haka ya fice,Ummi ma tashi tayi ta shiga d aki abun ta,Hajiya kam kallon Goggo tayi sanan tace        Goggo kinji shi kuwa?.  najishi Saliha, yanuna yarinya yarsa ce ba ta wani ba.       chab da sake wallahi tallahi.   Hajiya tafad a tana mikewa tsaye      Ummi bata iya bacci ba sai da ta sanar da Asiya wanan labari,Asiya tayi farin ciki sosai da sosai sai dai tana ganin Har yanzu Ummi ba ta fuskanci TUDU AKAN KWARI da take k ok arin d orawa ba,wanda tsallake shi abu ne mai mugun wahala .      Asiya na nan zaune tana tunanin mafita wa Ummi Halima ta shigo cikin gidan,hannayen ta rik e da manyan ledoji guda biyu,Kallo d aya Asiya tayi mata ta d auke kai        Ke yar matsiyata wa kikewa kallon banza.        Halima tafad a tana wata uwat jijjiga  Banza nake wa.     Asiya tabata amsa ba tare da ga d ago ta k ara kallon ta ba,da gudo ta tawo tayi kan Asiya daniyar zane ta domin tsabar neman tashin hankali yasa ta manta da heels din takalmin dake k afarta,jikake Tum tafad i a k asa, da sauri Anty tafito tana fad in     nashiga Uku ni Atine,dawa Allah ya had ani idan ba mat siyata ba, banda bak in ciki shine zaki kadata anan wajen.     Mamace tafito da d aki domin tasan bak aramin aikin Anty bane tace zata daki Asiyan da ko motsim tashin ta ba aji ba,fitowar ta yayi dai dai da k ok arin kai dukan da Anty ke shirin yiwa Asiya    A ah a ah Atine karki fara,wallahi tallahi. page[13&14]               Atine nafara gajiya da mugayen halayen ku a cikin gidanan h akurin da nake dake bafa na dole bane,sanda muke zaune dake k ark ashin inuwar miji d aya ne yazama dole,shirun da nake miki na mutunta wane amma tunda kinga bakya son hakan,Atine kitarka ta naki ya naki ki barmun gida.       Mama tafad a cikin b acin rai,ita kanta Anty tasan ta b atawa Maman rai domin duk zaman da suke Mama bata tab a cewa ta bar mata gida ba,ko yaran ma da suke cewa tabar musu gida Maman hanasu take to amma yau da kanta.       kinga sahura zancen na barmiki gida bai taso ba domin munzama d aya,kuma daman zaman duniya ai zo mu zauna zo mu sab a ne.     Murmushin takaici Mama tayi duk da daman ita ma d in bawai dan tabar gidan take magana ba kawai dole zaita mata baraza nane  zo mu sab a d in to Atine ni nagaji da wanan sab awar, dan haka kika kwashe naki kiyi gaba Allah yahad a kowa da alheri.          Sahura zo kiji. Anty tafad a tana kama hannun Mama zuwa cikin d aki      Sahura idan nabar gidan ina na kama,kinsan bani da kowa sai Allah sai ke, kuma kinga ni amanar mai gidan muce a wajen ki tunda kece babba,kiyiwa Allah kiyiwa ma aiki ki hak uri.           shikenan yahuce amma gaskiyya ki fata harkar auta ta,domin nasan Umar dai dai ke ne.        tom nagode.   Anty ta fad a tare da tashi ta fice zuwa nata d akin,Halima ta rufa mata baya.     Washe gari  Asiya da farin ciki tashiga gidan su Ummi nuna mata sabuwar keypaf da yaya Umar ya siya mata sakamakon rubuta jarabawar jamb da zasuyi,sai dai labarin da Ummi ta bata ya dakatar da wanan farin ciki daga  fuskar ta        Ummi wai kina da hankali kuwa?.  Kamarya ina da hankali. Ummi taba wa Asiya amsar tambayar da ta mata       Ummi banga alamun kina da hankali ba da har zaki fifita soyayyar wani akan ta mahaifiyar ki,Ummi kinsan mahaifiya kinsan girman mahaifiya.            Nasani Asiya amma wanan magana ake ta rayuwa ta gaba d aya, ko zan zauna ne a gidan suyi ta kallo na.      Girgiza kai Asiya tayi sanan tace   A ah Ummi baza su so suyita kallon ki ba kisani Ummi har yanzu yara ne mu, ba mukai cikakken lokacin da xa ace har munyi fito na fito da iyayen mu akan maganar aure ba.         Asiya ba fito na fito nayi da iyayena ba,alfarma na rok a wajen mahaifina.     murmushi Asiya tayi sanan tace   Ummi kisani wanan TUDU AKAN KWARI daikike k ok arin d orawa abune mai matuk ar wahala wajen tsallakewa, wanda a k arshe ma ba tsallakuwa zai ba,wahala zaki sha ki hak ura.         Asiya wane irin mugun baki kike mun,Asiya kar dai ace bak in ciki kikemun.         Kinsani bazan tab a zama mai bak in ciki a rayuwar ki ba Ummi,sai dai mai goyan baya da baki shawara akan rayuwa Ummi, Dan allah ki nutsu kiyi tunani mai kyau.      murmushi Ummi tayi sanan tace  Asiya nayi duk wani tunani da yakama ta nayi,Aure baitaba zama haram ba,kuma bai tab a zama rashin biyayya ba.          tashi Asiya tayi ta matso kusa da Ummi tare da d ora hannun ta a kafad ar ta         shikenan Ummi Allah ubangiji ya tabbatar da alheri,sanan inaso ko wane hukunci Abba ya yanke miki bayan ganin Master ki kasance mai biyayya tunda shima ya numa biyayya kuma hak in mune biyayya ba su ba.        rumgume Asiya Ummi tayi sanan tace  Insha allah Asiya nagode.         Ungo wayar kirashi Tunda kina da number din sa.      karb a Ummi tayi ta saka number da take haddace akan ta tatafi kira.    ______MASTER_______       zaune yake tare da yaran sa cikin mai t sakaicin gidan dayake naso, ko wanne yana sabgar gabansa,wasu na bushe bushen hayak in su wasu na nad e nad e.      Wayar shi tashiga ruri alamun kira nashigo wa,ganin bak uwar number yasashi d an jan lokaci kafin ya d aga.       Sasanyar Muryar tace ta daki dodon kunen sa        Assalamu alaikum.  Amincin Allah ya tabbata a gareki yah Ummi.       dariya tayi kafin tace   Ya akai ka ganoni.        Haba Ummi na me zai sa nakase gane wanan zazzak ar muryar taki.       dariya tayi sanan tace  Toh baka amsa sallaman ba.        Amin wa alaiki salam. dariya tayi jin yanda yaraba amsa sallaman sanan tace      Yaya barka da safiya fatan kayi bacci mai dad i.      mai dad i tare da mafarkin ki,sai dai rashin sake ganin ki jiya ya rage mishi dad i.      dariya Ummi tayi sanan tace  Yaya albishirin ka?.      Goro fari sol Ummi nah. ya amsa cikin zak uwa domin baitab ayin waya ta soyayya ba sai yau,wani irin farin ciki yakeji,wani irin yawo zuciyar shi nayi a sararin samaniya       Yaya ba yanzu zan fad amaka ba sai mungama waya.       dariya yayi sanan yace   Ai girman kine ranki yadad e, amma wanan wayar ta wace?.        Wayar Asiya ce,jiya yaya Usman ya siya mata kasan zamuyi jamb.        Nasani Ummi na saura kema ko?. yak areshi maganar da alaman tambaya      Nasani Abba zai siyamum kafin lokacin,yaya baka k arasamini labarin ka ba.       Ummi anjima idan mun had u zan k arasa miki.      Toh yaya amma kasan me?. girgiza kai yayi kaman tana kallonshi sanan yace     A ah.  Abba yace yana son ganin ka,za ayi mana aure.     Kaman saukar arado haka yaji maganar tata,sanan tafara masa amsakuwa a kunne, da k yar ya iya cewa       Ummi na banason wasa. yaya ba wasa nake ba fa dagaske ne.      Toh Ummi mene yakawo maganar?.   Had uwar da mukayi da kai jiya shine Tsalha yakaiwa Hajiya labari,kuma Goggo tazo shine tacewa Abba lallai ayimun aure.       sosai Mukhtar yaji dad in zancen nan na Ummi,duk da ya manta tarin abu dake gaban shi,Mummuna tabon daya shimfid awa rayuwar shi.         Shikenan Ummi yaushe yake so nazo.       Yau da daddare mana.    Shikenan Ummi na bari nafara shiri tun yanzu.     dariya tayi sanan takashe wayar,Master kam zama ya gyara yafara tunanin ta inda zaifara,kama daga shirya kanshi,domin bashi da wani kayan arzik i guda daya da zaisa yaje gaida siriki balle kuma hula da takalmin arzik i duk kayan shi na gayu ne,hannu yasa ya tab a sumar kanshi ita kanta tana b ukatar a kwashe ta.     Sunan Tsalha ne yadawo masa kunne da sauri yakira yaran sa sanan yace      Waye Tsalha a cikin gari?. Shiru sukayi gaba d ayan su kafin daga baya rooget yace      ina wanan gayen da muka tare ranar da kafara had uwa da Madam.  d aga kai Master yayi alamun ya gane,sanan rooget d in ya d ora da cewa   Tabbas shi naji ana cewa Tsalha a cikin gari.      To inaso aje a zubar  masa da mummunan jini.     Master yafad a tare da tashi yabar wajen,fita suma su rooget d in sukayi zuwa cikin gari,basu sha wata wahala ba suka gamu da Tsalha,wanda yadawo daga yawon d akko rahoto, binshi sukayi abaya har yabar wajen da babu cikowa sanan suka k addamar mai.    Jini iya Jini sun zubar mai kam,sai dai basuyi mai raunin da zakai shi lahira ba,sai dai doguwar jinya.  Master kam su rooget nafita shima yanufi wani shagon aski dake unguwar su,aka kwashe mai wanan cibiri-cibirin sumar dake kansa,lokaci d aya duk wasu kamanin sa suka sauya,a hanyar shi ta dawowa ya had o da mai yankan farce nan ma yatsaya aka yanke masa,sanan yadawo gida ya fara duba cikin kayan sa,sai da ya bincika sosai sanan yagano wata blue d in shadda, wacce taci uban squeezing yana k ok arin buge ta su rooget suka shigo gidan, da farko basu ganeshi ba domin kamanin sun canja Badoo ne yace.      Wai Master me ke faruwa haka?. hararar su Master yayi domin yaji haushin kallon da suke masa ga dariyar da Rooget ke b oye sanan yace      Me ka gani.  Bangane me nagani ba,gashinan ka aske sumar ka,kamar ma har farce kayanke,gashi kana neman buge manyan kaya kasa.        Gidan sirikai na zani. Master yafad a yana cigaba da tafiya,dariyar dasu ka saki ne su biyun yasashi juyowa,cikin muryar dariya Rooget yace       Kaga Master a gidan sirikai. Wata dariyar suka k ara saki sanan Badoo yace       Idan kaje me zaka ce musu?.  Banason iskanci fa.   yafad a tare da cigaba da tafiya,suna ta faman dariya yaje yabuge kayan ya ajiye su,sanan yadawo inda suke,lokacin sun daina dariyar zama yayi sanan yace     Abdullahi, Isah. d ago da idanun su sukayi suka kallesu domin su kansu sun manta rabon da akira su da asalin sunayen su.      Ina tunanin lokaci yayi da zan ajiye wanan rayuwa sanan kuma zaku ajiye,muka ma gaskiyya, a yau zanje gaida mahaifan Ummi kuma a yau zan a jiye du wata mummunar d abi a da nakeyi,domin nasan a yanzu nakai matakim da zansan na girma kuma ina fatan kuma kusan hakan.       Shiru sukayi gaba d ayan su,domin basu san meza suce ba,domin ko a harkar ma shine gatan su,shine mai gidan su,idan kuwa ya ajiye dole suma su a jiye.       Bazan yi muku dole ba,amma sai dai zan fita hak k in ku domin mun aika ta aikin b arna a baya a tare hakan yasa a lokacin a zan ajiye zanso na ajiye tare da ku,kafin zuwa lokacin da zamuyi nadamar da bata da amfani.     Girgiza kai Badoo yayi sanan yace  haba Master! yanzu akan soyayya zaka ajiye mana cin abincin mu?.        ba ajiye muku cin abinci zanyi ba,akwai wasu hanyoyin cin abinci da dama.     Master yafad a yana kallon su domin ganin yanayin jikin su       ka sake tunani dai Master. cewar Badoo d in,shikam Rogeet cewa yayi     Bani da abinda zanfad a domin hakan yayi, yana da kyau a kowanne lokaci d an adam yadinga waiwayar baya yana tuba akan zunuban sa.        Masha allah! Allah ya karb i tuban mu. Master yafad a tare da shigewa cikin d akin da yake nasa       Kai baka da hankali ne Rogeet?, baka da wanj ra ayi sai na Master?, sai abunda yace shi zakayi?.      Badoo yafad a yana janyo Rogeet d in kusa da shi      kai ya girgiza sanan yace  Badoo kaine baka da ra ayi amma ni daman inda ra ayin ajiye wanan rayuwar da muke fama da ita, na duba bi TUDU AKAN KWARI da nayi sanan nasan ta idan zanfara gyarashi.    da haka Rogeet yayi cikin d akin su ya hau had a kaya,dole ya koma ga iyayen sa, wanda yabarsu sabida rud in abokai da na duniya.          Master na cikin d aki yaji alamun fito da kaya,tashi yayi ya lek o ganin Rogeet nafito wa da jakar ghanna most go ne yace dashi      Mene haka?.  Master zan koma gida! zan koma ga iyaye na.       Tabbas kayi tunani,nima da ace ina da iyayen da zankoma wajen su da kafin aure na da Ummi sai naje, Amma dan allah kafin katafi kaban labarin me yaraba ka dasu?.    Master yafad a yana samun waje tare da zama,shima Rogeet d in zama yayi kan jakar ghanna most go d in haka ma Badoo dandamali kan rijiya yasamu ya zauna.      Dukkan ku nan kusan asalin suna na kawai,baku san asalin gari mu ba da komai, to ni d an asalin garin kano ne amma cikin k auyin kano KURA, mu 13 ne wajen mahaifin mu,ni kad ai ne wajen mahaifiyata, wacce ta d auki soyayyar duniya ta d oramun, duk da irin rashin k arfi ma mahaifin mu, kusan gidan yawa dai mussaman na k auye,mun taso ne cikin rashin kula daga mahaifin mu, kasancewar muna dayawa a gidan,mahaifiya ta na k okari sosai akaina, ni kad ai nasamu damar yim karatun boko a cikin y ay a 13 na mahaifin mu sabida mahaifiya ta nason na zama wani a rayuwa. Page[15&16]  Da k yar nasamu na kammala k aramar secondary,lokacin na hadu da abokan da suka fara koyamun shaye shaye, Mahaifiyata bata son wanan d abi ar kullum addu a take allah ya rabani da wanan abokan nawa amma kullum k ara kusa nake dasu.     Tun farko mahaifina baiso nayi karatun boko ba,ba wai dan yana da dalili ba sai dan kar mutane su zageshi a kan yakasa sa yaran shi a makaranta sai mahaifiya tace tasa kani, wanan shaye shaye da nafara yazama kamar wani abu da mahaifina zai fake dashi yadinga musgunawa mahaifiya ta, amma hakan baisa nayi hankali na daina ba, tsangwama da habaicu babu wanda mahaifiya ta bata sha a wajen a bokam zaman ta, har zuwa lokacin da nasa k afa nabar gari har zuwa yau ban koma wajen mahaifiya ta ba,ban k ara jin wani labari daga garesu ba,tabbas na aikata babban laifi a rayuwa ta,nayi wa mahaifiya ta butulci, na sa ta taji kunya a idon duniya.     Kuka sosai Rooget yakeyi, tabbas ya aikata babban kuskure a rayuwar sa, gashi anan d in ma bai cin ma wani abun kirki guda d aya da zaije yanuna acan ba.     Tabbas rayuwar ka cikin kuskure ce,ka aika ta babban laifi,sai dai shawarar da zan iya baka bata huce ka zauna ka nutsu kanemi k wak warar sana a,sanan kaje gida da zuwan gaida mahaifa, kadawo ka cigaba da sana a har allah ya dafa ma kaika lokacin daza ka sa mahaifiyar ka alfahari.             DARE        Bayan sallar magriba ya hau shirin sa cikin shaddar da yad auko, tasha gugar da Rogeet yayi mata,kanshi da ya sha aske d auke da hula,k afar shi sanye da takalmi way anda duk aikin Rogeet ne.     Kai tsaye k ofar gidan su Ummi ya nufa, yafi minti goma tsaye da tunanin ta inda zaifara,sai daga baya yayi tunanin kiran wayar da Ummi ta kirashi d azu.      Dai dai lokacin Ummi na zaune tsakar gida bayan tayi shimfid ar tabarma,Hajiya na cikin d aki tana ta aikin zubawa Ummi da Abba harara, ji take kaman ta shak esu gaba d aya kuma tayi alk warin indai itace uwar Ummi sai ta gayawa yaron nan maganar da zata hanashi k ara zuwa wajen Ummi,domin tabbas ta riga da taga ma yiwa Ummi mijin aure.      Asiya ce tashigo gidan, bayan tayi sallama ne ta matsa kusa da Ummi tare da rad a mata cewat Mukhtar na waje, kallon Abba tayi sanan tace       Abba yana waje wai.  tashi kije kiyi masa iso. Abban yafad a dai dai lokacin da itama Hajiya ta mik e da niyar fitowa.      Kallon shi Ummi take sosai yayi matuk ar kyau,kamar ba Master da kowa ke tsoro ba,dodon mutanen gari, ganin Ummi na kallon shi baki a sake yasa shi cewa      Ko banyi kyau bane?. dariya tayi sanan tace       Lallai Yaya! wane ya isa yace bakayi kyau ba a wanan kyakyawar shigar.       Dan allah da gaske kike Ummi.   ya tambaya cikin sauri amma da yanayi wasa, ita ma cikin yanayin wasan tace      da gaske mana yaya! Allah har kyalki kakeyi kaman wata.       naji dad i Ummi yanzu me za ayi?.  shiga ciki mana.   Tabashi amsa tana shigewa, kirjin Mukhtar wani irin bugu yake dum dum, zuciyar na wani mugun tsalle kamar zata fito, cikin secon guda zuciyar shi na bugawa sau biyu, kamar mai tausayin k asa haka yake taka k asa, ciki ciki yayi sallama domin wani irin nauyi yaji bakin shi yayi masa,     Amsa sallamar Abba yayi sanan yayi mik amishi hannu alamar musbaha, kasa da kai Master yayi sanan ya girgiza kai ya nufi wajen da Ummi ta nuna mishi ya zauna.     Hajiya na daga tsaye tana kallon irin rawar k afar da Ummi keyi har dasu kawo ruwa sanan ta shige d aki     Abba ne yace  To bawan Allah ko zan iya sanin ka kafin komai?.     wani irin dum kirjin Master ya bayar cikin rawar Murya yafara magana       Sunana Mukh..tar.   to malam mukhtar ko ban sanka ba bazan kasa sanin mahaifin ka ko wani naka ba?.      Abba yafad a alamun dai yana son k arin bayani a cikin sunan nashi      Iyaye na ba y an garin kano bane amma ni a kano nayi rayuwa ta cikin wanan unguwar.        Ko me ya rabaka da iyayen naka?. Hajiya tafad a tana k arasowa wajen ta zauna, kallon ta Master yayi sanan yace      Mutuwa. Abba ne yace  Allah yajik ansh da rahama, amma anan d in da kake zaune kai da wane kuma wace sana a kake ko aiki da aka sanka akai?.        Ina zaune tare da abokai na.      Sana a fah!.   Hajiya ta sake tambayar   Bawata tsayayyiyar sana a bace wacce za au ta fad anta      Au baka da tsayayyiyar sana a kakw hurewa yarinya kunne?.      Saliha!.  Abba yadakawa Hajiya tsawa sanan yace     Maganar aure ba ta mace bace dan haka kitashi kibar wajenan idan bazaki iya shiru da bakin ki ba.     Harar Abba tafarayi k asa k asa tace   ba inda zani wallahi.     Abba ne yayi gyaran Murya sanan yace   To dawace sana a kake so na baka auren yarinya ta?.       A yanzu bani da sana ar da zan rik e Ummi sai dai kafin zuwa k ank anin lokacin da Zamuyi Aure da Ummi zan mallaki sana ar da zamu zauna.     Murmushi Abba yayi sanan yace   Ina son na k ara sanin ka sosai.     d ago kai Master yay ya kalli Abba sanan yace      Baba fuskata ba b oyayyi bace ada,amma yanzu fuska ta abar b oye wace?.      Wane kai.   Hajiya tafad a azabure tare da tashi,domin a d ago kan da yayi ta hango kamanin Master domin daman idonta a kanshi yake        Wane Kai.   Tasake maimaitawa, abba ne yace    Wai saliha meke damunki ne dan Allah.  Kaga alhaji kyaleni, kasan wane wanan. tafad a tana nunashi da yatsa,girgiza ma ta kai Abba yayi ganin kamar ta zabura ko firgita sanan yace     Ki nutsu dan Allah.  Na nutsu ba kasan wane a cikin gidan ba ko! to wan nan la ananne dan iskan yaron nan Master shi ne a gaban ka.     A furge ce Abba ya mik e tare da fad in innullahi wa inna illahir rajiun      Ummi da Asiya dake cikin d aki ne suka fito da sauri jin Innullahin da Abba ya furta.    Mik ewa Master yayi zuwa inda Abba yake sanan ya durkusa kan gwiwo yin sa,cikin murya mai bayyana rauni yake magana      Abba tabbas nine Master mai mummunan hali,dan daban da kowa ke tsoro, na kamo da matsanan cin son Ummi yar ka, na durkusa akan gwiwo na ina neman kabani auren yar ka Ummi tun ranar da na fuskanci nafara son Ummi nayi nisa nafara ajiye munanan hali na, a sanda ummi ta sanar dani kana buk atar ganina, nak arasa a jiywa ragowar halin, na tuba a sanadin soyayyar Ummi, Abba ka tausayamun dan darajar da Allah yayi maka na d an adam.       Shiru Abba yayi dan gaba d aya baya fuskantar komai akan maganganun da Master ke masa, da sauri Ummi ta k araso wajen tare da durkusawa yanda shima Master d in yayi sanan tace       Abba dan girman Allah, dan girman annabin Allah, Abba karka

Chapter 4 of 10