Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
nas mai saurin tsiya ta iso gare shi ta yanke tunaninsa da kalmomi masu alamun Farida ce ta farka. A zabure ya bi ta a baya suka iso wani daki ba wanda ya san an kwantar da Farida ba. A tsaye akwai likitan wanda ya karbe ta kuma ya tuhumce shi, suka matsa masa don ya doshi gadon Farida cikin sauri wadda take kallon shi da murmushi a galabaice. ji?" "Alhamdulillahi tun da kin farka yaya kike Ta dan yi fari da ido. "Kalau nake yanzu duk da na zaci ba zan sake rayuwa da ku ba" SO Ya kada kai cikin yi mata kallon tausayi da 114 Mafiyan Masoyа Rahma AbdulMajid Ällah Ba Zai nuna mana rashin ki ba, Allah Ya Kara miki sauki" "Likita yace wai na sami shakar wani sinadari ne har sun dan dakatar da kai. Shi ne nake gaya masa cewa ba za ka taba cutar da ni ba ko ta halin kakа" Ya dan dubi likitan sannan suka yi wa juna murmushi. "Suna yin aikinsu. ne kuma haka ya dace...Basu san ma asibitin ku ba ke nan ashe garin saurin na kawo ki asibiti mafi kusa na kawo ki gida" Likitan ya sanya baki. "Aikina ne ya sanya ni in yi maka abin da na yi kuma aiki na ne na nemi ahuwa gare ka, ka yafc mana, muna kula da lafiyar wadanda kake kauna ne kuma suka yarda kana Caunarsu. Malama Farida na bukatar kara hutu da rashin tuna duk wani mummunan tunani, don haka sai a tace irin hirar da za a yi mata" Suka sake gaisawa sannan ya juya ya fita ya bar Farid wanda ya baro jikin gadon Farida ya zauna kujera mai kallon ta. Ta dan nitsa tana kallon sama cikin wani takaici mai cakuduwa da dauriya. "Bayan abin da suka yi min kuma suna son kashe ni. Zan mai da martani kan wannan cikin hanya mai tsanani" Ya dan rankwafo. A 115 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid "da ba don likita yace kada a dame ki ba da na so sanin ko su wa nene suka sanya miki wannan abu, don bai kamata a kyale ba Ta sake jaddada murmushinta na takaici, sannan ta kau da kai daga gare shi. "Ba maganar ka bane yanzu Farid. Abokan yi na ne kuma zamu yi" Ya yi shiru yana kallon ta har zuwa lokacin da ta dawo da idanunta gare shi fuj'atan. "Farid na yarda da kai kuma ina son boye wani sirri na a cikinka... na san likita ba zai rasa gaya maka ina da ciki ba, amma bana so su father su sani yanzu... daga ni sai kai muka sani sai likita, kuma zan bari ya fito a lokacin da ya dace" Farid ya kasa um ballantana um-um! Kalmar da yake ta sha`awar tabbatar wa yanzu tabbata ta kafar da motsinsa, wani duka yake ji a duk ilahirin wani abu mai agazawa nunfashi da kuzarinsa. Farida na da ciki da gaske. Ya kasa koda gyadawa ko kada kai don nuna mata matsayarsa. "Farid zai ba da mamaki in a ka ce ina da ciki ko...baka yi min wannan zato ba? Ka daure ka amince, ban yi wannan ciki ta hanyar banza ko lalata ba...ina da aure ne Farid, kuma cikin yana da ubansa..." Wayarta da take ta kokawa ta dauke hankalinta daga Farid, bata wasa da duk wanda ya san wannan lamba da aka kira ta a kai domin ba ta wasa bace, ta karkata kai ta dauko ta. Bata 116 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid san lambar ba, amma haka ta daga. Farid wanda yake jin mintsini a zuciyarsa ha jin wani karin labarin dugunzuma zuciya ya tsinci kansa yana mai amfani da damar kawuwar hankalin Farida daga kansa don ya fice daga dakin kafin ta ankara da kwayar idanunsa da ta kasa бoyс labarin zuciyarsa. "Farida don Allah ina kike? Just gibe me a chance to edplaine, Please!" Ta yi murmushi, tana me shaida muryar Ibrahim wadda ta bayyana cikin damuwa. "A ina nake? Ina duniya Balala ba daga lahira nake amsa wayar kamar yadda kuka tsara ba. Balli har da kisa abin yayi zafi haka? Kai amma ka siyo aikin da tsada, Ibrahim haduwa ta da kai ta saura a fagen daga ne kawai" Baya iya cewa komai ban da Farida tsaya ki ji amma duk maganar da ya dauko ta hana shi karasawa. Ibrahim na shaki sinaderin..... wanda tabbas babanka ne ya sanya min a wayar da ya ba ni domin na duba ajandar ku... tsarinku shi ne na mutu da bugun zuciya sai a ce don ka ki karban cikin dake jiki na ne ya sanya na mutu ko? Kai da wannan tsari na ku ya kai ga nasara da kun gama da duk wani abu mai suna Na'ibi, amma kash! Na farka, kuma ina so ka daure ku sake sabon shiri, ka san Farida bata san sallamawa ba" 117 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ta kife wayar. Sannan ta dubi gefenta amma babu Farid wamda ta zaci ya fita ne don ya ba ta dama ta yi magana a waya. * Har dare Mahdi na kai komo tsakanin falo da kofar dakin Farid wanda ya dawo ya wuce dakinsa ya kulle ya ki budewa duk bugun da kofar ta sha. Da misalin karfe takwas da rabi ne Mahdi ya samu magiyarsa tayi kai ya samu Farid ya bude masa kofa ya shiga dakin. Ya same shi dunkule cikin bargo da alamar yana fama da zazzabi. Duk dauriyarsa na kada suyi abin da suka saba sai da ya ji Farid ya kule shi. "Yanzu batun Faridar ne zai sa ka kashe kanka? Ka zo ka kunshe kanka a daki har ka fara zązzabi? Wai kai Farid..." Ya juyo ya katse shi. "Farida cikinta na aure ne ka san ma`anar hakan gare ni...mad Farida na da aure da wani ke nan tana soyayya da wani ba ni ba" Ya zaburo ya tashi zaune kwalla na fita daga idanunsa "Ban taba zaton haka ba... na jira ta da zaton zata zo ta ba ni isharar na fayyace zuciya ta ban san tana son wani ba har na yi nisa, amma ashe Farida ta yi nisa a soyayya...tabbas in ba don tayi nisa a soyayya ba da me zai sanya ta aure shi babu sanin iyayenta?" Ya dan daki cinyoyinsa sannan ya harde yatsunsa. 118 Mafan Masoya Rahma AbdulMajid "Dama ya zamo wanda take so shi ne ya so kashe ta...dama ya zamo wanda take so baya son ta dukiyarta yake so don ta dawo neman mai son ta da gaskiya ta same ni....amma kamar abin yayi nisa sai dai na yi ta fata" A hankali mamaki ya shigi mahdi kamar yadda ya tambaya a hankali. "Kana fatan ka sake komawa son Farida duk da tana son wani har tayi aure tana da ciki.Farid kana da hankali kuwa ko dai kishiyar uwa ta jefe ka? Ina zaton yaki kake da zuciyarka don ta mance Farida ashe zaka sake komawa son ta har da wani fata na banza?" Ya dube shi ya mike tsaye. "Zan iya baro soyayyar Farida ballantana na sake koma mata? Mad ka san me na ke yi wa Farida kuwa...Son ta nake, ita zallarta nake so ka san ma`anar haka kuwa? Na isa in gaya wa zuciyata ta bar Farida?" Ya tura Mahdi waje. "fita min daga daki, fita tun da kai ba me ganewa ba ne" Ya gwama kofarsa ya koma ya zauna cikin rike kai yana furta Farida na da cikin wani da aurensa ba Farid ba. A yanzu dai kuka yake. * Ibrahim ya ciro wani saitin kaya na karshe mai ruwan toka ne wandon da riga maras hannu mai ruwan kasa ya kalle ta da kyau sannan ya jefa ta cikin akwatinsa sannan ya mai da murfin akwatin ya rufe wanda ya dan rufe fuskar 119 Matiyan Masoya Rahma Ab duMa babansa da ya dade yana tsaye a dakin tzbayan akwati suka hada ido da Ibrahim da bai san yana nan ba, amma ya ki nuna wani mamaki ya mai da hankalinsa ga hada kayan da ke gabansa. "Ibrahim zaka tafi ne ka bar gidanku?" Ya hado wata jaka ta kayan wankansa ya ajiye gefen gadon kafin ya mai da amsa. "Zan dai bar gidanka ba wai gida na ba" "Ko me nene dalilin da zai sa ka bar ni din, ko dai saboda mace zaka bar ubanka?" Sai da ya kulle akwatinan ya tsayar da sannan ya fuskanci mahaifinsa. "Musamman nake gaya maka Baba zan bar gidanka kuma saboda mace, sai dai ba kowace maçe ba, mace wanda nake so amma kake son raba ni da ita saboda son zuciya. Ba kawai don ka so raba ni da ita bane na yanke shawarar karewar zamana da kai sai don niyarka ta raba wanda baka so da ransa... Baba ka yi yunkurin kashe Farida da dabara don kawai ka raba ta da danka shi ne zaka raba ta da ranta da duniyarta, zaka kashe matar danka ka kashe masa dansa dake cikinta wai duk don danka ya tabbata yadda ka zana rayuwarsa. Haba Dad! Mutum irin wannan ya cancanci mu ci gaba da zama tare?" "Ita ta ce maka na shirya kashe ta?" İbrahim ya kaďa kai cikin murmushin tafasar zuciya. "Ta ina zata gaya min? ka raba mu ai, kai ka gaya min yadda ka raba mu ka nuna mata abin 120 Mafiyan Mosoya Rahma AbdulMajid da ka dauka ban san ka dauka ba a waya ka raba mu domin ba ni da hanyar kubutar da kaina a wurinta...sai dai abin da ka 6oye ba ka gaya min ba shi ne yadda ka sanya sinadarin bugun zuciya a bayan wayar da ta shafa da hannunta kai ka je ka wanke naka hannun ita kuma ta shiga tayi ta shaka har abin ya kai ta ga kwanciya a asibiti rai a hannun Allah. Ka so ta mutu ka yada cewa kin karban cikin da nayi mata ne ya sa ta sami bugun zuciya. Baba kiyayya ta kai zaka kashe wa Na'ibi yarsa kuma macen da danka ya fi so duk cikin matan duniya don kawai ka tsara yakin kamfaninka, ashe ke nan jita-jitan da nake cewa kuna amfani da rayuka wurin yakin kasuwa kuna yi ke nan. Ka cire ni daga littafin rayuwar nan Dad, ba za a yi da ni ba, na rabu da kai da komai naka, mota da zan dauka da kudi na aikin da na yi ne ba wai na dukiyar uba da da ba. Tun da ba zan iya zuwa na kai ka kara wurin hukuma ba a matsayinka na uba na zan yi abin da zan iya shine nisantarka a iya rayuwata a karo na farko kuma na karshe. Sai wata ran" Ya dauki akwatinsa da jakar kayan kwalliya ya rataya daya ya ja daya ya kaikaita ta gefen mahaifinsa wanda ya kasa cewa komai ya fice daga dakin. Abdulhadi ya bi shi a guje ya tsaya a faranda yana kallon fitowarsa zuwa harabar motoci, duk ya ji ya karaya bai san abin da ke damun sa ba tsakanin karaya da takaici. Shin yakinsa da Na`ibi har ya kai yayi asarar dansa こ 121 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid daya tilo ko kuwa dai shi ne ba shi da gaskiya? Tun Ibrahim bai tafi ba duk kewarsa ta dame shi, karo na farko ke nan da zai rayu babu dansa masoyinsa Ibrahim da sunan yayi fishi ya bar masa gidansa kuma wai sun rabu. Lallai shi ya so kashe Farida amma laifin ne da ba zai taba bayyana amsawarsa ba. Gogewarsa ta fi gaban hakan don haka sanya ido dole ya kalli dansa yana barin rayuwarsa shi ne hanyar hakan, domin Ibrahim ba zai sake yarda da shi ba muddin bai amince da wannan laifi ya mika wuyan cewa shi yayi ba, ya san hakan domin ya gina rayuwar yarda da juna tsakaninsa da dansa ta hanyar da karyata ta wannan hanya zata yi wuya ta sake gina irin yardar da ke akwai a can baya. Ya daga hannu kamar ya kira Ibrahim a lokacinda yake kokarin tayar da mota, amma zuciya ta hana shi har sai da dan nasa ya sa motar a waje ya fice sannan ya ji ya jingina da bangon farandar ya kasa komai. * Farid wanda ke bin Mansur Nai`bi ka fada da kafada yana ba shi bayanan abubuwanda suka faru lokacinda yayi tafiya a yayinda masu aiki ke shigar da kaya, kuma matarsa wadda aka gama gabatar da Farid a gabanta take kokarin shigewa ita ma ta tsaya a yayinda ta ji tambayarta ta cewa wai ina Farida ta sami wata kaikaitacciyar amsa daga bakin Farid mai cewa. 'sir dama na ce kada na 6ata muku hutunku ne 122 Mariyan Masoya Rahma AbdulMajid da aiyukanku a lokacin da ake nesa domin wani abu ya faru duk da an dauki mataki' "Me ya faru? Da fatan babu Farida a ciki?" Ya tambaya fuskokinsu iri daya shi da matarsa don damuwa. "kan Farida ne kuma tana kwance a asibiti domin... "Farida na asibiti? Me ya sami yata, wa ya taba ta?" In ji mahaifiyarta wadda ta soma kara. ""Wasu sun yi yunkurin kashe ta ne ta hanyar busa mata faudar sanya bugun zuciya, amma na kai ta asibiti yanzu dai komai dai dai ta sami sauki" "Mu je asibiti" Inji Na`ibi wanda ya taso matarsa gaba suka juya suka koma motar da ta dauko su daga filin jirgin. Suka shiga baya cikin sauri Farid ya shiga gaba direba ya ja da sauri. Ita ce zaune gafen gadon Farida rike da yatsunta tana bibiyan duk wani motsinta cikin damuwa da tsarguwa na alamun zargi dake idon 'yar ta ta wadda ke yawan korafin bata damu dasu ba. A yanzu tana son ta zazzage duk damuwar da bata nuna wa 'yar tata bane na tsayin shekaru a wannan kwanciyar asibitin, amma a nan Farida da mahaifinta Na'ibi wanda yake tsaye da hannayen nan nasa a aljihu kan su a hade yake wurin wannan zargi, don haka duk kalmomin habaici tare suke aika wa wannan talika a iya zaman nan. Farid tuni ya fita tunda 123 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid zama ne na iyali duk da Farida ta sake gayyatarsa don ayi masa godiya amma bai wuce mintuna biyar ba ya koma waje. Abin da ya damu iyayen Farida kuma ta kasa gaya musu gaskiya shi ne waye ya nufe ta da wannan sharrin. Sam! Ta ki sanar da su duk kuwa da ta yarda da faruwar farmakin amma tace wani yaki ne da ya shafe ta ita kadai. Mahaifinta wanda ya nuna matukar bacin rai yayi alkawarin ba zata sake fita ita kadai ba sai da me gadin lafiyarta na musamman da zai kawo daga waje ba wadanda ta saba zaba a matsayin abokan yawo ba, amma nan ma ta dage da cewa bata bukatar a sauya mata irin na ta tsaron. "Father wannan fa ba wani abu bane da ya shafi tsaro ba, ni na kai kai na kuma na gaya maka yaki na ne, yanda ko zan yi wannan yakin zai ba ka sha`awa" "Farida ni da na fi ki sanin makamar duniya na amfanu da taimakon ki kan yakin kasuwanci da nake yi yaya za a yi ki ce akwai wani yaki naki ke kadai da baya bukata ta kuma ga shi har sun soma yunkurin kai ki lahira....Kada dai yana da alaka da shegen saurayin nan naki da kika guda saboda zalamarsu shi yasa kike son yi ke kadai" Ta lumshe idanu don ta 6atar da faduwar gabanta na gane wanda yake nufi. "Ah haba! Father kada ka sanya Ibrahim a wannan salon, an rufe caftarsa kada ka 124 Малyan Masoyа Rahma AbdulMajid bude....Ibrahim ba zai iya cutar da ni ba har ga neman mutuwa" "Well ki na da zabi na ki gaya min ko kada ki fada ba zan yi wasa da `yancin ki ba, amma ki sani `yancina ne in bincika duk abin da ya so taba min iyalina kuma in kin ga ban gano ba to ban bincika bane" 125 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Hudu Motar na garzaya wa hanyar fita asibitin ba ta inda ta shigo ba fitilunta na haska ko ina duk da ba har karshe direban ya kunna ba. Farid wanda ke kallon waje zuciyarsa na neman tsaigumin da zai ba shi ainahin makomarsa idanunsa suka yi arba da wani bawan Allah tsaye sanye da riga shet mai dogon hannu ruwan yashi shara-sharar da a na íya hango singiletinsa ta ciki ya zuba hannayensa cikin aljihun wandon jins. Ya ga wannan fuska wadda ta fara kona masa zuciya a ranar da Farida ta sami wannan tsautsayi, fuska ce ta wanda ya sha gabanta bayan ta fito daga wannan kulab kuma ta nuna masa 6acin rai. In zai tuna mutumin ya taba hannun Farida ko ta nan ne ya shafa mata abin da ba ta son ta fadi shi ne, ko shi ne ma na mijin da yayi mata ciki. "Direba tsaya" Ya umarci direban ba tare da ya tuna ba shi da hurumin yin hakan tun da me gidansu ne a motar ba har sai da direban ya tunasar da shi ta hanyar kallon sa da kin tsayar da motar kafin Na'ibi ya sanyo baki da umartar direban yá tsaya. "Wani abu ne Farid?" Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ya bukata yana me daga labulen wundonsa don ya hanga. "Sir yaron da na hanga tsaye shi ne wanda na ga ya sha gaban Farida daf da lokacin da wannan ciwon nata zai faru, yanzu kuma ga shi a asibiti, ina tsoro kada ya zo wani abun ne na..." "Kana da gaskiya koma da baya Micheal mu gan shi ko na san shi" Suka dan yi baya ba don suna jin tafiyar motar ba sai don ta iso bayan. A yanzu Na`ibi ne ya leka da kansa yana kallon wannan yaron wanda ya ke kaikomo maimakon tsayiwar da yayi da fari. Ya dan gyada kai. "Ok! Na san inda zancen ya bulla. Micheal mayar da mu baya ka ajiye motar zan zo ga yaron nan ina jin ina da hira da shi" "Baka zaton yana iya cutarwa?" Matarsa ta bukata murya a tsorace. Ya bigi kafadarta. "Wannan me saukin kai ne baya cuta, akwai magana ne tsakanin mu” "Mansur ba na son irin wannan gangancin naka, yaushe ka fara yarda da mutane a irin wannan kasar cewa akwai me son ka akwai mara son ka?" "Kwantar da hankalinki ina zuwa" Ya dan bugi kafadarta mafi kusa da shi wato ta dama, ya sauka daga motar nesa da wannan yaro. 127 Maryan Masoya Rahma AbdulMajid "Ibrahim na can tare da hankalinsa baya lura da mai shiga ko mai wucewa har sai da ya ragu yan mitoci tsakanin sa da Na'ibi sannan ya waigo da kyau ya kara tsayuwa cikin maye gurbin damuwarsa da fargaba. Na'ibi ya doso shi fuskarsa cike da murmushi sannan ya fara magana tun daga nesa da shi. "Ibrahim lafiya kake tsaye a nan?" Ya mika masa hannu kafin ya ba shi amsa suka yi gaisuwa irin ta maza masu shirin taryar duk abin da zai faru. "Babu lafiya... ina nan ne ina jinyar matata bata da lafiya" Na`ibi ya zumburo baki sannan ya share gumin hancinsa. "Oh! Barka! Kayi aure, Allah Ya ba ta lafiya". Yayi murmushi na karfin hali sannan ya kura masa ido. "Sir ko zan iya magana da kai kamar da da uba... ina da damuwa" Na'ibi ya tura hannu aljihu bisa al'ada sannan ya gyada kai. Ibrahim ya dan nisa sannan ya sake kura masa ido. "ka yafe min Father in zaka iya. Ba wata bace mata ta ba illa `yarka Farida. Ba ina nufin mata ta in ka ba ni ba, ina nufin mata ta da muka yi aure a Jamus cikin sunna da tsarin shari`a. mun zauna cikin jin dadi da kwanciyar hankali da kauna. Hah! Ranakun mu tare sune 128 Motiyan Mosoya Rahma AbdulMajid ranaku mafi girma da daukaka a rayuwata, har muka samu ciki. Wannan ciki shine kwarin gwiwar da muke jin zai ishe mu mu fuskance ku kuma da shi muka fara tunkarar babana. Ya nuna min ya hakura kuma ya amsa, amma haduwarsu da Farida ya muzanta ta ta inda bayan ta sami wannan 'ciwo ta ji ba ta son ganina... Ya dan matse kwallar da take shirin hana shi magana da kwarin gwiwa, me wuyar ta fito yana bukatar ci gaba da bayani ya tunasar da kansa. "A yanzu na rabu da babana, na kawo kaina gare ka, ko me kake so kayi masa da ni ina karkashin mulkinka, amma ina so kada kayi irin halinsa ka sada ni da matata" Ya matsa jikinsa a yayin da ya fara kwalla. "Tunda na san Farida na so ta ban taba nisa da ita a waya ko a ido ko a yanar gizo ba sai a wannan kwanakin. Ina asibitin nan duk kwanakinta a ciki, amma ta ki yarda ta gan ni. Na damu ina so na gan ta. Ina son ta ba zan taba yin wani abu da zai cutar da ita ba" Na'ibi wanda yayi zako ya kasa sabawa da kalmar cewa Farida da Ibrahim sun yi aure duk kuwa da kokarin da yake na ganin ya shigar wa kan sa da sabo koda kuwa zai tsaya a fuskarsa ne a matsayin wanda ya saba da gwagwarmaya. "Da kai da Farida kun yi aure a Jamus kuma kun zauna tare har kun sami ciki" 129 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ya jero labarin a hankali yana kallon Ibrahim wanda ya sanya hannu a aljihu ya fito da kwafi na takardar aurensu ya mika wa Na ibi wanda bai yi ragon azanci ba ya karba sai da ya dubi Ibrahim da kyau sannan ya soma dubawa. Ba shi da zabi baya da ya yi murmushi ya kawar da kai gefe guda don yayi tunanin da ya san ba zai iya ba. Yana so yayi girman kai wa mamaki, amma ya kasa sai ya soma niyar magana ya kasa. Babu tababa akwai kan sarki na nuna doka da like-like a takardar da ma zancen da ke ciki mai nuna cewa Farida da Ibrahim mata da miji ne. "Na san bamu kyauta muku ba, amma babu yadda zamu yi ne Father, muna son junanmu ni da Farida, kuma ba zamu iya sadaukar da kan mu ga gasar ku ba, ba ma ciki" "Dakata" In ji Na'ibi kan sa a sunkuye sai da ya ji Ibrahim shiru sannan ya dago. "Kun yi aure da Farida ba da sanina ba ko sanin mahaifinka, yanzu kun so mu sani ke nan, kuma ni yanzu ma kake sanar da ni....na san dai ba zaka sanar da ni a banza ba ko akwai abin da kake so na yi maka?" Ibrahim ya dan sunkuyar da kai sannan ya dago da nuna gazawa. "Ina so ka karbe ni ne a matsayin sirikinka ko da hakan na nufin na yi nisa da uba na ne, mahaifina ya kasa amsar Farida a matsayin sirika, kada ka zamo irinsa" 130 Matan Masoya Rahma AbdulMajid "Kasa karbąn mahaifinka neiyawa ta? Me nene asirin rashin lafiyar Farida?" Ya Kura masa ido a wannan lokacin don samo amsa koda kuwa ba a bakinsa ba. "ban da masaniya, Farida ta ki magana da ni, tana fishi da ni kan wani makirci da aka so-a raba mu don shi, na ji an ce ba ta da lafiya ne na zo nan asibitin, amma ta ki yarda a bar ni na shiga wurinta" "Uhummm! Wane irin makirci ke nan aka hada muku?" "Baba na ya ce mata tare muka shirya wannan aure don mu cuce ka, baya đa na rantse da Allah ba tare muka shirya ba, ta yarda da shi" Yayi ta kada kai sannan ya dubi Ibrahim karo na uku. "Yanzu Farida na da cikinka a jikinta...." "zaka sami jika father, ka yarda da aurenmu, shi ne abin farinciki mafi girma da ya tabа samin zuri`ar mu baki daya" Ya sake mai da hannunsa cikin aljihu. "ka je ka huta, zan kira ka nan da wasu awoyi don tattauna sakamakon tunani na, a yanzu ba zan iya fitar da komai ba ina dan kidime tukuna" Ya karbi lambarsa ya ki karban rakiyarsa zuwa ga motarsa sannan ya wuce yana tafiya a hankali yana kada kai da murmushin mamaki. A mota bai iya cewa kowa komai ba baya da dariya da yake, babu wanda yake amfanuwa da 131 Mafiyan Masoya Rahma AbduMajid tambayar da matarsa take, kamar Farid wanda ya matsu ya ji wani abu, amma babu abin da Na'ibi yace ban da 'Ibrahim Abdul Hadi ne, ya zo ganin Farida, amma bata yarda ya gan ta ba da ga nan ya rufe bakinsa ya na duba wayarsa, sako ya tura wa Wilson cewa su hadu a gidansa yanzu. A farfajiyar motoci ya tsaya ya sallami Farid cikin godiya da nuna jin dadin yadda ya kula masa da iyalinsa sannan ya bar shi ya dauki tasa motar shi kuma ya doshi falon da ya san lallai a nan Wilson zai jira shi. Yana zaune yana duba wani littafi dake kan tebur kusa da inda ya dogara kugunsa, yau tsayinsa ya kara fitowa saboda sanye yake da bakin wando da T shirt fara sol mara adon komai. Ya dago da sauri ya dubi fuskar Na'ibi wadda ta sanya shi saurin daure nasa bayan ya karanci damuwa a cikinta. "Me gida da fatan ba wata damuwa?" Shi ma ya zauna kan irin wannan tebur din. "Ashe Farida ta fi ka wayo, ta kuбuce makа tayi abu ba tare da ka iya sani ba" Ya sunkuyar da kai bayan yayi mitsi-mitsi da ido. "ban sanya wa madam Farida ido ba tun lokacin da ka ce a kau da ido ta je ta shakata wani abu ya faru ne, sir?" "Abubuwa ne suke juya kwalkwalwata. Farida ta auri Ibrahim aure na hakika, sun zauna tare duk iya zaman da na zaci tayi tana 132 Manyan Masoya Rahma AbdulMajid shakatawa a Jamus.Farida na da ciki a yanzu haka na Ibrahim, amma ba sa shiri, babansa ya san zancen kuma ya ki yarda. Farida na kwance a asibiti wani ya auna rayuwarta dakyar ta sha" Ya dan taso cikin mamaki. "Duk wannan ya Faru, Me gida?" "zauna in baka labari yadda komai ya faru filla-filla ba kuma na kira ka ne ka zo mu yi ta mamaki ba, so nake ka yi tunani, don ni na kasa" Lokacinda ya fadi hakan tuni shi ma ya sami kujera ya zauna, Wilson ya dawo da sanannen murmushinsa kan fuskarsa ya soma sauraron labari yadda Na'ibi ya samo. "Farid bai san wani abu kan duk wannan ba?" "Farid bai san komai ba, ya ma damu ya sani, shi ya ingiza ni na gano Ibrahim da ya sani da zai 6oye domin biyayyarsa ga Farida ta fi biyayyarsa gare ni Suka yi shiru na tsayin lokaci. "Amma hadin labarin nan na nuna da hannun Hadi a cutuwar Farida" Wilson ya ambata yana kallon nesa da inda suke kamar yadda tunaninsa ke yin nisa. "Me ka gano?" Na`ibi ya bukata a zumude. Ranka ya dade dubi lissafin nan. Hadi me saurin fushi da rashin dabara me dorewa, ya riga ka samun labarin auren Farida da dansa kuma ya ki amincewa biyu sau biyu kullun E 133 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid hudu take bayarwa, ta bayar da kwanciyar Farida don kada a haifi wannan jika. Me zai sanya Farida ta 6oye maka wanda ya nemi kashe ta in ba yana da irin kusancin da Hadi ke da shi ga jininta da son ta ba? Me

Chapter 7 of 11