Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tsaya in yi shirin da in mun hadu ba zamu sake rabuwa ba" Ta dan tsaya da jin wannan kalma, sannan ta juyo ta dube shi. 57 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid "Wane shiri zaka iya yi da ba zai sake raba mu ba, matsoraci?" Ibrahim ya dauko wani tsiraitaccen zobe daga aljihun damar kwibinsa sannan ya durkusa irin al'adar turawa a gaban Farida sannan ya mika mata. "Na gama shirina na karasa sauran rayuwata dake...Farida zaki aure ni?" Kumallon son sa da fargabar kada rayuwar dake faruwa a gabanta mafarki ne ya lullube ta. Ibrahim da gaske ya shirya. Ta tsinci kanta tana dariya kamar ta gatse. "Ibrahim kai kuwa wannan na mijin ne? ka shirya mu yi aure? Ibrahim ban san ko lokacin wa an ka kenan yanzu ba, amma ni ba nawa lokacin ba kenan" Bai daga daga durkusonsa ba haka nan bai rage tsayin hannunsa ba. "Idan har kin yarda zaki aure ni to yau ba zamu kwana ba sai da auren mu. Na shirya mana duk wani abu na aure, daga madauran aure irin na addinin mu har dan karamin biki na masoya masu gudun hijira domin tsira da soyayyarsu. Kina so na Farida ki yarda ki hada zuciyarki da 'yar uwarta. Na yarda da ba hakarkarina kawai aka diba aka yi ki ba, kai har 6arin rabin zuciyata da na rasa shine 6arin da ke cikin kirjinki, Farida ki bawa zuciyar nan dama ta hade ta zamo guda kamar sauran takwarorinta. Duka abin da nake gaya miki babu د 58 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid tsari ko shiri in kin kalli idanuna zaki gansu a cikinsu da gaskiya" Ta gama narkewa da yarda, amma saura taki daya ta mika wuya. "Menene ya baka shawarar irin wannan yanke hukumci Ibrahim?" Ya kada kai. "Sati guda da nayi cikin takunkumin da kika kakaba wa alakarmu, na karu da abubuwa da dama kan martabar soyayyarmu. Farida tunda uwata ta mutu na rayu na san zan iya rayuwa babu mahaifiyata. Rashin 'yan uwa daga wurin iyayena baya sanya ni in ji ko gezau, haka nan zaman makaranta na nuna min cewa zan iya rayuwa babu mahaifina, amma zaman sati daya babu alakar ko magana dake ya nuna min cewa ba zan iya rayuwa babu ke cikin rayuwar ba. Farida ni na san abin da na ji kuma na gani... Na san yadda nake jin an daba min wuka a duk lokacinda na kira ki baki dauka ba, ba ni da sukuni. Farida ina son ki fiye da komai na, ki bai wa wannan soyayya dama ta nuna miki kanta ta hanyar yarda da aurena. Farida idan zama da iyayena na nufin dole rabuwa dake to na gama zama da babana, ban san ke na ki bangaren ba...Zaki aure ni masoyiyata?" Tuni kalmomin suka fi karfin kafar Farida inda ta sami kanta durkushe a gabansa tana kuka yadda yake yi a lokaci guda tana kokarin murmushi don fayyace dadin da take ji. Tana wani gyada kai da sauri-sauri na zaukin shauki 59 Mafiyan Masoyа Rahma AbdulMajid ta mika masa hannunta inda ya sanya mata zoben tana fadin. "Ina son ka zan aure ka Baby... Ina son ka da yawa" Ibrahim wanda ya kara gyara gashin kansa ya rage shi matuka, yana sanye da farar kwat da farin wando da bakar shet da aka dora wa farin tai ya soke hannun amaryarsa a kafada wadda ita ma ke sanye da farin kayan auren turai jim kadan bayan fitowarsu daga masallacin malamin da ya daura musu aure a sunnance, babu kowa baya da su biyu da suke shan bikinsu na zagaye gari. Bakinsu ya ki rufuwa, suna tafe suna rera wakokin amarci su biyu ko dai Ibrahim na amshi Farida na bayarwa ko kuma shi yana yi tana amshi ko suna yi tare, suna ta samin gaisuwa da taya murna daga daidaikun jama`an da kan wuce su gamu da su kuma su san me suke ciki, wasu na ganin honeymoon ne, wasu kan tausaya musu a matsayin amare marasa jama'a masu matukar son juna. Wata mata mai alamar tsufa musamman ta wuce ta basu fulawa suka yi ta godiya, suka kara kan wanda suke rike da ita. Bayan Ibrahim ya fuskanci gajiya da bacci tattare da amaryarsa a lokacinda suka kusanto gida sai ya sanya hannayensa ya kwashe ta musamman ma da kankarar dake zuba tace bisimilla ya zura a guje da ita suka shige gidan nan da kamar wadda Farida ta san zata yi 60 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid amarci a ciki ta zabi mai kyawu da tsada na kin Karawa. * Farida wadda ta bar mijinta dunkule cikin farin bargo yana bacci tana ta wake-wake da muryarta mai zaki cikin gidan wanka wanda gilasine zalla da wanda ke dakin ka iya hango zuban ruwa da dodon mai wanka a ciki. Kamar yadda mai wanka ke hasashen dakin. Ta fito daure da farin tawul da wani kato irinsa da tayi gwaggwaro wa gashin kanta, bata ga Ibrahim a kan gado ba, babu kuma duriyarsa a dakin. Tayi murmushin jin dadi da walwala sannan ta soma kiransa da "Baby where are you?" bai amsa ba amma tana jin kamshin soyesensa a kicin don haka kicin din ta dosa. Ko ina akwai na`urar zafafa wuri, watakila hakan ce ta bashi damar fitowa daga shi sai gajeren wando da farar singilet. Ta yi sanda ta je ta rungume shi ta baya a yayinda ya mai da hankali yana soya wasu abubuwa, ta kwantar da kanta cikin tsakiyar bayansa. "Bally me kake yi da sassafen nan maimakon ka kwanta ka kara hutawa?" Ya dan jingino kansa bisa nata yana dan murmushi da lumshe ido. "Me kika san ina dafa miki? In kin fadi daidai zan baki kyautar kiss guda uku" Ta lumshe ido. "Kana yi min jajjagen dodon kodi ne da 'ya'yan basil" ご 61 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ya juyo ya rungume ta da sauri. "Kin ci wallahi, ashe kina tune?" Ta lunshe idanunta. "Biya ni goro na kawai". Ya sanya bakinsa a nata shima bayan ya lumshe idanunsa ya sunbace ta na tsayin lokaci inda nunfashinta ne kawai ya ke musu jagora. Ya janye bakinsa a hankali kamar ba don yana so ba, ya tsayar da idanunsa kan nata yana kiftawa da sauri irin na mai karaya. "Farida daren mu na jiya tare shine dare mara takwara da na taba yi a rayuwata kuma ina jin ba zan sake kamarsa ba" Ta rike tsinin karshe na hancinsa. "Zamu maimaita shi duk iya tsayin rayuwarmu Bally" "rayuwa dake Farida iyakar aljannata kenan, ina ciki wani yanayi da bana jin wani ma'auraci ya san da shi..Farida ina jin dadi, kin san me haka ke nufi, makwanci na dake daya, jikinmu daya, kicin din mu daya, toilet din mu daya komai namu daya, a yayin da a da ina zaton ko muryarki na ji a waya karshen dadin duniya kenan" Ta manna kanta a kirjinsa. "Na dade da hango hakan shi yasa ka ji na sallama zan rabu da kowa da komai don na kasancc tare da kai" Ya ciro kanta ya sake tura bakinsa cikin nata ta amsa masa na zirin lokaci, sannan a wannan lokaci ita ce ta zare bakinta ta zura masa ido. Matiyan Masoya Rahma AbdulMajid "Kayi alkawari duk rintsi duk tsanani zaka rayu da ni ba zaka rabu da ni ba?" Ya ruko fuskarta cikin manyan tafukan hannayensa. "Farida ina son ki ina son ki da matukar yawa, ina son ki fiye da dukkan rayuwa, ba wai alkawari kawai nake ba, ba zan iya rabuwa dake ba ne muddin ba zan iya rabuwa da raina ba. Kc ce ya rage ki yi min alkawari, amma ni na gama yanke wa kai na hukumci. Dake zan rayu iya rayuwarmu Farida" "Baby ba zan rabu da kai ba, ba zan taba iya rabuwa da kai ba, kai ne rayuwar da nake jin zan iya yi zan iya bayar da duk wani abina domin na same ta" Ya sake matso da bakinsa zuwa nata amma ta tare shi da yatsa. "Ban da dodonkodi na kada ya kone" A guje ya juya da yake ya ji kamshin ya soma sauyawa. Ya jujjuya sannan ya dauko abin kwashewa. Farida ta soma kokarin taya shi, amma ya ruko hannayenta biyu ya tura su kirjinta. "A`a! ni a doka ta amarya ta bata aiki har sai ta ce na gaji da hutawa bayan a kalla kwana uku sai mu zo mu fara tare, amma yanzu har gado abinci zai dinga bin ta" Ya sure ta a guje ya mayar da ita daki ya ajiye ta kan gado. "kada warin abinci ya bata min wankan ki, zauna ki caba min kwalliya, kin ji?" A R D こ 63 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ya surħbaci goshinta sannan ya fice da sauri daga dakin. Ta nutse cikin bargon tana more wani dadi da zuciyarta ke ciki, dama ashe haka aure yake, auren ma na masoyi? Bata taba jin abin da take ji ba kamar yau, duk wani nauyi dake kanta da damuwa ji take sayau ta sauke shi, ga mamakinta sai ta ji bata tuna matsalolinta na cikin gida, hasalima ta mance da barazanar mahaifinta. * Cikin wata daya Farid ya sauya ya zamo babban mutum. Tunanin sa ya sauya daga na daki daya zuwa na tunanin gina kansa. Yana zaune yanzu a gidan kasa mai daki biyu kowanne da bayan gida, da falo mai dauke da wani loko da ya ketara zuwa kicin da wani karamin falo na cin abinci, sai toilet na bakin falo da cikinsa babu abin da ya wuce wurin wanke hannu da kaskon tsuguno da ma`ajiyar sabulu. Dukan gidan babu inda ba a yi masa shirin da ya dace da shi ba. Tun daga falonsa da aka yi wa haden fari da bulu, dimadiman kujerunsa masu matasan tada kai bulalene masu ratsin fari kamar labulen da aka sanya a falon. Haka dardumar falon ita ma fari da bulune aka zana katon gida a jikinta da shi, akwai kayan kallo isassu duka a jikin bango a rataye kama daga talabijin din har manyan sifikun yada sauti, sai iya kwandishan katuwa dake zaune da Kafarta, haka dakuna suke da kicin kowanne 64 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid gyaransa mai tsada da kyau da tsari. A waje kuwa akwai inda yake ajiye motoci guda biyu, wato Honda Accord 2008 model wadda take tasa da Toyota Camry ta Mahdi wanda shi ma yana tare da Farid a wannan gida bayan da shi ma ya sami aiki da kamfanin sadarwa na Zain. Suna zaune a gidansu cikin kwanciyar hankali har sun fara aiwatar da abubuwanda da suke son yi a rayuwa. Domin a yayinda Mahdi ya gabatar da shirin aurensa har aka sanya shekara mai kamawa, shi kuwa Farid ya kasa nuna ko da kulawa ga kowace irin mace, ba kuwa domin komai ba sai don yadda ya fara fayyace matsayin Farida a zuciyarsa. Babu yadda za a yi ya ci gaba da cewa ba son Farida yake ba, ya damu da ita ta inda baya iya mantawa da ita a duk tsayin kowace rana, ya damu da rashin ganin ta da rashin jin ta. Ya dai dade da fahimta ko a ofishinsu babu wanda yake da hurumin tambayar ina Farida take don haka ya dena tambaya koda kuwa ba wai ya san inda take ba. Tun washegarin mika masa aiki da ya gan ta. Ya damu matuka yana kewar Farida komai yake yi kokari kawai yake, amma bisa gaskiya yana son ganin Faridar a gabansa, baya ganin ko wace mace ta kai ya Faridar ballantana ta fi ta, bai san lokacinda ya dena ganin bambancin asali da dukiya tsakaninsu da Faridar ba domin ba kokwanto yake ko soyayya tsakaninsu zai yi wu fata yake ta yiwu. Ya dauki Kalmar da Faridar ta taba fadi gaban babanta na cewa ba L R = 65 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid shi aiki zai taimaka ta manta da Ibrahim a matsayin ruwan dafa kansa, domin a tafsirinsa karara wannan kalma na nufin soyayyar Faridar ne gare shi, sannan a sharhinsa mutane irin Faridar masu jin tausayi da fahimtar dan adam da kololuwar wayewa basa iya daukan bambancin arziki a matsayin hujjar çancanta kamar yadda suke girmama kwakwalwa mai nunfashi wadda baya shakkar yana da ita, don haka ne ya zage damtse yake aiki da jini da tsokar kwakwalwarsa don ya ga albarkacinta kamfanin Na`ibi ya sami wata ciccibą da bai taba samu ba. Kuma lallai ya kai ga nasara domin taswirar da ya gabatar a kan yadda za a inganta samar da wutar lantarkin kasar Liberia wadda yaki yayi wa ninkaya ita ce ta sanya kamfaninsu ya doke na mutane irinsu AbdulHadi wurin samun dillancin samar da kamfanin wutan da zai ja ragamar aikin na kasar China, abin da ba a taba samun kamarsa wurin daga farincikin Na`ibi Bici duk fadin shekarar nan ba, domin ba kawai nasarar samun wannan kwangilar dillanci ba, samun kayar da Abdul Hadi wanda yake gadajjen abokin gasarsa wanda shi ma yayi ta barin kudi don samun wannan kwangila don ko ba komai ya doke abokin hamayyarsa amma suka samu suka kayar da shi cikin ruwan sanyi. Hakan ta sanya Na` ibi cikin farin ciki ya zaro mukullin sabuwar jeep din Highlanda ya mika wa Farid tare da kyautar kudi Naira milyan biyu. Kyautar da ta dada 66 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid shigo da Farid din taro wanda tuni ya kusa hattama gidansa da yake son ya sanya mahaifinsa ya zauna ciki kafin yayi aure. A yanzu yana jinsa matashin mai kudi da tsari da ilmi da babu wadda ta fi karfinsa muddin ajin su Farida ce. Abin da ya hana shi iya zamowa na hannun daman Na`ibi fiye da Wilson kamar yadda yake fata shine kekashe kasar da yayi na cewa shi fa ba zai yi wasu aiyuka da suka haramta a dokar neman kasuwa wai kawai don ya kasa wanı a kasuwa ba, don haka iyakarsa ga Na'ibi shine aikin da kwalkwalwarsa ke iya yi wa kamfani musamman da kamfanin AbdulHadi suka soma zawarcinsa ta hanyar kara masa albashi domin su same shi. こ 67 Mafiyan Masoya Rahma Abdul Majid Uku Na'ibi Bici wanda ke sanye da irin shigar da aka san shi da ita, wato riga shet da wando ya dora kafa daya bisa daya yana shan lemo a daya daga kujerun ganawa da baki na gidan ministan makamashi wanda suke 'yan asalin kauye daya sai tafawa suke suna dariya a duk hirar da suka yi don jin dadin nasara. Wannan ziyara ta zo ne a dalilin kawo kason ministan da Na`ibi yayi kan ruwa da tsakin da yayi na sama musu wannan kwangila. Ministan wanda yake sanye da doguwar riga fara sol mara hannu ta shan iska ya zauna rike da wani dan littafi yana dubawa yayi magana kafin ya dago kai. "Haba Munir! Ai ba sai ka yi wani abu na a zo- a gani ba ni ma ina da irin tawa bukatar" Sannan ya dago ya dube shi. "Da me zaka fi Hadi da zan damu in taimake ka in bar shi? Dukan mu fa abokai ne kuma 'yan kauye daya kai ma ka san dole ni ma akwai tawa alfarmar" Na`ibi ya ajiye kofinsa sannan ya daga kai sama. "Месе се bukatar Honarabul minister?" Bai amsa masa ba a lokacinda wani saurayi ya fito. Yana sanyc da rigar bulun yadin dinkin shan iska wando iya gwiwa haka rigar ma mai 68 Mafiyan Masoy я Rahma AbdulMajid hannu iya gwiwa. Duk da wankan tarwada ne amma gashin kansa kwance yake duk da ya aske mafi yawa, fuskarsa na da matukar kyau da alamar hutawa kamar sauran sassan jikinsa. Yana da yanayi na masu satkin kai musamman yadda ya rusuna ya gaida Na`ibi sannan ya dubi mahaifinsa ‘na`am baba?" "Ka san ko wanene wannan?" In ji minister wanda ya nuna Na`ibi. Yaron yayi murmushi sannan ya kada kai. "Ban san shi ba popsie" "Wannan shi ne ya haifi Farida" Kallon razana sannan fuskar farin ciki ta bayyana da fararen hakora sannan ya sake rusunawa ya kara gaida Na`ibi wanda shi dai nasa amsawa. Minister ya dawo ga Na`ibi bayan da ya dafa dansa wanda a yanzu ya karaso kusa da shi. "Na`ibi wannan shi ne dana Abdul Azeez. Dan daa haifa daya kenan da matata marigayiya Daliya 'yar kasar Moroco wadda ta rasa ranta a fashewar jirgi a Locarbie. Ni na raini abi na don Allah ya jarrabe ni da son sa yadda Ya jarrabe shi da son `yarka Farida. Вa don son kai ba da gaske ina gaya maka ya fi kowace zuri`ata nutsuwa, ya tsaya yayi karatu don likita ne, duk wata hatsaniyar duniya bata dame shi ba, mata ko shaye-shaye ko rashin da a duk kuwa da shagwaßa shi da nayi. Bana so ya taba rasa abin da yake so domin bai tabа son abin banza ba, cikin abubuwa masu nagarta 4 2 69 Mafiyan Masoy a Rahma AbdulMajid da ya taba so a duniya har da 'yarka Farida. Bai san ka ba bai san ta ba. Jaridar Ovation ne ya ga hoton ta ranar bikin fitarsu daga jami'a shi kenan ya kasa sukuni ban da na Farida. Da yak baya boye min komai sai ya gaya min abin a ke damun sa kuma nayi alkawarin ya sa ransa a inuwa zan nemo masa ita. Gaskiyar lamari saboda shine na neme ka har muka yi abokanta kuma nake damuwa da faranta maka rai. Fatana kuma fatansa ka hada shi da Farida" Na'ibi ya mike cikin mamaki inda ya fadi wata kalma cikin turanci wato 'this is material!' "wannan yaron danka ne?Abdul Azeez kana son 'yata Farida?" Ya sunkuyar da kai cikin kunya yayi dariya. "kai ne irin sinadaran da nake so 'yata ta so 1 kuma na samu" Ya kamo hannunsa don su fita. Zo nan fana, zo nan...wannan kyakkyawan saurayi. Zo mu je mu yi magana irin na maza" A filin kwallon Kwando da ke gidan suka tsaya suna fuskantar juna inda Na`ibi ya soke hannaye a wando ya ke tambaya. "Gaya min gaskiya wane irin so kake yi wa Farida Abdul Azecz?" Ya karkata kai irin na me matukar jin abin da yake fada. "I love her dearly! Idan har zan hadu da ita ta so ni mu fahimci juna tuni zan soma tunanin 20 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Karashe sauran ranakun rayuwata da ita. Ina son ta shine gaskiyar lamari baba" Cikin wata annishuwa da ba ko yaushe Na`ibi yake yi ba, ya sake dora hannu a kan kafadarsa suka fara tafiya. "ina mai tabbatar maka Farida zata so ka domin irinku take so... zan baka wata satar amsa da zata isar da kai ga Farida har cikin zuciyarta. A yanzu tana Berlin kuma tana fama da kadaici bayan rabuwarta da wanda ta so kuma suke son su yi amfani da ita wurin karya ni. A yanzu zuciyar Farida ta koma budurwa babu kowa ciki, zaka iya hanzartawa ka shiga ciki" "Ta yaya zan shiga ciki? Na je Berlin na same ta... zan iya zuwa yaushe?" Ya Ambato zantukan cikin zumudi irin na wanda ciwon so ke gararamba a zuciyarsa. Na`ibi ya kama hannunsa ya tafa da shi. "that's my boy. Haka nake so... ka isa Berlin ko gobe ne, zan fara shigar da kai in mun yi magana yau. Ka yi ta maza ka shige ta ku saba zata so ka na san `yata" Suka sake tafawa yace 'mu koma wurin mahaifinka mu ba shi albishir'. Suka koma ciki hannun Na`ibi na kafadar yaron nan wanda ya kasa sakewa da ka gan shi ka ga rainon bature amma mai ladabi. Farida zaune kan gado Ibrahim na kwance kansa bisa cinyoyinta tana wasa da yatsun hannunsa na dama suna hira cikin raďa kamar 71 Mafiyan Masoya Rahma Abdul Majid akwai wani a gidan bayansu. Wayar ta tayi kara ta duba lambar sannan ta yi masa alama da ya toshe baki wato babanta ne. ya toshe baki. Haka suke yi wa junansu duk lokacinda mahaifin daya ya bugo. "yaya Farida yau tun safe ba ki neme ni ba ko teďt?" Ta dan bata rai. "ina dan ciwon kai ne Father" "Ina ga ya kamata na zo na gan ki ko....?" Ta katse shi da sauri. "No father, ina so na zauna da kai na ni kadai har sai na huce "Sai kin huce me?" Ta dora hannunta kan fuskar Ibrahim tana dariya. "har sai na huce na mance da Ibrahim" Ko a muryarsa zaka iya jin sa'ida a yayinda suke tintsira masa dariya. "Haka ne `yata kina da gaskiya ko ni zan so kada ki shigo sai zuciyarki ta zamo ko haduwa tayi da Ibrahim ba zata ji komai ba, amma ina kewar ki, ina son ganinki, mamanki ma haka tace tana so mu zo nan mu hadu tare" "Father ka bari duk zan gaya muku lokacinda nake son mu hadu, ina kewar ka father, but na fi so na daure na gama wannan zaman ina samin nasara a haka" "Shi kenan ba komai. Amma akwai wani yaro da zan so ku hadu, wannan bana so kiyi min musu, dole zaki iya haduwa da shi matashi 72 Mafiyan Masoy a Rahma AbdulMajid ne kamar ki da zaki iya raba bakin cikin ki da shi, ku zauna ku yi hira ku fita tare....In gaya miki gaskiya, yana son ki son da bana jin wani ya taba yi miki. Sunan shi abdulAzcez dan ministan makamashin Najeriya Lukman Nura. Yana da duk siffar da `yar Na'ibi zata iya son shi, sai dai ba zan miki dole ba, kina bukatar ki gan shi tukuna ku daidaita... in kin so shi zan yi farin ciki, amma ki gan shi tukuna, gobe ina so ki je ki taro shi da yamma" "Amma father..." "ban ce kiyi min musu ba, kawai ganinsa zaki yi in bai yi miki ba ai ba dole ko?" "To father" Suka Karasa hira jikinta a sanyaye har ta ajiye wayar. Ibrahim ya taso ya rike ta "Lafiya na ga kin sauya? Yana zuwa ne?" Ta kada kai. "Father ba zai kyale ni nayi rayuwata ba... Wai wani Abdul Azeez dan ministan makamashi yana so na, ina ga shi yace da gayen ya zo nan ya takura min, don yace yana zuwa na je na dauko shi a airport, mu fita tare, mu zauna tare har na ji ko zan iya son sa mu fahimci juna" Ibrahim yayi shiru yana kallon kasa har na wani lokaci zuciyarsa na so tayi abin da ta saba na neman yin abin da ya dace. "Yaushe kika ce zai zo?" "Gobe zai zo Ya mike tsaye. A ا 73 Mafiyan Masova Rahma AbdulMajid "Kenan ya kamata na dan bace daga gidan nan muna magana a waya har ya tafi don kada ya gan ni" Da kanta na wani gefe ne, amma yadda take juyo da shi don ta kalli Ibrahim na nuna wata fusata da bata taba yi ba tunda suka yi aure, wani tiriri na so ya kona zuciyarta. "Me na ji ka cc?" Ya dada kwantar da murya "Wai da ina so ne na dan boye har ya tafi don kada.." "Ibrahim! Har yau kana shirin 6oye aure na da kai kamar wadda kake kyara Ta mike tsaye a kan gadon "Me kake nufi? Kana nufin ko yaushe ba zaka taba zamowa na miji ba. Har a fagen daga ba zaka yarda ni matarka bace. Ibrahim kana so na kuwa? Wane irin..." Kuka ya kwace mata ta fice daga dakin da gudu. Ibrahim yayi jifa da bargon da yaké kan sa ya tashi yana kiran ta amma bata amsa shi ba. Ya iso kicin inda ta juya ta jingina kanta da bango tana girgiza. Bai karaso kusa da ita ba ya tsaya a rikice a galabaice. "baby please, ba ina nufin abin da kika zata bane... na san bakya shakkar ina son ki fishi ne kawai amma... Ta juyo a fusace. "Ka rabu da ni kawai Bally. Ka rika ka nuna min ko wancne kai, nayi kuskure, ina son auren na miji ne mai tunani irin na maza ba mace 74yan Wasoya Rahma AbdulMajid kamata ba... tsoro ne ya sanya har yau iyayenmu ke zaton zasu iya raba soyayyarmu duk da goyon `yancin da suka yi mana". Duk abin da take cewa Ibrahim kara kusanto ta yake yana kada kai. "Bana jin tsoron kowa sai na Allah sai na Gacin ran masoyiyata. Farida bana son nayi abin da zai tayar da hankalin mu a wannan lokacinda ya fi kowane lokaci dadi cikin rayuwarmu. Farida mahaifinki ko mahaifina ina jin zasu iya jin sassaucin kiyayyarsu'ga auren mu da za a се muna da iyali, yau in Allah Ya azurta mu da haihuwa ko don saboda wannan jika nasu zasu ji suna kaunar mu da kaunar abin da muka basu.ki tuna basu da yawan 'ya'ya duk da suna so. Shi yasa ni a so na mu hakura mu boye auren mu har sai mun sami arzikin haihuwa sannan mu fito musu da gaskiya, amma in fitowata yanzu zata faranta miki rai ki kara yarda da ina shirin sadaukar da rayuwata kan soyayyarki zan fito ko yanzun nan" Ta juyo kamar da alamar ta sami sassauci a zuciyarta idanunta kan Ibrahim. "Kana shirin zama Daddy Bally?" Shi ma idanunsa a kanta cikin tausayawa. "Ina shirin zamowa Daddy na 'ya'ya ko nawa ne muddin zasu zamo 'ya'yan Farida ta" Ya kamo hannunta ya zuba kan kirjinsa. "Farida ina son 'ya'yana ina son mu sami zuri'a, ina son in zamo Daddy cikin gaggawa, ko ba don su Father da popsie ba ina son na ga 75 Mafiyan Masoya Rahma Abdul.Majid abin da Allah zai bamu a matsayin arzikin soyayyata ni da Farida. Please Farida let me have a child with you" Ta fada jikinsa ta rungume shi kamar zata cakuda namansu wuri guda. "Mu je mu samo guda ne?" Ta gyada kai. Ya ciro ta daga jikinsa yana duban ta. "Kin shirya?" "Ina shirye kuma ina kan layin masu iya samu a yau" Ya sure ta da sauri. "Bari mu gani" Ta rataye hannayenta a wuyansatna dariya suka koma daki. Da yammacin washe gari Farida ta sanya wandon jeanse bulu shar sannan ta sanya wata farar shimi mai kauri ta dora shet ja mai dogon hannu sannan ta sanya wani takalmi shoe mai fari wata `yar jaka kamar ta sanya waya fara wadda ta rataya ta tun daga kafadar hagu zuwa kugun dama. Ta bayyana a matattakalar da ke hada gilasin da falon su inda lbrahim ke tsaye yana kokarin kunna talabijin. "Na shirya". Tace a yayinda ta fan jingina da bangon tana hango shi. Ya juyo ya kale ta sama da kasa sannan yayi dariya. "Kin yi kyau amaryata" 76 Mafivan Masoya Rahma AbdulMajid Ta juya zata koma daki a fusace kamar yadda ta fito a fusacе. "Ina kuma za-ki?" Ya tambaya a rikice don ya san halin futsuwar amaryar tasa. "Zan je na sauya, don ba cewa na yi ma in yi kyau ya gani ba Ya kamo ta da sauri ya dawo da ita. SO "sam! Ba nufi na kènan ba. Ko wane lokaci kyau kike min, gara ki je ki yi musu ya kwala mana.Farida bana shakkar ki ba zaki taba yin shirin da ba zai miki kyau ba ko da ganye zaki daura, ni kawai Allah Yayi min sa`a ne kike so na amma da aure sai kin yi shela kafin ki zaбa. Zo ki je ki dauke shi, ki kai shi masauki, sannan ki dawowa masoyin ki mai jiran ki" Ta sunbace shi na al`ada ba don ana cikin farin ciki ba domin bata son fitar narr da ba don ya matsa ta ba. A wajen harabar filin jirgi take tsaye bata san kamanninsa ba bata kuma san koda sunansa ba domin har ta

Chapter 4 of 11