An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
[2:17AM, 3/5/2017] βͺ+234 803 052 4904β¬: πππππππ
πππππ
πππ
πΉ *_KHALEESAT_*πΉ
ππΌππΌππΌ
```Maman Abd shakur```
_PAGE_
0β£1β£
Saukowan jirginsu kenan maisuna
ARIK
AIRLINE a national airport abuja.
wanda
daga Indonesia yake, aikam na
gyara
zama dan naga masu fitowa daga
jirgin.
Wasu mata da maza nagani wanda
ga
dukkan alamu yan makarantane
suna
sanye cikin uniform dinsu dogon
wanda
da red riga saidan hijab akansu
dukansu
irin kayanne a jikinsu.
Kutsawa nayu cikin students din
chan
nahango wasu yan mata su 3 wanda
ga
dukkan alamu bazasu wuce 17
years ba.
Biyu farare daya kuma chocolate ce.
Mai suna fateema amma suna
cemata
TEEMA COOL tace ma mai suna
CHUCHU
da KHALEESAT wlh wanan
compition
din da school dinmu suka turamu
yayi,
yakuka kawatar ashe haka Indonesia
keda kyau? atleast mudan bude ido,
chuchu tace abii my sis. Teema tace
wai
maisa khaleesat yau bata magana?
tun
muna cikin jirgi bata cewa komi, ko
abinci da akabamu bata ciba cofee
kadai
tasha, chuchu tace wlh nima
nadamu,
khaleesat tai musu murmushi batare
datace komiba duk maganan nan
dasukeyi tafiya suke.
Suna fitowa sukaga motar
makarantan
su tazo daukansu mai suna
TURKISH
INTERNATIONAL SCHOOL.
Suna shiga motan khaleesat taji
gabanta
yacigaba da faduwa rike kirjinta tayi
saikuma tafashe da kuka sosai.
Teema da chuchu suka daddafata,
chuchu tace khalee kidena kuka plz
kifadamana meke damunki, teema
tace
ko bakida lpy ne?ko ciwon cikinki
yatashine? Khaleesat ta girgizakai
tana
matsar hawaye.
Chuchu tace khalee kinfasan dad
nawa
yace zaisai ma dukanmu gift inhar
mukai wining kuma munci soo cheer
up.
Khaleesat ta share hawayen
muryanta
mai kama da tayara kuma karama
tace
chuchu, teema wlh bansan mesaba
jinake
kaman wani abu zaifaru dani yau, i
can
feel it, dama tun tuni nake bad
mafarki,
takara fashewa da kuka tace i can
feel it
wlh my destiny is going to change
today
tacigaba da kuka.
Chuchu da hawaye yacika mata ido
dan
su ukun suna balaβin son junansu,
idan
antaba daya to antaba dukansu,
iyayensu abokanayen junane.
Chuchu
tace khaleesat kidena magana haka
adduβa zakiyi, kinsan we luvs u alot,
damuwarki damuwarmu ce plz
kidena
kuka. ahankali ta kwantar da kanta
kan
kafadar Teema. Daidai nan bus ta
tsaya
dan ankawo kofar gidansu khaleesat
sallama tayima su chuchu da teema
ta
sauko sukuma suka wuce dankai
kowani
dalibi gidansu.
Katafaren gidansu mai kaman dana
tsohon gwamnan ph ROTIMI
AMECHI ta
shiga gidane mai masifan kyau
kasan
gidan manyane.
Ahankali take tafiya tana janye da
trolley dinta, abunda yabata mamaki
shine babu mai gadi, kuma babu
securities din gidan.
Kofar falonsu tabude, batare datai
sallamaba abunda taganine yasa
idanunta suka fara juyawaβ¦
πππππππ
πππππ
πππ
πΉ *_KHALEESAT_*πΉ
ππΌππΌππΌ
```Maman Abd shakur```
_PAGE_
0β£2β£
Tuss din dataji alamun karan
bindiga
yasa taji juyawan da idonta yakeyi
yadena, sake dago daradaran idonta
tayi
taga babanta da mamanta kwance
akasa
cikin jini, wanda taga anharbi
babanta a
daidai saitin zuciyarshi, mamanta
kuma
akai, jakar dake hannunta tayar
takarasa cikin falon dagudu zata
fada
kan iyayenta amma mutumin ya
nuna
ariketa.
Tasowa yayi yana murmushi keta,
khaleesat tace Abban chuchu maisa
ka
kashemin iyayena?? Ba abokinka
bane??
Karka manta mu yayanku mune
muka
hada zumuntar dake tsakaninku
maisa?
mai iyayena sukama abban chuchu?
Kara dago kanta tayi ta kalli wasu
mutane masu bakakaen kaya tana
binsu
dai dai da kallo idontane ya sauka
kan
mai gadin gidansu shima rike da
bindiga.
Zatai magana Abban chuchu ya
kwasheta
dawani mahaukacin mari wanda
saida
jinita yadena aiki 4 dat moment,
yadau
bindiga ya saita kanta zai harbeta
amma
kuma saiya samu kanshi
dakasawa,ya
cije lebe, idan ya kalleta yana ganin
fuskar yarshi tilo CHUCHU yasan
sunason junansu barinma chuchu
tana
balaβin son khaleesat.
Maida bindigar yayi cikin aljihu
sanan
yajuya mata baya cikin kakkausan
murya yace khaleesat ban
kashekibane
saboda abu daya tak!! Shine yata
chuchu
, nasan yanda take sonki, amma
yanzu
zanyi maganin komi.
Khaleesat takara fashewa da kuka
gashi
ba halin guduwa, gashi ba halin taje
tataba babanta da mamanta datake
gani
cikin jini, kuka take kawai. jitayi
Abban
chuchu yace khaleesat! ta dago dara
daran idonta ta kalleshi saiji tayi
wani
feeeeeeeee ya fesa mata shalton a
idanunta biyu take ta sulale kasa
tana
ihu saboda azaba, duda haka baiji
tausayintaba yacema gurds din
dasuka
riketa ku gwalemin idonta aiko suka
gwale duda idanun sunyi balaβin jaa
saboda azaban shaltos amma haka
yakara fesawa saida shaltosa daya
yakarae a idanun khaleesat take
itama
tasume warwas awurin saboda
azaba.
Abban chuchu ya zabo mutane biyu
mai
gadi, dawani basamude yace kudau
yarinyanan inaso ku kaita chan
nijar,
nijar dinma a kauye, kauyen ma
cikin
kasurgumin dokan daji, dajinma
dababu
mahalukin mutum dayake zuwa
saboda
gudun kar wata rana ta tona mana
asiri.
Banason tadawo Nigeria. Suna
rawan
jiki aka fita da khaleesat sukasata
amota
sukaja.
Abban chuchu yafashe da dariya ya
tsugunna yana shafa fuskan baban
khaleesat yace oo dear amininna!
kai
kuskuren yarda dani arayuwanka,
gashi
yanzu duka dukiyarka tadawo nawa,
na
kashe idon yarka khaleesat wanda
har
abada tadawo makauniya. yakara
fashewa da dariya ya mike yacema
sauran bodyguard din kuzuba
kalanzir a
gidan ku kona, kuma kuyi maza
kubar
anguwan yanda babu wanda zaitaba
zaton kashesu akayi. saidai kowa
yayi
zaton gobarace takeshesu, yana
fadan
haka yadau wani file yafita daga
gidan
dayake anguwan shuru shuru ce.
πππππππ
πππππ
πππ
πΉ *_KHALEESAT_*πΉ
ππΌππΌππΌ
```Maman Abd shakur```
_PAGE_
0β£3β£
Yana barin gidan sauran guards din
suka fara zuba kerosene din sun
zufa
akan kujerun, katifu sai labelayen
dakin
sanan suka zuba kerosene din a
jikin
maman khaleesat,da babanta
wayanda
sun riga sun mutu.
Saida suka fito bakin kofa sanan
suka
kyasta ashana suka wurga cikin
dakin
aiko daki yakama da wuta sosai da
sauri
suka shiga motarsu sukabar
anguwan
batareda ko mutum daya yagansuba,
sai
murna suke dan Abban chuchu yace
zaibiyasu dakyau. Abunda suka
manta
shine Allah mai kowa da komi
wanda ya
hallicesu ya gansu kuma surely
zaibinma
wayandavsuka kashe hakkinsu.
Wuta citake sosai makota sunfarajin
kauri suka fito mutane dayawa
akaga
wuta hartafasa roof, nanda nan aka
fara
bada taimakon gaggawa, wani
makocinsu wanda yake shiri da
baban
khaleesat yace innalillahi wlh tare
mukadawo daga sallan azahar da
Alh, ya
shiga gida nikuma nawuce nawa
gidan
Allah ubangiji yasa basa cikin
gidanan
wutan yakama, ciro wayanshi yayi
yakira fire brigade sukace gasunan
zuwa, sanan yakira lamban baban
khaleesat amma bayazuwa.
Jiyayi gabanshi yafadi, da sauri ya
lalebo
lamban yayan baban khaleesat
LAMIDO
wanda shima anan abuja suke da
iyalinshi, yana dauka yace Alh kazo
gidan kaninka baban khaleesat wuta
yakama kuma baβa san inda baban
khaleesat sukeba.
Arude wan baban khaleesat maisuna
lamido yafadanma matanshi da
yaranshi
mota suka shiga suka taho.
Lokacin dasukazo lamido da
yaranshi
maza biyu dasuka biyoshi suka
karasa
da sauri yanda sukaga wuta nacine
yasa
hankalinsu yatashi kashe wutan aka
dingayi da kyar da sidin goshi wutan
ta
mutu kurmus.
Cikin wayanda suka zo aka kashe
wutan
kuwa harda Abban chuchu, yay
fuskan
damuwa kaman da gaske, bayan an
kashe wutan an tabbatar ta mutu
russ
sanan mutanen fire brigade da su
lamido ya yaranshi biyu maza masu
suna IDRIS, ISYA suka shiga
gabansu na
faduwa Allah sa baffansu baya cikin
wutan..
Ahankali suka fara bincike har suka
shiga falo wanda yake da sauran
abubuwa na hayaki saida aka gama
kashewa sanan lamido da sauran
mutane suka karasa ciki abunda
suka
ganine yabasu mamaki, baban
khaleesat
da mamarta jikinsu ya kone kurmus
yadawo toka amma fuskokinsu ko
alamun wuta yataba babu hasalima
saidai wani haske tareda murmushi
dake
kan fuskokin nasu sanan zufa a
goshinsu.
Lamido da yaranshi idris da isya
suka
fashe da kuka, lamido yadau kan
kaninshi ya rungume yana kuka
sosai
yace haba hydar maisa zaka mutu
ka
barni?kasan kai kadai nakedashi a
duniya kaine kadai kanina. Bazaka
tsaya ka aurar da yarankaba
khaleesat
da khalis?? Kuka yake sosai yama
fara
fita daga hayyacinci ambato
khaleesat
din dayayi yasa idris yace dad ina
KHALEESAT ????
πππππππ
πππππ
πππ
πΉ *_KHALEESAT_*πΉ
ππΌππΌππΌ
```Maman Abd shakur```
_PAGE_
0β£4β£
Lamido dake kuka sosai jin an
ambato
khaleesat wanda yakeso yakuma keji
da
ita yasa yadago kai ya kalli idris,
isya
yace dad TEEMA tacemin tare suka
dawo
ita aka fara saukewa a gidama, sai
alokacin Abban chuchu yay magana
yace
CHUCHU ma nagida itama tacemin
KHALEESAT suka fara saukewa.
Hankalinsu yakara tashi, daddaga
abubuwan dasuka kone suke suna
neman gawan khaleesat.
Idris yace dad! kowa ya juyo yana
kallonshi yace dad zokaga wanan ba
trolley dakasiyoma khaleesat bane
lokacin dakaje LOS VEGAS??
Dad ya karbi trolley wanda yasoma
konewa yace shine jikinsu yay
sanyi.
Abban chuchu yace da murya kaman
zaiyi kuka hala ita takone kurmus
shikenan narasa abokina da kawar
yata
Chuchu wayyo Allah na, yafashe da
kuka
sosai sai aka dawo shi ake lallashi a
falonβ¦β¦β¦β¦β¦β¦β¦β¦β¦β¦.
Kusan kwanansu 3 akan hanya
saboda
motan nabasu wahala, khaleesat
kuwa
haryau bata farfadoba arana na 3 ne
suka isa nijar wani kauye mai suna
DOSO sukaje akwai wani babban
daji
wanda ba kasafai mutane ke zuwa
dajin
ba saboda namun dajin dasuke a
ciki.
Cirota sukayi daga mota suka kwara
mata ruwan sanyi ajiki wanda hakan
yasa ta kwalla ihu wanda saida dajin
yadau ihun.
Daidai lokacin wani namiji cikakken
buzu dogo sosai amma yanada
cikakken
jiki danko kadan ba siriri bane,
kakkyawan gaske ne shi yanada
dogon
hanci da karamin pink lips, manya
idanun gareshi ga gashi akanshi
kaman
nadan India, sanye yake da dogon
wando da wani riga wanda yawancin
masu zuwa farauta ke sawa,
bayanshi
kuma ya goya kwari da kwafa wanda
yake harbe namun daji dasu, akalla
shekarunshi zasuyi 27. bayanshi
wasu
mazane 2 amma basukaishi girmaba
dansu yarane yan 20 haka soboda
hunting yakeyi, kowanensu najan
akalan
dokinshi. Jin ihu yasa dukansu suka
tsaya chak yaran zasuyi magana
wanan
hadadden namijin saurayin maisuna
HYDAR ya daura hanunshi a
lebenshi
sukai shiru.
Kulle dawakan yayi ajikin wani
bishiya
sanan ya ciro kwari da kwafan shi
sabida imma wani abune su kashe
abun
sukuma yaran suka ciro addodinsu.
Tafiya suke sadaf harsukakai inda
ssukejin ihun amma saisuka labe
cikin
ganye, gani sukayi wata yarinya
wanda
idonta akulle tana kuka sosai tana
baba
mai gadi karku jefani cikin rijiya,
karka
manta alherin da babana yama dan
Allah kumin rai, dayan yace umarnin
oga mukebi khaleesat tacigaba da
kuka
tanato kuban abinci yunwa nakeji.
Hydar na ganin zaβa kisan kai, yasa
yaji
ranshi yabaci, zuciyanshi na
tafarfasa
umarni yaba yaranshi su tsaya a
wurin
bari ya dauko dokinshi, zuwa yayi
ya
hau dokinshi da wani irin gudu
yafito
filin jikake sukutum sukutun alamun
takun doke ya doso inda suke,
Suna ganin wani ya gansu yasa
suka
daga khaleesat suka jefata cikin
rijiyan
amma kafin ta karasa cikiβ¦β¦β¦
πππππππ
πππππ
πππ
πΉ *_KHALEESAT_*πΉ
ππΌππΌππΌ
```Maman Abd shakur```
_PAGE_
0β£5β£
Kafin takarasa cikin rijiyan hydar
nadaga kan doki kafin yakaraso
inda
suke ya saki kwari da kwafa, Allah
yabama haydar baiwar saitin abu
kawai
sai arrow din ya chaki gefen wando
makarantan jikin khaleesat ya bulla
bango, sai abun yadawo kaman
hook,
hakan yasa bata karasa cikin rijiyan
gabaki dayaba kafafunta asama
kanta
akasa abunda haydar baisaniba
shine
kan khaleesat na cikin ruwan rijiyan
saboda rijiyan acike yake.
Gadan gadan yayo kansu mai gadi
wanda tuni suka fara gudu, dan
kallon
muscle din hydar kadai sukayi
sukasan
wanan namijin zaiyi bijimin karfi,
gudu
suke hydar na binsu kan dokinshi
ciro
sandan kwafa din yayi daga
bayanshi,
hannushi daya kan akalan dokin
dayan
hannu yasa ya bige kan dayan guard
din
dake tareda mai gadi, aiko yafadi
akasan wajen,mai gadi baiyi wata
wataba yacigaba da gudu,
hydar ya daki kan dokinshi a zuciye
tareda cemishi tsaya HISANN, chak
dokin yatsaya.
Hydar ya diro daga kan dokin, ya
mikar
da guard din yakaimai wani wawan
nushi a hanci tareda cewa maitai
muku
dazaku kasheta?yasa kafa ya
kwasheshi
kaban amsai? Zaikaimai duka na
uku
yaji tass mai gadi daga nesa dasu
ya
harbi hydar a muscle dinshi, yatako
ya
tsaya kusa da hydar ya saita bindiga
kanshi yace sakeshi, hydar yasaki
guard
din mai gadi yajashi sukabar wurin.
Hydar rike hanunshi yayi dake
bleeding
sosai, rigan dake jikinshi yacire,
danaga
kirjin hydar saida na tsorata yanda
kukaga HIRTIK na India film haka
hydar
yake saidai hydar yamafi hirtik.
Yaga
rigan yayi ya daure hanunshi gam,
tareda dan kara saboda azaba
dayaji,
juyawa yayi yana tafiyanshi na
cikakken
namiji karasawa yayi wurin rijiyan
amma kallo daya yama khaleesat
yay
maza ya dauke kai.
Gabaki dayan rigan khaleesat ta
kwaye
tayi sama ta rufe mata fuska, Allah
yasa
da bra a jikinta, yaran da hydar
ketare
dasu suka yi magana daga
maboyarsu
mufito NAMIJI?? Dan haka suke
basu
ketare umarnin hydar kodako
menene,
cemusu yayi ku tsaya lokacin
fitowanku
baiyiba.
Karasawa yayi jikin rijiyan hanunshi
daya yasa yarike kafan khaleesat
gam,
saikuma dayan wanda aka harbeshi
yasa
yana kokarin cizge arrow din daga
jikin
bangon rijiyan, kara yasaki sosai
saboda
yanda hannunshi kemishi azaba ya
fizge
arrow din da karfinshi aiko yaciru,
dayan hanun kuma yaciro khaleesat
wanda yay mamakin rashin
nauyinta.
Shimfideta yayi a kasa kusa da
rijiyan
duk abunda yakeyi yana kauda
fuskane
saboda bayason ganin tsiraicin
mace,
hanunshi na rawa yasa yaja rigan
daya
rufemata fuska ya sakko da rigan
jikinta
alokacinne ya kalli fuskanta dumm
yaji a
kirjinshi.
Yaran dayake tareda su yakira
bareed,
burhan, da sauri suka fito daga
maboyarsu suka karasa bareed ya
taba
hanun hydar yace kai suka harba??
batare dayabashi amsa ba Yace ku
dauramin ita kan dokina mutafi
gida.
daurata sukayi kan dokinshi, shima
suka
taimakamai yahau dokinshi sanan
suka
fara tafiyaβ¦β¦.
[2:18AM, 3/5/2017] βͺ+234 803 052 4904β¬: πππππππ
πππππ
πππ
πΉ *_KHALEESAT_*πΉ
ππΌππΌππΌ
```Maman Abd shakur```
_PAGE_
0β£6β£
ABUJA.
Haka aka sallace dad din khaleesat
da
mum dinta, amma baβa ga gawan
khaleesat kaman yanda Abban
chuchu
yafada sai aka dauka hala itama
takone
kurmus ne.
**************************
Asalin labari.
Alh lamido da Alh hydar wa da kani
ne,
sukadai iyayensu suka haifa inda
iyayensu suka rasu sukabar musu
tarin
dukiya.
Alh lamido ya auri matarshi mai
suna
benazir inda ta haifa mishi yara 4,
HYDAR ne babban danshi,sai IDRIS,
ISYA
sai autansu TEEMA.
Alh hydar ya auri matarshi hauwa
jabo
inda ta haifi yara biyu KHALIS sai
KHALEESAT.
Alh lamido da Alh hydar suna zama
na
amana, gasu da son junansu baβa
taba jin
kansu, gabaki daya sun hada kan
iyalinsu. Hydar da khalis suna
MEXICO
inda suke karatun likitanci acahn,
kuma
har yanzu Alh lamido bai fadamusu
zance mutuwan Alh hydar ba dan
yasan
hankalinsu zai tashi barinma khalis
harsu kasa karatu.
Abban chuchu abokin dad ne sosai
partners ne awani company dasuka
bude
mai suna TAKAFUL. Yarinyarshi
chuchu
saβan khaleesat ce, tanason
khaleesat
sama da tunanin mai karatu, wani
irin
shakuwa sukayi da khaleesat wanda
bata
iya wuni bataje gidansu khaleesat
ba,
yanzu haka ma tana asibiti an
kwantar
da ita dan lokacin daβaka fadan
mata
khaleesat gobara yakama gidansu
kuma
tamutu sumewa tayi awurin anzuba
ruwa anyi fifita amma bata
farfadoba,
alokacinne ABBAN CHUCHU yafara
tunanin dabaisa ajefar da khaleesat
ba
gashi yanzu yarshu tilo na neman
mutuwa saboda wata banzar
khaleesat
achan.
Abban chuchu kullum burinshi shine
ya
mallaki duka dukiyar Alh hydar,
saboda
Alh hydar yafishi da komi ga kudi ga
dukiya, koina ansanshi, talakawa
nasonshi saboda yawan
taimakonshi,
saisa ya kasheshi kuma kafin
yamutu
saida yasa Alh hydar yay signing
cewa
dukkan kudinshi sun koma na
Abban
chuchu wanan kenan.
*************************
Alh lamido zaune akatafaren
falonshi,
matarshi benazir kusa dashi idonta
yay
ja, sai idris,isya da teema wanda ta
kwanta jikin mamanta tana kuka
sosai
tafijin mutuwan khaleesat kan kowa
saboda tarefa suka rabu a school
bus.
Benazir cikin murya mai taushi tace
Alh
yakamata ka kira yan makaranta
khalis
da hydar ka sanar dasu, yakamata
khalis
yasan iyayenshi sun rasu, Alh ya
kalli
matar tashi yace Hj idan na fadan
musu
khalis will be devastated gwara
yanzu
mukirasu sudawo gida, dama jiya
hydar
yakira yacemin sunyi hutu amma
basuson sudawo Nigeria ne.
Hj tace shikenan Alh hakan yayi,
saikuma zance teema ka ganta
jikinta
yay zafi kaman wuta nabata hakurin
taki, Alh yace my baby, ta dago
fuska
yace zo wurina, da gudu takarasa
wajen
Alh tafada jikinshi tana kuka tace
dad
kacema khaleesat tadawo, da kyar
dad
ya lallaceta tai shiru.
πππππππ
πππππ
πππ
πΉ *_KHALEESAT_*πΉ
ππΌππΌππΌ
```Maman Abd shakur```
_PAGE_
0β£7β£
NIJAR.
Sina karasawa gidansu hydar, hydar
ya
diro daga kan dokinshi tareda sakin
kara, kallonsu bareed yayi yace
zaku iya
tafiya gidanku, tare sukace to
NAMIJI
suka juya kowanensu yatafi gidansu.
Dayan hanunshi mai lafiya yasa
yadau
khaleesat chak akafadanshi ya shiga
dan
karamin gidansu na kasa da ita.
Wata yar tsohuwa wanda akalla
zatakai
sittin ta taso da yarensu na buzaye
tace
hydar maiya sameka a hannu???
Wacece
kuma wanan ka dauko??
Cije lebenshi yayi sanan yace ummi
abar
maganan nan zuwa anjima yanzu ke
ceci rayuwan yarinyar nan dan bata
numfashi, ummi tace oya shigo da
ita
daki.
Ummi tana gaba suka shiga dakin
tabarma ta dauko ta shimfida afalon
nasu da ba kujeru sai simenti kadai,
shimfidar da khaleesat yayi akan
tabarma ummi ta taba jikin
khaleesat da
alamun damuwa tace hydar samo
ganyen magarya yanzunan da ruwan
zam zam.
Fita yayi dukda hanunshi na azaba,
makotansu suna saidawa zuwa yayi
ya
siyo ya kawoma ummi. Zama yayi
kusa
da ita yaga tabude baki khaleesat ta
zuba
iskan bakinta a ciki sanan ta danna
kirjinta ahankali khaleesat tai wani
tari
sanan ruwa dayawa yafito daga
bakinta.
Ummi ta karbi ganyen magaryan ta
wanke sanan ta matse ruwansu
tabude
bakin khaleesat tazuba ta matse
hancinta harsaida ta hadiye.
Kallon fuskan khaleesat tayi taga
yanda
jijiyoyin idonta dasuke akulle suka
fito
baro baro, hanunta takai tabude
idon
khaleesat taga gabaki dayan idon
haki
yacikashi, babu bakin tsakiyan
idonta
gabaki dayan idon yakoma fari,
saikuma
haki, ummi tace hydar ban ruwan
zam
zam din ya mika mata jiki na rawa
shima yadawo kusa da ita ya zauna.
Ummi takara bude idon khaleesat
din ta
diga ruwan zam zam wanda hakan
yasa
khaleesat tai ihu, saikuma tai shiru
tacigaba da bacci, hydar yace ummi
maike damunta??
Juyowa tayi ta kalli dan nata hydar
hanunshi ta kama ta bude ta zuba
wasu
magunguna sanan tasa wani karfe
tana
neman bullet din hydar sai cije baki
yake, da kyar ummi taga bullet din
taciro
sanan tasa magani a hannun ta sa
wani
farin kyalle ta kulle.
Tace hydar Yarinyar nan tana fama
da
ciwo sanyin kashi, kanta kuma yay
zafi
sosai alamun da abunda ke
damunta,
sanan kuma idonta ya mutu har
abada
bazata kara gani ba saidai wata ikon
Allahan, tadawo MAKAUNIYAA.
πππππππ
πππππ
πππ
πΉ *_KHALEESAT_*πΉ
ππΌππΌππΌ
```Maman Abd shakur```
_PAGE_
0β£8β£
ABUJA
yaune ranar da HYDAR tareda
KHALIS
suka diro naija, Alh lamido da
matarshi
Hj benazir sukaje daukosu, su hj
benazir
anci gayu ga tabarau a idanunnan
tai
kyau abunta kamar swt 16 nanko ta
ajiye yara 4.
Hydar na hango mamarshi benazir
da
sauri yazo ya rungumeta mother
huuuuhh kinyi kyaufa nafa zaci
teema
ce wollah, hj benazir taja hancinshi
tace
teeman ce ai, khalis ya iso wajen ya
ballama hydar harara yace aisai
abani
wuri nima na rungumeta ko takace
kadai?
Hydar yace baza a matsa ba din, hj
benazir tana dariya tace kai go gefe
joor,hj benazir ta rungume khalis,
Alh
lamido dai yana gefe yana
murmushi
sukaje suka gaida Alh lamido?
daganan sai gida.
Sun shiga gida kowa yamusu sannu
da
zuwa amma sun lura babu wanda ke
cikin walwala, sai bayan anci ansha
sanan dad yakira meeting falonshi
kowa
ya hallara.
Bayan gaisuwa da dad yakara musu
yace
khalis hydar ku kadaine kuka rage
bakusan komiba yace ku mazane,
kuma
maza aka sani da lallashin mata,
kuma
kusan cewa komi daya faru haka
Allah
ya tsaro ayau inaso na sanar muku
dacewa kanina hydar, tareda
matarshi
jabo, da yarshi kanwarka khalis
khaleesat duka sun koma ga
ubangijinsu
sakamakon gobara daya kama
gidan.
.
Khalis salati yake aranshi, yanzu da
gaske mum da dad dinshi da lil sis
dinshi
khaleesat sun rasu?? No way
gaskiya
hala basu bane.
Haydar hawayene kawai baiyiba
yanzu
da gaske harda little pumpkin dinshi
khaleesat?? Yarinyar dayake sonta
tun
tana karama kukan zuci yafara dan
baida masoyiyar data wuce
khaleesat bai
fada mata bane dan yanason saiya
gama
karatu.
Khalis kasa daurewa yayi yafashe da
kuka, teema kaman yarinya ta
rarrafo
tazo ta shige jikinshi itama tana
kuka
sosai da kyar dad ya lallashesu
sukai
shiru shidai hydar ba bakin kuka
amma
idanunshi sunyi jaa alamun tashin
hanakali duk suna zaune falon anyi
jugum sukaji sallama, dad ne ya iya
bude
baki yace shigo.
Abban chuchu ne ya shigo tareda
chuchu
wanda tarame sosai takara haske,
teema
ne tatarota tana chuchu ya jikin??
Yaushe aka sallameki?? Tace yau da
safe
teema taja hanunta suka tafi
dakinta.
Falon yarage su dad sai yaranshi
maza
da khalis, Abban chuchu yakara
gyara
zama ya kalli khalis yace khalis
karkaji
ko dar a kirjinka dan babanka dan
aljanna ne, sunyi mutuwar shahada,
muna adduβa Allah ya jikansu kowa
yace
amin.
Dauko file din hanunshi yayi ya
mikama
Alh lamido, alh yakarba yace Abban
chuchu name?? Abban chuchu ya
gyara
zama yace tun satin daya wuce
muna
office Alh hydar ya aika akirani, ina
zuwa yamikamin file dinan wai nai
signing ya barmin dukiyarshi gabaki
daya, kowa na falon saida ya kalli
fuskar
Abban chuchu.
Kafin yacigaba da magana hydar ya
katseshi a zuciye dan dama hydar
tun fil
azal ya tsani mutumin, hakanan
zuciyarshi bai yarda dashiba, cikin
tsawa yace kan wani dalili baffa
zaibarma duka dukiyarshi banci
yanada
yara har biyu?? Ban yardaba
mikamin
file din nagani, dad ya ballama
hydar
harara yakoma ya zauna.
Dad yace Abban chuchu cigaba,
yace Alh
lamido iya abunda nasani shine
yacemin
yabarmin duka dukiyarshi ne saboda
yanaji ajikinshi yakusa barin duniya,
wai ga dukiyarshi duka yabarmin
halak
malak na taimaki musulmai da ita.
Hydar zaiyi magana dad yadaga
mishi
hannu yay shiru.
Dad yace Abban chuchu nafi kowa
sanin
halin kanina na yawan kyauta, so
bawani matsala indan yabarma duka
dukiyarshi saboda yasan cewa nizan
iya
daukan nauyin yayanshi batare da
korafi ba ko kyashiba, so bawani
abu ya
kalli khalis yace ko kanada nacewa
son??
Ahankali khalis yace dad banda abin
cewa tunda yay kyautan shiyasan
dalilin
yinshi Allah yakai ladan kyautan
kabarinshi kowa yace Ameen,
Abban
chuchu ya sauke ajiyan zuciya
finally
yasha.
Har anmanta da zance ancigaba da
fira
sukaji muryan hydar yanacewa dad
amatsayina na wanda yakaranshi
PATHOLOGY inaso nayi performing
AUTOPSY a jikinsu saboda nagano
dalilin, kokuma abunda yakawo
mutuwar suβ¦.
Abban chuchu jiyayi fitsari na
neman
zubo mishi wanan wani irin jaβirin
yarone mai shegen naci????β¦
PATHOLOGIST shine likitan dayake
dealing da komi nakan gawa, shi
likitan
gawawwaki ne abunda hydar ya
karanta
kenan.
AUTOPSY shi text ne da akema
gawa
daya mutu dan agano musasbabin
mutuwanshi, dalilin mutuwarshi,
abunda
yajawo mutuwarsu.
πππππππ
πππππ
πππ
πΉ *_KHALEESAT_*πΉ
ππΌππΌππΌ
```Maman Abd shakur```
_PAGE_
0β£9β£
Dad yace wai hydar me kakecewa
haka
ne?? Kazaci a turai kake dasuke kai
gawa mutually, tun randa abun
yafaru
mukaje muka birnesu, idan kuma
son
sanin abunda yajawo mutuwarsu ne
ai
kafi kowa sanin gobara ce, kuma
kadena
irin maganan nan zakaja khalis ko
wanin mu yafara tunanin kaman
kashesu akayi, da sauri Abban
chuchu
yace hakane wlh.
Hydar yace dad amma kunce baβaga
gawan little pumpkin ba (khaleesat)
??
Dad yace eh, amma munfi kawo ita
takone ne kurmus. Hydar ya kalli
khalis
da yay tagumi yay shiru yana
tunanin
iyayenshi yace jeka shirya kayi
wanka
muje gidanku.
Inhar little pumpkin takone kurmus
ne,
inaganin tokan zan gane jikin
mutum ne,
amma inhar banga tokan dake nuna
alamun jikin mutum neba to zansan
cewa bata gidan lokacin da gobaran
yafaru, daga hakan ne dole nai
bincike
starting 4rm maiya kawo gobaran??
dakuma kan masu gadin gidan
tareda
guards din saboda aisu basu
mutuba,
maisa su kadai suka mutu??
Dad yace kai hydar kacika taurin
kai,
yaro sai nacin balaβi sai alokacin Hj
benazir tai magana tace Alh kyau
kenan,
ya tsaya kan aikinshi kabarshi Alh
yayi
aikinshi, kuma kasan mu kanmu
bamusan maiya kawo gabaran ba,
nafi
kowa sanin halin jabo bata sakaci
da
kayan dasuke kawo wuta, saisa
nima
abun yaban mamaki sosai, kaga
gwara
hydar yay aikinshi koya fito damu
daga
duhu, Alh lamido yay shiru saikuma
yace
kinada gaskiya matana, kuje kuyi
wankan anjima saikuje.
Abban chuchu da zufa ya rufeshi
yana
wanan wani irin mayene?? I have to
do
something, i have to make hydar
disappear 4 good, dole kamutu dan
kana
neman ka tsokano tsuliyan dodo.
Alh lamido yace lpy Abbn chuchu
naga
kana zufa?? yay murmushin yake
tareda
share zufan kanshi yace bakomi,
tunawa
nayi inada meeting a office dad yace
to
bari akirama chuchu kutafi, yace
barta
anjima nazo daukanta yafice daga
falon
wuff.
Alh lamido yay shiru yana tunani hj
benazir tace lpy?? Yace wlh matana
i
found it strange hydar bai tamayin
abu
mai mahimanci haka batare da ya
shawarceniba, har yay kyauta da
duka
dukiyarshi, hj benazir tace kasan
baffa
akwai kyauta, kuma yanason Abban
chuchu sosai dan amininshi ne hala
saisa
yay hakan.
Dad yace kuma hakane Allah sa
mudace
shikuma Allah kai ladan kyautan
kabarinshi, hj tace amin.
Ina labarin khaleesat da hydar dinta
na
nijar??? Sai kuma gobe in sha Allah.
Shin hydar abuja na iya gano
musabbabin wuta?? Yana iya gano
cewa
khaleesat bata cikin gidan wuta
yakama??
Khaleesat na warkewa??
πππππππ
πππππ
πππ
πΉ *_KHALEESAT_*πΉ
ππΌππΌππΌ
```Maman Abd shakur```
_PAGE_
1β£0β£
NIJAR
kwanan khaleesat 5 kullum ummi
nabata
magani amma haryanzu bata
farkaba,
abun na damun ummi itadai tasan
tayi
iya yinta.
********
Ummi likita ce, amma irin likitocin
kauye, a wurin mamarta takoya,
yanzu
haka ita kadaice likita a kauyen, ko
haihu zaβayi ana kiranta ta karbi
haihuwan. mijinta yarasu tun hydar
na
17. ummi ita tacigaba da kula da
hydar
da kanwarshi ZULAIHAT wanda
yanzu
take 18, hydar tun farko yataso
mutum
ne mai zuciya, yanason ummi da
zuliahat sosai, jss3 yakai a karatu
ya
dakatar saboda rashin kudi, gashi
ummi
kullum wahalan aiki yakamata shizai
fara ciyar da uwarshi yanzu, dalilin
dayasa yake farauta kenan, idan
yasamo
dabba wurin farautan yadawo cikin
gari
ya sayar dahaka suka hada kudin
harsukasa zulaihat a makarantan
gwannatin kauye inda yanzu take
jss2.
-***********
Kullum idan ummi ta fita hydar
shizai
zauna da khaleesat yayta kallonta,
shi
kanshi baisan dalilin yin hakanba,
abu
daya yasani shine yana tausayinta,
maita musu dasukeson kasheta??
itako
zulaihat tun randa aka kawo
khaleesat
din tacema hydar , ya hydar dan
Allah
ina sonta da kawa sai yay murmushi
yace