Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
manta. Ta koma cikin motarta inda babanta ya kira ta. "Yana ciki bai gan ki ba yanzu ya kira ni kina ina ne?" "Father ina mota ina jiran sa in ya fito kace masa ya same ni gaban mota, ba zan iya jira waje ba na gaji" a Bata rufe baki ba sai ta ji an dan kwankwasa motarta. Ta juyo ta dube shi. Babu tababa shine bakonta. Yana rataye da jaka a 77 Mafivan Masova Rahma AbdulMajid kafadarsa duk da yana sanye da kayan gida. Wato zabbuni mai nauyi da yayi masa kyau. Fuskarsa tayi kama da masu saukin fahimta. Та tattaro murmushi ta fora a fuskarta a yayinda ta fito daga motar ta fuskance shi. "Kai nc.... "Abdul Azeez, na san kin manta sunan". Suka yi musayar hannu a yayinda tayi murmushi ta yi fari. 99 "Kayi hakuri kan nawa ne... Ya gyada kai. "Na san haka kuma zan taimaki kan naki a dan zamana:. Ta wuce ta bude masa but ya jefa jakarsa sannan sannan ya dawo kujerar gaba ya zauna ta ja mota. "Ina zan kai ka masauki don na san ka gaji?" Ta yanke hirar gabatar da junan da suke a yayinda ta kama hanyar titin shiga gari. Ya dan dubeta kamar yadda ya jima yana satar kallon ta a tafiyar nan. "Ban gaji ba muddin baki gaji ba, na zo ne don na dan zauna dake mu yi hira, amma in kin gaji zan je ni ma na huta". Ta sha kwana cikin cin taya. "Na fi so ka huta don gobe kamar muna da dokaci in ba sauri kake ba, zamu zauna mu shiga gari" Rahma Abdul Majid 78 Mafiyan Masoya "Yadda kika ce, sai ki sauke ni a otel din da yayi miki, amma bana son Stars, sun fan cika hayaniya * Jifar ta yi da Jakarta ne ya janyo hankalinsa na cewa ta dawo har ta shigo falon ya zaburo da alamar ya jima yana jiran ta. Ya yi gumi kashirfan kamar ba sanyi ake ba duk kuwa da babu na`urar zafafa gida a kunne. Daga shi sai gajeren wando. "Kin dawo" ya ambata da sauri yana shirin tahowa gare ta. Ita kuwa hankalinta na kan yanayinsa da ya fadar mata da gaba ko wani abu ya faru. "Baby lafiya? Me ya sa ka yi wurjanjan haka.. gumi fa kake...Gaya min lafiya?" Ita ma tuni ta rike shi tana duba jikinsa Yayi ajiyar zuciya ya lumshe ido. "Bar ni kawai, babu abin da ya faru sai kewar ki da...da gaskiya bari in gaya miki da kishi... ina so in yi miki magana bana so in 6ata mana tsari, na rasa yadda zan yi ban san a halinda kike ba, duk na damu" Ya ruko ta da kyau idanunsa cikin nata ayayinda take dariyar keta. "Na san kina tare da wani na Farida... na damu ba ni da mafita, na san yadda kowane na miji yake iya ji in har Farida na tare da shi" Ta toshe bakinsa sannan ta yi magana. "Ina tare da wani amma ba waninka ba. Belly baka da wani a wurina kai kaďai ne. kada 7 Mafiyan Masoy a Rahma AbdulMajid ka bari kishi ya kashe ka kan abin da ka kago gobe ma zai sake faruwa don kishiyarka na son yin doguwar hira da ni Ta fashe da dariya a yayinda ta ji cikin mamakinta ya fada jikinta ya kankame ta ya sunne kansa cikin kirjinta yana fadin. 'Na yi kewarki Farida...rayuwa na kara tabbatar min bata da dandano in ba ki cikinta'. Ta fahimce shi. Tunda suka yi aure basu taba rabuwa na awa daya ba sai yau, dole ya ji wani iri. "Kuma dole rayuwa ta ci gaba da yin dadi domin ba inda zani na bar ka”. * A wata 'yar haraba da ke otel din da aka kebe saboda irinsu masu hirar kadaita Farida се zaune gaban AbdulAzeez dukansu sun yi matukar suturar sanyi saboda maido da jiki da yayi tun a daren jiya. Dukan su suna shan kayan zafi a yayinda suke hirar. "Farida bisa alada irin wadda muka tashi da ita masoya kan jinkirta lokacin fadin soyayya gatsau har sai sun sami lokaci mai daman a fahimtar juna da tsara yadda wannan ranar fadin albarkacin baki zata fi dacewa, wasu kan ja lokaci suna wannan shirin har sai lokacin da Kalmar tayi amai ta fito da kanta ba bisa lokacin da aka tanada ba a sabili da gajiyar 6oye ta ko kuma wani dalili ya tilasta hakan. Duk na san hakan kuma nayi duk wannan tanadi, don haka kada ki ji ina gaya maki sirrin zuciyata ki zaci kamar rana tsaka ne, kayya! Farida na dade ina 80 Mafiyan Masoyaа Rahma AbdulMajid son ki so irin wanda ban taba jinsa ba a rayuwata ballantana in taba yi wa wani. Sai dai ko kadan ban taba tunanin cewa dole ne na sami dacewa da soyayyarki ba, na san zuciya, tana dauke da 'yanci ne ko da kuwa mutum bai ba ta shi ba. Ni dai ina fita hakkin zuciya ta ne, kuma ina shirye da fita naki hakkin" Ya dan kura mata ido kamar yadda take kallon sa tun dazu. "Farida ina son ki ban san yadda zan yi da kaina ba, amma tuni jiki na ya fara gaya min cewa kina da inda kika sanya zuciyarki... ban ga so na a idonki ba, amma kuma gaskiyar lamari daya shine ba zan iya rabuwa dake ba, ina son ki ne muddin rayuwa, zabina daya shine na sanya kai na a hidimarki muddin zan dinga samin sanyin zuciya a ganin ki da jin ki, koda ba zaki iya so na ba Farida kiyi min wata alfarma ita ce ta kada ki yanke da ni, kada ki sake yi min nisa, zan yi manejin koda ganinki ne da murmushin ki da nuna min sanayya a matsayin goron da rayuwata zata iya samu... Ya dauke murya ya dan fara kallon wasu wuraren daban yana wasa da yatsunsa cikin junansu, kamar yana jin kunyar kansa da maganganun dake fitowa ta bakinsa cikin tilas. "Ki yi hakuri kamar na cika ki da surutu ko? In kina da abin da za ki gaya min kowane iri ne ban damu ba" Farida wadda ta jima tana kallon sa da karantarsa ta kidime cikin sanyin jiki ta rasa 81 Mafiyan Masoya Rahma Abdul Majid abin da zata ce. Lallai bata ji wani zauki a wannan dingimemiyar soyayya da bata da gurbi a zuciyarta ba, hasali ma hirar ta dan ginshe ta saboda kewar masoyinta, ji take tamkar yana misalta mata soyayyarsu ne ita da Ibrahim, amma gaskiyar da ba zata iya kaucewa ba ita се yana matukar son ta. Ba a bakinsa kawai ba, ta karanci matukar soyayya a idonsa, da yanayinsa. Yayi kama da maza masu fadawa tarkon soyayya mai tsanani kuma su yi shahada a gare ta. Ta fan kawar da kai gefe tana kada kafarta. "Kayi hakuri AbdulAzeez, na ji duk maganar ka, kuma duk wani hasashe da kayi akaina haka yake, ina...ina son wani, amma ina da matsala da su Father kan hakan. Ina cikin wannan tukuna, amma...ba zan yi maka alkawarin wani abu ba duk da ba zan hana ka abin da kake neman alfarma ba" Ta dawo da idanunta gare shi inda ta samu yana kallon ta cikin neman dauriya a karaya, ya sake sunkuyar da ido yana matsa yatsunsa. "It's ok, zan yi hakuri zan yi godiya ga duk yadda kika tare ni, sai dai ki sani, zan ji dadi idan kika sanya ni a duk wani service din ki da zan iya... ina son hakan tun daga karkashin zuciyata" Da wannan suka kawo karshen zancen su suka tashi daga wannan wuri da kamar yanzu sun gane bai kamace su ba suka koma cikin yama. 82 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Farida ta is0 gida a gajiye bata manne jikin mijinta kamar Yadda ta saba ba, bayan da suka sunbaci juna kawai sai ta hau kujera ta zauna ta rike kanta na gajiya, shi kuwa ya doshi ma`ajiyar kayan sha ya soma hado mata mai zafi. "Yaya ganawar taku ta kasance?" "Mun yi mun gama kuma mun fahimci yadda zamu fahimta" Yayi dariya. "Yaya kika ga candidate din na Father?" Ta dan lumshe ido na gajiya. "Man! He is in love.... Yana cikin soyayya da gaske, kuma abin da tausayi, abin sha`awar shine yana da irin saukin kan da ba zan sami matsala da yana so na ba koda kuwa bai dena so na ba, ba shi da irin zukatan `ya'yan manyan Africa da suke jin duk abin da suka so sai sun samu, jininsa da rainonsa na farar fata yana masa aiki.... Banbancinku shine in da shine kai, da tuni an yi abin da na so mu yi don mu gama da su baba...bai da zafin ra'ayi da akida irin taka, bambanci na biyu shine ba ni da takin son sa kamar yadda ba ni da takin kin ka” Bata san ya bar falon ba sai da ta ji karar sakin ruwa nesa da su. Ta bude ido ta ga baya nan. Ta san kwanar zancen a guje ta mike ta zubar da gajiya ta fada neman sa tana kiran 'Belly...ina kake baby' A gidan wanka ta same shi ya saki shayar zafi kansa ba tare da ya cire singileti da gajeren 83 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid wando ba. Ta fada ciki itama ba tare da ta cire kaya ba. Ibrahim wanda yake jingine ruwa na zuba akansa kamar yadda hawaye ke zuba a idonsa bai kalle ta ba. Ta iso gare shi a tsorace ta ja kafaďunsa ta girgiza. "Ibrahim me ya faru?" Ya dan dube ta. "Na zaci haka zata faru, na zaci rana irinta yau zata zo... Farida zan rasa ki a lokacinda na fi bukatarki a rayuwata, yaya aka yi na kasa daurewa shi ne takaicina” A rikice take don bata san abin da ya faru ba da ba don haka ba ita ma da ta fashe da kuka. "Me ya faru da zai sanya ka rasa ni?" "Har zaki tambaye ni? Me kike ji a zuciyar ki kan saurayin da kika je kiką hadu da shi... kin fara hangen dacewarsa fiye da ni... yana son ki ya fi ni saukin kai, ya fi ni mika miki wuya...Farida akwai mika wuyar da ya wuce rabuwa da iyayenmu da dukiyoyinmu domin mu yi hijira da soyayyar mu?" Tunda ya fara magana kada kai take na nuna rashin fahimta, amma da ta ga ta kasa samin hankalinsa sai zuba yake yana kara kuka ita ma sai ta shige jikinsa tana kukan. "Ban nufi haka ba, ban taba nufin haka ba... ka yi hakuri, kai ne rayuwata kai ne dadina kai ne dacina yaya zan yi na hada ka da wani, ina yi maka bayanin abin da na karanta ne ban san zai yi maka ciwo ba. Am so sorry. I love you...i love you" 84 Mafiyan Masoyа Rahma AbdulMajid Suka rike juna kam suna kuka ruwan zafi na dimarsu a baya * Mahdi ya shigo falon inda Farid ke zaune yana sauraron bugun sauti a rukodar falon da ya tilasta mata juya baitukan tsohon mawaki Micheal Bolton wanda yake fadin halinda na miji ke shiga yayinda yake soyayya a cikin wakarsa ta 'When a man loves a woman'. Ya jefe shi da wata jaka mai tambarin Zain yayi sauri ya cafe bai ce masa wani abu kan jakar nan ba ya ajiye ta gefe. "Oboy! Ina nan karban gaskiyar lamari daga hannun Boltin" Ya ja tsaki ya sami kujerar bangaren cin abinci ya zauna ya dauki wata tuffaha dake cikin wani tangaran na ajiyar kayan lambu dake kan teburin ya gatsa. "Kai ya dama.. baka damu ka duba me na kawo maka ba ballantana ka gode" Da sauri ya dauko jakar ya bude yana fadin 'oh yi hakuri na tafi ne' "Za ma ka dawo" Ya bude jakar mai dauke da kan waya samfurin Blackberry. Ya taso da sauri ya nufo shi. "Wa ka kawo wa wannan?" "Idan baka so ajiye min, kai kace kana son sayen blackberry baka da lokaci, shine na ga yau a na promo a kamfanin mu na ma`aikata na karbo maka tun da ni ina da ita" 85 Mafiyan Masoyа Rahma AbdulMajid Ya rungumo shi ta baya yana duba wayar. "Bold 2 fa! Kai Allah na gode da irin wannan shegen aboki da ka ba ni... saura na kawai na sami Farida na kara shi kenan kun ishe ni zaman duniya" Mahdi bai da zabi ban da fashewa da dariya. "Yanzu me nene na Farida a wannan lamarin?" Farid ya koma kujerarsa da sauri domin ya ba shi labari. "Yau na samu nayi magana da mutuniyar wallAhi don murna barin ofis nayi na kasa aiki. Mad nayi magana da ita! Ka san way a hada mu? Chairman da kansa. Ina zaune a ofis ya kira ni muna wasu tattaunawa kawai sai ga wayarta. Bayan sun gama magana sai yace mata ga na'ibinta nan su yi magana. WallAhi tayi min kalmomi masu dadi...ban da sakewa da na ji a muryarta sai kuma kalmomin yaba min cewa ta ji an ce ina aiki kamar agogo, na dauke duk hankalin ofishin, ta gode min da ban bata kunya ba kuma tayi alkawarin zuwa min da tsaraba....Kai Mad ina cikin sunan ka yau mad, amma na jin dadi" Mahdi wanda yake masa kallon haushi ya kasa tanka shi har ya gama. "Toh yanzu me nene na dadi a ciki, na zaci cewa tayi tana son ka ko tana kewar ka...kawai don me gidanka ta ce ka kyauta a aikin da ta sanya ka sai mc? Farid ban san ka da son mutane don dukiyarsu ba, amma gaskiyar 86 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid lamari dukiyar Chairman din ka ta ruda ka...dukiya ce kawai zaka so ka mallaka da zai sanya ka haukace haka ba wata mace ba. Haba Farid kada ka fadi ba nauyi mana" Ya ja tsaki ya dora kafarsa daya bisa hannun kujerar. "Matsala ta daya da kai wauta irin ta asalinku `yan fari... Yanzu Farida ita kadai ba Material bace da za a haukacewa sai an hada da wani kudi? Baka fa taba ganin Faridar da nake fadi ba duk ka bi ka ishe ni. Macen da ta ishi kanta da bata bukatar agazawar komai hali ko jiki kafin a so ta ita ce Farida. Idan da za a kwace duk abin da na mallaka da wanda zan mallaka a musanya min shi da Farida na yarda na wanye rayuwata daga ni sai wando sai singilet sai abin da zan faranta mata rai" Mahdi ya tashi a gajiye yana dariya. "Ai baka hadu ba tunda kace a bar ka da wando da cewa zaka yi daga kai sai Farida..." Suka kwashe da dariya inda Mahdi ya shige da ragowar tasa ya bar Farid nan ya koma fagen tunani. * Abdul Aziz ba kamar kullun ba yana ta asarar kwallon da ya saba ci a duk lokacinda suke wasa da mahaifinsa na kwallon sanda. Har dai mahaifin ya ankara sannan ya tsaida sandar ya dogara da ita sannan ya kalli dan nasa. 87 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid "Yaya kuka yi da Farida? Sai ce min kake komai daidai amma ban san me nene dai dai ba, ban ga daidai a dabi'arka ba" Ya kalli sama kamar me neman daukin mala`iku kafin yayi magana. "babu komai kawai dai tana soyayya da wani, ke nan ba zata so ni ba" "To me nene sabo. Dama ba mahaifinta yace tana son wani kuma yana kokarin raba su ba?" Ya juyo ga mahaifinsa cikin murmushin takaici. "Ba da wannan saukin ake raba so ba Abbana... da a na dena so cikin sauki ka san da ni na fara rabuwa da Farida tun kafin na san ta don kada na ji kunya a ce ina son yariya a jarida.Na ga matukar soyayya tattare da Farida wadda ita da kanta tana shan wuya kafin ta sami dadinta. Farida bata rabu da wanda take so ba don ba tace min ba bata kuma nuna hakan na da sauki ba..." "Kana jin akwai bukatar ka daure ka manta da ita ke nan?" "Abin da nake da tabbacin ba zan iya ba kenan...ba kawai yadda mace ke shiga zuciyar namiji Farida ta shiga zuciyata ba, kamar ma ba hanyar ta bi ba ma dungum... na dai tabbatar da cewa ba zan same ta ba, ba rayuwar kauye muke ba ballantana a yi maganar auren dole. Farida ta riga ta so wanina, amma fa duk da haka zan kasance ne tare da ita koda ba don zaton wata rana zata so ni ba, amma don tsoron 88 Mafiyan kada na sake maimaita ranakun da nayi bana ganin ta bana jin ta na rungumi kaddara na ganin ta koda daga nesa ne" "Kada ka zame min shahsa Abdulaziz! Idan na dauki ciwon son ka kafin ka san Farida yanzu kuma ba zan gane son ta da yi mata bauta tana son waninka ba, haba sai kace ba na miji ba, wane galahangar ne a duniya zai yi haka ban da kai. Ka shigo gidan nan ka gaya min ka manta da yarinyar nan shine wajibinka kuma cikin gaugawa" Ya saki sandar ya shige ciki da sauri cikin haushi inda ya bar Abdulaziz na yi masa kallon jahili al`amarin da yake magana. Ibrahim na kwance yana baccinsa, hanunsa kan filon da Farida ta dora bayan da ta zare jikinta daga shi. Tana tsaye a bayangidan tana jiran dakikun gwajin fitsarin da take ya cika cikin zumudi da doki. Ta cire tsinken daga 'yar robar fitsarin bayan da lokacin yin hakan yayi ta duba da zarwar ido. Alama ta fito mai nuna cewa lallai ciki ya shiga jikinta. Bata tsaya 6ata lokaci ba ta saki wata kururuwa wadda sai da ta wuntsilar da Ibrahim daga kan gadon zuwa Kasa. Ya fado bayan gidan ya rike ta a tsorace. "Belly mun yi nasara! Yes we made it!" Ya san kwanan zancen don haka kawai kwace dan tsinken gwajin yayi duk da bai san ina alamar cikin take ba. "Ina alama kin tabbatar?" 89 Mafiyan Masoya Rahma Abdul.Majid Tuni fuskarsa ta fara bayyana murmushi da ta nuna masa sai kawai yayi wo cikin daki da tsinken tamkar a cikin tsinken cikin yake. Ya na dubawa yana hajijiya. Can sai ya tsinci kansa ya kai wa Allah sujjada yana fadin 'na gode ubangijina' Ta iso gare shi ita ma ta durkusa ta kai sujjadar tana dawowa ya ruko ta yana duba ta sama da kasa har ya kai ga cikinta inda ya tsaya yana raba ido akai. 'Farida? akwai dana a cikin nan?" Ya rungume ta yana zubar da hawaye "Yanzu lokacin komawa mu fuskanci gida yayi ke nan?" * Salma wadda take cikin shiga irinta kasar su Eritirya wato laffaya koriya mai zanen fari babu abin da ya raba ta da Farida baya da tsawo da Faridar ta fita sai `yar alamar dake bambance tsufa da kuruciya. Ta iso falon kunshe a kafadar mijinta Na'ibi Mansur sannan ta wuce wata kujera ta jefar da Jakarta sannan ta bi ta a yayinda shi kuma ya wuce kantar tattara ababen sha ya tsiyayo mata wani maganin gajiya ya iso gabanta yana mika mata. "Welcome home sweetie" Ta dan yi ajiyar zuciya sannan fari da ido kana ta janyo hannunsa ya fado kujerar shi ma. "Na yi kewar ka da duk gidan nan na mu...Na yi kewar 'ya' ya na" Ya kwashe da dariyar da bai saba yin irinta ba. 90 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid "Salma ke nan, ba ki yi kewar kowa ba don zuciyarki bata kewa, ki bar dai zancen a sannu da zuwan da na yi miki" Ta dan bata rai. "Me yasa kullun kake yawan tuhuma ta da ban damu da ku ba ne? bana son haka Mansur" Ya dan kashingida can kusa da kafadarta. "Ba karya nake yi miki ba. Salma in har kin yi kewar mu me nene zai hana ki zuwa ki gan mu? Wane aiki kike da ya zamo wajibi sai kin nisanci iyalinki ban da dai haka kika zaba. Farida tayi fama da matsalolin zuciya kan soyayyarta da dan Hadi, na kuma gaya miki, amma ko wannan bai isa ya sanya ki zo ki ga `yarki ko ki je can Germany tun da kuna kusa ki duba ta ba? Ko kadan aikin kula da yara da bukatunsu nawa ne, to na dauka, yanzu ma na san akwai abin da ya kawo ki kasar nan, amma ba don kewar mu ba, don haka ina yi miki sannu da zuwa” "Ka ba ni nan da shekara daya na kulla muradina, na zamo shugabar kungiyar mata masu tattali da tsafta ta duniya, ina tabbatar maka da cewa daga lokacin sai kun gaji da ni, duk aikin da kayi zan biya ka zan baka lokacina fiye da duk ilahirin zaman mu" Ya kalli ilahirin fuskarta sannan ya sa hanna ya kamo wani yanki na dogon gashinta dake sauka gadon baya ya shinshina sannan ya rike. "Yaushe? Sai wannan ya zamo audiga ya kade ya tsufa, fuskokin mu sun tamuje kafin na 91 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid sami lokacin ki? Me kike so yanzu da wannan zuwan?" Ta kwanto jikinsa. "So nake mu kwana biyu ni da kai muna morewa sannan rana ta uku sai ka raka ni mu je kasar Moroco inda muke da taron tsayar da dan takara, kowa zai zo da nasa mijin ko abokin zama Yayi dariya sannan ya ce 'uhum..' "Wato idan dai na gane zaki ba ni cin hanci na kwana biyu sai mu je na biya ki aikin ki ko a zuwa taro" "Ba fa haka na ce ba. Zamu je taro amma kuma na zo na zauna da kai mana" "ko ma yaya kika sanya ba zai sake yi min zafi ba, sai dai kada ki manta Farida zata dawo a ranar da kike so mu je taro, don haka sai ta sauka mun gan ta kafin a wuce in yayi miki to in bai yi miki ba sai ki je ke kadai" "Yayi min mana, ai ni ma ina son ganin yata, idan ta zo da wuri sai mu tashi daddare ko?" Ya mike tsaye ya ciccibe ta. "Mu je ki fara biyan zama da ni tunda kin amince. Ba zancen gajiyar tafiya don ba a jaki kika zo ba" * Ibrahim na kamala ajiye jakarsa ya zauna kujerarsa ya zaro waya, Farida ya kira suke ta hira har zuwa lokacinda jirgi ya soma ninkayan tashi sannan suka yi sallama cikin kewa. 92 Mafiyan Masoya Rahma Abdul Majid "Kada ka damu ina tare da kai. Ka gama sasantawa da shi sannan jibi mu sake haduwa ko?" Kalmar karshe da ta karanto masa ke nan da ta fahimci dimbin damuwa a muryarsa, sannan ta sumabci wayar ya mayar mata sannan ya kashe tasa. Jirgi ya tashi ya bar Ibrahim cikin tunani mai dagula kwakwalwa, zaton Farida na cewa damuwarsa ita ce rabuwarsu da kuma yadda zai fuskanci babansa ya samo asali ne kan yadda suka kulla yarjejeniyar shi zai fara zuwa ya shawo kan mahaifinsa don da ta isa ta wuce wurinsa su tafi tare dukansu uku ga mahaifinta a sasanta. Amma ainahin damuwarsa ta karkata ne kan wani sirri da ita Farida bata san da shi ba kuma tsoron yadda zata kaile shi ne ya hana shi gaya mata. Wannan sirri ba na komai ba ne sai na zuwansa ya auri Faridar a 6oye. Ibrahim wanda mahaifinsa ke zaton ya ta`allaka ne da sha`awar Farida ba son ta ba yayi masa tayin daukan nauyin tafiyarsa a boye zuwa ga Faridar wadda leken asirinsu ya tabbatar masa ta doshi hanyar Jamus, inda suka kulla yarjejeniyar zai dauki nauyi ya kuma kawar da kai daga yaudara da more rayuwa da Ibrahim zai yi da Farida ba tare da aure ba ko da kuwa hakan zata nuna cewa ya gudo ne babu yardar mahaifin nasa, kuma in so samu ne yayi mata ciki su yi hotuna na samar da tabbacin hakan sannan in ya koshi ya baro ta ya dawo ya bar wa mahaifinsa sauran aikin da ya ke ganin yayi wannan sadaukarwa 93 Mafiyan Masoyà Rahma AbdulMajid dominsa wato karya lagon Na ibi da wannan wulakanci a kan 'yarsa da tanyara ta a duniya a matsayin karyar su shi da dansa. Duk da lokacinda baban Ibrahim ke ba shi wannan shawara ya kufula matuka ya kuma ga wallen uban nasa, ya daure ya amince da wannan tayi bayan kwana daya tak ba don komai ba sai don ya isa ga Faridar dake shirin kubuce wa rayuwarsa, a yayinda mahaifin nasa ya kanjamar da asusun sa na kudi don kada ya iya yin wani motsi na radin kansa, sai dai a zuciyarsa ya kudiri niyar auren Farida da niyar zama da ita har iya rayuwarsa, kuma in suka sami karuwa zai zo ya gaya wa mahaifin nasa cewa bai yi aikinsa ba. Yanzu dai abin da ya kama hanyar zuwa Najeriya yi ke nan, kuma ba wani abu ne ke damun sa ba illa yadda zasu kai ruwa rana shi da mahaifinsa kafin su yarda da kaddara, watakila ma su rabu, amma in so samu ne yana son su gama wannan abu gaba daya Farida bata san wancan sirrin ba koda kuwa sun rabu da mahaifinsa ko suna tare. Wannan lamari ne ya zame masa abokin hira har ya iso Najeriya ya kuma shiga motar da mahaifin nasa ke tukawa zuwa gida suna hirar jin dadi suna tafawa. A tsakiyar babban falon nan dai da babu komai sai shinfidun darduma da jefi-jefin kujeru, AbdulHadi ya zubo wa dansa lemo shi ma ya zuba nasa sannan suka soma kai komo suna sha. 94 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid "Na ga kana cikin damuwa, na san za a y haka, rabuwa da kyakkyawar yarinya irin Farida wadda aka zauna da ita fiyc da wata biyu ba Karamin lamari bane. Amma ka yi hakuri tunda ka yi min aiki na yadda ya kamata na yi alkawarin zan yi amfani da ko da duk dukiya ta ne na samar maka wadda ta fi ta" Ya fadı yana dafe da kafadar Ibrahim yana dariya bayan da suka kurbi lemon tare. "Daga yau tsalle-tsallen da Na'ibi ke min ya kare, zan tozarta shi da `yarsa...Haaaahaaa! Sauri nake gobe tayi mu fara aiki....Dana ka haifu kuma ka goge min bakin cikin rashin yawanku" Ibrahim ya sunkuyar da kai sannan ya fara magana. "Dady ka yi hakuri ban yi aikin nan yadda ka sanya ni ba.." Ya dago ido suka kalli juna shi da mahaifinsa wanda ya dauke wuta, sannan ya ci gaba da magana. "Na je Jamus yadda muka tsara kuma na ji dadın zamana da Farida, sai dai a matsayin miji da mata ba wai kawai wata mistress ba. Na auri Farida bisa sunna ne da kuma shaidar Kotu. Sannan a halin yanzu tana da ciki na dan da nake son ya soma zama dana na fari a rayuwata...sabanin yadda ka ce Dady ka yafe min. Farida son ta nake ba sha'awarta ba, don haka baba in akwai abin da zaka yi wa Baban Farida ya ji haushi shine ka karbi 'yarsa a 95 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid matsayin matar danka, ka rungume mu, Farida shirye take ta amshe ka a matsayin uba muddin mahaifinta ya ki ba mu hadin kai kuma..." "Ya isa bari na ji magana" Ya ko yi tsit a yayinda AbdulHadi ke nuna shi da yatsa cikin mamaki. "Ka auri Farida ka се?" "Eh baba! Kuma tana dauke da jikanka na fari" "Ke nan ba yadda na ce

Chapter 5 of 11