Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
a duk fadin duniya haushin da kamar ya fi dalilansa na jin haushi yawa. Dansandan ya kawar da wannan yanayi da tambayar wannana baiwar Allah mai tsaye tana wasa da mukullin mota kusa da makalalliyar Jakarta dake kusa da hammata. "Ke ce kika kade Mr Gebriel da mota?" "Ni ce na kade shi' Ta amsa da karfin gwiwa har yanzu bata kalli mai satar kallon ta cikin rudani ba wato Farid. "Wace ce ke malama?" "Suna na Farida Na`ibi Bici" Sunan ya girgiza duk wanda yake wurin ban da Farid wanda ya san kowacece, abin mamakin da yake jira shine makircin da ya kawo Farida. Amma dansanda mai rubutu da mai sauraro duk sun bar aikinsu sun nuna nitsuwa. "Amma ranki ya dade yaya a kayi da kika buge shi baki tsaya ba?" 38 Mafiyen Mosoye Rahma AbdulMajid A yanzu ta dora idanunta kur kan Farid, duk da bata kalle shi sama da kasa ba, amma yanayin kallon na nuna raina shi tayi. "Ina da wasu matsaloli ne da suka sha kai na shiyasa har na bige shi ban sani ba, bayan na bige shi na ji tsoron tsayawa saboda rashin hankalin `yan-zauna gari-banza da zasu iya daukan hukumci a hannunsu basa barin wa Allah ballantana hukuma" Da alamar da irinsa take shiyasa ta sanya ido kansa tamkar da shi take magana. "Shin ranki ya dade kin san ma'anar bige mutum da laifin hakan a idon hukuma musamman bayan ka gudu?" "Na sani koma yaya ne laifi ne, amma kun san zan iya kaucewa ba tare da wani hukumci ba, amma na kawo kaina a yi min hukumcin da ya dace da laifina, muddin hakan zai iya bai wa mai raunin lafiya, domin ban san yana jin jiki ba sai a jarida na gani. Na shirya daukan nauyin duk abin da zai kawo masa lafiya, don haka ne na kawo kai na gare ku don a sada ni da lafiyarsa" Dansanda mai rubutu ya kalli Farid. "kai kuma aikin ka ya kare sai ka bar wurin nan" Farid cikin rikita, raunin jiki da sanyin gwiwa ya juya ya bar wurin inda a cikin zuciyarsa ya ji yace da Farida na bar ki lafiya amma Kalmar bata fito ba. A 2 39 Maliyan Masoya Rahma AbdulMajid A kofar dakin Gabriel babu kowa sai wasu kabilun sa da basu jin turanci da karamar 'yarsa wadda take jin turanci amma bata da isasshen bayanai. Ya tambaya ko yaya me jiki yarinyar ta amsa masa da cewa an ce su fito ana yi masa wasu gwaje-gwaje, sannan ta ji ana cewa za a wuce da shi asibitin kashi idan kudi ya zo. Ya tsaya yana nuna tausayawarsa sannan ya ke cewa yana sauri zai koma. Basu yi aune ba sai ga wadda ya gudo biye da shi. Farida ce cikin rakiyar `yansanda sai dai da alamar ba kamata sukayi ba tsaron lafiyarta suke. Ta iso ga kofar dakin har zata tambaya ko nan ne amma da ta ga Farid sai ta ji babu bukatar tambaya. Duka mutanen suka dan dare na tsoro suna gaishe ta, bata bata lokaci ba ta wuce ga yarinyar cikinsu wadda da alamar ita ta fi damuwa don har yanzu shasshakar kuka take. Farida ta sunkuyo gare ta. "Yarinya wace ce ke?" Ta amsa cikin kallon idon Farida. "ni ce 'yar Gabriel da mota ta kade min babana" Sai da Farida tayi ajiyar zuciya ta kada kai sannan ta daure ta dan yi fari da ido. "Ki yi hakuri da ni nice na kade baba da "mota יי Bata rufe baki ba sai ta ji mari daga hannun yarinyar nan wadda bata tsaya nan ba ta kai mata cakuma tana ihun fadin 'ke ce zaki kashe min baba?' wani dansanda ya zakudo don kwace ta daga hannun yarinyar amma da sauri a1 40 Mofiyan Masoyа Rahma Abdul Majid Farida ta kada masa kai ya tsaya, hakan ya sanya yarinyar wadda da alamar makwabinta daya tilo baya wurin tana abin da ta ga dama don haka babu wanda yace mata kanzil sai da ta tsaya da kanta tana Kara shasshaka. Da tsayawarta Farida ta yi kasa ta durkusa a gabanta ta ruko hannayenta tana kallon ta cikin ido sannan ta soma magana cikin nuna tausayi da taushin murya cikin turancinta na bakin kasar waje. "ki yi hakuri ba so na ne na taba kade dan adam ba, tsautsayi ne ya faru, babban kuskure na shine kasa samin kwarin gwiwar tsayawa da nayi domin na fuskanci kuskurena, amma ki yarda da ni duk yadda kuke jin zafi haka na ke ji, zuciyata bata huta ba cikin kwanakin nan biyu har sai da na miko kai na ga hukuma. Ki sani na shirya yin duk abin da zan iya na ganin mahaifinki ya sami lafiya, koda hakan na nufin duka karfina ya kare, zan kula da shi zan kula dake kin ji ki yafe min" Yarinyar ta kura mata ido cikin sanyin jiki har zuwa lokacinda Farida ta shafi kanta sannan ta sake ware ido ta tambaye ta 'kin yafe min kawata?' bata da zabi baya da samin kanta yana gyadawa na nuna yarda. Mikewar Farida ya zo daidai da lokacînda wata mata ta bayyana tana ambaton ina muguwar take, ku nuna min ita cikin lankwasasshen turanci.daure take da zani biyu kan wata rigar leshi fari maras isashen hannu, ta ci dauri da gwaggwaro kalar zaninta C 2 41 Mallyan Masoya Rahma AbdulMajid bulu mai kyalli-kyalli, ta rame ta koke, ban da fata da jijiya babu komai da ya rage mata sai tsawo. Ramar ta hana a tantance halin da fuskarta ke ciki na muni ko kyau, watakila haka take watakila kuma rashin isar abinci ce. Da sauri ta shigo ta sha gaban Farida wadda take tsaye a yanzu da niyar shiga dakin me jinya. amma ta tsaya da ta ji hayaniya. Matar nan ta dubi saura da suke tsaye tana tsalle da jikinta kamar mai shirin shiga filin kokuwa. "Me kuke jira kallon ta kuke? Ba itace ta ke son kashe dan uwana ba? Don kina da kudi? To yau zan nuna miki cewa talaka ma ba a bar shi a baya ba. Abin da kika yi wa kani na sai an yi miki a yau. Duka mu je ba lafiya. Ki sa hukuma ta kashe mu Sauran suka yi wo kan Farida wadda ke kallon abin mamaki, amma kafin jami'an tsaro su yi aikinsu, tuni Farid ya yiwo gaba ya kare ta sannan ya daka tsawa. "Ya isa!" Duka suka tsaya kamar masu bin umarnin Allah. Shi kuwa yana ta hucin fushi yana kallon su daidai ko akwai mai shirin bijirewa. "Na dana sani yi da jin kunyar kai na na zamowa na daya daga cikinku. Cikinku talakawan da sau tari masu kudi na zargin cewa kuna jin haushin su ba don wani dalili ba sai don baiwar da Allah Yayi musu. Lallai yau kun tabbatar haka muke. Na san da talaka ne yayi abin da wannan baiwar Allah tayi muddin ya zo 42 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid mana da uziri zamu tsaya mu saurare shi, amma dubi abin da kuke shirin yi wa wata mace don kawai tana da kudi. Don ta kawo kanta gare ku da neman gafara da shirin daukan nauyin laifinta, kun manta da cewa tana da karfin cewa itace kuma ba zata yi komai ba ta kwana lafiya. Tana da hujjar cewa ba ita bace kuma babu me hujjar cewa lallai itace. Amma duk da haka ta kaskantar da kanta ta zo muku daga ita sai ita ta hana shigar jami`an tsaro tsakanin ku da ita, ta baku hakuri, wannan bai ishe ku girmamawa ku yafe mata ba? Idan bai ishe ku ba ku sani zan janye daga duk wani kokari da kuka san ni kadai nake muku zan juya baya don na zo tabbatar da an yi gaskiya ne ga wanda ya cancanta, amma idan kuka nuna min baku cancanta ba zan nuna muku tawa iyawar, nine shaidar da zata samo muku hakkinku ko ku rasa to zaku rasa din kuwa" Duka suka sunkuyar da kai kamar wadanda ruwa ya ci, wani da ya iso gaban kofar dakin mai jinya don hana ta shiga ya kauce a hankali, a yayinda Farid ya juyo ga Farida cikin sanyin murya ya nuna mata kofar dakin domin ta shiga , ta gyada kai tana murmushin mamaki sannan ta shiga. Kafar Gebriel wadda ta cakude ita ta fara sanya ta tashin tsigar jiki har da hawaye, dakyar ta karasa kusa da shi, sannan cikin kada kai tace. 5 43 Maflyan Masoya Rahma AbdulMajid "Haka nayi da kai? Wai ni nayi haka da kai?" Ya dan lumshe ido. "Yata na yafe miki,ba zaki taba yin hakan da saninki ba, na kuma ji duk abin da mutane na suke yi miki a waje, na ji kokarin da dan uwana dan Najeriya yayi domin ya kare ki ya sanar da su gaskiya. Ki yi hakuri da su fishi ne na ganin halinda jininsu yake ciki, ki yafe wa 'yata mai marin ki, tsoro ya sanya ta, don bata da kowa sai ni...ni kuma na yafe miki Allah Ya kiyaye mu duka a gaba" Babu abin da take nanatawa ban da Kalmar 'Am so sorry' Mutanen na waje cirko-cirko har ta fito ita da Farid a lokacin da alamar wani kakkarfan direbanta da aikinsa na iya fin na direba zuwa na mai tsaron lafiya ya karu a ketaren, ta kalli mutanen daya bayan daya a yanzu bata ce da su komai ba baya da yarinyar da ta sunkuya ta sunbata a goshi sannan ta ce mata 'sai na sake zuwa ko?' 'bye aunty' ita ma ta mayar mata. Та dubi Farid sannan tace masa 'walk with me' wato biyo ni. Farid ya ji nauyi kamar ba shi ne mai jin haushin Farida ba ya ji ba shi da dalilin kasa bin umarninta. Ta karbi mukullin motar daga hannun katon nan tayi masa umarnin shige wa kujerar baya, sannan ta yi wa Farid umarnin shiga gaba da kai a yayinda ita kuma ta shiga wurin tuki. Tuni motar ta dumama kanta iyaka Farida ta ja 25 Mefiyon Masoya Rahma AbdulMajid zungureriyar motar da in banda kallon wuce gine-gine baka sanin tana tafiya. Komai a motar fari ne kamar akwatin gawa, akwai kofa a cikinta da ta raba matuki da mai gidansa na baya, kenan wanda Farida ta tura baya ba ruwansa da su sai an neme shi. tuki. "Me sunanka?" Ta tambayi Farid ba tare da ta kalle shi ba. "Farid Akil" Sai yanzu ta dube shi sannan ta koma ga "Waw! Sunan mu kusan daya" Ta yi wani murmushi da gefen kumatu daya da ya lotsa kwalamar kumatun nata da yayi matukar sanyaya wa Farid koda bai tantance dalili ba. "Dama ka san ni na kade shi ne?" "Na sani kuma har na gaya wa babanki cewa yayi wani abu don na sani Da alamar yana maganar ne yanzu da jin a na son a yi masa `yansandan ciki "Oh! Kai ne wanda baba yace ya san ni na yi wannan aikin?" Tayi dariya sannan ta sha kwana. "Believe me, ba don gargadin ka ne na fito ba, na jima abin yana damuna, amma duk wadanda na turo su yi wani abu ba su yi ba shi yasa na zo da kaina, amma da yadda na tafi in na so tafiya na tafi kenan" "Na sani ai" Shi ma ya amsa daga kokon zuciyarsa. 45 Mallyan Masoya "Wane aiki kake?" Rahma AbdulMajid "Ban sami aiki ba tukuna" Ta dube shi da mamaki. "Me ka karanta ne da baka sami aiki ba?" "Na karanta Computer science ne" "Da kyau! amma me ya hana ka samun aiki da wannan karatu me tsada?" "Na ci jarabawa ne da yawa shi ne ma'aikata suke jin na yi musu tsada" Ta sake yin dariya da kyau. Basu dade ba suka iso ofishin nan da ya zo satin da ya shige. A babban falon yau ba kamar ranar shigowarsa ta farko ba domin kowa ya mike ya bayar da hankalinsa ga Farida. Ta isa ga wata doguwa kamar ta wadda ke cikin shigar sut da siket bakake kalar karin gashin da ta zuba wa kitso a kanta. "Akwai wani ofis da babu ma`aikaci?" Ta kada kai. "No ma'm" Ta kada kai ta wuce da sauri sashin gabas inda take cewa 'sai nawa ofis din ne babu kowa' Ta tura kofa, faffadan ofishin ya bude mai matukar haske komai fari da ruwan milki. Akwai sashin karban baki akwai na aikin ofis, a teburinta akwai sunan ta da aka adana da ruwan gwal a wasu abubuwan aikinta kamar su gidan biro da akwatin takardu. Ta nuna masa kujera ya zauna sannan ta doshi teburinta. Ga mamakinsa sai ya ga ta kwashe duk wani abu da 46 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid aka rubuta sunanta ta doshi wata `yar kwaba ta watsa su ta rufe sannan ta dawo gare shi bayan ta danna wata lamba a waya. "Za ka rike min wannan ofishin daga sati me kamawa har na dawo, kafin nan na samo maka wurin aikin da ya dace" Ya ji ya rikice yana kallon fadin wurin babu kakkaftawa, wai da gaske ne ko a mafarki, ofishin Farida...ko ma dai wasa take? Bai taba raya wa kansa aiki a irin wannan wuri ba "Farida me kike nufin..." Mahaifinta wanda ya bankado kofa ya fado ofishin cikin yanayinsa na sirara masu haiba. Yau kuma da wata T shirt mai sunan kamfaninsa fara da malafa irin T. shirt din, da alamar wani abu zasu yi da ya shafi sanya wannan kaya. A masifance yake don haka har tunanin Farid ya tsayar wanda in ban da dauriya wannan mutum na ba shi tsoro. Har yanzu bai kalli inda Farid din yake ba ba kuma don bayа son kallon ba sai don abin da ya kawo shi ya shafe masa ido. "Wata matsala ce Father?" "Da kin je wadan nan mutanen dajin sun miki wani abu zaki gane me nake nufi...ba sai da nace kada ki yi komai kan mutumin nan ba ni zan dauki mataki nace ki je Burge, ina zaton kina can ashe ke kina can wurin shashanci" Ta dan yi murmushi sannan ta zagayo zuwa gabansa. Rahma AbdulMa jid 47 Matiyan Masoya "To ai ga shi na hutashshe ka Father. Na je na karar da komai da kaina, kuma gobe zan yi tafiyar, yanzu ba sai ka yi komai ba. Mutumin na karkashin kulawarmu na wakilta masu yin komai a kan lafiyarsa..." Rawar dari zuciyar Farid take yayinda kafin Farida ta gama magana idanun mahaifinta sun hau kan sa kuma sun tsaya a can. "Me wannan yake a wurinki, kada shi ya kai ki ga yin wannan wautar?" "Sam! Shi na kawo shi ne a matsayin sabon networker din ku kafin na dawo daga tafiya ta" "What! You must be out of your mind!" Ya nuna Farid da hannu. "Baki san yaro ba kawai ki kawo shi ki cе yayi min aikin ofishin dake daf da ofishina? Wannan yaron da yake jin bai da kunya kuma ina daf da koya masa ita.. shi ya aiko da takardar cewa ya san ke kika bige wani da mota kuma zai ja da ni" Ta ruko hannun mahaifin nata tana murmushi tana magana cikin sanyi. "Zai yi kunya Father, zan gargade shi, lallai na san shi, na san yana da Kwarewar da zai iya rike ofishin kafin na dawo zaka ji dadin aiki da shi ba...." Har yanzu idanunsa na kan Farid ya umarce shi da ya fice daga ofishin. Nan ne Farida tayi abin da ta saba, ta sanya ihu ta kira mahaifinta. "Father! Kada ka yi min haka...Idan bai kware ba ka sanya idanu kansa mana kana yin 48 Motiren Maseys Rahma AbdulMa jid hakan... na yi maka alkawarin Farid zai zamo irin yaran da kake so, kada ka manta digiri na na farko kafin Networking na karanta ilmin sanin dabi`ar dan adam ne. na karanta irin wadanda kake so kuma Farid na cikinsu. Abin da yayi min ba don wata gaba ce ba koda kuwa irin wadda ke tsakanin mu da talakawa ba, yayi ne don irin yanayin kekashewarsa akan gaskiya, in ba haka ba bai san ni ba bai san kaba, ji yayi ya kamata a biya hakki kuma na biya ba sai magana ta wuce ku amfani juna a abin da na san zaka bukace shi ba...." Ta yi ajiyar zuciya sannan fari da idanu. Father! Kai ne ka ce babu abin da zan nema a wurinka baka yi min ba ban da auren Ibrahim...yanzu ina neman alfarmar ka bai wa Farid dama yayi aiki da kai a nan, wannan ba wai alfarma kawai nake nema ba, yana cikin dabaruna na rabuwa da wanda kace na rabu da shi, domin idan Farid na rike da ofis dina zan yi tafiya mai nisa hankalina kwance har na manta abin da kake son na manta. Idan kana tuhumar rashin iya aikinsa sanya shi karkashin idanunka" Ta dan mannu da kirjin mahaifinta wanda da alamar ya soma saukowa. "Please father" Yana ta kikkifta ido na karaya, sannan ya dubi Farid ya nuna yatsunsa biyu ga idanunsa sannan ya mai da ga idanunsa, wato alamar ina kallon ka. 1 2 49 Matiyan Masoya Rahma AbdulMa jid "Congrat! Ka ci albarkacin 'yata, amma ka sani akwai matsanancin ido a kanka" Farida ta sunbace shi a goshi cikin godiya sannan ta dubi Farid ta yi masa barka, а lokacinda babanta ya tsala kira ga Wilson.Ya shigo cikin shiga irin wadda Farid ya tafa ganinsa da ita. Shine dogon mutumin nan mai kyan kamanni da alamar tsadar rayuwa da ya tare shi a farkon shigarsa wannan ofishi. "Sa idanunka a kansa,sabon ma`aikaci ne" Ya amsa sannan yayi hannu da Farid. Na'ibi tuni ya bar ofis din ya koma nasa. Wilson ya dan mammatsa hannunsa, sannan ya dubi Farida cikin fuskarsa din nan mai yawan murmushi. "To ranki ya dade ko za ki bar ni da shi mu dan yi musayar wasu tambayoyi" Farida ta dauki Jakarta. "Sure is all yours, ka dai bar shi ya fara aiki sati me kamawa, ni zan fita sai kuma na dawo". Ta daga masu yatsu, irin yadda turawa suke sallama, cikin murmushi ta fita. * Mahdi na zaune gefen katifa ban da kamo hannun Farid da yake yana tafawa da shi babu abin da yake sai karawa da kykyata dariya. "Abokina yanzu ka haye kenan" Ya dan yi rausaya na murna. "Mad! Wai nine nake da gida babu abin da yake bukata sai jakar kaya na. ina da mota ta gani a fada, zan dinga mallakar kudi naira dubu dari hudu a wata! Na kasa gaskatawa" 50 Matiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ya fadi da baya zuwa cikin katifar sannan ya dawo ya sami idanun Mahdi akansa yana dariya. "Gobe Mad ka fara tattara mana `yan abin da zamu yi amfani da su kafin na dawo, gobe za a bani mukulli, kawai sai mu koma jibi da safe tun da zan karbi hutun zuwa tattara daga gida" "Ni kuma a wane matsayi zan koma gidanka matar ka nake ko danka?" "A matsayin mai dafa min abinci mana ka gane ai, ko dubu hamsin nake baka da abinci ai ba laifi, mu da har aikin dubu talatin a wata mun nema mu ci gaba da dambe kan wannan katifar" Suka sake tintsirewa da dariya har da faduwa duka kan katifa. Har Mahdi ya gama ya tsaya yana kallon Farid wanda dariyarsa ta ki karewa ne saboda cakuduwarta da murna. Sai da ya lafa bayan da jikinsa ya ba shi a na kallon sa. "Me kake ji a zuciyarka kan Farida yanzu?" Farid ya dube shi da kyau sannan ya tofar da wani nunfashi. "Me kake nufi? Kada dai kana son taso da maganar soyayyar da kullun kake tuhuma ta da ita? Idan ita ce ka kwantar da hankalinka, ina murnar samin aiki ne amma ba ni da wani abu har yau kan Farida" "Ba nufi na kenan ba, watakila don hakan ce a zuciyarka shiyasa ka fassara ni. Nufina shine sanina da kai a wancan satin, Farida itace mace da ka fi tsana a duniyarka kake kyararta da yi 51 Maryan Masoya Rahma AbdulMajid mata munanan zato. Yanzu da ka ga wadan nan halaye tattare da ita yaya ka koma jin ta?" Ya tafa hannu. "Gaskiya kallo na ga Farida ya sauya, maimakon haushin ta sai na ji ina jin haushin kai na ne zalla da nayi azarbabi wurin yanke mata hukumci cikin al`adata, kamar har yau kauyancin da nake zaton ya fita dga kaina na nan daram. Farida bata da girman kai bata da munanan halayen da na zata, tana da matukar ilmi, tausayi, da saurin fahimta. Abu daya da ya ta hankalina a wancan lokaci bai wuce yadda take da mahaifinta ba da bangaje ni da ta yi. Sai dai daga baya na fahimci cewa Farida rainon turai ce zuryan da suke da wani irin `yanci kan mahaifansu da basu daukan ladabi ko rashinsa a tsakaninsu da iyayensu, haka nan fishinsu na mawadata wanda kan hada da fashe-fashe a gida watakila shi yasa ta bangaje ni ba tare da ta waiwayo ba. A yanzu wanda nake da sauran jin haushi ko tuhuma bai wuce mahaifin Farida ba. Bama haduwa tun bayan kawuwar Farida, wasu ma'aikatan sun tabbatar min da cewa baya zama dama a kasar nan sama da sati biyu a shekara, tun bayan dawowar Farida, dama ya zauna ne a Kokarinsa na shirin mayar da ita waje da yake, kuma in zata sama masa matsala ya kan zauna ya kwan biyu. Yanzu ya hana ni ofosihin da ta ba ni da cewa sai ya ga aikina na wata shida zan kuma nuna masa ko ofishinsa zan iya rikewa... amma yanzu damuwata ita ce ina Farida ta 52 Mafyan Masoya Rahma AbdulMajiр shiga? Ban sake sanya ta a ido ba tun washegarin da ta ba ni aiki, na tambaye ta lambar wayarta sai murmushi tayi ta ce min babu bukata, ina gudun kada kawai ta dauke ni aiki ne ba ta dauke ni wani na daban ba. Ban san dalili ba ina jin kamar ina son kulla amintaka da ita, amma ko ina take a halin yanzu?" 53 Mafiyan Masoya Rahma AbduiMajid Biyu Girgijen da kamar baya tafiye shine ya maye gurbin talabijin din da Farida ta mayar abin kallon ta a cikin jirgin saman da ke dauke da ita zuwa kasar Jamus maimakon Afrika ta kudu. Sai dai koda idanunta na kallon girgijen zuciyarta na cikin kuna da kadaici. J take kamar ita kadai ce a duniya cikin wannan hali da ta jima tana gudun shigarsa, kuma ga shi ya tirnike ta a cikin wannan tafiya. Dun yawon da tayi da shiga wasu lamurra da basu shafe ta ba a farkon wannan satin zuwa karshensa tayi ne don ta katse damar da zuciyarta ke da ita na tsananta tunanin Ibrahim. Ya dai sha kiran lambarta tare da yi mata sakwanni masu motsa zuciya, amma tayi nasarar kin karaya ta tanka shi har sai a yanzu da ta shiga jirgi ita kadai a kujerun da aka yi jefi-jefi domin jin dadin Bussiness class a cikin jirgin. A yanzu ta karaya matuka duk wata soyayya da ta san tana yi wa Ibrahim din da ta taba lafawa yanzu ta tashi, tana kallon kyawawan rayuwar da suka taba yi da Ibrahim din tun daga makaranta zuwa sauran sassa. "Idan muka yi aure miyar katantanwa zan dinga yi miki?" Ta kalle shi da zare ido. "Saboda me?" 54 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMalid "Saboda na lura duk wani abu da ke da alaka da ruwa kin fi son katantanwa" Ta karkata kai tana kallon sa kallon so da shauki. "Baby zamu yi aure kuwa?" "Idan bamu auri juna ba wa zamu aura Farida? Ban san ke ba in zaki iya auren wani na, amma ni dai Farida ba zan iya rayuwar aure ba sai da ke...Baby na ina son ki fiye da yadda na san soyayya... Hawaye suka ci karfin idanunta ayayinda take wannan tunani. "I love you Bally... I love you so much" a Haka take gaya wa hotonsa dake bayyane fuskarta a yayinda zuciyarta ke tafasa mai saduwa da kwakwalwa. Ta tashi ta bar wurin don kada wani ya hange ta ta koma toilet. A filin jirgin saman motar masaukinta ta iso aka dauke ta kasancewar tuni a intanet tayi hayan masauki da gida irin wanda ya dace da ita. Direban bai bar ta ba sai da ya damka ta ga masu aiki a wannan faffadan gidan na kasa. Suka dauke mata kewa ta hanyar nuna mata ko ina a gidan suka sanya mata kayanta a inda ya dace sannan suka tafi suka bar ta. Wai yanzu ita kadai ce zata rayu a nan duk da halin da zuciyarta ke ciki, zata yi rayuwar da bata san ranar da zata kare ba muddin bata san ranar da zata manta da Ibrahim ba. Ta dubi agogo, karfe tara agogon jamus ta buga har da 55 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid mintuna biyu, ta fada bayan gidanta ta face wanka da ruwa mai matukar zafi sannan tayi shigar sanyi mai matukar armashi tunda bata da zabi ban da zagaye birnin Berlin. Ta je wuraren wasanni da dama irin wadanda ta iya amma sun kasa yi mata tasiri, don haka bata da zabi illa mika wuya ga bakin ciki ta dawo gida don tayi ya ishe ta tun kafin goma da rabi ta kulla kanta. Ta sauka daga tasi ta kara rufe kanta da hular rigarta tana shirin fylfyalawa don shiga cikin gidanta kafin kankarar sanyin ta sauka a fatar kwanyarta sai ta ji an rike hannunta. Da fargaba ta dago kai ba tare da shayin kankara ba don taga wane mai karfin halin ne. suka hada ido da Ibrahim wanda yake cikin shigar sanyi amma babu kwakkwarar hula a kansa. Suka yi wa juna kur kowanne zuciyarsa na duka na dalilai mabanbanta. Farida dai dalilanta na da yawa cikin su har da wata 'yar rahusa da zuciyarta ke samu don ganin Ibrahim sannan fargabar ganin ba zata a lokaci guda sai rikicewa, yayinda shi Ibrahim din dalilinsa bayan samun sa'idar ganinta tausayi da tsoron lokacinda zai bata kafin ya samo hankalinta su ne suka addabi zuciyarsa "Am sorry" Ya ambata cikin kwallar da ta karya shirun da zuciyarsu ke ciki. "Me ya kawo ka nan?" Ta tambaya cikin sanyin murya. 56 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMalid "Na biyo ki ne... na sami labarin kin taho nan shine na zo na zauna tare da ke" Ta dan sanya karfi ta kwace hannunta daga nasa a yayinda kuka ke yi mata barazana. "Excuse me?" Ta ce masa sannan ta kama hanyar gidanta. Ya sassarfa ya sha gabanta. "Farida ki yi hakuri ki saurare ni... Na san kin yi fishi da ni saboda karya zaton ki a kaina, ina baki hakuri,amma ki sani ba yi na bane, tuggun mahaifina ne domin ya raba mu,. Na yi duk abin da kika so, amma ya koma da baya ya 6ata.Farida kin san dalilinsa nayin hakan don ya 99 raba mu ne... Ta kalle shi cikin nuna alamar gamsuwa amma ba da zancensa ba da fishinta. Ta saki ajiyar zuciya. "Idan ka gama bayaninka sai ka kama hanya, domin mahaifin ka yayi nasara, na rabu da kai kuma mun rabu" Ta shige harabar gidanta a yayinda ya sake sharowa a guje ya tokare kofar da ta so rufewa da kafa. "Farida ki yi hakuri kin san ina son ki ba zan iya rabuwa dake ba....babu mai yin nasarar raba mu... Na san zaki zo nan, amma ban biyo jirgi daya dake bane don na

Chapter 3 of 11