Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 10
 ku kwashe kayan nan ku fita dasu daga nan. jin shiru babu amsa ne yasa ta d ago kai daga sai dai bata ga kowa cikin office d in ba,wani mugun tsaki taja.  wai me Mukhtar yake so ya mayar mata da office ne?. Gaba daya tunda Mukhatar ya shigo rayuwar ta take fama da k aluba le kala kala, wa´anda ta kasa game musu. Tabbas taso Mukhtar tana kan son Mukhtar amma bata fatan ta sake komawa halin da ta tsinci kanta abaya tun daga ranar da tafara haduwa da master har zuwa yanzu babu wani abu da yake dai dai a rayuwarta . Shekaru shida da suka huce. Ranar da kaddarar ta ta sauya, ranar da tafara haWuwa da master a rayuwarta, baya ga sanin sunansa da kowane mutum ke unguwar yayi, amma wasu basu san fuskarshi ba.     Ranar  ta kasance ranar juma a da misalin karfe 08:03 na safe. Danda zon Waliibai ne ke kok,arin shiga makarantar secondary ta mata mai suna (Shikeh Ahmad community secondary school) cikin dandazo d aliban na hango Ummi da Asiya way anda a lokacin bazasu huce shekara sha biyar ba zuwa sha shida, suna sanye cikin uniform na junior student, tafiya suke kaman basu a cikin d aliban da suka makara, babu wata damuwa a tattatare  dasu, sun gab da gate Win makarantar ne suka jiyo hayaniya daga gefen makarantar, kai tsaye Ummi ta nufi wajen domin ganewa idont. Asiya ce ta riko hannun ta tare da cewa  Meena wai bakya ganin uban lattin da mukayi amma zaki tafi kallon rigima.   wani kallo Ummi tayi mata sanan tace  ke wallahi sai naje nagane wa idona bance ki biyoni ba. . Cika ta Asiya tayi ta nufi cikin school itama Ummi ta nufi inda tajiyo hayaniyar, matasan samari ne irin marasa jin maganan sun gaye wani matashin saurayi wanda ake kira da Tsalha.  Da alama munfunci ka akaita. cewar Ummi tana k arasowa wajen domin kowa yasan halin Tsalha da munafunci.  kai kudaina b ata mana lokaci kuyi mai abinda nasako. cewar wani matashin saurayi wanda da alama shine ogan su, kallon sa Ummi tayi tsaf yana sanye cikin riga da wando na k anan kaya wandon nan ya zazzago har ™asa (ass down) suma ta taru akanshi ta kuma cukurkud e waje daya, bata samu ganin fuskar shi ba ya juya mata baya, amma tana hango sar™o™in dake ma™ale a wuyan shi. A hankali ta tako har inda yake sanan tace  Haba malam,kamar baka da imani zaku sa mutum haka a gaba,har kana cewa kar su b ata maka lokaci. Tun daga farkon fara maganar ta yake jin saukar Muryar ta acikin dodon kunnen sa, jin tayi shiru yasa shi waigo wa. idanun sa suka sauka akan k aramar kyakyawar fuskar ta,cikim rashin sa a idanun su suka had e da na juna,wani irin abu yaji a zuciyar sa inda itakam Ummi bataji komai ba sai ma murgud a masa baki da tayi tare da cewa.       Malam mene kake kallona,ni hak uri na baku nasan halin Tsalha da gulma da munafunci amma kuyi hak uri idan zaku iya, idan bazaku iya ba kuyi duk abinda kuka ga dama halinshi yaja masa Tana fad in haka takama hanya ta huce, gaba d aya a tarihin rayuwar shi babu macen da ta taSa kallon idon shi ta gayamai magana haka sai wanan k aramar yarinyar.    Master mene abun yi?. d aya daga cikin yaran shi ya fad a   barshi ya huce. ya bashi amsa agajar ce cikin muryar nan tashi ta rik akk un ´an daba. Sosai Tsalha yaji dad in taimakon da Ummi tayi mishi amma munafukat zuciyarshi sai ta raya mishi wai Ummi da Master na da ala™a, cikin ranshi yana cewa.  Dole na sanar da mahaifin yarinyar nan,yasan rashin kumyarta har takai ta tari manyan ´an daba haka ido-da-ido. Ummi kai tsaye cikin makaranta ta nufa, kasancewar ba jaka a hannun ta yasa tahuce kai tsaye batare da ta tsaya wajen da ake tare masu makara ba.  Gaba daya Ummi ta manta da wanan lamari da yafaru kafin zuwan ta makaranta, k arfe 12:30 aka tashe su kasancewar yau juma a ce. _____MASTER_____ Tun da yarinyar nan tabar wajen yaji gaba d aya kamar ta tafu da wani abu daga jikin shi, dakyar ya lallaba suka koma gida sai dai ko da suka koma kasa fahimtar komai yayi, gaba d aya yarinyar yake son sake gani,so yake ya ganta yaja nata horning akan abinda tayi masa, wanda shi kan shi bazai ce ga abinda tayi masa ba. Ganin bazai iya jurewa ba yasa shi tashi ya nufi can makarantar tasu. Yafi awa d aya zaune yana jiran su fito domin tabbas sai yaci mutuncin yarinyar nan sanan zai iya bacci, abinda yasawa zuciyar shi kenan. yana nan zaune d aliban suka fara fituwa har sanda Ummi tafito wacce bata ma kula dashi ba ta kama hanyar gida.   A baya ya fara binta har su karaso idan babu hayaniyar mutane sosai. Cikin kaushin Murya ya fara mata magana.  Ke. Tsayawa tayi ba tare da tuyo ba, domin ko ba da ita ake ba kiran ya shige ta, ™ara maimai tawa yayi  Ke. Juyowa tayi idanun ta suka sauka akan fuskar sa. Wani irin abu taji ya dake zuciyar ta mai kama da tsoro, amma dake ita din jaruma ce dake wa tayi amma sai dai takasa kallan sa cikin ido, har ya karaso inda take. Asiya kam tun farko ta gane shine Master shugaban yan daba na unguwar su, mutumin da kowa yake tsoro babba da yaro, mata da maza, a ranta tace   Me Ummi taja mana haka ne?.   Malam lafiya zaka dinga bina a baya kana ™wala mun  kira kamar wacce kake bu bashi. Ummi ta faWa cikin wani k aramin k warin gwiwa bayan tagama yak i da tsoro a cikin zuciyar ta  Nazo yi miki warning ne. yafad a shima cikin sauke murya daga k arfi zuwa sanyi  warning!  waye kai?. Ummi ta jero masa way ayanan tambayoyin cikin salon rainin hankali irin nata.  okay! shikenan kije. yafad a yana mamakin kansa na yanda ya kasa komai    Ko baka ce ba ai zanje. Ummi tafad a tana hucewa,ita dai Asiya baki sake take kallon wanan lamari.    Tunda ga wanan rana Mukhtar Master yakamu da wani abu a cikin ranshi, rana bata tab a fitowa tafad i bai saka Ummi a cikin idanun sa ba, wanda shi kanshi bai san menene dalilin wanan ba, haka itama Ummi duk sanda yayi mata magana sai dai tayi mishi rainin hankali ta huce, baza tace tana jin ba dadi da tare ta dayake ba sanan ba zata ce tana jin dadi ba, Sai dai yau da gobe tafi ™arfin wasa. Haka rayuwar tai ta juyawa yau fari gobe bak i a kullum wata shak uwa ce take ratsa Mukhatar da Ummi wanda babu wani da yasan wanan  alak ar kasancewar Mukhtar Master cikaken mara jin magana ne a unguwa, shi bazakace masa yaron yan siyasa ba sabida idan yatashi rashin mutuncin sa har su ba kyalewa yake,basa sace sace shi da yaran sa ko haurawa mutane gida amma duk wani aikin ta asa bazaka rasa su a ciki ba.    A zuwa yanzu sun d auki shekara guda da rabi tare da Ummi,kullum shak uwa sabuwa ke shiga zuciyoyin su. wacce ta zama soyayya mai k arfi sai dai k arancin shekaru na Ummi duk da a yanzu ta girma ta matsayin s.s2 amma bata fahimci hakan ba, rashin nutsuwa da mai da hankali irin na Master kuma shima baisa shi ya fahimci yafad a son Ummi ba.    A kowacce rana sukan had u sau uku ko sau hud u lokacin tafiya makarantar boko, lokaci dawowa, lokacin tafiya islamiya wani lokacin su had u lokacin dawowa.    Asiya na musu iya ka cin k okari ba ruwan ta dafad awa wani, sai dai a kwana biyu ta fara fahimtar Ummi takamu da sonsa Master, mussamam da yazama a yanzu tana yawan maganrashi fiye da yanda take yi da. Asiya tana k okarin taga ra fahimatar da Ummi kan cewa ta dakata ta fahimci tafara son Master domin tasan abu ne mai kamar wuya, amma Ummi ta™i fahimta, amma tana son tasamu lokaci ta zaunar da ita tayi mata bita. Legend's pen TUDU A KAN KWARI.    (Short stroy) Mallakar Sayyid writer (Legend) Pagi na huWu 04    Da sallama Ummi ta shigo gidan nasu, sanye take da doguwar riga da kuma hijabi light blue, uniform din su na islamiyya kenan.  Ba ta sami kowa t sakar gidan ba yasa ta huce kai t saye cikin d akin ta. Bayan ta cire uniform ne tafito ta shiga d akin Hajiya, zaune ta same ta, tana karatun Al,qur ani. hakan yasa tafito tanufi cikin kitchen ta zubu abinci.   Batayi nisa cikin cin abincin ba Asiya ta shigo cikin gidan, zama sukayi tsakar gidan sai da Ummi ta kammala sanan Asiya tace su tashi su shiga d aki. Sai da suka zauna a Wakim Asiya tace  Ummi inaso ki fahimci magana ta, babu wasa ko shirme a maganar da zanyi. Šaga kai Ummi tayi alamun taji.     Ummi kin fahimci wani canji kwana biyu a tsakanin alak ar ki da Mukhtar?.   Asiya tafad a tana kallon Ummi wacce ta girgiza kai alamar  a ah .   Ummi ki fahimce ni, tabbas kwana biyu alak an ku ya canja, ko ta wajen sa ko ta wajenki.  Wai wane irin canji kike magana a kai Asiya?. Ummi tafad a alamu k osawa da maganar.  Ummi soyayya: soyayya tashiga zuciyar ki, ko da shi  bata shiga zuciyar sa ba.   Tsaki Ummi taja kafin tace  To Asiya shikenan ni bazanyi soyayya ba ko kuma bazan so shi ba?.  Meena ba haka bane. Asiya tafad a cikin kwantar da Murya sabida idan tana son Ummi ta fahimce tane,shiyasa take mata Amfani da wanan sunan (Meena).     Meena ba haka bane, dole zakiyi soyayya amma kisani Mukhtar ba irin mutumin da zakice zakiyi soyayya dashi bane.    ko zaki iya fad amun wani dalili. Asiya bata kai ga bude baki ba suka jiyo Hajiya na rafka salati, da sauri suka tashi suka nufi cikin d akin ta.      kai wanan yaro Allah ya wadaran sa ya la ance shi.   Hajiya tafaWa ta cikin Wayar da take. Su Ummi kam gaba Waya hankalinsu nakan wayar anan ne suka jiyo ana cewa.     Wallajillhi sun sassarashi kuma sun hana a d auke shi ma balle akai shi asibiti.      kai wanan yara Allah yayi mana katangar k arfe dasu da sharin su.   Hajiya tafad a sanan takashe wayar ta. Ummi ce ta mat so tare da cewa  Hajiya meyafaru haka?.   Hhm wanan la anan yaron meyake da sunane.? ,su kaje su ka sassara yaron wajen Marka,sanan suka hana a d auke shi a kai shi asibiti, kai wanan yaro Master yake kowa Allah ya la ance shi. wani mugun abu me nauyi kaman dutse ya dirga a kirjin Ummi ya tsaya cak, da kyar ta iya mikewa tafice Asiya ta rufa ma ta baya.  Zama sukayi jugum jugum ba ma iya magana kowa da abinda ke yawo a zuciyar sa, sai kusan minti goma sanan Asiya ta ce.  yanzu kinga dalilin?. Ummi bata iya cewa komai domin ita a yanzu babu abinda yake damun ta kaman zagi da la antar da Hajiya tayi wa Master.     Washe gari a hanyar su ta tafiya Makaranta ne Ummin take tambayar sa.    Wai yaya me yahad aka da wani yaro jiya?.  Wanne kenan. ya tambaye ta shima  jiya yara nawa ka kula?.  Akwai na safe akwai na yamma. yabata amsa cikin halin ko in kula.   To kuma nawa ne ka daina mutane fa suna zagin ka.  To a zage ni mana Meena, mene abun haushi ko zai dame ki?.  zai da meni mana. Ta bashi amsa. Tsaya wa yayi cak sanan yajuyo dan bak aramin dadi maganar tayi masa ba, domin yariga da ya gama tabbatarwa yakamu da son Ummi mai girma.  yanzu Meena dan anzage ni sai kidamu?. yasake maimaita mata tambayar. Ba tare da  taji nauyi ko wani abu ba ta sake bashi amsa.  Tun da nace zan damu zan damu mana,kai bakasan yanda nake son ka bane?.  Runtse ido tayi bayan tadawo daga tunanin da ya d auke ta, tabbas tasan taso master kamar ba gobe, sai dai a yanzu kam tacire shi da komai nashi a rayuwar ta,kuma ba ta fatan ta k ara had,a hanya da abinda ya shafe shi.  Tashi tai tafara had a kayanta dukda lokacin tashi baiyi ba amma gaba d aya bata jin zata iya k arayin komai a yau d inan. kasancewar ita kad ai zata tafi ba tare da Asiya ba dole sai dai tahau keke, hakan yasa kai tsaye ta nufi gate ta fara tafiya.  Tafiya kad an ce zata kawo ka bakin titi,amma Ummi a yau sai taji tafiyar na k ara ninka kanta. Idon ta na kallon k asa take tafiya, sai ji tayi anriqe hannunta katamau, Har tana kok arin faduwa. A  fusace ta jiyo sai dai idanun ta ne suka fad a cikin nasa, wanda yasata had iyar wani irin yawo jikake  muk ut.  Wani irin murmushi ya sakar mata wanda yasa zuciyar ta rawa, da sauri ta dauke kan ta tare da fusge hannun ta haWi da ja baya duk a lokaci guda. Hakan ba ™aramin dariya ya bawa kyakyaan farin matashin mai kama da larabawa. tabbas wanan zaki iya rantsewa cewar bazai iya furta ko da kalma d aya bace da harshen hausa, domin tunda ga kyakywar kwantanciyar fatar shi, har zuwa kwantanciyar bak ar sumar shi, duk na larabawa ne. Cikin wani irin salo ya bude baki tare da fad in.  Hajiya meenahhh. ya faWa yana jan ™ashen sunan, sanan ya Wora da cewa.  Kin canja gaba d aya. .Wani  irin dogon tsaki Ummi ta ja sanan tafara k ok arin huce wa. Hannu ya ™ara sawa zai kamo ta, tayi saurin zamewa tare da cewa.  kar kar da ka kuskura hannun ka ya ™ara ta Sani.    Okay Madam. ya faWa yana Waga hannu biyun sai kuma yace.  But please&  Hannu ta d aga mishi alaman dakatarwa.     kai tunanin ka kanada wani abu da zaka k ara fad amin? kai tunanin ka akwai wata kalma taka da zata k ara shiga k wak walwa ta?, wallahi mukhtar babu wani abu naka da zai k ara shiga kunne ya zauna face ya fita ta inda ya shiga.   Shiru yayi yana kallon ta, tabbas Meena ta canja, canji sosai wanda ba iya na jiki ba har na zuciya, domin tabbas Meena bata taba iya juriya akan lamarin sa, tabbas yana da babban aiki a gaban sa na dawo da soyayyar sa cikin zuciyar Ummi. Dukda ta ta soyayyar ko rawa ba tab ayi ba duk tsawon fad i tashi da yayi a rayuwa.    Cikin wani irin  yanayi ya k ara bud e baki  Meena bance ki yadda da kalamai na ba, Meena bance kalamai na su zauna a kanki ba, amma dan allah kiji ni ko da baza su kar asa shiga kunnen ki ba. Na yarda ni mai babban laife ni Meena , idan kin kirani da butula ma bazan ce ba haka nake ba, Meena idan kin kirani da Marar imani a soyayya bazan yi musu ba, amma dan allah ki fahimce ni, kiji ni ko da bazaki yarda dani ba.         Mukhtar wanan ba Ummin da ka sani shekarun baya bace, ba shasha shar yarinyar da tazab i soyayya akan iyayen ta bace, ba banzar yarinyar da tazab i farin ciki wani bace akan na iyayen ta, Mukhtar nasan kaina.    Ki daina jifan kanki da way anan kalamai Meena, ko a da d inma kin san kanki.    Mitcheww. ta ja wani dogon tsaki sanan ta huce domin tabbas hucewar ta shine alheri, domin matu™ar way anan idanun nasa suna kallon ta, wanan muryar tashi nashiga kunne ta, to tabbas zata iya manta komai da duk wani alwashin ta domin tabbas a iya wanan tsayuwa ta tabbatar wa da kanta babu wani abu da yarago a son da tayi wa Mukhtar Master. ~~~Mukhtar kam yana cikin tashin hankali babba ba k arami ba domin gaba d aya ya gama ganin tsantsar k i da tsanar shi a zuciyar Ummi. Kai tsaye mota ya shiga yaja bai t saya ko ina ba sai USMAN SHIRAZ SPECIAL HOSPITAL babban asibitin kud i daka jahar kano, asibitin da yatara manyan likitoci na k asashen k etare. Cikin v.i.p ya nufi wani d aki kai tsaye ya bude k ofan d akin ga shiga.    Babban d aki ne da ake ajiye patients,wata mata ce da baza ta huce shekara 37 ba zaune kan gado da alama itace mara lafiyan, duba da kanula dake d aure a hannun ta, k ara sawa yayi inda take tare da zama gefen gadon, cikin muryar rashin lafiya tace      sannu da zuwa. Da murmushi sosai a fuskar sa ya amsa da cewa.  sannu ya jikin naki.?    jiki alhamdulillah ya aikin?.      Aiki ai mun bari shi legos, bari na koma wajen likitan nan ko ya zo. yafad a tare da tashi. Kai tsaye wani makaken office ya nufa, inda yasamu wata nurse yayi magana da ita, bayan yan mitina tafito daga cikin office d in sanan ta bashi dama ya shige. Gaisawa sukayi da likitan sanan yace   Doctor nazo ne akan maganar gwajin da kuka yiwa mata ta!.    ____UMMI____ kai tsaye tafiya ta fara ba tare da ta tsaya neman wani mai keke ba, sai da tayi tafiya mai nisa sanan ta tsaya, sakamakon zafin da taji kafarta ta fara,      ita kanta tayi mamakin irin tafiyar da tayi domin tafi rabin tafiyar, bata sha wahala ba ta samu keke ta k arasa gida, yau ba ta ko lek a d akin hajiya ba tayi cikin d akin ta, kan gado tafad a ta kwanta tare da fashewa da wani irin kuka marar sauti, gaba d aya rayuwar soyayyar ta da Master ce tafara dawo mata cin kwanyar kanta kamar wacce take kallo a majigi.    Tun daga ranar da kalmar so tafita daga bakin Master zuwa kunnu wanta, wani b angare na farin ciki ya tsaya a rayuwar ta, har zuwa yau. ~~~~~~         Meena dagaske kina sona. maganar da fara yi mata amsakuwa a kunne kenan, lokacin da ta furta kalmar cewa  bakasa irin son da nake maka. Wanan Murmushin da zata iya cewa ta zarar shi da wani Murmushi a rayuwar ta, tazara ce mai yawa, ta sakar mishi tare da d aga masa kai.      (Allah ubangiji ya rufe sani gaibu ga bayinsa, yabarwa kanshi kad ai sani domin shine Al maliku al kalik,u.)  Tabbas da Ummi tasan saurin da takeyi a wanan lokaci zai zamana shine,sauri na k arshe da zata k arayi cikin farin ciki na tsawon lokaci mai yawa da tayi shi da kyau. Da ace tasan saurin da take zaizamana sillar bud ewar damuwa da matsala mai tsawo a rayuwar ta da batayi shi ba.   Ummi ki daina saurin nan dan Allah yayi yawa. Asiya tafad a ganin duk sun huce sauran d aliban dasu ka taso tare.  Asiya bakisan yanda nakeji ba, kyautar da yaya mukhtar yace zaiban gaba d aya ta rufe mun idanu.    Tsalha da yazo hucewa ne yabi Ummi da idanu jin ta ambaci kyauta da kuma yaya Mukhtar, canja akalal tafiyar shi yayi zuwa bin bayan su Ummi da Asiya way an da gaba d aya rayuwar su basu kula da wani mutum da ke bin su ba.   Cikin filin makarantar gwamnati dake kan hanyar su ta dawo daga islamiyya inda nan ne wajen had uwar su da Master, domin wajen yayi nisa da islamiyar tasu kuma yayi nisa da gida. Zaune suka tarar dashi yana sanye cikin kayan shi yan kullum wato k ananan kaya, da sauri Ummi tak arsa kusa da shi tare da fad in.       Yaya na nadawo. kallon ta yayi cikin so da k auna sanan yace.  Yawwa Meenatu an dawo lfy?.  lafiya klau yaya, yanzu ina kyautar da kace zaka mun. Tsalha dake gefe kam yana ta faman baza ido ko idanun sa zasu hango masa wane yake tare da Ummi. Sai dai idanun basu bashi damar gani ba sosai har zuwa lokacin da Mukhtar ya zaro zube ya zura Ummi hannu, da sauri Tsalha ya juya.     Ummi kam wanI irin farin ciki taji lokacin da Master ya saka mata wanan zoben a d an yatsa sanan yak ara da cewa.   Meena ina so kiyi mun alk wari guda d aya. cikin tsantsar soyayyar da itama batasan adadin girman ta ba tace.  Yaya wane irin alk wari ne?.    Amina inason kiyimun alk wari duk runtsi duk wuya duk t sanani da zafi ba zaki  guje ni ba, Ummi zan so ki sama da raina, zan tsaya akan son ki iya kacin numfashi na, sonki zai zamar me ni jagora a cikin rayuwa ta, zai zame mini fitila mai haske a cikin duhun rayuwa ta. Ummi zan rayu da sonki zan mutu da sonki zan tashi da sonki. Wani irin murmushi mai tsayawa a zuciya Ummi ta sakar mai sanan tace.  Yaya na so ka a sanda bansan mene ne so ba, na girma da son ka a cikin rayuwa ta , zan rayu da sonka a cikin rayuwa ta, sanan za rok i na mutu da sonka a raina, yanda zan tashi dashi, sonka shine yazamar mini bangon da nake jingi na dashi, bango da yazama ma tokara a gare ni, akan ka nasan farin cikin rayuwa yaya, sanka ne zai zame mini hanyar farin ciki na har abada.  Idan har ina ganin ki a kusa dani, ko ina ganin ki a cikin duniya ba ni da wata damuwa ko bacin rai Ummi, kinzame mini alkhairi mai girma a rayuwa ta, ke cd mace ta farko da ta nuna soyayya ko kulawa a gare ni Ummi. Na so ki da duk kan numfashi na, zan soki ko babu numfashi a tare dani.  Yaya idan son ka  zunubi ne, to wallahi bazan tu ba bah. Legend's pen TUDU A KAN KWARI.      (Short stroy). Mallakar Sayyid writer (Legend)          Pegi na biyar 05& .   Ummi ki kula da zoben nan kar Hajiya ta gani. Asiya ta fad awa Ummi dai dai lokacin da take shiga gida, Murmushi Ummi tayi sanan tace.   karki damu Asy zan kula,amma dai kifara soyayya. banxa Asiya tayi da ita ta shige gida. Dai dai bakin k ofar gida Ummi taci karo da Tsalha na fito wa daga cikin gidan, wani irin dum taji a k irjin ta yayi, bawai dan tsalha baya shiga gidan ba ha sali ma Tsalha d andakin hajiya ne,amma yau kawai ta ji gaban ta yafad i ta tsora ta da ganin shi. Jiki ba k wari tashiga cikin gidan, tun daga kallon da ta ga hajiya na ma ta taji wani irin abu ya tsaya mata a ma ™oshi, da kyar ta iya had iye wani yawo mai mugun d aci sanan tace.  Hajiya nadawo.    Daga ina?. cikin rawar baki tace  Maka..rantahh. Tasowa Hajiya tayi zuwa inda take sanan tace    Wace makaranta?, na ce wace makarantar dan uban ki. shiru Ummi tayi gaba d aya ta gama tsorata, ba tai aune ba sai ji wani azababben mari tai a fuskarta, tu ni tayi tangal tangal zata fad i domin tabbas marin ya shige ta.      Wallahi Ummi sai kinci uban ki, mu zaki mayar yan iska?, a turaki makaranta ki tsaya yawon kula samari, wanan ne karo na uku da tsalha ya ganki, yayi miki magana na farko a matsayin shi na wanda ya isa dake amma baki gyara ba, ya ganki na biyu yayi miki magana shine zakice yayi ta fad a

Chapter 2 of 10