sannan ta ɗauki wayar,hannun ta na rawa ta bi kiran Ummahn ta da ya katse,tana jin muryar Ummahn ta sai ta fashe da kuka,cike da damuwa Ummahn ta ce,
'Ke Uwata lafiya? Me ya faru kike kuka haka?'
"Ummah na shiga uku,yau na takalo faɗa da aljani."
A tsorace Ummah ta ce,
'Kin shiga uku ko mun shiga uku Uwa? A ina ki kai gamo da aljanin? Ko dai malam Shaƙundum ne ya yi mana turen aljanun?'
Cikin kuka Uwa ta labartawa Ummahnta duk abinda ya faru,a rikice Ummahnta ta ce,
'Ya akai ya san inda muka je da abinda muka karɓo? Duk yanda akai wannan hatsabibi ne Uwa,kar ki sake ki yi wasa da shi,ki jawo shi a jiki,yanda ya san sirrin Hajiya da ɗan ta har da jikokin ta,to ba ƙaramin amfani zai yi mana ba a wannan tafiyar,sannan kamar yanda ya ce ki dakata kar ki yi amfani da maganin nan mu jira mu ga nan da lokacin da zaki gama yaudaro mana shi,mu yi amfani da shi dan cimma burin mu.'
Kalaman Ummah ba ƙaramin kwanciyar hankali suka dasawa Uwa ba a ran ta,a hankali ta samu bakin gadonta ta zauna suka ci gaba da ƙulla yanda za su samu nasarar mallake dukiya da gidan Jubair baki ɗaya.
Uwa ce zata karɓi girki a wannan ranae, dan haka sai ta maida hankali wajen girka abinci mai daɗin gaske da taimakon Ubaida wadda ta ƙware a girke-girken zamani da na gargajiya, sai da Uwa ta gama jera komai a sashen Jubair kamar yanda suka saba sannan ta dawo sashen ta ta faɗa wanka,ta jima tana dirzar jikin ta da kayan wanka masu gyara fata sannan ta yi alwala ta fito zuwa ɗakin ta,kwalliya ta tsara mai kyau kafin ta gama dare ya yi har ma Jubair ya dawo,shiryawa ta yi cikin wani leshi mai laushi da tsada,an yi masa wani irin matsattsen ɗinki sai ta feshe jikin ta da turaruka ta yafa wani yalolon mayafi ta ɗauki wayar ta ta kulle ɗakunan ta,sallama ta yiwa Ubaida sannan ta wuce sashen Jubair.
Ƙamshin jikin ta ne ya daki hancin shi dan haka cikin wani irin yanayi ya ɗaga kai ya kalli kyakkyawar bafulatanar dake gaban shi tana taku kamar wata hawainiya,murmushi suka sakarwa junan su,hannu Jubair ya buɗewa Uwa ta taka a yangance ta je gare shi ta zauna a saman ƙafafun shi,a shagwab'e ta ce,
"Gaskiya ni dai Hammaah ka tashi mu je mu ci abinci idan yaso sai mu zo mu yi kalar hirar da ka ke so,yau baka ji irin gajiyar da na yi ba."
Murmushi ya yi sannan ya ce,
"To ke dama yaushe ne baki gajiya fisabillahi Hafsy?"
"Au haka ma zaka ce? Kar fa ka manta ni ban saba aikin wahala ba ko a gidan mu,amma saboda matar ka ta saba da wahala tana maka girki ka tursasa ni nima nake yi maka girki da kaina,ka ga kuwa dole na gaji."
Nan take Jubair ya haɗe fuska kamar bai taɓa dariya ba,dan kuwa ya tsani duk abinda zai taɓa darajar Ruƙayyan shi,tashi ya yi a ɗan hasale ya wuce wajen cin abincin,turus ya tsaya ya yi yana kallon saman dinning table ɗin,ganin ya tsaya yana kallon saman dinning ne ya sanya Uwa ƙarasawa,tana isa ta ƙame cike da matsanancin tsoro da fargaba tare da tashin hankali,menene wannan take gani?
'Munkaila.'
Shine sunan da ya ɗarsu a zuciyar ta............
[20/10, 7:52 am] HAERMEEEBRAERH ✍️✨: DUK NISAN DARE....
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 5:
A nutse Uwa ta danna horn a bakin gate ɗin gidan nasu tana jiran mai gadi ya buɗe mata. Buɗe gidan ke da wuya ta fahimci mahaifinta na gida bai fita ba kamar yanda ta yi zato. Sai da ta gaida mai gadin nasu kafin ta wuce ta adana motar ta a waje ajiye motoci, mayafinta ta sake ja ta lulluɓe duk inda ya dace a jikin ta kafin ta ɗauki jakar ta da wayoyin ta ta fita.
Tafe take tana sake gyara tsadaddiyar doguwar rigar ta gudun kar mahaifinta ya yi faɗan bata sanya hijabi ba. A babban parlourn gidan ta tarar da su suna karyawa cike da so da ƙaunar junan su,shigar ta ce ta katse musu hirar tasu suka zuba mata ido suna kallon ta. Cikin wata iriyar murya ta dattijai mahaifin Uwa ya ce.
"Ah ah Hafsat me kike yi a gida da sassafe haka? In ce dai lafiya ko?"
Sunkuyar da kai Uwa ta yi ƙasa tare da ƙarasawa cikin kyakkyawan wajen dining area ɗin gidan,sai da ta durƙusa har ƙasa ta gaishe da iyayen nata kafin ta samu waje saman kujera ta zauna,kanta a ƙasa ta sa hannu ta share hawayen dake zuba a idanun ta,ganin iyayen nata sun zuba mata idanu da wani irin yanayi a fuskokin su na tsoro sai ya sa zuciyar ta rauni k'warai da gaske ta hau zubar da hawaye,nan take hankalin su ya ƙara tashi mahaifiyar ta sai ta matso ta samu waje kusa da ita ta zauna ta kama hannayen ta dika biyun ta ce,
"Sanar dani damuwar ki Uwata, tashin hankalin ki tashin hankali na ne,ɓacin ranki ɓacin raina ne,wa ya taɓa ki yanzu garin Yola ya shaida na yi sabon maƙiyi?"
A sheƙe mahaifin Uwa ya kalli matar tashi da hankalin ta ya yi bala'in tashi,gyaran murya ya yi kafin ya ce,
"Ke muke sauraro ina sauri zan fita kar ki tsaida ni akan shirmen banza."
Nan take jikin Uwa ya fara rawa,dan kuwa ba ƙaramin tsoron mahaifin nata take ji ba,ɗan sakar mata fuskan da ya yi na ɗan lokaci ne ya sanya ta manta asalin shi waye,jiki na rawa ta furta.
"Abbah dama uhumm..dama Ruƙayya ce ke da ciki...shine... shine...."
Cike da ɓacin rai mahaifin ta ya kalle ta ya ce,
"Ruƙayya na da ciki ke kuma baki da shi shine kika zo nan gidan uban ki da ake rabawa a baki naki kason ko?"
Girgiza kai Uwa ta fara yi tana ja da baya daga saman kujerar da take kai,cike da masifa mahaifin ta ya fara magana,
"Uwa ki kiyaye ni akan wannan baƙin kishin naki,kin san Allah...duk sanda kika kaso auren ki a karo na biyu sai dai ki nemi gidan da zaki zauna,saboda ba zan ci gaba da ganin ki kina zawarci ba,ke bakya jin kunya ne ki yi ta abu kamar marar ilimin addini? Alhamdulillah ni na sani har a wajen Allah na fita haƙƙin ki Uwa,na baki ilimin addini har kin kai babban matakin da ko wa'azi zaki iya yiwa wasu,na baki ilimin zamani kin kai matakin Masters,sannan na baki na zaman duniya tinda ba a iya garin Yola kika yi karatu ba kin je gari-gari a faɗin ƙasar nan dan neman ilimi,amma duk da haka har yanzu baki ɗauki abinda nake faɗa maki ba balle abinda kika karanto a duniya,ke wace iriyar yarinya ce ne Uwa? Yaushe zaki yi hankali ki gane Allah ne mai yi a sanda ya so,kuma ya hana a sanda ya so? A kan ki aka fara rashin haihuwa?"
Ganin irin faɗan da mahaifinta ke yi mata ne ya sanya ta sanya kuka mai matuƙar ƙuna,dama ta riga ta sani in har ta same shi a gida to fa ba lallai burin ta ya cika ba,ita kuwa ko sama da ƙasa zasu game waje guda sai ta salwantar da yaran Ruƙayya har ma ta yi sanadiyyar raba su da duniyar kowa ya huta. Duk wani abu da Abbahn ta ke faɗa ba jin shi take yi ba a daidai wannan lokacin,zuciya da hankalin ta na can suna tunanin yanda zata aiwatar da mugun nufin dake cikin ranta,dukan table ɗin gaban ta da Abbah ya yi ne ya sanya ta zabura ta kwasa da gudu ta wuce sama tana gunjin kuka.
Cike da tsananin tausayi irin na ƴa da uwa Ummah ta kalli Abbah ta ce,
"Haba Abbahn Hafsat ! Me yasa zaka sake ƙunsa mata baƙin ciki akan wanda take ciki bayan baka bata dama ta sanar da mu damuwar ta ba dan...."
"Ke ji mana dakata min dan Allah ! Kina nufin tsayawa zan yi na ji shiriritar wannan yarinyar? Akan wanne dalili to? Kanta aka fara rashin haihuwa? Shin ta kai matan Annabi daraja ne tinda Allah bai basu haihuwa ba suma? Kar ki manta fa Nana Aisha har ta bar duniya bata taɓa haihuwa ba,to ita wacece dan Allah ya jarabce ta zata ɗaga hankalin ta muma ta ɗaga mana namu,na fa ga take-taken ta so take ta kashe auren ta dawo ta sake yin zaman zawarci a gidan nan,to ina mai tabbatar maku da ke da ita,duk sanda ta kaso auren ta zaku bar min gida na,ki kira ta tazo ta bar min gida ta koma gidan mijin ta,kar na dawo na tarar da ita a gidan nan,kin ji na faɗa maki."
A matuƙar hasale ya kwashi wayoyin shi guda uku masu tsananin tsada ya ɗauki makullin motar shi ya ja kujerar da yake kai baya ya fita ya bar parlour'n,yana fita drivern shi ya taso ya duƙa ya gaishe shi tare da karɓar makullin motar ya wuce gaba.
Sai da Ummah ta tabbatar da fitar shi sannan ta haura sama wajen Uwa dake ta risgar kuka kamar wata ƙaramar yarinya,Ummah na shiga Uwa ta tashi da gudu ta rungume ta tana ci gaba da kuka,cikin sigar rarrashi Ummah ta ce.
"Maza ki sanar dani abinda ke damun ki in magance maki shi,idan shi ba zai iya ba ni zan iya,haka kawai,so ake a kashe min ke da baƙin ciki? Shi yasan zafin rashin haihuwa ne yana namiji? To ba zai yu ba,babu wanda zai sanya min ke zubar hawaye haka ya kwana lafiya."
Cike da jin daɗi Uwa ta zauna ta sanar da Ummah duk abinda ke faruwa a gidan,har da ƙarin auren da Hajiya Dada ta ce Jubair ya ƙara matsawar ba a haifa masa magaji ba. Nan da nan kuwa ran Ummah ya ɓaci ta ce,
"Lallai ma Dada,ashe zata iya manta alaƙar zumuncin dake tsakanin mu ta bijiro da waɗannan halayen? Wa take da shi da ya wuce mu? Mu ne nata ko ta ƙi ko taso,kuma dukiyar Jubair da yardar Allah ke da ɗan da zaki haifa anan gaba zaku ci ta,tashi ki wanke fuskar ki ki shirya mu fita,ni za a kawowa lalata?"
Tsallen murna Uwa ta doka sannan ta ɗafe mahaifiyarta tana godiya da farin ciki,cikin tsananin murna ta ce,
"Dama na san ba zaki bar hawaye na ya zuba a banza ba,uwata mai share min hawaye na,uwata maganin kuka na,ki jima ki yi ƙarko Ummahna ina son ki."
Farin ciki ne ya mamaye zuciyar Ummah saboda ganin shalelen nata na murna,cikin ƙanƙanin lokaci suka shirya suka hau mota ɗaya suka bar gidan,tinda suka fita suka keta titin dake shinfiɗe a unguwar tasu ta Karewa,har suka shiga cikin gari basu daina gudu ba, nausawa suka yi cikin wata unguwa dake tsakiyar garin Yola,a ƙofar wani gida suka tsayar da motar su Ummah dake tuƙawa ta fito sanye da baƙin tabarau tana taunar chewing gum tana yatsina hanci tare da tsartar da yawu,a wulaƙance suke kallon unguwar da ta ke dauke da gidajen yaku bayi har suka tsaida kallon su akan gidan da ke gaban su,gida ne na ƙasa da aka yiwa flasta da siminti aka shafe shi da farar ƙasa tin daga waje har cikin gidan.
Bakunan su ɗauke da sallama suka shiga cikin gidan suna yatsina,wata mata suka gani da tsohon ciki tana zaune gaban ta wata yarinya ce duƙun-duƙun da ita tana kashi a poo,matar na riƙe da buta ta tsartar da yawu ta ce,
"Ah ah Hajiya yau kune ke tafe? Bismillah'n ku bari na ɗakko muku tabarma ku jira malam ɗin,dan kuwa ya zaga gona sai dai kuma idan zaki sa waya ki kira shi dan ya san da zuwan ku."
A yatsine Ummah ta tauna Chewing gum ɗin ta sannan ta buɗe jakar ta ta zaro waya ta kira malam,tana gama sanar da shi sun iso ta katse,cikin ƙanƙanin lokaci Malam ya iso yana washe baki,ɗakin da yake karɓar baƙi ya buɗe musu suka shiga ciki,waje ne mai kyau har da kujeru da carpet saboda tarbon baƙi irin su Ummah,duk da yanda wajen yake a share a tsaftace bai hana su Ummah yatsina ba kamar sun zauna a saman kashi,sai da Malam ya ajiye kaucin magungunan da ya samo a daji sannan ya zauna yana washe baki ya ce,
"Hajiya ku ne ke tafe da safen nan? Allah sarki, ai gona na je,ina hanyar dawowa kika kira ni."
"Uhumm Allah sarki, to sannu fa,damaaa.."
Murmushi ya yi sannan ya ce,
"Dakata Hajiya,ai wannan aikin da kuke tafe da shi na riga na san da shi,kun yi jinkiri k'warai baku zo da wuri ba,domin kuwa tin wata biyu da suka gabata nake saka ran zuwan ku amma shiru."
Cikin tsananin damuwa Uwa ta ce,
"Yanzu kana nufin Malam babu abinda zaka iya yi akan matsala ta?"
"Idan na ce maki ba zan iya komai ba ai ban amsa suna na shaƙundum ba ko? Maganar zubar da cikin ita abokiyar zaman ki nake magana akai yanzu,ina so ku sani shi wannan ciki sai an haifo shi duniya da ikon Allah,sannan cikin nan tin a daren da na yi mafarkin zuwan ki nake bincike dan in gano me za a haifa na kasa ganowa har yau,abu na gaba kuma shine zan baki maganin da zaki dinga sakawa yaran kishiyar ki a abinci sai dai sharaɗin maganin a hankali yake aiki,sai dai a wayi gari yaran sun bugawa Uban su muguwar sata ta ban mamaki sun gudu sun bar gidan,za su shiga duniya su yi karuwanci su lalace kamar yanda kike buri,sai dai kuma akwai wata babbar matsala..."
"Mu dai bamu ga matsala ba Malam,yanzu karb'i nan,duk wata matsala da ka gano ka kawar da ita,bana son jin komai bana son ganin komai,na yarda da kai, na amince da kai zaka share min kuka na da na ƴa ta, dan haka na bar maka wuƙa da nama a hannun ka,ka yanki inda ka so."
Gudun kar aikin shi ya lalace ya rasa inda yake samun cin abinci sai Malam ya tsuke baki bai sake magana ba,maƙudan kuɗin da za su kai kimanin dubu ɗari biyar ya amshe yana ta zuba godiya,nan da nan ya tashi ya hau haɗa magungunan da zai baiwa Uwa, yana kammalawa ya basu suka yi sallama suka wuce gida.
Koda suka je gida basu wani jima ba Ummah ta sallami Uwa ta ce ta koma gida kafin mahaifin ta ya dawo ya tarar da ita a gida,sai da ta sake jaddada mata yanda za ta yi amfani da magungunan sannan suka rabu kowa na farin cikin sun kamo bakin zaren matsalar su...........
[20/10, 7:52 am] HAERMEEEBRAERH ✍️✨: DUK NISAN DARE....
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
*Wannan littafin na kuɗi ne,duk wanda yake group ɗin nan ya karanta bisa amana,dan Allah kar a yi sharing da friends a bari na kammala dika,sai a baiwa duk wanda za a baiwa,da ku yi sharing da ƙawayen ku gwanda ku taimaka ku tallata musu haja ta su saya ko da kuɗin cefanen su ne. Na gode.*
PAGE 8:
A hankali Ruƙayyah ta zagaye su ta wuce ciki ta samu waje ta zauna saboda ta yi matuƙar gajiya kamar wanda suka tako da ƙafa haka take jin ta,gilmawar ta ne ya sanya Jubair saurin dawowa hayyacin shi,riƙe da hannun Malika ya nufi tsakiyar parlourn da duk ta wargaza komai kamar wata yarinyar goye,cike da dakiya ya kalle ta ya ce,
"Yanzu baby duk ke ce kika yi wannan ɓarnar?"
Sunne kai ta yi tana wasa da hannayen ta,cike da shagwab'a ta ce,
"Papa ban san zaka zo ba,da na san zaka zo da na haƙura da zuwa prom ɗin,da ni zan je ɗakko ku a airport."
Hajiya Dada ce ta karɓe zancen da cewa,
"Ina fa za ki so uban naki ya ga wannan ta'asar da kika yi? Shi wanda kika raina a gidan shi ya ƙyale ki,ai dagewa zai yi ya baki jikin ki ya kammale miki shi waje ɗaya,wataƙila kin samu natsuwa,yarinya sai kace rainon gwauro?....ah ah Samhah me nake gani haka? Kema ciki ne da ke? Kun gama turancin kenan?"
Cike da jin kunya Samhah ta wuce ɗakin da suke ajiye kayan share-sharen su da goge-goge,murmushi Ammar ya yi kafin ya kama hannun Hajiya Dada ya samar mata da wajen zama,itan ma murmushin ta saki ta ce,
"Alhamdulillah mun godewa Allah,ya Allah ba dan hali na ba Allah ka azurta yaran nan da ƴaƴa maza,wanda za su tausaya musu a lokacin da tsufa ya riske su,Allah ka basu masu albarka,Allah yasa kar na mutu sai naga magadan ku."
Jubair ne ya buɗe baki zai yi magana,Ammar ya riga shi ta hanyar faɗin,
"Ameeen Hajjajunmu Allah ya ƙara maki imani da lafiya,ku yi haƙuri ban samu na zo na ɗakko ku ba,na so na yi surprising mutanen gidan ne sai dai kawai su ga na ɗakko ku,amma hakan bai samu ba wannan rigimammiyar ƴar taka duk ta rusa komai."
Ammar ne ya kalli Malika da ta maƙale shi ta zauna daf da shi kamar zata zauna a cinyar shi ya ce,
"Kar ka ɗorawa babyna laifi,da ace ka sanar da ita zuwa na da duk haka bata faru ba,gashi nan garin bata surprise ita ta baka,ka duba ka ga yanda ta farfashe abubuwa masu tsada?"
"Humm Allah dai ya shirya mana zuri'a,mu ta can wa ya isa ya mana wannan iya shegen bamu duba masa fatar sa ba?"
Zumɓura baki Malika ta yi a lokacin da Hajiya Dada ta gama maganarta tana kallon ta,cike da jin haushin an sata gaba ta miƙe cikin wasu irin kaya matsattsu kuma yagaggu,dan kuwa ta gaban rigar gaba ɗaya a fafake yake,iya saman cikakkun ƙirjinta ne kawai a rufe,sai gefen cinyar ta da yake a tsage har ƙasa,ba kaɗan ba jar rigar ta karɓi jikin ta,tsukakken ƙugun ta ɗaure yake da wani siririn golden belt ɗin da ya sha stones masu kyau sai walƙiya yake,gashin ta irin na fulanin asali ta karkaɗa kafin ta sa hannu ta cire dogayen takalman dake ƙafar ta ta riƙe su a hannu ta haye sama. Duk abinda Malika ke aikatawa idanun Jubair na kai,a haka Samhah ta kammala kwashe kwalaben da suka fashe ta goge wajen ta mayar da kayan aikin ma'ajiyar su. Ƙararrawar dake sanar da zuwan ɓaki aka kaɗa,cikin azama Ammar da ya san wanda ke danna ƙararrawar ya miƙe yana murmushi, restaurant ɗin da ya yi order abinci da abun sha ne suka kawo abinci dan tarbon baƙi,sai da ya karɓa ya sallame su ne ya koma da abinci niƙi-niƙi. Ya riga da ya san idan Samhah ta san da zuwan su za ta ce za ta yi girki,kuma ba zata iya ba duba da cewa ba wani aikin wahala take yi ba da cikin.
Sai da suka shiga ɗakunan da aka sauke su suka yi wanka suka shirya sannan suka fito cin abinci,Ammar ne ya kalli Ruƙayya da ke sunkuyar da kai ya yi murmushi sannan ya ce,
"Ni fa Ruƙy kina bani mamaki,har yanzu da muka yi shekaru kusan goma sha takwas baki iya sakin jikin ki da mu? Gaskiya ke a fulanin ma ta daban ce."
Murmushi ta yi kawai ta samu waje a inda Jubair ya fitar mata da kujera ta zauna riƙe da cikin ta da ya yi tsini sosai,suna zama Malika ta sakko cikin gajeran wando iya cinyoyin ta da wata rigar sanyi ƙatuwa mai dogayen hannuwa,gashin kanta a baje a saman kafaɗun ta tana waya tare da bada tabbacin gata nan fitowa.
Ko ta kan mutanen gidan bata bi ba ta tunkari kofar fita daga gidan,sai da ta tsaya ta sanya takalminta ta ɗaure igiyar shi sannan ta ce,
"Pops na fita wajen Afdhal yana waje yana jira na yanzu zan dawo."
Hajiya Dada ce ta kalli Ammar sannan ta kalli Jubair,kafin ta maida dubanta kan Malika da ta buɗe ƙofar ta yi waje abunta hankali kwance,cike da ɓacin rai Hajiya Dada ta ce,
"Ba zai yu ba ! Inaaa ba zan lamunci iya shege ba,jikar tawa ce ke yawo tsirara cinyoyi waje? A gabana... a gaban idanun ku ta fita ta tafi wajen wani ƙato duk baku hana ba? To kai Ammar meye amfanin ka kenan? Ai dole yarinya ta raina ku a yi mata magana ta hau zuba shegen turanci kamar ƴar joji bush."
Shiru wajen ya ɗauka,domin kuwa gaba ɗayan su suna jin hucin ɓacin ran Hajiya Dada na sauka a jikin su,wajen cin abincin ta bari ta wuce ɗakin da aka sauke su ita da Ruƙayya,ganin haka ne ya sanya Ruƙayya miƙewa da ƙyar ta ɗebi abincin daidai yanda ta san Hajiya Dada zata iya ci ta bi bayan ta da shi.
Iska Ammar ya furzar ya na dafe kan shi,a hankali ya furta,
"Irin wannan ɓacin ran nake jiye mana shi yasa nake hana ta wasu abubuwan,ke kuma sai ki ce wai ai haka ake yi ba matsala bane,da ace kin taimaka min wajen baiwa yarinyar nan tarbiyya irin ta addinin mu da al'adar mu da haka bata faru ba."
Jubair ne ya yi saurin cewa,
"Kar ka ɗora mata laifi ɗan'uwana,yarinyar nan tana zuwa makaranta,makaranta babba wadda ta haɗa da INTERNATIONAL students,mutane ne ta kowanne fanni na duniya take tare da su shi yasa ta koyo wasu halayen da babu su a al'ada da addinin mu,da ace a Nigeria take ai wani abun ba zata yi shi ba,kai dai kawai mu yi ta taya ta da addu'a shine mafita."
Ruƙayya ce ta dawo ɗauke da abincin da ta kai wa Hajiya Dada ta kalli Jubair da Ammar ta ce,
"Taƙi ci,dan Allah ku je ku lallashe ta,dan ko a jirgi ma banga ta ci wani abun kirki ba."
Ammar ne ya karb'i abincin ya tafi ɗakin Hajiya Dada,ya jima sosai suna tattaunawa kafin ya dawo ya na hamdala,zaune ya tarar da su Jubair a parlour suna hira,a hankali ya isa bakin window ya na leƙen su Malika dake hira ita da Afdhal riƙe da hannun junan su,girgiza kai ya yi cike da takaici ya bar wajen,duk hirar da ake yi hankalin shi na kan Malika. Sai da suka kusan barin parlour'n sannan ta shigo gidan cike da maɗaukakin farin ciki,kusa da Jubair ta zauna ta na washe baki ta ce,
"Papa gobe friends d'ina za su haɗa min party saboda rashin samun damar halartar prom da ban yi ba,abokai na su na so na da yawa."
Ta ƙarasa maganar ta cikin wani ƙayataccen murmushi ta ɗauki Apple ɗin dake saman table ɗin gabanta ta gatsa, Samhah ce ta ce.
"Su na dai tsoron ki,tinda idan basu yi maki abinda kike so ba zaki hau fushi da su ki na yi musu masifa."
A shagwab'e Malika ta kalli Ammar ta ce,
"Daaaddd."
Murmushi kawai ya yi ya shafi kanta ya tattara mugs ɗin da suka sha shayi ya wuce kitchen da su,zuciyar shi fal tunani kala-kala.
Washegari da safe su Jubair asibitin da Ruƙayya ta saba haihuwa a duk sanda ta samu ciki suka tafi,duk wani abu da ya kamata su yi sun yi sun kammala lafiya,daga nan sai suka wuce siyayya wani babban mall,zuwan su ke da wuya Ruƙayya ta ga wasu masoya na sumbatar junan su a tsakiyar mutane ko kunya basu ji, a matuƙar kunyace ta laɓe a bayan Jubair tana tafiya kanta a ƙasa,banda dariya babu abinda Jubair ke yi mata,cike da tsokana ya ce,
"Madam ko muma za mu nuna musu tamu kalar soyayyar irin ta ƴan Nigeria ne?"
Cikin sauri ta girgiza kanta ta yi gaba ta bar shi a baya yana yi mata dariya. Haka rayuwar su Jubair ta ci gaba da gudana a kasar turai suna jiran ranar haihuwa ta zo,dan kuwa daf take da haihuwar,Samhah kuwa watan cikin ta takwas ta na da sauran wata ɗaya kafin ta haihu.
Duk wani rashin ji da zuwa party,da yawo babu sururar arziƙi da Malika ke yi akan idanun Hajiya Dada,sai dai Jubair kanshi ya yi mamakin yanda ta dena damuwa da hakan balle ta yi faɗa akai. Malika kuwa ta ji daɗin yanda Grandma ɗin nata bata saka mata ido ba wannan zuwan balle ta hana ta rawar gaban hantsi.
****************************
A can Nigeria kuwa hankalin Uwa ya kasa kwanciya tin bayan da su Jubair suka wuce ƙasar waje,duk wani duba da tsubbace-tsubbace ta yi akan sanin abinda Ruƙayya zata haifa amma abun ya ci tura, ƙarshe ma Munkaila ne ya zaunar da ita ya yi mata bayani dalla-dalla wanda ya sake sanya ta ciki damuwa,cike da tashin hankali ta kalli Munkaila wanda shigar shi sashe nata kenan babu jimawa ta ce.
"Yanzu ka na nufin haka zan zauna