Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
zai sanya Ibrahim ya rabu đa babansa duk abin da zai yi masa muddin bai nemi ransa ko na Farida ba me zai sanya Farida ta yi watsi da Ibrahim mijinta muddin ba ta ga zasu raba ta da ranta ba. Biyu sau biyu fa hudu ce me gida na" Naibi ya dinga gyada kai na samin gamsuwa. "Na ji kamshin hakan, amma ban sami hujjojin dafa wa ba sai a wurinka... an so kashe Farida yayinda aka sami damar gaya mata Ibrahim baya son ta da gaskiya". Wilson yayi dariya a hankali. "Amma kuwa Ibrahim na matukar son ta. Ga shi har ya ba mu kansa" "Me zamu yi da shi?" "Me gida na kana abu kamar ba kai ka koya min ba, ka san dai ba zamu kai Me gida Hadi wurin `yansanda ba, mu zamu yi masa hukumci. Ranar soyayyar Ibrahim da kayutarsa ke nan" Na`ibi ya sanya masa ido don mika wuya ga dabarar me dabara "A gayyaci Ibrahim, ka ba shi gida ka yi masa daurin talala da sunan zaka sasanta shi da Farida in ta warke ka ga duk sun zama na mu, amma fa zaku yi tozali da tsohon abokinka 134 Manyan Masoya Rahma AbdulMajid bana, Oga Hadi. Kai dama ina nan zaku hadu na ga kewa". "Sai kuma me?" "Sai ka hadu da Hadi ka sanar da shi duk abind a aka gano da kuma hujjojin kayar da shi, babba ma shine dan cikinsa na shirin tona masa asiri a idon duniya don ya bayar da hadin kai.... Ka ga yana da zabi ko ya fita ya bar mana takarar kwangilar 96 Column ya sanya hannu a masu goyon bayanmu ko kuma daga nan sunansa ya tafi kwandon shara ka ga... Na`ibi ya saki hannu ya ja tsaki. "Kai kullun batun kudi da gasa ne a gabanka in2 maganar iyali na kana maganar a bar mana kwangila... ya taba kasa mu ne a neman kwangila?" Duk maganar da me gidansa yake yana kada kai cikin murmushin ruwan sanyi watakila ma shi yasa ya ba shi damar ci gaba da magana bayan ya yi tambaya. "ko kadan yau ba kudi ne a gabana ba ranka ya dade saukake maka abu na ke son yi. Hadi bai taba kasa mu ba, amma bamu taba cin riba kansa cikin ruwan sanyi, ba, wannan karon ina son hakan ta faru cikin ruwan sanyi kamar yadda kai shi kotu daga baya zai zo mana cikin ruwan sanyi....Haba yanzu in muka ce mu wuce da shi wurin `yansanda kai tsaye ka san kashe kudi gida biyu ke nan, shi ma ka san fa me kan sarki ne fa zai kashe za a kashe masa masu hanya zasu yi masa kara. Koda na san zamu yi 135 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid galaba amma dakyar, amma in har mun kasa shi a wannan kasuwar bayan kudin da ya kashe a kanta, darajarsa za ta kara zubewa a idon masu iya son goyon baya a duk lokacin da rigima za ta hafa ku, sannan fa in ya tsaya ja da kai a kotu shi yana kashe uwar kudi ne kana kashe riba...." "Na ji na gane... shi kuma dan yaya zan yi da shi in yi ta rikon sa?" "Da sunan Farida na kara murmurewa kuma kana shawo kanta ba. In an gama shari'a, zamu yi masa hukumci da sunan ubansa ne yayi masa don haushin ya kalubalance shi...kai me gidana in wannan tsari ya tabbata Hadi ya fita daga littafin mu na masu yi mana ta`addanci" Shi ma sai da yayi dariyar saboda gamsuwa, sannan ya koma gefe daya yana danna wayarsa. "Bari na kira yaron" Wilson ya dauke wuta dif. "Hello Ibrahim? Ina gajiya... a ina kake a halin yanzu?... to na dan yi tunani kan maganarka kuma ina son ganin ka gobe zan sanya a zo a dauke ka a kawo ka inda zamu gana Ya kashe wayar ya dubi Wilson. "A otel yake, gobe zan gana da shi a gidan Merry, ka yi hanyar yadda zai zo can zuwa sha biyu na rana zan isa wurin sha daya da rabi". "An gama ranka ya dade" Ya juya ya bar dakin ganawar kafin Wilson * 136 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ibrahim ya dan nisa ya karkata kai gefen hagunsa ba inda Farid yake ba. "Me nene hadin ka da Farida?" Ya tambayi Farid wanda ke kallon sa cikin kokarin boye duk wani zafi. "Kamar na fi ka bukatar jin wannan amsar, ko ba komai na san mene ne" In ji Farid wanda ke kokarin yin ta maza don ya kwaci hakkinsa na mazakuta, ko ba komai ya samu ya janyo hankalin wanda ya tambaya din da jin girmar tuhumar da yake har ma ya kalle shi cikin ido. "Ni? Wa nene ga Farida?" Ya dan mike daga jinginar da yayi da teburin. "Ni ne mijin Farida da ta aura cikin tsananin so duk da ni da ne ga babban abokin hamayyar mahaifinta AbdulHadi. In kana da labarin tana da ciki to ni ne uba ga abin da yake cikinta..." Ya dan sarara sannan ya sunkuyar da kai. "Tana fishi da ni da zaton cewa ina da masaniya kan cutuwar da tayi...ba ta ba ni damar da nake bukata ba na wanke kai na, amma nayi mata uziri don sanin kaunarta gare ni da cewa tana ganin ban kamaci na yi mata haka ba, ta ji zafin abin matuka, sai dai ba zan dena jira ba, wata rana soyayya za ta ba ni dama a wurinta na wanke kai na tsaf" Ya dago ya kalle shi da kyau. "Amma fa mata ta ce da ba zamu taba rabuwa ba" Σ Rahma AbdulMajid 131 Mafiyan Masoya Kwatsam sai Farid ya sami kansa yana mai rage jin haushi da zafi, kai! Kamar ya ma saba da yanayin nan take. Farida ta auri wani ke nan ba shi ba kuma tayi haka ne don tana son sa har shi yasa ta 6oye wa mahaifanta, akwai alamar har yau tana son sa duk kuwa da tana zarginsa da cutar da ita, amma ta kasa bayyana hakan ga mahaifanta don kauna. Haka ma wanda take so yana yi mata matukar so wanda in bai fi shi ba zai yarda su yi tangangan. Can wani bege na dama a ce shine da Farida cikin wannan yanayi ya kama shi har ya sanya shi tsanananta kallon da yake yi wa Ibrahim ba tare da ya san yana yi ba. "Zaka iya gaya min kai kuma me ke hada ka da Farida bayan da na gaya maka ko ni wa nene?" Yayi murmushi ya sunkuyar da kansa cikin jin nauyin rashin sanin takamaiman lokacinda ya 6ata yana kallon Ibrahim. "Ni?.. Ni abokinta ne kuma me yi mata fatan alheri, amma ban san tayi aure ba in gaya maka gaskiya. saibayan faruwar wannan lamarin...wafi abu ne da nake fatan in har ta ba ni dama na ji karin bayani abakinta...sai daị in ya tabbata kai ne mijinta kun yi auren, zan so ka san ka sami mata, jaruma ce kuma mai halin kwarai...ka rike ta kuma ka faranta mata rai. Kа san cewa wata alheri ce a rayuwarka da wasu ke fatan samu ba su samu ba, kuma kai kanka zai yi wuya ka maimaita samun irinsa. 138 Moyan Masoya Rahma AbdulMajid * Merry ta dan waigo ta dubi bayanta ba don bata gan shi ta madubin gabanta ba sai don mamakin zuwansa a wannan lokaci. Ta ko tabbatar shi ne yake tsaye a kofar katon dakin yana murmushi, ta mai da kanta ga madubin inda ta ci gaba da gyaran gashinta. "Me ciyamanan ke yi a gidan Sa-daka yau a lokacin da matarsa take gari?" Ya zubo hannayensa na al'ada cikin aljihu sannan ya karaso cikin dakin. "Duk wani abu naki da yake gidan nan na sanya an kwashe miki shi zuwa sabon gida da ke kan wannan adireshin" Ya ja linzamin maganar har ya a jiye mata adireshin a kan karbun miron dake gabanta. "Abin da ya saura naki sune wannan kayan gyaran gashin naki sai ki kwashe abinki da kanki. Nan da mintuna arba`in wasu zasu bakunci gidan nan, amma ke zaki iya komawa sabon gidanki da ya fi nan kyau da girma" Ta dube shi da sauri cikin zallar mamakin da bai cakudu da komai ba duk da fishi na son maye gurbinsa. "Mene ne ya zo kuma? Me yasa kake min haka? Kullun cikin canjin gida ba zan taba cewa ga muhalli na ba. Ko dansanda ko soja ba su kai ni sauya muhalli ba tun da na fara zama tare da kai ciyaman wai... Ya shafi kumatunta yana murmushin kashita har zuwa hafarta sannan ya rike. 139 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Sauyi Plan ne na ciyaman din ki gara ki karba da hakuri. Ya sake ta inda ya doshi kwabarta ta kayan bacci ya soma tattara mata yana magana. "Nan da mintocin da na ambata ina jin zan yi ajiya da ba zamu so ta san dake ba...Ibrahim din Farida kuma dan abokin mu Hadi zai bakunci gidan nan na mika wuya gare ni...kin san ba zan so ko ke ki so saurayin kawarki ya gan ki a turakar sirikinsa ba..." Da sauri ta dafa shi. י "wane Ibrahim?Balalan Farida? Me zai kawo shi kusa da rayuwarka?" Ya sake ruko hannayen ta. "Kwantar da hankalinki sallamawa ce yayi ga masoyinki kuma zai mika wuya ga duk makircina na kai karshen Hadi mu huta a karo na karshe. Wannan mintoci na da muhimmanci don haka ki bar nan kafin su cika" Ya sunbace ta sannan ya fita ya bar ta tana murmushi "Ciyaman dinki ya kusa dawowa don uwar gida ta kusa tafiya" Ta rankwafa ta soma kwashe kayanta da sauri tana fadin bukatarmu zata biya. Har sai da yayi nisa sannan ta dakata ta duba ta tabbatar ya fita sannan ta yi watsi da kayan ta fashe da dariya. "Dubunki yana ta,cika Farida. Ramuwata gare ki tana ta kara fin gayya zaffi, yau 140 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid saurayinki zai zo har inda na sani, zai zauna inda watakila ni kadai na sani bayan ubanki Ta fashe da dariya sannan ta sake karantowa kanta wani zancen. "Wannan kumatun kika mara kika watso wa wannan kayan jikin kayansa waje daga gidanki wai don ina kawo masoyina gidanki kika kira ni karuwa ina kawo miki maza gida. Yanzu sakayyata gare ki shine har ubanki nake kai wa London din da kike jin don kin kai ni zaki mare ni. To yau kin ji karin wani dadi kan dadi...za a kawo min masoyinki...ina da hotuna da babanki zan yi da masoyinki ki san lallai ni karuwa се Farida". Kau! Ta ji zafin marin ya dawo mata har ta tuna ranar da abin ya faru. Wata rana ce da suka cika kwana uku a tsakiyar birnin Landan inda tayi rakiya ga kawarta Farida wadda ta je buikin wata kawarta da aka yi a can. Sun dawo gida ne daga biki ta sami Merry kawarta a cikin uwar dakinta suna saduwa ita da wani katon mutum da alamun dan Najeriya ne, amma bata san shi ba, abin yayi mata ciwo matuka yadda da ta taso ta sha gaban Farida zata yi mata magiya Faridar ta kife ta da mari ta nuna mata kofar fita, har ta biyo ta da kayanta da fasfo da tikitinta cewa kada ta sake zuwa gidanta tunda ita 'yar iska ce kuma tana bata mata gida. Wannan kunyata da tayi gaban saurayinta wanda ya gayyace ta zuwa nasa gidan don su karasa abin da suka fara ya hana ta iya more z manta a dakinsa inda shi ma 141 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid ya kore ta don ba zata biya masa bukata ba. Ba shiri ta dawo Najeriya inda ta fara shirin daukan fansa kan Farida ta ko halin kaka. Da fari ta so matuka ta yi ramuwarta kan Farida ta hanyar anfani da Ibrahim amma kasancewar ita ba wata ba ce bayan da wadda ta daga ta ta yar da ita sai ya zamo ganinsa ma bai samu gare ta ba don bata da matsayin da zata isa inda yake. Ko da yake tana da kyauwunda zai iya kai ta ga kowace turbar maza masu son kyawawa da alamun shi Ibrahim tunda ya dora idanunsa kan Farida ya kulle irin wannan dama,, amma kuma kamar akwai wata damar wadda bata kullu ba in ta biyo ta wurin mahaifin Farida. Mutum ne da yake rayuwa shi kadai shi da aikinsa a da ya'yansa tunda matarsa ta ki zama wuri daya, sai dai hakan bai hana shi ajiye wuri musamman da ya kan leka wasu matan idan bukatar hakan ta taso, duk kuwa da ba shi kan zabar wa kansa ba saboda yawan aiyuka, idon=garinsa wato Wilson shi ne kan yi haka. Kuma ta hanyar Wilson din wanda ta nema ta samu ya biya ta da sada ta da me gidan shi wanda yayi marhabun da zama da ita muddin zata amshi bukatarsa ta tsugunar da ita a nesa da jamaà yana biya mata duk wata bukata ta duniya da zata so, amma da sharadin zata yi kamar ba a halicce ta ba a rayuwar iyalinsa musamman ma in matarsa ta zo gari yana son tayi kamar bata taba ganinsa ba. Ta amince da haka a zahiri, amma a badini zata yi hakan ne da niya biyu, na MenaR Masoya Rahma AbdulMajid Sarko tara abin duniyar da ta gani ta na biyu sai shaidun cin zarafin wadda ta kira ta Karuwa don ta ga yadda tayi da jinin da ta ke jin fito daga ciki har take ganin tsarkin kanta da najasar Merry. ta Ta katse tunaninta a nan ta shiga kwashe kayanta inda take fadin'Bally na Farida sai na zo tunda Allah Ya kawo wa angulu garin dadinta kusa wato masa * Bai gama sabawa ko natsuwa da inda aka ce an kawo shi a matsayin mazauninsa na wucin gadi ba sai dai ya mika wuya ga zaman falon yadda ya mika wuya ga duk wani abu da zai dawo masa da Farida. Ya na zaune a kujera daya duk iya zaman sa a falon duk kuwa da an gabatar masa da abubuwan ci da sha na alfarma a wurare da dama, kama daga gabansa har zuwa falon abinci, amma babu wanda ya tanka. Abin da zai iya tankawa shi ne zuwan Na`ibi wanda yace masa nan da awa daya za su sadu. Awa daya da mintuna biyu kacal da ga yin maganarsu da sirikinsa sai ko ga shi ya iso falon. Shi kadai kuma cikin shiga mai sauki kamar yadda aka san shi da kamannin saukin kai. Da sauri ya isa gaban kujerar Ibrahim wanda ya tashi tsaye da sauri ya na yi masa maraba. Ya mika masa hannu suka gaisa sannan ya girgiza hannun ya saki ya doshi wata kwaba ta kayan sha maras sanyi. 143 Mafiyan Masoya Rahma AbduMajid "Baka ci komai ko ka sha komai ba Ibrahim?" Ya nufo shi da kofi guda biyu ya rike naasa sannan ya mika masa nasa ya koma kujera mai kallon ta Ibrahim ya zauna sannan ya umarce shi da ya zauna. "Ka dinga jin ka a gida, domin wannan gidanka ne, ni na yi maka masauki da shi don ban ji dadin cewa kana zaune a otel ba" Ibrahim ya kurbi abin shansa sannan ya sake yin zaman ladabi da jiran abin da ya kawo shi. Shi kuwa alkali ya dora kafa daya bisa daya cikin sakewa. "Ibrahim na juya maganarka kuma na yi bincike a kanta, na sami tabbacin cewa Farida na da ciki kuma naka ne. ba abu ne da zan ji dadin sa ba da fari domin kuwa ba boyayyen abu ne gare ku kiyayyarmu ga kasancewarku tare ba, amma sanin kanka ne zan iya amincewa da abubuwa guda biyu a duk lokacin da suka zo gaba na. Daya duk inda aka ce jinin Farida zan so shi domin kasancewarsa jinina ko da kuwa da na kare aka cakuda shi,na biyu ba karamin kyauta ka zamo min ba muddin da gaske ne ka fahimci inda mahaifinka ya sanya gaba ka kuma kyale shi don kasancewa tare da ni. Ibrahim zan iya amincewa in ba ka Farida kuma in gyara tsakaninku in fauki nauyin auren ku in har abin da ka zo min da shi haka yake..." 44 Mayan Masoya Rahma AbdulMajid "Da gaske ne Father. Na hakure wa zama da babana na wani lokaci don zan so rama wasu abubuwa da ya yi min" "Da gaske kuwa ni ma zan agaza. Sai dai samin tabbacina zai danganta da yadda ka bi dokoki na ne kawai. Zan so ka zauna a gidan nan ba ruwanka da kowa har zuwa lokacin da Farida za ta sami lafiya ku sami ganawa, а wannan bangare ni kuma zan yi kokari in ga na ci gaba da shigar mata da kai tun kafin ku fuskanci juna, zan yi iya yi na in kubutar da sunanka daga zarginta. A takaice dai nan da mikewar Farida zan gama amincewa da sadar da aurenku ga shari`ata muddin za ka yi min ni ma nawa aikin...Aikina ba shi da zagon kasa ko makirci illa kawai tsayar da gaskiya. Na san mahaifinka ne ya so kashe Farida, amma ko kadan in har zan hada zuri`a da kai ba zan ja da wannan zance ba, domin kuwa ba abin da zan so ya fito jika ta ko jika na ya sani ya kuka da shi ba ne. Sai dai fa ba zan sake amincewa da Alhadi ba don ya shiga inda ba za a iya shigar min ba. Abin da kawai zaka yi min shi ne ka shiga yakinda nake da shi kan sabuwar kwangilarmu don ka dauki fansar da kake son dauka ba wai don ba zan iya ba sai don baka naka fagen, zamu bata masa rai a haka kuma wannan ya ishe ni fansar abin da ya so yi wa yata kurna matarka. Ina so duk dabarar da na fito maka da ita don nuna haka ka biye min. alkawarine ba zan cutar da kai ko saba maka A 145 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid alkawari ba, domin ba ni da riba kan haka in na yi a wannan karon. Farida ta riga ta aure ka kuma ba zan kashe ta ba, haka nan mahaifinka da yayi amfani da dabarar kisa ya riga ya tsiraita ta ta inda babu wanda zai amfanu da ita, ke nan muddin kuna raye to kai da Farida miji da mata ne da babu yadda zamu yi da su, amma goron amfanuwa da nawa aikin shi ne ka yi min wannan alfarmar ka ga ni kuma yadda zan saka" ba.' Ya juya ya nisa ba don ya fita daga tsoro "Zan yi haka father, kuma na ji dadin da ya zamanto baka nuna za ka amfanu da zargin da kake yi wa mahaifina na neman hallaka Farida ba, domin wannan kusan shi ne abin da zai iya karar da kusancin mu da iyalin mu a ruwan sanyi. Fata na Allah Ya taba zuciyarsa ya san kuskuren da ya so yi wa rayuwarsa ta wannan hanya, wannan ne zai sanya na mika wuya ga duk wani shiri da zai girgiza shi ya san lallai abin da ya so tabawa babban laifi ne taba shi" A nan Ibrahimi ya gama nasa kaulin ya sake kasa kunne ga hirar Na`ibi wanda a yanzu ya sake ne yana hira da shi kan dalilai biyu, kara ba shi tabbacin sakewa da shi da kuma bugun ciki na hikima don samin abin da zai dafa nan gaba a tuggunsa, duka dai sun a ginuwa kan alkawarin da yake nanata ya daukar wa Ibrahim din don karin neman yardarsa. * 146 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Tabar bata kare ba ya cire ta ya taka ya mutsittsike ta saboda fitar da wani sashi na takaicinsa, amma ba a hada minti uku ba ya ji yana bukatar ya sake kunna wata duk dai kan dalili daya wato rage takaici. Ya sakala ta a bakinsa zai nemo abin kunnawa amma sai ya ji an kunno masa wuta. Ya dubi me kunna-masa tabar ba don bai gane shi ba sai don baya son dauke idonsa har sai ya rage fargabar da ta ke kalubalantarsa. Na`ibi yayi murmushi sannan ya jingina da makarar tafkin da ke bayansa ya kawar da ka. "ka yi mamakin ganin mutumin da ka jima yana matsayin wanda zuciyarka ke yawaita tunawa a rayuwarka. Ni ma haka, sai dai mamakin ganinka bai kai min mamakin yadda abu ya kai ka ga yunkurin kashe Farida ba don kawai tana son danka...Huf! Na fi ka samin irin wannan dama a lokacin da Ibrahim yayi ta zarwa a gida na yana son na ba shi Faridar, amma sai na ga kisa ba dabara ce ta isassu ba kamar ka. Matsalata da kai saurin sikewa Hadi... Shi ma ya kunna tasa tabar a yayinda AbdulHadi ya nisa yace 'me kake so da ni yanzu?" "me ko nake so da kai ma?.. oh na tuna, so nake in gaya maka fansar da zan dauka kan abin da ka yi min babu yawa, na san ka so kashe min yata, kuma ina da shaidun da zan tona asirinka ciki har da Faridar da ka so kashewa da danka 147 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ibrahim wanda ya bar ka ya koma hannuna da zama don jin ciwon abin da ka yi. Sai dai duk bana son wannan ina so ne ka janye kawai daga sabuwar ja-in jar mu ni ma na kashe maganar. Ba wani abu bane illa kawai ina so in ga ka nuna wa duniya kasawarka a gabana. In kana ga ba zaka iya wannan ba nan da kwana uku sai ka sanar da ni domin na sami gabatar da karar da za ta tozarta ka fiye da hakan a gaban duniya musamman in aka ce danka na goyon bayan makiyanka da yin shaidar da za ta kayar da kai. Kuma ka san wani abu?" Ya zo kusa da kunnen AbdulHadi yayi masa rada. "Duk zai yi haka ne wai don na ba shi Farida aure... zan kuma nuna masa zan yi hakan har sai ya sake sannan na dawo maka da abin ka yadda kake so ba tare da ya aure ta ba. to yaya ma za a yi na bai wa wanda ya so kashe Farida Kimar surukuta?" Ya juya zai bar wurin yana fadin. ‘Sai na ji ka' Hadi ya janyo shi da karfi cikin fishi ya ko dawo yana kallon kafadarsa. "Ka san ba zan taba yin abin da kake so ba" Ya yi murmushi. "Babu dadi ka mika wuya nan da nan shi yasa na baka har kwanaki uku ka tunana. Kada ka damu zuwa lokacin zan sani ko za ka yi ko ba za ka yi ba" Ya juya ya bar AbdulHadi na yin wani nishi da bai san iyakar inda kirjinsa ke kaiwa ba. 148 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid * Farid ya sami lokacin Farida a wani zango mara amfani gare shi a yanzu watakila ma sai cutarwa. Farida na asibiti ta takura da cewa shine zai zamo mata abokin hira a kusan duk lokacinda take zaune ido biyu a lokacinda shi ya soma yakin da bai yi imanin zai ci nasara ba wato yakin raba zuciyarsa da son Faridar wanda ke karuwa a duk lokacinda ya zauna da ita har ya ji kamar sake kara ninkaya yake. Tana shan shayi daga jingine a bango hannuwanta biyu rike da kofin kamar wanda yayi mata nauyi, ta kan kale shi a duk lokacinda ya fadi wani abu da ya bata mamaki ko dariya sannan ta tanka shi. Tana jin ta sami sauki kuma tana da karfin fita daga 'asibiti. Ciwonta shi ne kewar Ibrahim da tunanin me za ta yi musu da son yardar wa kanta da kanta cewa za ta iya yin wani abu in ta fito daga asibiti da zai sanya ta iya ci gaba da rayuwarta ko da kuwa ta gama da Ibrahim mijinta ta duk hanyar da ta so. "Idan zan iya tambaya Hajiya, me yasa kika nisanta kanki da rayuwar Ibrahim mijin ki da lafiyarki" Ta kalle shi shiru har sai da ta hadiye shayin da take ta tsiminsa a bakinta. "kamar kana da wani karin bayani....Ka yi min mana don na ga ka san lamarin sosai" Ya mommotsa yatsunsa na hannu sannan yayi murmushin rudewa. a に シ 149 Mafiyan Masoya Rahma AbduMajid "Kawai dai gani na yi bai kamata ba, yana matukar son ki muddin har zai iya mika wuya ga mahaifinki kan yayi duk abin da zai yi da shi ko da zai cutar da babansa....Ban sani ba in har ya kamata in gaya miki ko bai kamata ba, amma abin da na san su Chairman na shiryawa na amfanuwa da shi kuma su yar da shi a nan gaba ba zai zamo adalci ga dan cikinki ba....Oh! ban san me ya sanya nake gaya miki ba, amma ina jin kamar bai kamata ba, mutumin yayi duk abin da zai yin a daukar fansa kan abin da yake zargin mahaifinsa da yi. Ya rabu da shi ya koma cikin tawagar Chairman, amma kuma kamar ba wai sun karbe shi ne da.... Ta jima tana rike kanta don kada ta yanke masa magana amma a yanzu ta kasa. "Ibrahim na tare da father? Kuma suna shirya wani abu? Ya rabu da mahaifinsa? Kan me... Yaya?" Ya mika wuya ga in ma katobara çe to ya riga yayi ta. "Ina ga dalilinsa shi ne na yá nuna wa mahaifinsa bakin ciki kan yadda yake son raba ku, amma kamar Chairman zai amfana da haka, kuma yadda na ji yana fadi shi'ne ba zai sasanta ku ba in ya gama amfanuwa da Ibrahim abin ba zai yi dadi ba gare shi. Farida ina ga ki yafe wa mijinki ku sasanta daga yadda abin ke son kasancewa, yana matukar kaunarki, ba zai yi wani abu da zai cutar da ke ba, in ba shiri aka yi masa ba, in ba haka ba me zai sanya ya rabu da 15 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid mahaifinsa ya koma ga naki har ya mika wuya ga duk abin da za a yi wa nasa mahaifin" * Ya yi matukar mamaki da firgita na ganin wani mahaluki da ba Na`ibi ba a wannan falon, kafin ya tantance ko wa cece sai ya ji ya fara jin sanyi domin kamar tana da alaka da Farida. Ya sauko matattakalar a hankali, sannan ya mai da murmushi bayan ya iya tuno ta cif-cif. "Ah! Merry? Yaya aka yi kika san ina nan?" Yayi tambayar ne don ya sami amsar cewa Farida ce ta turo ta, duk kuwa da ya san hargitsinsu da Faridar, amma bai ga ta yadda zata san yana gidan nan ba in ba ta wurin Farida ba. A tsaye yake a gabanta abin da ya sanya itama ta mike tsaye ba don kara girmamawa gare shi ba sai don ta nuna masa kwalliyarta daga sama har kasa. Ya ko kare mata kallo har ta tuna masa da Faridar da baya mantawa don sukan kwashi kama ta siffar jiki da irin kwalliyarsu da ta zamo daya. "Kana lafiya? Yaya masu jiki?" Ta kawar da tambayarsa. Hakan ya dan ba shi mamaki, amma ya dawo da tambayar ta wani salo babu karaya. "Mai jiki na wurin jinya, ba tare kuke ba?" Ta koma ta zauna cikin

Chapter 8 of 11