Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
jid kwarewa ta kawo nasara gare shi da asara ga AbdulHadi sai dai tana hakan ne don samun damar gabatar masa da bukatarta ba tare da ya wadata da ita ba, don haka Farida ita ta fi amfani da wannan kasada da fari bayan da ta sanar da rmahaifinta cewa tana soyayya da dan abokin gasar kasuwarsa, amma babu bata lokaci ya nemi da ta bukaci ko menene a wurinsa amma ba wannan ba, ganin Ibrahim ya kawo kansa ga Na'ibi a guje ya zaci cewa wata makarkashiya ce daga mahaifin yaron domin ya bullo masa ta wata hanya tunda ya zame masa karfen kafa, don haka babu bata lokaci ya kori Ibrahim cikin bakaken maganganu, a karo na biyu Ibrahim ya sake bayyana masa a mai neman auren Farida ko da kuwa hakan na nufin ya nisanta da mahaifinsa, amma maimakon sassauci Na'ibi bai kore shi zalla ba sai da ya hada da marinsa. Mahaifinsa yayi masa Allah Ya kara ya kuma yi masa alkawarin nisanta shi da duk abin da ya zamo nasa muddin ya dage da son Farida. Ibrahim ya fara jin sadaukarwa, amma bayan haduwarsa da muradin zuciyarsda wadda ta ke kiransa Balala maimakon Balarabe ta zubda hawaye maras iyaka da nuna masa cewa dole su ci gaba abinda ya sanya ya ji wauta ce ma gare shi yayi tunanin rabuwa da Faridar wadda tuni ta kaurace ta yanke alaka da duk wani abu na mahaifinta da ta fara yiwa jagoranci musamman abin da ta fi kwarewa wato harkar sadarwa muddin bai amince da 20 Mofiyan Masoya Rahma AbdulMajid soyayyarta da Balalanta ba. A yau takanas Na`ibi Bici ya bukaci ganin 'yar tasa bayan da ya sake tika AbdulHadi Bici a kasa a gasar samin wata kwangilar samar da sadarwar gidan gwamnati da suka yi tare kan dasa maduban hangen nesa a barukokin kasar nan. A ofshinta ya shaida mata wasu shaidu dake nuna kokarin yakarsa da Ibrahim yake yi don farfado da mahaifinsa don haka wannan waazi ko dama itace ta karshe muddin ba zata rabu da Ibrahim nan da kwanaki uku ba, to shi ma zai dora mata takunkumi hana kusantar dukiyoyinsa. Farida ta rasa amsar da zata ba shi da ta wuce na baro ofishiinsa cikin fishi yana kira bata ko waiwaya ba ta fice ilahirin ofishin. * A tsallaken filayi oba din, gefen wata mata wadda take ta faman gasa dankali tana sayar wa uku paihamsin nan Farid yake zaune bisa wani dogon benci shi da wani dattijo wanda da alama shi ma ba shi da wurin zuwa ya ci dankalin ban da nan wurin. Ba hira suke ba amma sukan tono kalma daya biyu su yi musaya ko kan titin ko kan dankalin. Dattijon wanda ya cinye guda biyu ya kunshe daya da alamar yana da wanda zai kai wa, ya mike bayan ya biya kudinsa da wata dunkulalliyar wazobiya ya dan dubi Farid yace masa 'bie'. Farid ya bi shi da kallo bayan ya amsa har zuwa lokacinda ya isa ga titin yana ta shirin tsallakawa don kada kafar tsufa ta yi masa tawaye. Farid bai dena kallon sa 21 Maliyan Masoya Rahma AbdulMa jid ba ba kuwa don yana birge she ko kushe shi ba sai don ganin da alamar wannan tsoho tsohon dan boko ne, da jin kalmomin turancinsa ba na ji a bakin hanya bane na zaman aji ne, kuma ajin me kyau, watakila ma bai yi yawon cin dankali abakin titi ba a yayinda yake kamar sa amma dubi yadda rayuwa ta mayar da shi, babu amfanin bokon babu amfanin yawon neman kyakkyawar rayuwa, to ina ga shi wanda tun a samartakarsa ya fara yawon cin rogo ko dankali daga arewa har kudancin Najeriya, kada fa ya zamo tsufansa kenan zai zamo irin na wannan dattijo?! Gabansa ya zaftaro ya fado bayan tuna wannan kalma daidai lokacinda wata jeep-salon mai kirar bayan kwado launin azurfa samfurin Infinity ta yi sama da wannan tsoho da dankalinsa ya dawo kasa ba don ta dawo da shi ba, sannan ta kaikaita ta ci gaba da gudu. Ihu bai kaure a titin ba sai na motar da tsohon kasancewar babu kowa bisa titin, sai shi sai me dankali da karamar `yarta da suka taso a guje. Ban da tsalle da ihun kiran tsohon nan babu abin da mai dankali take yayinda `yarta tuni ta bi motar a guje amma da ta ga ba zata iya kamo ta ba tuni ta dawo, shi kuwa Farid ya sami damar daga kyallen hankicin sa a kan titin inda motoc suka lura suka soma sulo sannan ya durkusa ya dauki kan tsohon wanda yake ta kakari kafarsa ta yi raga-raga. Wata mota kirar pijo 307 an manna mata stiku a gilasin gaba daya an rubuta Press daya an rubuta The Nation 22 Mofiyen Mosoya Rahma AbdulMajid ita ta fara tsayawa inda wani akawu mai janta sanye da shet da wando da ta yi ya sauko da sauri ya agaza wa Farid wurin kokarin bai wa tsohon nan kulawar farko, sannan ya fara kiran taimakon gaugawa kan wayarsa a lokacinda mutane ke ta fitowa don agaji. Da shi da Farid ne suka shiga motarsa suka bi ta ambulance a baya inda suke hirar abinda ya faru cikin jimami. Farid ne ke ba shi labarin abin da ya faru kasancewar ya shaida komai, amma wata tambaya da mutumin yayi ta kusa da karshe ta ja hankalinsa. 'Yaya? Wace irin mota ce?' itace tambayar kuma tana nufin abubuwa da dama. Da fari tana nufin aikin jarida da ya tabbatar wannan dantaliki na yi, watakila ma ya sami labari kenan aikin kudinsa yake bayan na ceto, na biyu shine kamar ya san motar nan, ya san ta ya san kalarta da lambarta. Ita ce motar da yarinya Farida ta hau ta wuce ta busa masa kura, duka abubuwan da suka shafi Farida babu wanda ya manta ko ina ya gani zai tuna. Kenan wannan tambayar ba zai iya sayar da amsarta duka ba akwai bukatar tsanaki a ciki. "wata Infinity ce silber color sai dai ban ga lamba da mutumin ciki ba, amma da alamar irin masu hali din nan ne da basu mai da rai a bakin komai ba" A kofar asibitin tuni an gabatar da makarar daukan wannan mutum, kuma ga mamakin Farid wasu 'yan jarida masu daukar hoto tuni sun isa wurin da alamar abokan aikin wannan 23 Matiyan Masoya Rahma AbdulMa jid abokin taimakon nasa ne, haka nan shi ma mai taimakon tuni ya fitar da rediyonsa yana son yi masa tambayoyi. "kada ka damu abin da muke kokarin yi shine tona asirin irin wadannan masu kudi dake daukan rai a banza a idon duniya, ina son rubuta rahoto kan wannan hatsarin da ma wasu da suka fara zamowa ruwan dare a kasar nan. Amma dole sai da taimakon irinku masu gani a ido da kuma karatu" Bai musa ba domin tuni ya riga ya kullaci abin da zai iya. Suka yi hira da bata wuce abin da ya bayar a mota ba, a yayinda ' yan sanda ma suka ja shi domin yin nasu binciken shi da mai suyan dankali. * Farida ta shigo gida a tsorace tana busa mota kamar tana cikin gosilo, me gadi har wuntsilawa yake saboda ya bude mata. Ta shige cikin sukuwa ta sanya motar cikin wata farfajiya dake kallon sashin falonta maimakon layin takwarorinta motoci, sannan ta sauko da gudu ta dafa kafadar wasu jami'an tsaron gidan da suka iso gare ta. "A wanke min motar nan yanzu kada a bar komai jikinta, sannan kada wani ya neme ni yau, ina da bukatar kadaici" Ta shige ba tare da ta jira amsar su ba. А falonta ta yar da jaka ta soma tsalle na kaduwa yayinda ta dauki wayarta ta falo ta latsa lambobin Ibrahim. "Hello honey kin isa gida?" Matiyan Masoya Ta fashe da kuka. Rahma AbdulMajid "Bally kai da Father zaku kashe ni, kuna jawo min bala`i" Muryarsa da alamar rikici a-yayinda yake tambayarta 'me ya faru Farida me nene kike kuka?" "Balala na bige mutum da motata hankalina baya wurin, watakila ya mutu watakila ya musakance, hankalina na tare da matsalar ku kai da Fathe.. Ibrahim.." "Kwantar da hankalinki, a ina haka ta faru zan dauki mataki?" "Akan fly over na.....Balala ni na kashe mutum kuma babu dama na tsaya...oh! God!" "Kin kyauta da baki tsaya ba, zan aika ayi abin da ya dace...amma in kika tsaya zasu iya yi miki lahani kin san mutanen Africa yadda suke tunani, yanzu kada ki fitar ke ce don tunda baki tsaya ba zai iya shafar sunan gidanku don haka..." "kai gida ya dama kyale ni" Ta yi jifa da wayar ta rike kai ta fada kujera. Duka abinda ya ke kwantar mata da hankali na wasu `yan dakiku shine cewar Ibrahim zai yi wani abu. * Ya zauna kofar dakin yana murmushi sannan ya soma karanta ta kamar haka: 25 Matiyan Masoya Zuwa ga Farida. Rahma AbdulMajid 9th/8/2010 Ni ba dan jarida bane kamar yadda kuka zata ko kuma na ambata ba, sam! Ni wani talaka ne mai kare hakkin talakawa yan uwansa da duk iya karfinsa. A jiya talata goma ga watan Agusta kika yi arangama da wani dattijon talaka da ya kammala kalacinsa a tsakiyar titi saboda rashin gata ya rage abin da ya ci don ya tsallaka titin ya kai wa marainiyar 'yarsa da bata da gata sai shi, kika dauke shi da motar ki kirar Infinity mai ruwan silba lambar KJA 243. Wani abu da ya fi jan hankalina shine rashin tsayawar ki da nuna gata ga wannan rai da ba shi da gata sai Allah, kika bar shi a nan kwance mutu kwakwai rai kwakwai. To albishirin ki ko da baki so ji ba, ina son in taubatar miki da cewa wannan bawa ya rayu, amma ba dole ne rayuwar ta sake yi masa amfani ba. Akwai yiwuwar zai rasa kafarsa in har ya tashi, in fa har ya tashi kenan, domin tashin ma babu tabbas, kasancewar har yanzu da nake yi miki magana baya ko uffan, kuma ba a sami hada kudin da za ayi masa gwajin kwalkwalwa ba. yarsa wadda bata ci bata sha sai ya rage máta tana nan hannun titin Allah bata sami mai bata ci ba ballantana taimakon arundugun kudin tayar da kafadar mahaifinta. wannan lamari ya ja hankalin yan jarida musamman ma na The Nation yayinda daya daga cikin jami'an su ya raka mu har asibitin ya kamala duk wani bincike 2t Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid kan yayata mai wannan danyen aiki. Abin da yayı musu cikas shine sanin kowane ne mе wannan wulakanci ga talakan kasa, abinda ni kadai kawai na sani, ni na san ke ce kika aikata kuma ina da ingantattun bayanai da zan iya bayar wa akan haka amma ban yi ba. Na san zaki tambayi kanki dalilin da ya hana ni ko na neman wani abu ne gurinki? Sam! Ba haka bane, bana neman wani abu a wurin ki baya da hakkin wannan bawan Allah. Ki kula da shi ki dauki nauyinsa, amma idan kika ki yin haka, to zan yi abin da ya dace, ina da hotunan wannan lamari da kwafen wannan wasika tawa gare ki zan kara bayani na aika ta shelkwatar 'yansanda masu neman ki, da kuma kafafen yada labaru domin matsa wa yansanda lamba. Shi dai wannan bawan Allah yana nan kwance a asibitin koyarwa na jihar Lagos. Sunansa Gabriel Moses, ina zuwa duba shi har tsayin awoyi arba'in da takwas in ga ko kin yi wani motsi idan baki yi ba ni zan yi inshaAllahu Da ga Farid Akil 08063800300 Ya rufe takardar ya tura a wani ambulan mai kan sarkin gidan Jaridar Aminiya, sannan ya kalmashe ta yana cikin fara'a. Bai san ya karanta wannan wasika tasa da karfi ba sai da ya ji tafi da shewa sannan ya daure fuska, bai 27 Maliyan Masoya Rahma AbdulMajid juyo ba don ya san Mahdi ne sai da ya dawo gabansa sannan ya dube shi. "kai kuma ta yadda kake rubuta wasikar soyayyarka kenan?" Ya sake ballewa da dariya yayinda Farid ya ja tsaki ya mike. "Wannan ce wasikar soyayya?. Ni wannan wasikar ma ba ita na yi wa ba, babanta na yi wa nayi amfani da sunanta ne kawai amma shi nake so ya karanta don kamar ya fi ta hankali... kai wai baka yarda da cewa gamon tsiya kawai nake da yarinyar nan, amma ba wai ina binta bane, na gaya maka abin da ya faru jiya ko baka yarda bane?" Dakata dakata. Kwantar da hakilonka... yanzu gaya min manufar wannan wasika taka da tasirinta" Ya dawo gare shi. "manufarta itace na gwada tawa iyawar ko zan iya kwatar wa talaka hakkinsa ko kuwa a'a" Mahdi ya kalle shi cikin nuna tausayi da takaici. "Farid ba sarka muka zo yi garin nan ba, aiki muka zo nema in baka sani ba ka sani, in har ba zan baka shawara ka ji ba to ka yarda cewa in ka jawo bala'inka ba zan jira ka ba...yanzu ka sami irin wadan nan manyan mafiyoyi da 'ya'yansu ka ce zaka ja da su kai a wa ko a me?" Ya juya ya koma daki. 28 Motiyan Masoya Rahma AbdulMajid "Idan bala'In ya samu ka rantse da Allah ba ka san ni ba, domin ni fa ban tsayawa, jira ni a nan * Balala ya sauko daga faffadar matattakalar daga shi sai gajeren wando bulu yana kiran Guddies. Wani mutum ya bayyana da sauri, cikin shirin kwat baka da sauran kayan hadinta, yace 'yes sir' Ibrahim ya dafa shi suka karasa gaban kofar tangaran mai zuwa farandar falon. "Guddies aikin taimako kai kadai zaka iya yi min...Farida ta bige wani dattijo jiya bayan rabuwar mu, hankalinta ya kasa kwanciya, ina cikin damuwa..." Yayi ajiyar zuciya. "Na sami labarin an kwantar da shi a asibitin koyarwa, ina so yanzu ka je ka nemo inda yake, ka yi duk abin da a ka bukata na kudin da zai ceci rayuwarsa ko nawa ne ka sanya min bill, zan ba ka naka kason amma ka.." "sir an kama ta ne a wurin?" Ya kada kai cikin nishin nuna damuwa. "Ba a kama ta ba, kuma shi ne abin da ya fi min dadi, bata tsaya ba, babu wanda ya san ita ce, amma ka san Farida, ji take tamkar tayi kisa, don haka hankalinta ba zai kwanta ba...Sunan gidansu bana so ya fito a lamarin nan ballanta nata, don haka ka je ka ceci rayuwarsa da aljihuna a matsayin sadaka" Ya sake bude baki zai yi magana amma Ibrahim ya nuna shi da yatsa. 29 Matiyan Masoya Rahma AbdulMajid "Mutumin nan kada ya mutu Guddie, idan ya mutu hankalin Farida ba zai ta6a kwanciya ba, kenan nawa hankalin zai tashi, idan kuwa kai ka jawo wannan kuskure to hankalinka ya bar kwanciya" Ya nitsu yace yes sir sannan ya juya ya fita. Ibrahim ya sake latsa lambobin Farida amma kamar dazun bai samu ba ya ci gaba da shafa kai fuskarsa a cakude yana fadin. "yarinyar nan don Allah kada ki sanya kanki a wani hali. Babu abin da zai faru" A karshen layi Guddie zai karya da motar sa zuwa kan babban titi amma sai ya ga tsayuwar jeef skuardia wadda ya sani a gefensa ta yi masa wuta sannan ta sauke gilas. Abdul Hadi ne da kansa cikin irin shigar Guddie yayi masa ishararsa da ya lakanta da hannu ya ko amsa cikin kashe wutar motarsa ya fito ya shiga ta mai gidansa. Suka kalli juna sannan Guddie ya sunkuyar da kai. "Maimakon sakon da Ibrahim yayi maka ina son tura ka Bahrain daren yau ka je ka sha iska ba don kayi min komai ba, sannan ga sadakar milyan biyu. Aikin da zaka yi min shine kawai na tabbatar da aiken Ibrahim bai samu ba kuma ba tare da ya san bai samun ba..." "Amma chairman..." "Kada ka ce min komai, ka san komai na sani, gasar dake tsakani na da Na`ibi ba zallar ta kasuwa bace ta rayuwa ce. Bana son `yarsa ta 32 Motiyan Masoya Rahmu AbdulMa jid auri dana, ka ga watakila kasa taimakon ta bana in yayi ya sanya ta kufula, bukata ta biyu itace yadda jaridu suka fara buga labarin wannan hatsarin watakila a kai ga tonon asirin cewa 'yar Na'ibi ce ta aikata, kuma dole abin ya 6ata masa suna, abin da kuma nako so kenan, don haka idan biya min wannan bukata a milyan biyu zai yi kadan to na kara ya zama uku" "Na yarda Chairman amma.. "...Amma in baka yi yadda nace ba babu kudi babu Bahrain watakila ma babu aikinka, domin ni ne mai wuka da nama ba Ibrahim ba, amma in ka yi ban da wannan garabasa zaka shiga cikin makusanta da suka san sirrina" Ya sunkuyar da kai cikin ruwan sanyi yayi dan tunani sannan yace "Ok sir Farid ya zaro mayafin rufarsa da niyar zai kwanta ya fanshe gajiyarsa bisa katifa, amma ga mamakinsa sai ya ji an bangaji kofar dakin an shigo irin shigowar da ba ta abokinsa ba. Ya zabura don ya duba sai ko ga karin abin mamaki, su uku irinsu daya sanye da singileti bakake da fararen wanduna da bakin tabarau, kawunansu kulle da hankici. Wani wanda ya saba da shigarsu amma bai saba da kamaninsu ba shine na hudu wanda yana shigowa kawai nuna Farid yayi yace 'ku kama shi". Mai daukan wuya mai daukan kafa mai danke hannuwa suka cafke shi yana kakarin fadin me nayi.. ku su waye... ku sake ni, amma 31 Matiyan Masoya Rahma AbdulMajid babu wanda ya tanka shi sai a cikin wata jibgegiyar mota mai rufaffen gilasi wadda ta ba shi amsa da zurar sa a guje. Basa duka basa tanka zantukansa amma suna rike da shi har ya bada gari ya sallama cewa dan kwanjin nan nasa ba shi da rana ban da daukan nauyi da damben mutum daya ko biyu. A gaban wata shirgegiyar farar lemozin suka yi faki suka daidaita kofofin inda suka bubbude suka jefa shi cikin waccan. Kwatsam sai ya gan shi gaban wani mutum da ke zaune shi kadai a kujerar alfarma amma kuma ba tare da yayi kama da masu kudi ba. Siriri ne matuka, amma maimakon ya sanya abin da zai sanya shi yayi kauri sai ya sanya shet mai yankakken hannu mai ratsin fari da baki da wando baki duk da babu zanzaro sun nuna tsadarsu, fuskarta birkice da kasumba da alamar dattijo ne da ya damu da aikinsa baya kama da masu laifi kamar yadda yake kama da masu gaskiya. Da alamar mai son sanya hannu a aljihu ne domin ko daga zaune hannunsa na aljihu. Ya dubi Farid fuskarsa da sauki ba walwala babu dariya. "Kai ne Farid?" "Ni ne me zan yi maka?" Ya tambaya cikin tsageranci, mutumin ya dada karkata kai. "Abin da zaka yi min shine ka fitar da kanka daga harkar `yata kafin ka yi nadama. Takwarar ka bata gaya min tayi wani hatsari da mota ba sai a wasikarka na sani, na gode da wannan. Sai 3. Mofiyan Masoya Rahma Abdul Majid dai ina so ka mai da hankali kan abin da ya shafi rayuwarka, idan ma zaka shiga ta wani to ban da ta gida na domin kuwa bana yafe wa mai shiga rayuwar gidana. Maganar wanda `yata ta buge ta tabbatar min da faruwar hakan kuma na tausaya, zan kuma yi wani abu a kai, amma ba yadda ka tsara ba. Kawai dai ina son kada kuruciya ta debe ka amma bana jiran ka ba ni umarni ko shawara ka ji ko?" Farid ya daure tsoro ya daure mamaki ya kwakulo abin da zai iya cewa. "Kamar ni kake domin ni ma ba na jiran a ba ni umarnin abin da zan yi ranka ya dade, don haka shawara daya, idan ba ka yi abin da ya dace zuwa gobe da sha biyu ba ni ma zan yi yadda ka iya." Ya taba baki sannan ya gyada kai. "To bari mu ga wa zai bata ko ya batar ni da kai...Ku mayar da shi gidansa" Kafin ka ce kwanbo tuni sun jefa shi cikin motar da suka kawo shi ciki sun zura a guje Suka bar waccan motar a kan titi. Farida fara kal cikin jar T.shirt da gajeren jan wando da suka yi mata kyau musamman da ta hada da farin kambas na motsa jini ta dogara da karfen da take motsa jinin a kai tana duba jaridar, wadda tayi amfani da kalmomi na tausayi da masu zafi kan lamarin bige mutumin da gwamnati bata san da shi ba don talaka ne kuma a ka gudu, kamar yadda jaridar ta dauko 33 Matiyan Masoya Rahma AbdulMajid rahotannin mutane masu yin tofin-Allah-tsine kan masu irin wannan dabi'a ta wasa da ran talakawa. Ta ciro kai ta dubi mahaifinta wanda ya bata jaridar tsaye yana jiran ta, hannuwansa sanye cikin aljihun da bai yi wa zanzaro ba duk kuwa da yana sanye da farin tai kan bakar shet din sa. Ta kada kai cikin matukar damuwa. "Ba na kawo miki don ki damu bane na kawo miki ne ki ga abin da kika yi kuma ki san cewa akwai wanda ya san ke ce kika aikata har ya turo min gargadi kuma na gargade shi..." Ya juya mata baya yana dan taku a katon falon. "Ina so ki bar garin nan gobe ki tafi Johannesburge can gida a South Africa ki zauna har sai na kashe zancen nan... zan yi wani abu a kai amma so nake ki tafi don ba na so a taba jin sunan ki ko na gida na a ciki... kuma ga shi har wani ya san ko aikin wane ne, ke nan ina, da wasa ni da mai wannan aiki" "Father!" Ta ambata cikin mamaki da tsorata. Shi ma ya juyo da yanayinta. "In bar kasar saboda me? Don kawai kada a ji sunanka? Koda mutumin nan zai mutu? Me zai baci in na fito kafin wani ya fito na ce ni ce kuma na bada hakuri, nawa ne abin da za a biya ya ba shi lafiya? Babu abin da zaka ce sai na gudu. Father rai muke magana, kana maganar suna" Ya dako tsawa. 34 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid "Yes ina maganar suna ne da rai, suna na ba irin sunan kowa bane, ya fi rai a mafi yawan lokuta, and... bana in kika ce za ki yi wasa da suna na don son ran ki zan miki hukumci ba irin na da da uba ba...Farida gobe da safe nake son ki bar kasar nan, and rashin bin umar ni na zai kwankwasa ki kin ji ko?" Ya juya ya fita a fusace a yayinda ta bi shi da kalio. Yana 6acewa ta jingina da bango cikin wani dogon ajiyar zuciya da ya raka zamewarta daga bangon zuwa kasa. "Father! Why popsie why?" Ta dubi gefenta inda wayarta ke soke kusa da tawulin share gumi, kamar tana niyyar kiran Ibrahim ne, amma daga baya ta ji wani tunani ya doshi zuciyarta. Kamar fa ita ce ke haukar son Ibrahim amma shi tuni ya ja da baya ya sallama...Ibrahim baya son gaya mata ne amma ya hakura da ita. Da a ce Ibrahim din da ne da wannan lamarin da shi za a ci a side, amma yanzu dubi yadda ya bar ta ita kadai, bayan shi ta fara gaya wa a duniyar nan, kuma ya ci gaba da yi mata karyar ya dauki mataki, amma har yau shiru. Ta rike kai hannu bibbiyu. Karo na farko kenan da ta ji tana son barin kasar kamar yadda babanta ya sha yi mata tayi. Lallai akwai bukatar ta yi nisa inda zata rage jin duriyar Ibrahim, sai dai kafin ta yi hakan tana bukatar ta ceci ran da ta sanya a uku sakamakon son Ibrahim din tunda daga shi har babanta ba su damu da lamarin ba. Amma kuwa idan da gaske A 35 Maliyan Masoya Rahma AbdulMajid Ibrahim baya son ta yanzu ya cuce ta domin bata san ta inda zata fara mantawa da shi ba. Tayi jifa da hannayenta wadanda basu rabu da jikinta ba ban da dokuwa da iska da suka yi, ta so fashewa da kuka amma wani sashin dauriya a zuciyarta yace mata sam. Kada ta yi kuka. Gwada mantawa da Ibrahim kamar yadda ya gwada mantawa da ke yayi nasara. Ta tashi tsaye tamkar me maye tana tangadi ta bar falon motsa jinin. * Farid na kwance a tsakiyar daya-dayan dakin su, yau sa'arsa guda babu Mahdi wanda yayi tafiya cikin zabarin neman aiki. Rashin sa'ar gare shi shine tsoro dake masa tasiri wurin hana shi daukan mataki. Yana tuna maganar mutumin da ya kira kansa mahaifin Farida. Koda yake bai bayar da wata cikakkiyar gabatarwa wa kansa ba amma babu musu shine mai mai`aikatar nan da ya je neman aiki. Tuna shi da ma`aiktarsa da 'yarsa Farida abu ne da ke bukatar lokaci musamman ma bayan sun yi tozali ba a talabijin ko a rediyo ba, ido biyu cikin mota daya kusa da juna, amma gargadinsa gare shi ya fi dacewa da samun lokaci yanzu, kamar haibarsa na sanya wa Farid ya ji kamar ya bi umarni ya janye bakinsa daga wannan zance, amma kuma yana jin mazakutarsa da zuciyar kafiyar da aka san shi da ita da tunanin taimakon wanda aka cuta suna ta yi masa magiya kan ya bi abin da ya gindaya na cewa in 30 Matiyan Masoyo Rahma AbdulMa jid ba a yi komai ba nan da sha biyun gobe to lallai zai yi wani abu. Me zai yi ban da zuwa gidan yansanda da na jarida ya sanar da cewa yarinyar nan mai girman kai da rashin ladabi shagwa6a6biyar da bata ganin mahaifanta da gashi ita ce tayi wannan aiki. Da wannan tunanin da na tsoron kada a far masa cikin dare ya kwana ya tashi ya kuma jira ko zai ga wani canji daga wurin Na'ibi Bici zuwa ga mara lafiya yana mai yawo tsakanin gidansa zuwa asibiti har karfe goma sha biyu da rabi sannan ya mika wuya ga haramarsa ga fara lekawa wurin `yansanda. Ya tsaya cikin fargaba yana ta gyara kwalar rigarsa a gaban kantar 'yansandan da suke tsaye daya na rubutu daya na yi masa kallon raini da wulakanci da tsoratarwa kwatankwacin abin da fuskarsa ta saba nunawa. "Uhum! muna jin ka kai ne cikon na biyar da ya zo yace ya san wanda ya kade mr Moses,kuma duka karya suke, idan kai ma wasa ka zo yi ka sanar tun da wuri domin ba zan sake daukan wasa kan maganar nan ba, 'yansanda muke ba abin wasa ba" Farid ya daure tsoro da alamomin kashe gwiwa yay i ajiyar zuciya. "Na san wadda ta bige mr Moses" Dan sandan ya gyara tsayuwa cikin murmushi. "Au! Mace ce ma? To wacece ta bige shi...?" a 37 Mafiyan Masoya "Ni ce na bige shi" Rahma AbdulMajid Muryar mai zaki da ban mamaki ta fi isa ga Farid fiye da dansandan wanda dauke ido kawai yayi daga kan Farid din zuwa ga wadda ta bayyana a bayansa. Turancin ta babu alamar turancin kasa sai kace sarauniyar ingila ke magana. Koda muryar bata saba wa kamanninta ba, Farid bai taba ji ba sai yau. Yarinyar da ta bangaje shi ba tare da yayi mata komai ba, ta bangaje wani mahaluki da mota da bai yi mata komai ba shi ma. Yarinyar da ya fi jin haushi

Chapter 2 of 11