Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 10
to gashi yaganki na uku.       Cikin rawar murya da rashin sanin abin fad a tace.  Wallahi Hajiya k arya yake.  Karya ko?. Hajiya yafad a tana k ara jawo ta, ta fara kimar ta kamar ba ita ta haife ta ba, sabida hajiyan gani take ta gama raina mata hankali domin ga zoben da Tsalhan yace anzura mata a yatsa, kuma tasan a rayuwar Ummi babu irin wanan zoben a hannun ta. Sai da tai mata mai isarta sanan ta kyale ta tashiga d aki tare da fad in.  Kuma ki jara ya dawo shima ya d ora miki nashi, sanan ba sai nace na ra baki da kowanne d an iska ba Ummi, ki cigaba karki daina. Daga haka tashige d aki abunta, da kyar Ummi ta iya jan jiki tayi d akin ta, Kuka sosai tayi kafin bacci ya d auke ta wanda bata tashi ba sai washe gari. Da t samin jiki ta tashi domin baya ga duka da tasha a durku shen da take kuka bacci ya d auke ta. Agogon d akin ta kalla ganin k arfe shida na safe yasa ta tashi, ta nufi cikin Kitchen ruwan zafin ta tagani akan tukunya ta d iba ta shiga toilet, ta dad e tana gasa jikin ta, tana hawaye kafin tasamu ta watsa ruwan ta fito.     Sai da tafara gabatar da sallar asuba sanan tadawo ta d ora magriba da isha, bayan ta idar ne tahau shirin ta na makarantar boko    ____Master kam tun rabuwar shi da Ummi kai tsaye gidan dan majalisa Hamisu k waro suka nufa shi da yaran sa, inda suka je yimasa warning akan aikin da yasasu kuma bai biya su cikon kud in su ba.      Ba tare da sallama ba suka shiga cikin gidan har zuwa babban d akin da yake zama da b akin sa, kamar ko da yaushe yau ma d in tare yake da bak in nasa suka shigo, tsai tsaya wa suka yi carko carko ba tare da sunce ko k ala ba, amma kana ganin yanayin su ka tabbatar da ba zaman lafiya suke da b ukata ba, hannu na rawa Hamisu k waro ya bud e drower d in dake kusa dashi ya zaro musu cikon kud in su ya basu, duk da su ne suke sasu ai kata ta asan amma suna mugun jin tsoran su.    Roget shine babban yaron Master shine yasa hannu ya karb i kudin sanan suka juya suka fice, d aya daga cikin mutanen dake zaune da Hamisu k waro ne yace.  Honorable wai kuma tsoron way anan yaran kuke?. wani kallo Honorable Hamisu k waro yayi mai sanan yace.  Murtala wasa kake, ai way anan yan iskan yaran abin tsoro ne ga k asa ma ga baki d aya bamu ba, domin way anan kwata kwata basu da wani amfani a rayuwa, amfanin su d aya ne idan aikin ta addanci ya tashi.  To honorable kusa a kame su mana. Murtalan yasake fad a.  To kai Murtala banda abun ka, idan aka kame su su waye zasuyi mana aikin ta adancin ko zamu sa ko yaran mu?.   gyad a kai Hamisu yayi yana mamaki  ( wanan wace irin rayuwa ce yan uwa,  mutumin da zakayi aikin ta addanci akan sa ko domin ka burge shi, shine zaifara ai ba taka).    Daga gidan Honorable kam su Master kasuwa suka biya. Domin Master da yaran sa ba irin yan daban da abince ke ga garar su bane, ko way anda suke cin abincin siye, ko gidan dasuke zama zakayi mamaki idan kashiga domin ko ina a kintse yake tsaf tsaf, domin kowa da akwai aikin da aka raba masa yanayi kullum da safe, sanan duk wanda yab ata waje ko yaci wani abu to fa sai ga gyara a lokacin. Siyayyar kayan abinci sukayi sosai sanan suka dawo gida, inda Master ya raba ragowar canjin gida uku domin kowa yasan yanda akeyin rabo,kaso d aya na saving ne wato ajiya sabida matsalal yau da gobe ko rashin lafiya, kaso d aya na Master sanan kaso d aya na sauran yaran ne Roget da Badoo. Sai dare sanan tunanin Ummi yadawo kanshi, ko tana wane hali? duk yanda yaso ya ayyanawa zuciyar sa Ummi na cikin farin ciki abu yaki yi yuwa, zuciyar shi ta ™i yarda da hakan. Da k yar bacci ya d auke shi. Washe gari kam da huri ya shirya ya nufi hanyar da suke had uwa da Ummi duk da yasan yanzu k arfe 7 na safe ne kuma Ummi tana kaiwa 7:45 watarana ma har 8. B abgaren Ummi kam bayan ta gama shiryawa cikin unifoam ne ta fito t sakar gidan, inda ta tarar da Hajiya na shara Abba kuma yafito daga d akin sa.  Abba ina kwana. tafad a tana durkusa wa. kin kwana lafiya?.  Lafiya klau Abba. tafad a tana juya wajen Hajiya wacce ta tare ta da cewa.  Wanan shirin kuma na menene?.  A ah Hajiya ya zaki tambaye ta shirin menene bayan kinsan na makaranta ne. Abba ya bawa Hajiyar Amsa.  kaga na riga na gama gane ka, bazaka iya t sawatar wa da yarinya nan ba,sabida son da kake mata yayi maka yawa. Cikin fushi Abba yace.  kinga Hajiya ba na son cin mutunci da rashin kunya, me kike so na yiwa yarinyar nan?, bayan kinga ma yi mata duk wani hukunci, kince kin dake ta bayan na dawo na shiga d akin naga ta a kwance, naga yadda kika fasa mata jiki, so kike nima na k ara mata wani yanda zamu kashe ta ko mu illata ta?.    Kaga ni ba wanan ba, yanzu dai wallahi yarinyar nan ba inda zata fita. makaranta dai ba ki isa ki koma a yanzu ba, ba kunzo k arshen zango karatun ba?, to ke da zuwa sai temprint.   Hajiya ta fad a tare da shgewa d aki, Abba ne ya kalli Ummi sanan yace.      Maza kije ki cire kayan ki kinji, makarantar kiyi hak uri zuwa ga ba.  Toh Abba. kawai tace tare da tashi ta shiga d aki.Wani kukan ta k ara fashe wa dashi wanda ba ta tsaya ba sai shigowar Asiya.   wai bazaki makarantar bane na ganki a kwance?. Asiya ta tambaya tana k ara shigo wa cikin d akin.  jin shirun Ummi ne yasata k ara mat sawa inda take, sai jin shashek ar kuka tayi.  Ummi is everything okay?. shiru Ummin ta k ara yi.  please Ummi talk. hijabin jikinta ta d aga tare da nuna wa Asiya bayan ta, da sauri Asiya takai hannu wajen tare da Cewa. Ummi me yafaru waya dake ki. jiyowa Ummin tayi a karo na farko tun shigowar Asiyan sanan tace.  Hajiya.    Me kikayi?. Asiya ta tambaya cikin k asa da Murya.       Allah ubangiji ya tsinewa Tsalha. Ummi tafad a sanan ta bata labarin duk abunda ya faru, tun daga dawowar ta har dukan da akayi mata, har abinda yafaru yau da safe.      Ummi ya kamata muyi magana akan makomar rayuwar ki da Master,abinda nasha fad a miki ko da yaushe kenan. Tashi Ummi tayi ta d akko jakar ta, peaper ta yago sanan ta d auki biro ta hau rubutu. Bawanu long note ta rubuta ba, ta nad e ta tare da mik awa Asiya.  Nasan Mukhtar yana can yana jira na, dan Allah karki fad a masa komai kawai ki bashi wanan kice mai banda lafiya. Kara Asiya tayi tare da mik ewa ta fice.     _____MASTER Ganin har k arfe 08 na neman hu cewa.  Ba Ummi ba d oriyar ta, ya tayar mai da hankali sosai da sosai, yana cikin wanan tashin hankali ya hango Asiya ita kad ai ba Ummi. Da sauri ya k arasa tare da cewa. Asiya ina Ummin?. murmushi yak e tayi sanan tace.  Ummi bata da lafiya,amma ga wanan takarda tace a baka.   karb a yayi ba tare da jikin shi ya yarda da abinda Asiya tafad a,, kafin ya bud e takardar ya karanta Asiya ta b ace, Kalaman cikin takardar sun matuk ar sanyayar mai da jiki.      Yaya ina sonka, ina sonka ina sonka zan rayu da kai zan mutu da kai, duk tsanani da zafi zan kasamce da son ko, dan allah yaya duk abinda zai faru karka janyewa soyayya ta.       Gaba d aya kalamn Ummi sun tafi da duk wata nutsuwar sa. jikin shi yana bashi wani mummunan al amari, tabbas baya tunanin yasa yarinyar nan tayi TUDU A KAN KWARI? tafa d a soyayyar sa bayan bai kama ce ta ba. Haka yayi ta zama a wajen har san da Asiya tadawo. Ba k aramin mamaki tayi ba ganin Master inda tabarshi, sai dai wanan karon da yaran sa bashi kad ai bane, a hankali ya k araso inda take sanan yace.       Asiya zan tambaye ki, ki fadamun duk gaskiyyar da kika sani kada kiyimun k arya, meya faru da Ummi?. Zama Asiya ta zaiyyane wa Master duk abinda tasani. sanan ta jaddada masa sunan Tsalha domin ita fa duk sabon da sukayi tsoron Master take.     Daga nan kai tsaye gida Asiya ta nufa, tana Allah Allah ta shirya ta nufi gidan su Ummi domin tana son su gama duk wata shawara a yau, da sallama tashiga cikin gidan, sai dai rashin amsawar da akayi mata ya tabbatar mata da Mahaifiyar ta bata nan.      Anty ce tsakar gidan tana zaune kan turmi, bawani kaya bane a jikin ta d aurin kirji ne, domin anty ba ma abociyar saka ya bace, duk yawon da zatai cikin unguwa da wanan d aurn kirjin sai hijabi, gata irin mai rushe shen jiki ce amma haka take yawo. da anmata magana sai tace ba aure gare taba, indai kaga anty da complete kaya to unguwa ta nesa zata, amma ko gidan iyayen ta ko shiga cikin kasuwa haka take yawo.      Ke ubanki wakike wa wanan kallon? shegiya mai kama da d inya.    Anty tafad a tana zabgawa Asiya uwar harara, Asiya bata ce da ita k ala ba ta huce. domin daman Ummi ce ke tanka mata.    Halima ce tafito daga cikin d akin su tana sanye cikin d inki doguwar riga ta lace da ta kame jikin ta sosai da sosai, ˜afar ta tana sanye cikin uban heels din takalmi, sai uban kamshi turare take yi.      To kema Umma kya kula wanan shegiyar yarinyar, tana ji gidan ubanta ne kuma sun cinye shi a gado.   Halima ta fad a tana tunkaro inda Anty take.     ke halima kyaleni inci ubanta, Uwar ta ma haka muka buga da ita ta kyaleni balle kuma yarta.         Dan Allah Anty kyale yarinyar nan, ki kalle ni.   kallon ta anty tayi sanan tace  naganki.   Zan fita. Ta faWa tana kashe ido  zuwa ina?.  Nema. Taba ta amsa tana fara tafiya  to Allah ya tsare hanya. fitowa Asiya tayi zuwa gidan su Ummi.  To gantalalliya. An fice kenan.  Gantalalliya ba tahuce wacce tafita yawon ta zubar ba. A  gaban Uwarta har tana cewa a tawo mata da tsara ba. Asiya tafaWa  tare d ficewa.   Wallahi sainaci uban ki, shegiyar yarinya mai kama da Winya. ~~~~~ Zaune suke cikin Wakin Ummi. kasancewar Hajiya batanan ya basu damar sakewa suyi magana.  Ummi ki yiwa kanki faWa, ki nema wa kanki sau™i, ki nema mana.  na tambaye ki wani abu mana?. Šaga kai Ummi tayi alamun ina jinki.  Hajiya tasan da Master kika tsaya?. Girgiza kai Ummi tayi.  Amma tayi miki wanan dukan? to kisani Ummi duk randa hajiya tasan da Master kike tsayawa, wallahi abunda zatai miki sai yafi wanan, karki ga Abba yana supporting nake wallahi ko shi yasan da Master kike tsayawa Ummi zaki ji jiki.  Asiya kamar bikin sa soyayya ba?.  Ta ina zan santa nida ban taSa yi ba.  To Asiya kifita daga lamarin soyayyata dan Allah.   Shiru Asiya tayi domin taga ne gaba Waya Ummi taga ma tafiya akan lamarin Master.   ~~~~~ Washe gari ma Ummi bata samu damar zuwa makaranta ba. Hajiya ta hana ta haka sukai ta fama har tsawon sati guda.      Gaba Waya Mukhtar yafi ta haiyyacin sa,ya shiga damuwa, tunani yayi masa yawa, abinda bai tab a ba a rayuwar sa kenan damuwa akan lamarin wani, tun tasowar sa har zuwa girma da rayuwar sa amma gashi ya shiga akan Ummi yashiga damuwar da bai tab a ba, shiga irin ta ba, idanuwan sa kullum zafi suke masa. Ummi kawai suke son gani, Zuciyar shi kullum zafi take masa, Ummi take son gani. A yanzu ko yayi shaye shayen na sama na lokaci kad an ne, tunanin yake dawo wa cikin zuciyar sa. Har takai da ya fara sambatun da kiran sunan Ummi da daddare.                Yau takama monday. Ummi ta sami damar zuwa makaranta, domin yin temprint. Sanyw take cikin bak ar doguwar riga ta abaya, tayi rolling da jan mayafi, tana sak ale da jakar rataye ta zuwa unguwa. Domin sunyi magana da Abba zata biya gidan Anty Nafisa, dan har yanzu Hajiya ba sakar mata fuska take suyi magana ba.       Asiya ce tafito daga naso gidan itama tana sanye cikin doguwar rigar lace tasa k aramin veil mai kyau, yan mata da sukeji ta tashe da kyau ga ilimi, domin dukkan su ba banza ba suna da k ok ari sosai afanin boko da arabic, rankayawa sukai suka nufi makaranta, Ummi sauri kamar ta tashi sama domin tabbas tasan yau zata had u da Master nata, Mutumin da ta tabbatar wa da kanta shine mahad in farin cikin ta.          ki rage wanan saurin karkije ki fad i.   Asiya duk randa kika k ara cewa na rage sauri akan lamarin Yaya Mukhtar,wallahi sai namiki rashin mutunchi.        Ummi taba wa Asiya amsa tana cigaba da saurin ta , tab e baku Asiya tayi sanan tace     ki kamo gobe ma.   page[11&12]       Tsyawa Ummi tayi ganin sun k araso wajen da suka saba had uwa da master, Asiya kam gaba tahuce domin bata da niyar tsaywa,ta cire hannun ta akan lamarin Master da Ummi tunda ta fuskanci kamar Ummi batason tana shiga lamarin         Asiya ina zaki. kallon ta Asiya tayi sanan tace        Tafiya zanyi mana Ummi mai zan tsaya nayi.        wai ke Asiya mene haka,sai kitafi ki barni anan?.         kinga Ummi na fuskanci ba b ukata ta kike akan lamarin ki ba nacire hannuna gaba d aya sai dai nayi miki fatan nasara.     daga haka Asiya takama hanya ta huce, tsayawa Ummi tayi tabbas bata kyauta wa Asiya da take hantarar ta akan lamarin nan,amma gani take kaman bata son soyayyar ta da Master dane gaba d aya,itakam duk wanda zaiyi tunanin raba ta da Master sai inda k arfin ta yak are, (tana wanan tunanin ne roget yaron Master ya samu damar yi mata way anan hotonan da master ya tura  mata a office)         bata fargaba sai mutum tagani a kusa da ita, wani lallausan murmushi ya sakar mata,irin wanda kwana biyi yake gani a mafarkin da takeyi.       a hankali ta mayar masa da martanin murmushi sanan tace         Yaya.  Meenah i missed you.        missed you more yaya, dan allah kar ka kara nisa da gani na.      insha allah, Ummi dan allah kiyi mun alkwari kasancewa tare dani har abada.      hannunshi ta kama ta d ota a saman nata sanan tace       yaya a ko yaushe ka tuna da wanan alk warin dani Ummi ka d auka, duk tsanani duk wuya ina tare da kai,ina tare da sonka.        murmushi yasake sanan yace   nagode sosai Ummi naa, nima nayi miki alkwarin zaka sance bango a gareki, zan kasance t sanin da zaki dinga takawa a ko yaushe, zankasance fitila mai haskaki a ko yaushe, Ummi ina sonki da dukkan rayuwa ta, Ummi kece macen da nafara so a rayuwa ta, banta b awa wani tarihin rayuwa ta ba amma Ummi yau zan baki.         tafiya suka farayi sanan Ummi tace ina sauraronka       Da farko sunana Mukhtar Adam Mukhtar haifaffaen garin jigawa,mahaifina d an asalin garin kano ne amma zama yakai shi jigawa inda anan yake aikin shi,mahifiya ta yar asalin dutse ce anan suka had o da mahaifina sukayi aure,haihuwata da kwana d aya allah yayi wa mahaifiya ta rasuwa, inda k anwar mahaifiyata Anty Halima ta k arbe ni, Anty halima itace macen da nafara so kamar Uwa ina sonta a  matsayin mahaifiya duk soyayyar  da d a yakewa mahaifi Anty Halima na keyi wa.     na tasu cikin gata daga wajen Mahaifina,Anty Halima da kuma Abba mijin anty halima, ina da shekara Uku Allah yayiwa mahaifina rasuwa daman kuma baiyi wani auren ba bayan rasuwar mahaifiya ta, kasancewar a garin jigawa muke bansan wasu dangin mahaifina na nan kano ba haka itama mahaifiyata ita da Anty halima kawai iyayen su suka haifa,family din su ba irin mai yawan nan bane, suma su biyu ne a wajen iyayensu kuma sun rasu, ita kuma Allah baibata haihuwa ba.      Anty Halima da mijin ta suka cigaba da rik eni yanda suke mun har zuwa lokacin da yan uwan mijin ta suka sashi a gaba sai yak ara aure,Anty Halima ba tadamu ba nima kuma banda mu ba,ana haka Abba ya auro Jummai wata me siyarda awara anan farkon layin da muke, tun shigowar Jummai kasan da tashin hankali ta shigo domin Anty Halima bata kula ta ba,sai taita sababu da surutu dana fito waje zata k wad eni to anan Anty Halima zata kulata itakuma ta sami abinda take so, ana haka Jummai tasame ciki,nan fa Abba ya maida duk wata kulawa kan Jummai duk da bawai ya daina kula da Anty bane amma ya canja yamaida kaso 80 na kukawar shi ga Jummai anty kuma kasu 15,wata rana na shigo d aki na tarar da Anty ta na kuka,ba dinga tambayar ta meyafaru tace bakomai.        Kukan dana ga Anty nayi yasani a damuwa har nakasa bacci gaba d aya, cikin dare naji Anty tana addu a akan Allah yabata haihuwa,tun daga lokacin nima nafara tayata addu ar ana wanan zaman ne Jummai ta haifi yar ta mace wacce aka sakamata Lahira sunan Maman Jummai ne.      Abba yad auke kaso 15 din kulawar dayake bawa Anty ya k ara mai da ita kan Jummai ya zamana ni da Anty munzama yan kallo a wanan gidan,tun a wanan lokacin na taso da tsanar Jummai,Lahira har da Abba haka mukayi tazama nida anty har bayan shekara biyu fa haihuwar Lahira .      Nadawo daga wasa kawai naga Jummai tashiga wani shago Musa mai kayan miya wanda dama mak wafcin ta ne sanda take siyar da awara,lokacin banfi shekara 7 dan haka banyi tunanin abunda suke ba kenan kawai dai a yanayin da tashiga yasa na gane ba abin gaskiyya zasu aika ta ba, ko da nasar da Anty sai tace k arya nake dana dage da rantse rantse sai tace ba ruwana.     bayan sati biyu naje makarantar dare da mukeyi sau naji yan wasu ajina ana musu bayanin akan bai hallarta mace ta kwanta da namiji wanda ba mijin taba ko tashiga d akin wanj namijin hakan yasa na d auki alwashin sai na tonawa Jummai asiri ko Abba zai rabu da ita yadawo wa da Anty farin cikin ta (ban san cewa zanyi TUDU NE AKAN KWARI  wanda zai tarwatsa duk wani farin ciki a rayuwar da nake ciki ba,wanda zai juya sama ta ta koma k asa)            Ranar talata da bazan manta da ita ba nadawo daga wanan wajen wasan da nake zuwa naga Jummai ta shiga wanan d aki, kai tsaye na nupi wajen sana ar Abba nace yazo ba lafiya a gida a kid ime ya biyoni shida abokan sa guda biyu sunje nace ba lafiya yasa suka yo mai rakiya dai dai shagon Musa na tsaya nace ya shiga ciki,tsayawa yayi yana cewa  ina ne nan, me zanyi a ciki. gyad a kai nayi sanan nace         Abba ba lafiya kashiga ciki. jin haka yasa d aya daga cikin abokan nasa danna kai yashiga sai dai fitowad da yayi a guje yasa su abba tambayar shi ko lafiya,rike Abba yayi sanan yace     bazaka shiga ba kai haladu shiga kagani.      d aya abokin nasu ne yashiga shima ya fito yana maimaita innullahi wa inna illahir rajiun       a kid ema Abba ya fusge ya shiga sai dai shirun da sukaji yasasu ka bi bayan shi.    a kwance suka tarar dashi alamun ya suma, Jummai kam iyhu ta fashe dadhi da fad in       nashiga uku ni jummai na shiga uku. sanan ta nuna ni da yatsa tace       yanda kazama sanadin tonuwar Asiri na wallahi sai nazama sanadiyyar to nuwar naka asirin.       da k uruciya bangane me take nupi ba aka kama Abba aka fita dashi zuwa chemist,kai tsaye nayi gida domin sanar da Anty sai dai mutane na gani a k ofar gidan sunyi carko carko wasu suna shiga wasu nafita, da gudo nayi cikim gidan sai dai ji nayi anrik e ni.     wani b akin mutum dogo da alaman d an sanda ne domin nagane shi ana kiran shi da Judge da k arfi na fusge hanuna sai dai ya rik eni da karfi yanda bazan iya k wace wa ba tun ina fushe fusge har na nutsu domin a yanda nake ganin ana fitowa da gidan cikin tashin hankali dole nasan wani abu ne yafaru.     Ana haka wata k awar Anty tafito,kallo na tayi sanan tace Mukhtar zo nan,cikani yayi natafi tare da cewa       Adda me yafaru a gidan mu.   cikn rauni da sanye ta ce        Mukhtari sai hak uri Allah yayiwa Halima rasuwa.     kamar anbuga min guduma haka naji maganar tata sai dai maganar da naji ana fad a ta dawo dani daga fad uwar da nake shirin yi       aka kashe ta dai ko, kai Jummai ce takashe ma Uwa gata can yan sanda zasu tafi da ita.      ban k arajin komai ba natafi k asa sumamme, sai dare na gane inda nake lokacin har abinne gawar anty ita kuma Jummai yan sanda sun tafi da ita, gida ya rage dagani sai Abba.      Bayan kwana uku da kashe Anty Abba yafara wata rashin lafiya sakamakon Musa yagama fad an duk wata gaskiya domin tun kafin Abba ya aure Jummai suke tare har sukayi aure,yarinyar ma da akace yar Abba ce ashe yar wajen Musa d in ce,wanan abu ya k ara tashin ciwon nashi,kwanan sa biyu yana jiya Allah yad auki ransa sai dai kafin ya mutu sai da ya damk a amanata a wajen d an sanda abokin sa wanda shine sanadiyar duk kasancewa ta a wanan hali,Ummi nasha wahalal rayuwa mai yawa a hannun wanan mutumin,nasan zafin maraici a hannun wanan mutumin,naga mummunar rayuwa a hannun wanan mutumin,Ummi k arshe nina kashe wanan mutumin.      juyowa Ummi tai ta kalleshi inda shikuma ya d aga mata kai alaman eyh      to garin ya? kuma wace kalal azabar rayuwa kasha a wajen sa.        Ummi zan k arasa miki amma ki gama da makarantar nan,inda zamu tafi sai na baki.      toh kawai tace sanan takama hanya ta shige cikin makaranta,zuciyat ta fal da tunani kala kala a game da rayuwar Master,wanda ya k arawa soyyayarsa girma da k arfi a cikin zuciyar ta.      Ummi ba su gama da makaranta bs sai wajen k arfe 04 hakan yasa bata samu biya gidan Anty nafisa ba,kai tsaye gida suka dawo tare da Asiya wacce tabata duk wani labari da Master ya bata, sosai tausayin Master ya shiga zuciyar Asiya itama a wanan karon, a haka suka k araso gida inda ko wacce ta shiga nasu gidan.      kamar ko yaushe da sallama Ummi tashiga cikin gida, tayi mamakin kin amsa sallamar da Hajiya tai mata duk da tasan bawai sakar mata fuska take ba saidai tana d an amsa sallamar ta da gaisuwar ta,d aki tashiga jiki ba k wari ya hau canja kaya, sai dai sallamar Goggo da tujiyo ya matuk ar tsorata ta a fili tace.      Me yakawo wajan jarababbiyar matar kuma.  Goggo kam fad i take       Sahura ina yarinayar nan,.    Tana fa ciki Goggo itama yanzu ta shigo daga yawon zancen nata.      Hajiya ta bawa Goggo

Chapter 3 of 10