Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ka yi aikin nan ka yi ba?" "Ka yi hakuri baba, ina son ta ba zan iya cutar da ita ba" Ga mamakinsa sai ya ji mahaifin nasa ya fashe da wata dariya da ta cika falon, har yana kamo hannun Ibrahim yana tafawa da shi a dole. "Ka yi min wayo yaro...kai amma kana da wayo...je ka ka huta je ka ka huta" Ya hana Ibrahim magana har sai da ya hakura ya tafi nasa falon a kidime be san me mahaifinsa ke nufi ba. Yana sosa kai kwance a doguwar kujera wayar ya danne ta da kafadarsa can kusa da kunnensa. "Ina ga hala da yake yanzu ya ji maganar shi yasa tayi masa banbarakwai, kuma ya kasa sanin ina zai dosa da maganr kawai dariya yake 'wai na je na huta' Ta yi shiru ta rasa abin da zata ce ban da ajiyar zuciya, can da ya ji shirun yayin yawa yace. 96 Mafiyan Masoyа Rahma AbdulMajid "Zamu yi magana anjima na sani in ya soma sabawa da zancen watakila mu kai ga wani abu mai muhimmanci yau watakila kuma a kai wani sati, amma kamar yadda muka tsara duk abin da ake ciki ba zai wuce wannan satin ba..." Ya dan hada ido da ainahin abin da ya ke ta zaton inuwar zuciyarsa ce, ashe da gaske baban sa ne a tsaye a falon. "Bari zamu yi magana an jima" Ya furta mata hankalinsa na kan baban nasa. "Kana magana ne da matarka?" Kalmar ta fi zamowarta tambaya haifar da mamaki da rikicewa, kafin yace eh sai da ya tambayi kansa ko me mahaifinsa ke nufi da amincewa yayi amfani da Kalmar mata kan makiyiyarsa Farida? Ya yanke shirun da zama a gefen kujera. "Ka ce tana da cikin ka ko?" "Haka ne Baba" Yanzu bai da zabi baya da amsa ko wace tambaya yadda ta zo. AbdulHadi ya shafa kai sannan yayi wata 'yar makyarkyata ta nuna karaya tun kafin a fade ta. "Da na na yi wauta, na raina ainahin son da kake yi wa Farida, har na baka wannan hidima da ka kasa yi min. sai dai duk da zafin da na ji na kuma yi tunani na ga cewa ban yi asara ba... Na'ibi ya dade yana cuta ta kuma yana yin pasara, ban so hada zuri'a da shi ba, na so na yi amni da 'yarsa na rama wasu sashi na cutarsa gare ni, amma kuma a nan ma ban yi nasara & 97 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid ba...hum! Ko da yake na hangi nasara ta wani bangare wanda shine karin samun zuri`a a gidana. Ibrahim ba da tsarina ka zamo shik enan dana ba, na yi iya kokarina na sami kari, amma abun bai yiwu ba, na mika wuya ga cewa zan sami wannan kari ta hanyar ka, to ga shi ka fara cika min burina..." Ya mike tsaye ya zuba hannu a aljihu. "Zan karbi Farida saboda jini na da ke tare da ita ina son sa...' Ibrahim wanda ya tuma tsalle ya mike ba tare da ya sani ba da yake murna ce zalla ke sarrafa shi ya doshi kirjin ubansa wanda suke musayar idanu... "Baba da gaske zaka amince da Farida?" "ka je ka kawo ta, zan tafi tare da ita, zan taka har gidan Na`ibi da farar tuta mu rungumi juna saboda martabar abin da ke cikinta" Ibrahim ya shige jikin mahaifinsa yayi masa kam har ma yana juya dan tsohon mara alamar nauyi. Yana furta, 'ina son ka ubana...na gode ubana' hawaye suka fara zuba a idonsa. Da kyar baban ya shawo kansa suka sake zama, kuma ya hana shi zumudin kiran Farida da yake ta yunkurin yi da niyar su zauna su dumfari abin. "So nake ka yi mata ba zata irin wanda na taba yi wa mahaifiyarka... so nake kace mata ta zo na ki yarda zaka shirya mana wani fito-na fito. In ta zo ka bari kafin ta fara haduwa da kowa ta gan ni kwatsam, sai nayi mata albishir, 98 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid cikin wannan muma tata mara iyaka nake so mu je gidan Na`ibi" Ibrahim wanda cikin zumudi daka kawai yake ta amsawa yana shirin sake latsa lambobin Fasrida sai da dakyar Abdul Hadi ya sake shawo kansa. "Dakata! In ka yi magana da ita yanzu cikin wannan farin ciki ai zata gane. Kawai ka daure ka kyale har sai an jima ka soma sabawa da wannan farinciki inda zaka iya daurewa cikin maganarka ba tare da ta gaue ba" * Duk da doki da damuwa da Farida da Ibrahim ke ciki kan ganin muhimmancin zuwanta a washegarin amincewar babansa, dole zuwan nata ya sami jinkiri sakamakon yawaitar hazo da ya hana akasarin jirage tashi daga ilahirin yammacin turai, abin da ya kara jinkirin kwanaki biyu kan yadda aka tsara, abin da ba yana na nufin Ibrahim da Farida ba kawai, har ma iyayen Faridar masu shirin tafiya Maroko ba zasu sami ganinta ba kasancewar zata kara yini biyu kan iya yadda zasu iya jiran ta. Wannan bai zo wa Farida da damuwa ba domin a kankin kanta ta fi son ta zo basa nan har su kammala tsarin su ita da Ibrahim da mahaifinsa kafin su dawo don ya zamo da sun hadu sai dai a tare su da gaskiya tsagwaronta. Kamar yadda AbdulHadi ke ta tsara wa dansa yadda za a yi ko zuwa dauko Farida daga filin jirgi bai bari yayi ba, cewa yayi duka su je ainihin kulob din 99 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid da su Faridar suka saba haduwa su jira ta a can, Ibrahim yace mata can zasu hadu, in ya so maimakon shi sai ta ga mahaifinsa yayi mata ba zatan albishir. Ibrahim ya ji dadin shirin kuma ya aiwatar duk da cewa ita Farida da bata san dawar garin ba abin na matukar damun ta, amma ta daure, hakan ya sanya ta tuno tsohon aboki Farid, wanda tace ya zo ya dauke ta daga filin jirgi zuwa wannan kulob. Farid ya zubar da duk wani ratayayyen kaya da ke kwabarsa yana wake-wake na jin dadi, amma bai gamu da kayan da suka yi wa wannan rana ba. Ya fara yanke tunanin zai garzaya shagon sayar da kaya cikin gaugawa don haka ya fara kwashewa yana watsa su ciki tunda babu lokacin sake tsara su. "Wannan da ka dauka ta dace da fitar ka da Farida zuwa Club muddin ba matsa wa kanka kake son yi ba" Mahdi ne wanda ya gama huce takaicin sa a falo ya biyo Farid faki yake fadin hakan a yayinda ya farga da wata farar shet mai jikin roba da gajerun hannu da Farid din zai jefa a kwaba. "Kai Allah? Da me zan hada ta?" Ya karaso ya karbe ta. "Kwarai zata kawata surar jikinka in ka hada ta da dirty jeans. Sun dace da zuwa Club din da ba dole ne ka sami abin da ya kai su ba a kasuwa in ka jc yanzu" 100 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Farid ya jefa ta bisa gado ya dangana da ma`ajiyar wanduna na musamman ya zaro ainihin jins din da Mahdi ya kwatanta wanda aka yayya6e shi da wasu riguna da ake hada su, ya zare shi ya jefa shi kan gado sannan ya daga wa Mahdi manyan yatsunsa biyu na nuna jinjinawa kana ya fada bayan gida a gujc.. A falo ya hadu da Mahdi bayan ya gama shiryawa har da wani farin takalmi sawu ciki mai tsinin baki, turare na tashi, yana goge fuskarsa da hankici na gumin zumudi dake tsattsafo masa. "Mota ta ba laifi kuwa? Ko kana ga...?" "Bata ma san ka da mota ba tace ka zo ka tare ta, haba mutum! Ka je ka tare ta a matsayinka ba a na wani ba" Ya juya zai fice yana girgiza kai. "Ka ce jumla mufida! Sai na dawo" Mahdi ya kwanta a kujera yana masa kallon raini da dariya. "Allah Ya ba da sa'a Ibrahim na zaune a motarsa ya kwantar da kujerar direba gefensa akwai mahaifinsa da suke ta hira ta annishuwa har zuwa lokacinda ya hangi tsayawar motar da yayi zargin Farida ce a ciki. Cikin murmushi ya dada lafar da kansa ya dubi mahaifinsa 99 "Ga ta nan" Suka zubo mata ido yayinda take musayar dariya da saurayin da ya dauko ta wanda shi ma 101 Maliyan Masoya Rahma AbduMajid har ya sauko daga motar, amma da alamun Farıdar ta gamsar da shi wasu maganganu da suka sanya ya koma cikin motar koda yake jikinsa babu laka. "Wa nene wannan tare da ita kuma?" AbdulHadi ya tambaya idanunsa na kaikomo tsakanin Farida da Ibrahim. Daya daga cikin ma'aikatan babanta ne da tace ya je ya dauko ta tunda ni ban je ba, ina ga sun dan fi shakuwa ne shi yasa" Ya dawo ga babansa firgigi. "Ta shiga Baba ka je ka same ta ku tattauna ina so in je wurinta ina kewar ta, ba zan iya kara dadewa fiye da wannan ba" Yayi murmushi sannan ya doki kafadar dan nasa. "An zo karshe ai me kake ci na baka na zubewa? Yanzu zan ba ta kyautarta kai kuma ka shirya duk taka ce" Suka tafa ayayinda wayarsa ta yi wani kuka na musamman. Ya zaro da murmushi na ganin lambar Farida. "Toh ga ni na zo baka dauko ni ba, baka kai ni gidanka ba, ka ce na zo Club duk na cika umarninka me gida sai ka ba ni goro na" Yayi murmushi ya lumshe idp. "Minti biyar yayi yawa zaki sami goron ki na san kin iso wurin ai, kuma ni ma ina nan kusa dake kin ji?" Mahaifinsa yayi dariya ya kashe masa ido sannan ya fita a yayinda shi ma ya kashe waya 102 Mofiyan Masoya Rahma AbdulMajid yana bayyana dumbin farin cikin da ya cika masa ciki. Can gefen wani ruwan ninkaya ta zauna kan wata doguwar kujera da ta fi kana da tsinin bishiya, idanunta na kan masu kada jitar da basu fara waka ba amma ba don tana matukar tare d su ba. ta kan dakata tayi waige-waige, amma da ya tabbatar mata da saura mintuna biyar sai ta gwammace ta mayar da hankali ga wuri daya har zuwa cikan mintunan. Ya bayyana a gabanta kamar mafarki sanye da fararen sut da wando, ciki akwai shet mai ruwan kofi. Yana murmushi har suka haďa ido a yayinda ta mike tsaye ba tare da ta san ta mike ba illa da zuciyarta ta tilasta mata yin hakan. Kwarai gaban ta ya rikito kasa, amma can cikin kwalkwalwarta sai ta ji kamar ta soma samin fassarar wannan ba zata da mijin ta ke son yi mata yana cakudewa da faduwar gabanta. Mahaifin sa ne zai yi mata maraba da kansa zuwa cikin wannan zuri'a ke nan!. Ta ji faduwar gabanta na cakuduwa da murna, bugun zuciya, da. saukar wani nauyi da jin nauyin kuma. Mutumin da ta jima tana taka rawa a ofishin mahaifinta a fannoni da dama na dakile kasuwancinsa duk kuwa da suna soyayya da dansa. Bata dauki hakan komai ba illa yakin kasuwa da ofishinta keyi da wani ofishi don nuna kwarewa kuma shi ya san ta a hakan, sannan a zaton ta hakan zai taimaka wurin kara fada-a jinta a kunnen nata mahaifin da take : 103 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid ganin kamar shine wuka da nama na wannan gaba. Da fari saurayinta kuma mijinta a yanzu Ibrahim ya sha kira da babbar murya kan tayi watsi da wannan taka leda da take a madadin mahaifinta da cewa abin zai ci gaba da jan kafa kan harkar soyayyarsu, amma a lokacin gani take Ibrahim na hakan ne kawai don ya kasa iya ja da ita a harkar kasuwancin. Amma a karshe ya samu ya fahimtar da ita cewa ko kadan baya nuna iyawarsa don kayar da ita shi yasa suke kai labari kuma hakan na janyo wa mahaifinsa asarar da kansa shi ma ya ji yana zargin son ta a gare shi. Ta gamsu da wannan dalili wanda ya sanya ta kaddamar da murabus dinta daga fadar mahaifinta a ranar da Farid zai fara dora idanunsa a kanta. Ko da yak eta dade da rage zuwa aiki ko wannan taka leda. Shin sirikin nata zai kale ta da wannan tariya da take yi, ta tambayi kanta a gaggauce a lokacin da ya nuna mata kujera da ta koma ta zauna, shi ma yana kokarin zama da alamar zancen nada tsayi matuka. Ya sake dariyar da ta fan rikita ta ta ji ba ta bukatar sakankancewa da zaton alheri. "Farida kenan! Nice meeting you! Na ji dadin ganin ki don mun dade bamu hadu ba....ina jin tun a Honalulu ko wajen gabatar da taswirar bankin lantarki ga central bank na Kasar Kenya da muka gabatar ni dake bayan dana ya ki halarta a saboda ke" 104 Моyan Masoya Rahma AbdulMajid Ta ji hantarta ta kada. Babu yadda za a yi a tuno da wannan rana cikin mutunci ba ta ji kunya ba. Rana ce da cikin ido da ido babu wani shamaki ta kayar da sirikin nata a daya daga cikin kwangilolin da suka kara fintikau ga kamfanin babanta kan nasa kuma ta hanyar siddabarun da lallai ya san ita ce ta aikata. Ya dan shafa gefen hancinsa da yake fitar da maiko sannan ya katse tunaninta. "Na zo miki da ba zata kamar yadda dana ya gaya miki, amma bana jin ba zatan irin wanda kika taba zata ne" Ta ji ta amince da maganarsa amma da me ta amince ciki bata sani ba. "Dana ya so ki Farida so na hakika, amma daga baya ya amince cewa rawar da kike takawa wurin daidaita mahaifinsa ba wai kawai ba zai bar ku ku yi soyayya ba, a a sai ma kina bukatar a dauki fansa a kanki... Farida kin yi gagarar da ta baki kariya ta hanyar komai da zamu iya afka miki da ita baya da soyayya, don haka in na gama yi miki bayanin abin da muke nufi dake ina fatan ba zaki yi fishin mun yi amfani da zuciyarki ba, mun kasa yi ne da kasuwa" "Me kake son gaya min?" Ta ji ta tambaye shi ba da saninta ba "Farida kamar yadda nace miki dana yana son ki kuma na bukaci da ya ba ni daman a dauki fansa a kanki ta hanyarsa kasancewar ya ji ciwon abin da kika yi min, shi yasa muka sami yarjejeniya na cewa zan dauki nauyin 约 105 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid zamansa dake a Jamus don ya more dake kamar yadda ya dade yana fata, amma bayan kin sami ciki wannan kwangila zata kare ya rabu dake... maganar aure da kuka yi duk akwai matakai da muka dauka kan hakan da zasu tabbatar da shi a bogi, don haka yanzu zamu koma yakin mu ne yadda muka saba don dana ya ji dadin iya ja dake na tsara hakan, domin bayan ma a ce ya gama biyan bukatar soyayyarsa dake, na san zaku iya kulla kiyayyar da zata ba shi damar mara min baya mu fuskance ki da kyau. Don haka cikin da ke jikinki ya zamo wata kyauta daga garemu da zaki iya yin yadda kike so da ita Ya dai ga tana dariya da hakora, amma daga shi har ita basu san ko ta me cece ba, don haka ya ciro wata waya daga aljihun kirji na ciki ya kunna ya mika mata. "Idan baki yarda ba zaki iya gani a hóto yadda muka tsara wannan yarjejeniya ni da dana. Kuma zaki iya yarda tunda kika ga ya amince da cewa ni in yi miki bayani dalla-dalla don shi ba zai iya fuskantar ki ba...." Tana kallon duk yadda abin ya faru a waya, yadda Ibrahim ya zo ya karanta wa mahaifinsa amincewarsa da yarjejeniyarsu da yadda suka tafa suka ci gaba da tsarawa kuma Ibrahim din yana dariya yana murna. Ta ji ya ishe ta bata bukatar iya karasawa, saboda mintsinin da duk ilahirin jikinta ke yi mata. Ta sami kanta tuni ta 106 Matiyan Masoya Rahma AbdulMajid mike tsaye tana mika masa wayarsa ba tare da ya mike ba shi. "Me yasa kika tashi bamu gama magana ba ai, a kalla kya tsaya ki gama kallon wannan film din ko?" Ta girgiza kai ta watso jajawur din idanunta da basu da niyar kukan da ke son su da abota. "Zan duba yadda zamu hadu...zan rama ta yadda ya dace... ban da abin cewa yanzu Ta saki wayar da ya ki karba sannan ta fice daga wurin a guje cikin rangaji na nuna rashin ikonta da ilahirin jikinta. Motar Farid a yanzu tana makwabtaka ne da ta Ibrahim a inda suka yi sabon faki. Yanayinsu ne kawai baya makwabtaka da juna domin a yayinda Ibrahim ke tsugune a kujerarsa kamar me jin kashi yana jiran ko dai mahaifinsa ko Farida ko su biyu ko waya mai kiran ya shigo. Ya bi ya damu amma cikin farinciki, yarda da zumudi. Ya kan dauko wayarsa kamar ya buga ya ji sai kuma ya zargi kånsa da kansa na rashin jimiri da yawan gaggauwa, a haka yake duk da ya kan saci kallon Farid wanda ya kawo Farida wannan wuri, amma da yake bai da wata sana'`a da shi bai dame shi illa dai kallo na wanda zasu gaisa nan gaba bayan Farida ta fito. A nasa bangaren Farid ya rasa abin da yake masa dadi. Ya kwantar da kujerarsa ya kwanta yana kallon rufin motarsa. Iyakwandishan na buga shi amma baya jin tana komai ban da kara masa azaba. Wa Farida ta je gani a club kuma C 이 107 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid me take nufi da shi, watakila fa tana son wani ba shi ba abin da bai san yadda zai yi ba in ya faru. A iya tasa wayewar na miji da mace ne kan zo Club kuma shi na miji ne da mace Farida suka zo, amma ba a shiga da shi ba ta shiga ita kadai. Bangaren lallashine kawai a zuciyarsa ke kokarin bai wa Farida wani uzirin da cewa hala wani fannin kasuwancin su take yi a Kulab. Shi ma kamar Ibrahim idanunsa basa nisa da kallon kofar da Faridar ta bi ta shiga sai dai shi baya satar kallon Ibrahim don wata manufa sai pon kawai idanunsa sun ketara, domin bai gan shỉ da Farida ba bai kuma san shi ma ita yake jira ba. Duka sun yi arba da fitowar Faridar cikin sa`a sai dai damar da Ibrahim ya samu na 6allo motarsa ya fito don ya tare ta Farid wanda ya farga da tana nufo motarsa ne bai sami wannan damar ba sanadiyar tsayawa ya gyara kujerarsa da ya kwantar, watakila saurin Ibrahim ya kara samun alaka da lura da yayi da fuskar Farida, wadda tuni ya ji ta kayar masa da gaba sabanin Farid da ke fatan ta sami 6acin ran a wannan wuri da ya ke jin ba a shiga da shi ba. Ga mamakinsa sai ya ga makwabcinsa ya sha gaban Farida har da daga hannunsa na dama kamar zai ruko wani sashi na jikinta baya da wani kallo da ya lura tayi masa na tsayar da hakan. Farid ya ji yana jiran karin abin da zai sa ya fita ya nuna wa Farida mazakutarsa ko kiftawa baya yi. "Sako ya isa yadda ka tsara" 108 Mofiyan Masoya Rahma AbdulMajid Farida ta ambata cikin murya mai rauni amma cike da kuzari. Ibrahim tsakani da Allah ya rikice sai da ya hadiye wani yawu da ya tsaya masa kafin yace 'Baby me ke faruwa ne? Baba na ne ya...?" Tuni ta kaikaita ta wuce shi tana sauri ta doshi motar Farid yayin da shi yayi tsaye a rikice ya dube ta ya dubi cikin kulab din bai san abin da zai yi ba. Tuni Farida ta fada mota ta buga murfin da karfi. "Mu bar wurin nan da sauri Farid" Yadda ta fada haka a ka yi domin ya hadiye tambayar da ya shirya yi mata na lafiya, ya bi umarni yayi wa motar wawan taku. Ibrahim ya fada cikin kulab din da iya iskar nunfashinsa amma sai suka hada kirji da mahaifinsa mai shirin fitowa. Ya dan ja da baya kafin yace masa. "Mai ka cewa Farida?" Ya dan daga kafadunsa sannan ya soka hannu a aljihu "Babu komai na dai raba ku ne da yadda zan iya.. tun da ka zaci ka fi ni wayo shi ne ni ma na nuna maka ni na haife ka" Ya matsa can kusa da mahaifinsa kamar zasu daku duk kuwa da kokarin da yake na ya mallaki zuciyarsa. "Dad! Na yarda da kai ka yi min haka..." Ya dawo da baya cikin nishi sama-sama a yayinda mahaifin ke cewa. 3 E 109 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid "Me kake jira? Doke ni mana, mu yi dambe saboda na raba ka da wadda ba zata taba son ka ba sai don ta ruguza ka. Am sorry, na raba ku" Ya girgiza kai ya fice daga wurin inda mahaifin ke karar kiransa amma bai tsaya ba ya fada motar kamar me sukuwa ya fige ta daga wurin ya bar fasinjansa tsaye wato babansa. * Farida ta fara kasa kallon gabanta, duk da tana zaton damuwa ce tayi mata kanta, amma kuma abin ya soma faskara, tana jin muryar Farid daga nesa yana tambayarta 'Are you Okay?' ta gyada kai na amsawa wanda koda ta gama, ji take har yanzu kanta na kaďuwa, ta sha shiga damuwa iri-iri amma bata taba jin yanayi irin na yau ba. Ji tayi ta rufe idanunta da sauri saboda duk abin da take kallo gizo yake mata kamar ruwa na narkewa, Farid na narkewa, gaban motarsa da take faman kallo yana narkewa kanta na ta gyadawa, babban su shine nunfashinta da kamar yake fin karfinta. Tana jin muryar Farid a tsorace yana kiran sunanta, amma kuma muryarsa kara nisa take har ta dena jin sa dungum sai wani yanayi maras dadin kallo ko ji. Farid tsaye a kofa idanunsa na zagaye asibitin amma zuciyarsa na can tare da tunani dubbai. Mai ya sami Farida ne ko kuma me ya hada ta da wani? Dama tana da wani ciwo ne bai sani ba? Uwa uba idan wani abu ya sami Farida me zai cewa iyayenta? Yayą zai yi da 1 t 1 S 1 110 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid mafarkin rayuwarsa? Duk rokonsa ga Allah cikin buga bango shi ne kada ya ji mugun labari. Yana jin tsoron kadaicinsu a wannan asibiti. Ko shi bai san asibitin ba amma watakila su Farida su san shi. Asibitin masu dashi ne kuma shi ne mafi kusa da wannan kulab duk da yana wani kadaitaccen layi, ma`aikatan asibitin har sun soma dena kama da `yan kasa saboda tafiya bisa Ka`ida. Likitan me kama da marasa lafiya saboda kiba da katon ciki ya fito yana gumi ya Бaбballe gaban rigarsa. Balaraben Misra ne daga gani har ma a irin turancinsa. Ya dafa kafadar Farid bayan ya tare shi. "Ka kwantar da hankalinka da sauki, an cecі Fayuwarta" Şannan ya wuce da shi ofishinsa bayan doguwar ajiyar zuciyar da suka yi duka. Ya dauko robar ruwa daga firijinsa ya bude wa Farid. Sannan ya koma kujerar sa yana magana. "Da ta kara minti talatin ba a kawo ta asibiti ba sai dai wata... kuma zai yi wuya a gane abin da ya kashe ta baya da bugun zuciya da za a ce" Wannan kalmomi suka sanya makoshin Farid jin yana bukatan wannan ruwa ya kwankwada idanunsa na kan likitan. "Месе се taka?" Tambaya mai tsauri, amsarta ta zuciya ta wato rayuwa ta ta sha bamban da amsar da ya daure ya fada cikin in-ina wato 'shugaba ta ce' "Gaya min, kana bukatar mutuwarta ne?" 111 Mafiyan Masoya Rahma AbduMajid Ya dan matso da kirjinsa ga teburin ba da saninsa ba, sai da zuciyarsa ta yi shakkun rashin jin tambayar sosai kafin ta amince da cewa tambaya ce wadda bata san ta ina zata ba da amsarta ba saboda yawan amsoshin. "Me ya same ta? Za ta mutu ne? Farida? Na so kashe ta? Ka san ko me cece gare ni?" Ya zubo tambayoyin wasu a hankali wasu da karfi, amma likitan ko gezau. "Shi ya sa na tambaye ka ko mece ce gareka ai don ban sani ba" "Ita ce komai na ina rayuwa don ita a halin yanzu, ina kaunar ta da dukkan kaunata...gaya min me ya same ta ba dai za ta mutu ba ko?" Likitan ya karanci yanayin gaskiyar da yak enema a kwayar idanunsa sannan ya dauki biro ya kama rubutu. "Mun sami sinadarin.... a shafe a danyatsanta na tsakiya ta inda tsakaninsa da hancinta baya wuce cm sha biyar har tsayin mintoci biyar. Shakarsa da take da sauri kuma a matsayin mai ciki na iya gaggauta toshe jijiyoyi masu kai iska ga zuciyarta wanda hakan na nufin bugu da karfi na tsaya daga zuciya cikin kasa da sa'a daya, ka san me bugun zuciya ke nufi...." Ya tsayar da rub utun ya dubi Farid wanda tuni ya mike tsaye. "Ba zata taba kai kanta ga abu mai halakarwa irin wannan ba, kenan mai iya kusantarta ko ta jiki ko ta waya ne ka iya bata, 112 Mariyan Masoya Rahma AbdulMajid kamar a lokacinda take tare da kai ne kenan ta samu "Shine zan kawo ta asibiti kafin ya gama aiki in ni na sa mata? Baka tunani ne, Farida shugaba ta ce kuma ina son ta....Amma ta...ta sanya ni na kai ta Club... wani saurayi ya tare ta daga waje kamar zai rike ta sai ta kauce...ranta a bace ta fito daga club din amma ni ban shiga ba... me ya faru kenan wannan saurayin ne ko wani daga ciki?" Likitan ya mike daga kujerarsa sannan ya dawo ga Farid. "kamar kana da gaskiya...amma zaka zauna nan tare damu har sai ta farfado ta nuna mana gaskiyarka... Nan ne asibitin iyalan gidansu...na santa ita da babanta tun a turai...b azan yi wasa da tsaron lafiyarsu ba. Don haka ka yi hakuri nan da wasu a woyi zata dawo hayyacinta, zamu sani ko baka da laifi ko zamu kira hankalin jami`an tsaro kan lamarin" Farid ya mike yana murmushi. "Ko kwana nawa ne ba zan bar nan ba har sai Farida ta farfado, ba don tuhumarka ba sai don ta isa hakan a wurina..." Masu aiki suna ta kai komo idanun su tun suna kan Farid har suka soma aminta da shi domin yanayin damuwar sa. Yayi wa abokinsa waya sau daya don ya sanar da shi halin da yake ciki, amma da ya bukasci dole ya zo ya same shi kuma ya ki yarda da maganar Farid na kada ya zo sai komai yayi daidai sai Farid ya kashe • 113 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid wayarsa ya kara rasa abolkin hira. Wata kalma da ta hanashi tsaye ko zaune sai zarya itace Kalmar cewa Farida na da ciki. Ya rasa hanyar samin tabbacinta domin kuwa likitocin basu wata magana da shi ban da na cewa tana samun sauki. Ya fi kokarin ya amince da zargin jin kunne amma hakan ta ci tura. Cikin wa Farida ke da shi? Bata da aure, kuma kamar ta fi karfin tayi cikin da bai da uba. To me ake nufi? Rainon turawan ne ya motsa? Koma me nene ina ne mafita gare shi in har zancen ya zamo gaskiya? Kalmar na dukan zuciyarsa ya ji yana Allah-Allah Farida ta farka ya sami tabbacin hakan fiyc da tabbacin wanke shi da laifi. "Tana son ganin ka" Wata bakar

Chapter 6 of 11