Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
domin manufarsu ta soyayya ta fi tamu ta kiyayya... Farida ta kubuce min kamar yadda Ibrahim ya kubuce maka, sun gane duk makircin da muka shirya musu kuma a halin yanzu suna tare da junansu a matsayin ma`aura babu abin da nake jin zamu sake iyawa in ba zamu kai lamarin ga abin da be kai ba wato tsine musu da cire su daga sunayenmu. Kafin mu kai haka nake son mu dawo bic. Mun yi nisa da yawa ya isa haka ya kamata mu dawo..." Ya sake mikewa tsaye ya fuskance shi da natsuwa amma babu murmushi. "Na yarda wukata....... ina so kai ma ka yar da taka mu bar wannan gaba mu sake kulla zaman lafiya a karo na biyu kuma a matsayin surikan juna ko ba don farin cikinmu ba don farin cikin 'ya'yanmu. Ga hannuna" .........ya kura masa ido cikin tafasa bai kalli ko inda ya miko hannunsa ba ballantana ya mika nasa. "Kana tune da cewa ka kai matsayin neman ran 'yata Farida" "Ka yafe min an sami babban kuskure a nan...Farida ta yafe min" Ya kada kai.. "Ba zan sake sanya hannu a hannunka ba Andul Hadi ka janye duk makircinka" 170 Mafiyan Mas ya Rahma AbdulMajid "Comon! Daurewa za ka yi...ni ma ba wai don bana jin haushin ka ba ne, amma na daure don hakan ya fi alheri..." Ya jima da hannunsa tsaye, amma da ya ga babu niya daga Na'ibi na sanya hannu sai ya janye yayi murmushi. "Farida ta auri Ibrahim cikin sunnar ma`aiki har suna shirin samun karuwa. Ina sake rokon dama a wurinka na ka yardar mana da ita a matsayin matar dana, kuma zan yi kokari na ga mun zo wurin ka ni da shi don yin baiko a al'adance....zan ba ka lokaci kayi tunani idan har ka huce sai ka gaya min waya na zo na same ka" "Ka san ina Farida take?"" Naibi ya kawar da amsar wancan dogon zance. "Tana tare da mijinta ai...kana son ganin ta ne?" "Ka ce ta zo ta gan ni ina da magana da ita ta Karshe kafin na ba ka amsar bukatarka" "Za a yi haka na gode.... Amma ka daure ka yi tunani, na biya wajibi na na sauke nauyina...mu ne yau ba mu ne gobe ba.... ya`yanmu ba na`urori ne da za mu ci gaba da tsara su ba... na bar ka lafiya" Yana ficewa daga falon ya dauko wayarsa ya latsa lambobin Wilson. "Hello Wilson meet me at home now'" i Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid AbdulHadi na bayan motarsa yana murmushi yana kada kai ya ciro wayarsa ya latsa lambobin Farida. "Na`ibi ba zai sauya ba" Ya ambata kafin ya kara wayar a kunnensa. Can ta dauka. "Farida mahaifinki na son ganin ki...Eh...to ya ce ba shi da magana da ni har sai ya gan ki...ki daure ki je yau don na san mutumina yana da taurin kai wani lokaci wani lokacin kuma yana da saurin sallamawa. Watakila idan ya gan ki ku sasanta in kun gama na ji yadda kuka yi, amma ki daure ki je ki same shi yanzu...shike nan, ba ni mijin naki...Bala...to yaya kuke?...ka lallashi matarka ta je ta ga mahaifinta, na san ba zai iya sauya ta ba idan ya yi magana da ita karshe zai sallana, amma a halin yanzu bai bar kofar wata tattaunawa tsakanin mu ba..: to shi ke nan"" * Wilson ya karkata kai yayi murmushi ya sosa kasumbar da ta dame shi da kaikayi. "Ranka ya dade za ni in yi aski....idan ita Anti Farida ta zo ta kuma dage a kan tana son ka amince da auren, ka amince mata ka kuma a gayyaci angwayen. Za mu koya musu darasi na har abada tunda in an bar su zasu yi taurin kai ne suma har abada" Na'ibi ya kashe tabarsa ya juya kujera. "Je ka yi askinka, amma ka sani bana son kuskure domin ba zan taba amincewa har ga zuciyata da auren kasada ga dukiyata da sunana da Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Farida ke so ba, tunda kuwa Hadi ya shigo wasan gadan-gadan ina son mu yi bugun karshe" "Ka taba kama kuskure a kowane kudirina ranka ya dade? Ballantana a damar karshe?"" Shigowar Farida da karfi ya karar da maganar inda duk suka zuba mata idanu. Tana rike da hannun kofar yayinda babu walwala ko gaisuwa ta ce 'ga ni Dady' Wilson ya yi tari ya rusuna ya gaishe ta babu murya sannan ya juya ya fita a kaikace kasancewar bata bar jikin kofar ba sai da ya bar falon sannan ta karaso ciki ta mayar da kofar Ta sunkuyar da kai tana tsaye a gaban sa gab da gab yanzu "Ga ni Father" "Sannu da zuwa, sami kujera ki zauna maganar mu ta karshe се" Ta ko amsa umarninsa ta zauna, sannan ta dago idanu don sauraro. Ya nisa ya miko hannu ya dauki wata 'yar takarda don kawai yayi wasa da ita lokacin magana, sannan ya fara. "Kin gudu Farida zuwa wurin wasu wanda kika san ban so duk kuwa da barazanar da suka yi wa rayuwar ki baki daddara ba kika bar ni ni me fafutukar kare lafiyar ki a matsayin uba.... Sai dai ba wannan ne ya dame ni ba, hasalima ina son in sanar dake cewa lallai ina mai ba ki hakurin abubuwan da na sakaye miki lokacin da ba ki da lafiya. Wannan ya biyo bayan dabaru na kare lafiyar taki ne ba cutar dake ba, amma ir baki ji dadi ba ina mai baki hakuri kan hakan....tambayoyina ba su da yawa guda ne uku 173 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid kuma ina so ki ba ni amsa tunda ga kwalkolin zuciyarki kuma a sanin cewa karo na karshe ne tambaya ta farko ita ce kina da masaniya cewa A. Hadi ya zo nan kuma ya nemi in ba ki damar auren dansa. Kuma kina jin dadin haka?" Ta dago tana ci gaba da wasa da yatsunta. "Yes father" "Fine! Tambaya ta biyu....duk da neman salwantar da ranki da alaka da iyalin A.Hdi suka kusan yi wanda ya nuna miki manufarsu akan komai kin sake amincewa da auren Ibrahim a karo na biyu kuma zaki zauna da wannan barazana?"" A nan ma ta sake dagowa. "Father Bally ba shi da hannu kan abin da ya faru kuma ka sani har rabuwa yayi da mahaifinsa kacokam domin wannan lamari.... kamar yadda kace kai ka boye min gaskiyar hakan bayan na so in sani.... Ke nan ba shi da wata barazana gare ni muna son juna zamu zauna da juna'"" "Tambaya ta karshe..." Yanzu cike fuskarsa take da karin walwala da murmushi. "Kun san cewa ni da A. Hadi ba za mu taбa zamowa surukan arziki ba haka nan ba za mu zamo kakannin arziki ba ga zuriyar ku amma kuke shirin dauko wannan alaka don kanku ba kwa duba zuriyarku?"" "Father... kun taba zamo wa abokan arziki kai da A. Hadi kuma bai bawa duniya mamaki zamowar ku makiya ba... ke nan sake zamowar ku masoya nan gaba saboda mu abu ne me yiwuwa ba kuma wani mamaki ko haramci ga 174 Monyan Masoya Rahma AbdulMajid bakan.... zamu yi iya kokarin mu don ganin hakan ta sake faruwa a dalilin aurenmu.... wani Karin haske akan ko mun so kanmu ina jin ba ka nufin wannan magana da kyau.. domin a saboda Kiyayya kun taba mantawa kuma da bukarun ya`yanku na soyayya kuka je ko wane nisa wajen neman rabuwarmu... ina jin don mun fauwala rayuwar soyayya kan kiyayyarku kuma mun koya wa 'ya`yanmu baya nufin son kai in har na ku bai nufi son kai ba.... ka duba father in dai ga zuri`ar da zamu samar ne, ku kakanni ne baku son juna, mu ko iyaye ne muna son juna. Duk da tambayoyi uku ka ce zaka yi min ke nan kamar ka gama father, ina so in tabbatar maka da cewa mun shirya rungumar koamai ba ma tambaya kawai ba don mu zauna da junan mu cikin soyayya ni da Bally...please I want you to bless that father" Ya nisa sannan ya katange dawowar nunfashinsa da murmushi ya kuma kra mata ido. "That's my girl... ki cewa A.Hadi da Ibrahim ina son ganinsu tare gobe da misalin karfe bakwai na yamma don su nemi aurenki a wurina... zan kuma shirya musu liyafa irin wadda ta dace da surukai na" Ta zaburo ta kuma zaro ido amma ya tare ta da tagumi cikin yalwar murmushi. "Kada ki damu in har sun iya zuwa gidana me zai hana in ba su 'yata zan bayar dake Farida" Ta rungume shi da murna har da hawaye ya amshe ta yana dariya 'kada ki damu `yata ki je ki gayyato su kada ki yi latti, ok?" A i 175 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Da zumudi ta sake shi za ta zaro waya amma ya katse ta "Um-um! Not on phone... ki je har inda masoyi kuma mijinki yake ki yi bikin wannan farin cikrda shi kin ji?"" "Haka ne father sai na dawo..." Ta sumbace shi sannan ta ya yi Jakarta ta fice daga wannan majalisa. Ta dauki kamar mintuna uku da fita kafin ya dawo da yanayinsa na bacin rai kan fuskarsa a yayinda ya latsa lambar Wilson. "Yaya aka yi me gidana?" "Ta amince da daukan duk tsautsayin da auren ta zai janyo...ke nan za ta amince da daukan tsautsayin abin da zan yi...bayar da karatun karshe"" "An gama oga na karfe nawa?"" "Karfe bakwai na yamma'"" "Allah Ya ba ka sa`a me gidana" * Har ya shigo ba ta sauke kafarta daya dake kan daya ba, tana ci gaba yiwa faracen hannunta gyara, ko dagawa ta kalle shi ba ta yi ba. "Kai na zo a sa`a...wannnaan kwalliyar tawa ce ko ta me gidana ko ta aikin da na zo miki da shi?"" Har yanzu ba ta dago ta kalle shi ba. "Na taбa kwalliya saboda kai ne Wilson? Kada ka dinga bata min kasuwa mana" "Amma da kin san kasuwar da na kawo miki bana zaki yi kwalliya saboda ni Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ta dan kalle shi bayan ta tsayar da wukar feke farcen kan babban yatsarta. "Bana kuma me kake tafe da shi" "Bonanza! Yes it's a Bonanza....kudi Cash zunzuruyun dala dubu dari daya. Hutu na wata shida a Hawaii da duk wani jakuzziy da kike so. Uwa uba saurayin da kike so ki karba da duk dukiyarki ga shi kyauta manne da kafadar ki wato Ibrahim A. Hadi" Ta fashe da dariya sannan ta koma gyaran akaifarta. "Wa zan kashe bana wa zan raya da zan sami irin wannan gàrabasar?"" Ya matso kusa da ita yana rada cikin zakuwa da neman amincewa "Shi yasa nace miki garabasa... domin babu wanda zaki kashe illa gobe da yamma bayan Ibrahi ya farfado ki nemi ganinsa a asibiti ki tsara masa cewa abin da ya same shi shi da mahaifinsa shirine na Farida bayan ta gana da mahaifinta ya gamsar da ita. Ke sai ki zare da saurayinki ki bar mu da yakin mu da Farida" A firgice ta tambe shi tambayar da ta dame ta. "Ibrahim ba shi da lafiya ne?" "Aa! Lafiyarsa kalau yanzu, zai dai sami rashin lafiyar ne yau kafin bakwai na yamma" "Zaku kashe dan mutane? Wilson kada ma ka gwada haka" "Idan zan kashe shi ne ina za ki same shi gobe ku tattauna Allah Ya raba mu da kisa, kawai dai so muke mu ba ki Bally na Farida mu mu samu sa'ida. Ke ce dai in ba ki amshi aikin mu ba kin yi N 177 Mafiyan Masaya Rahma AbdulMajid shi a kan kari kuma a tsare irin tsarin da aka san ki da shi ba zan iya kare ranki daga tsautsayin hakan ba. Domin wannan ogana ke kira aikin karshe... kin kuma san duk aikin karshe kan sami ة tsautsayi Ta sauke kafar ta janyo hannunsa zuwa kan cinyoyinta dake bude tun da dadewa. "Bai kamata in musa ka ba don ba ka taba kawo min kasuwar da babu riba ba. Zo na fara ba ka Alakoro kafin na cika maka aiki...ko na ce mu yi sallama da kai don inna sami Bally ko me gidanka bana jin zan šsake sani" Wando baki da shet mai ruwan toka da farin tai ya gama sanyyawa sanman ya tsaya shafe shafe a gbana madubi cikin zumudi da wake-wake. Mahaifinsa wanda ke sanye da shadda da wando farare masu dibar ido kuma da alamar ya gama kintsawa ya zo ta bayansa dauke da kwat din wadon jikinsa ya mika masa. "Ya isa kwalliyar Ballin Farida ai ka ishe ta haka ka sanya rigarkau tafi kada mu yi latti. "Ka tabbatar na kdu a ango Pop?"" Suna fuskant juna a yanzu cikin murmushi da kallon Kauna. "Ka hadu na A. Hadi da Farida mu je kada mu yi latti". Ya karbi kwat din ya sanya sannan suka baro dakin. Har zasu sanya kafa wajen babban falen amma sai mahaifinsa ya tsayar da shi da hannu. Mafiyan Masoya Rahma AbdulMalid "Ba ka yi rokonka na karshe ba... za mu fita neman babban sa`a ka san yaya za mu dawo?" Ya daga hannu sama cikin dariya. "Allah ina rokon shigo wa gidan nan da Farida babu shamaki a wannan karon ya zamo in zan dawo kafata kafar matata" Abdul Hadi yayi dariya. "Ba dai nan gidan ba...Farida ta fi karfin gidan nan...kai dai mu je a baka ita tukuna.Farida ta fi karfin gidan tsoho muddin tana sirikar A.Hadi. mu je ango kada mu yi latti" A waje direba ya rusuna ya mika mukulli ga AbdulHadi wanda ya wuce ga muhallin tuki. Ibrahim ya kalle shi cikin yalwar farinciki "Pop kai ne direbanmu yau?" Ya nuna shi da kwayar mukulli. "Me gida yace mu biyu yake son gani. In na dauki direba ya zamo bamu cika sharadi ba yaya ke nan? Shiga mota mu je muna da sauran mintuna ashirin kuma a gabansa nake so su cika mana in so samu ne" * Ta dauki wani dogon kofin tangaran mai bulun filawa ta na goge shi da farin kyallen cikin murmushin tsanananin farin ciki wanda bata ankara tana yi ba har sai da ta hada ido da Farid wanda ya kawo kansa don taya wannan aikin sa kai da ta tsira. Shi ma wani tangaran yake gogewa amma idanunsa na kanta yana murmushi da irin nasa manufar ta bambanta da tata. Cike yake da sanin ba fagen Farida ba ne aikin kicin da gogegoge ba, amma ta rasa abin da zai cike mata 179 Mafiyan Masoya Hahma AbdulMajid mintocin zumudin da suka addabe ta ne na jiran masoyinta don shimfida sabuwar rayuwa cikin yanci da walwala. Yanzu da a ce shi ne ya sami zuciyar wannan abin kauna tasa da irin wannan tafkin soyayya haka za ta zake ta shigo fagen da ba na ta ba don saboda harshensa da tumbinsa? Ya rasa Farida, ta yi aure, tana da ciki, kuma kamar ita da Ibrahim Balala babu abin da zai taba raba su saboda yadda suka so juna ko suke kan son junansu. Amma fa ya kasa kau da kai zuciyarsa na gaya masa karyar cewa takwarar tasa fa na iya son sa, kuma duk inda tayi murmushi ta cancanci a taya ta. "Kana kallon farin ciki ya sa ni shisshigi ko shi yasa ka ke min dariya?" Ta fassara murmushinsa don katse kallon da yake mata sannan ta mai da idanunta kan jera wasu tangaraye da take gani kamar ba su zauna kan muhallansu ba sannan ta ci gaba da magana kafin ya ce komai duk da yana shirin cewa. "Ba zumudine ya sa n a kwace aikin nan ba Farid kamar yadda ka za ta illa yau rana ce gare ni da zan tuna wasu farin cikina na baya don na hada da na yau da na gaba in tabbatar da dorewarsu. Na taba tsintar kaina ina irin wannan aiki lokacin da nake wani kwas a Brassels kuma farkon ziyarar Bally a gidana. Ni na yi masa girki yana tsaye a inda kake yana taya ni jera kwananika a muhallinsu ni ina kicin. Bamu sake kwatanta wannan kwanaki ba sai bayan auren mu inda a karamin gidan daga ni sai shi babu ko mai shara. Don haka yana shara ina kade tebur, ina dahuwa 18 Mahyan Masoya Ralma AbdulMalid 1 Ι : yana wanke-wanke muna hirar soyayya da wasanni. Duk wancan a baya sun faru ne lokacinda babu `yanci amma yanzu ga su nan zasu soma faruwar dindindin daga yau.... Ta tsaya ta dube shi dą kyau. "Kuma kai ne sila na faruwar yau. Da baka ankarar da ni ba da yau din da rayuwar gaban ba su faru ba. Ba ni da abin gode maka Farid"" Yayi fari da ido sannan murmushi. Duk ta zubar masa da abin da ya so fada duk da bai samu abin dadi a maganarta ba, tun da kuwa ba samun ta zai yi ba. "Babu godiya tsakanina da ke Farida" Ta tsira masa ido tana murmushi. "Farid ka taba soyayya kuwa?' Ta ji tambayar ta kußuce daga bakinta a karo na farko tun tsayin lokacin da jikinta ke ba ta cewa shi ma fa yana son ta yana sadaukarwa ne kawai ga abin da take so, ba ta taba son tayi tambayar ba duk da tambayar ta sha matsa kanta domin ta fito. Ba ta so ta san gaskiyar lamarin da zai iya watsa abokantarta da mutumin da take ganin shi ne kashin bayanta a yanzu. Shi ma kamar ya fahimci tambayar kubucewa tayi domin kuwa fuskarta ta kawu daga tsammanin amsa. Ko shi ba zai so ainahin amsår ta fita ba a lokacin da yake ganin amfaninta ragagge ne. "Na taba jin so, amma ban yi sa'a ba don son maso wani nayi" Ya bayar da amsar ba tare da ya dago fuskarsa ya kalle ta ba, haka ita ma sai cewa tayi. 'Oh! Am so sorry' 181 Mafiyan Masoya * hdidMaiid Rahma AbdulMajid AbdulHadi ya yi tagumi yana kallon gabansa, motar na sharara gudu, hannunsa na ajiye kan sitiyarin ba don yana juya shi ba. "Allah Ya sa wannan lamari na ku ya kawo Karshe ta hanyoyi da dama..." Ibrahim ya dube shi. "Ban gane karshe ba" Yayi murmushi sannan ya cire taguminsa domin ya karya kwana. "Ni da Na'ibi ba mu yarda da juna ba, komai zai fito daga hannun junan mu mu kan sanya shakku da zaton akwai makirci, wannan ne ya sanya muka kasa shiryawa tun tsawon lokaci duk kuwa da kowa ya wadata da sharrin kowa, kuma da ba haka muke ba. Abokai ne na gaske masu kishin kauyensu. Gaskiyar lamari itace ni na haddasa matsalar, amma Na'ibi ya fi ni zakewa bayan da ya sami amintattun kwararru a bayansa kamar Wilson, da Adamu, da Farida `yarga da ma wani sabon yaro Farid... tun a da ya fi ni iya zaben ma'aikata da kashe kudi a kansu.... Sai dai Alhamdulillahi gani a hanya zan je karar da abin i da na fara. Fata na Allah Ya, sanya Na'ibi da gaske ya shirya ya kare" "Amin" In ji wanda ya koma murmushi cike da yakinin karewar ce ta zo da fara sabon shafi na aminci ta hanyar soyayya. Farida ce a ransa da tunaninsa da idonsa, me za ta shirya masa? Yaya za su ga juna? Kamar yau a ka daura aurensu, yana jin za su yi haduwar amarya da ango. Amma 1 1 a a n a ם ar 182 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid kwatsam karan juya sitiyari da taka burki ya kawo karshen wannan hotuna don kallon ainahin abin da ke gabansu. Duhu ya fara gani saboda girman Daf din wadda ta karkato kan titi za ta shiga dayan hannun ba tare da la`akari da ko babu mota a kan hannun da ba nata ba. Abdul Hadi yayi yunkurin kaucewa ta hanyar dauke kan tasa motar zuwa filin baya da daf din ta bari, amma kamar a tsorace mai daf din ya dawo da baya, abin da ya sake ba shi damar hankida su cikin daji don su tintsira babu iyaka cikin motar da bata dena gudu ba. Na`ibi wanda ke cikin shigar doguwar riga mara hannu ta shan iska kuma yana zaune a daya daga kujerun dogon falon na kusa da mashigar gidan yana raba idanunsa tsakanin jarida da agogo, baya kallon Farida wadda take ta zarwa tana duba agogon tana kiran wayar da ba a dauka. Can sai ya mike yana kallon agogo. "Farida ni ina da abin yi in ba ki da shi. Awa daya da mintuna arba`in na kara na jiran angwayenki. Ba ni kara ko sakan daya....in sun zo sai ku ci marabarku, kuma ku sake shirya wani lokacin da zamu hadu, idan basu zo ba sai ki fahimci gaskiyar cewa AlHadi ya tabbatar miki da cewa babu abin da zai canja tsakanin ni da shi...." Ya jefar da jaridar ya juya ya kama hanyar matattakala. Ita dai sakate tana kallon sa, a-rikice take ba ta jin dadi, ba ta san dalili ba, me zai hana su Ibrahim zuwa baya da sun yi sallama yace mata sun bar gida? Yanzu kuma ta kasa samun sa a 183 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid waya ba don babu layi ba sai don ya ki daga wayar. Me haka ke nufi? Ta sake komawa gwada lambar... * Karfe goma sha daya kamar wadda ta buga a tsakiyar kunnensa ya ji ya farka a irin duniyar da bai taba jin nauyinta ba. Kansa na ciwo kuma yana dauke da nauyi, sannan kamar wuyansa a kangare yake cikin wata roba. Ya so sanya hannunsa na dama ya shafa amma sai ya ji hannun ma na wani karajin ciwo duk da daurin jikinsa bai hana shi motsawa ba a guje ya mayar yana nishi, sannan ya dan mika wuya ga kwanciyar. Nan take ya ji yana waro wa kansa abin da ya faru. A hanya suke shi da mahaifinsa zasu gidan sirikansa gaisuwa suka yi mummunan hatsari mai kama da shiri. Ya dubi dakin baki daya babu mahaifinsa. To ina yake kuma a wane hali yake? Tambayar a cikin zuciyarsa ta zo daidai da bayyanar wata me aikin jinya wadda ta ambata Kalmar 'ka farka?" "Ina Baba na?" Ya bukata yana hadiyar yawun fargaba. Та soma neman kubucewa. "Yana nan kwance yana bacci...yana samun sauki...yaya naka jikin? Bari na kirawo likita" Ta juya za ta fice a yayinda ya daure ciwo ya sanya hannun ya janyo ta. Suka hada ido da nasa idanun maras rahma sannan yace mata a "Ina son ganin Babana ko ki kai ni ko ki saura nan tare da ni" Yana kwance rigingine, babu riga a jikinsa sai koren kyalle da aka rufa masa zuwa kirji, kamar 184 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid babu wata tawaya. a jikin nasa sai dai yana madaddewa ta jin jiki. Ibrahim dake dingisawa dakyar ya iso inda fuskarsa take ya dan zura masa ido kamar ya zubda hawaye. Ya dena jin nasa ciwon domin kuwa da alamar radadin da mahaifinsa ke ciki ya dame nasa ya shanye. Can dai ya ambata 'Sannu Daddy'lokacin ne mahaifin ya tsai da wani kakarin numfashi da yake sannan ya dan bude ido ya kalle shi. "....Ibbbraaahhim kai ne?" Ya dafa kan mahaifin nasa da hannunsa na hagu mai sauran lafiya "Ni ne yaya kake ji?" Ya dan dubi mai jinyar. "Ko za ki ba mu wuri na dan yi magana da. dana?" Ta gyada kai sannan ta fita ta tsaya a kofa. Ya dawo da idanunsa kan Ibrahim bayan ya tsawaita nishinsa sannan yayi murmushi. "Ban gaya maka cewa ban yarda da Na'ibi ba?.... Ga shaida ta samu...Na`ibi ya so ganawa da `yarsa kafin ya gayyace mu sannan bayan sun gana din Farida ta kaurace mana sai a waya har aka tabbatar mun fada rami....hum!... ban sani ba ko za ka iya yarda da ni... idan na ce ban yarda da Na'ibi ba har da Farida domin na san ko me Farida tayi min a lokacin da baka rayuwarta da lokacinda ka shigo rayuwarta.... Koma dai yaya ne ka sani Na`ibi yayi nasararsa ta karshe a kaina, ya raba ni da dukiyata da sa`ata amma ban daddara ba ina motsi...yau ya kawo karshen motsin nawa ya raba ni da raina kuma ta hanyar 185 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid amfani da ſana....Ibrahim ka sani wannan abu ya faru ne da hannun Na`ibi, ban kullace ka ba don an yi amfani da kai don na san ba ka sani ba, amma a yanzu ka sani, kai ne zaka saura musu kai ne halifa na kai ne a gaban Na'ibi ko ka yarda ka zama bawa ko kuma ka rike kanka ka ja da su. idan da zabi na za ka bi da nace in kai dana ne da ya haifu to ka daukar wa ubanka fansar ransa da aka raba shi da shi... kada ka bar Na'ibi ya shara ko ya sarara kamar yadda ya kai ni karshe, amma ka kare kanka daga sharrinsu, musamman ta hanyar Farida. Tun da yake maganar Ibrahim baya son katse shi ko da da sannu don wahalar da yake sha wajen hada kalmomi don tsananin ciwo, a waje daya tausayi da yarda sun sanya yana tasirantuwa da hangen abin da ma mahaiufin nasa bai gaya masa ba a cikin matafiyarsa. Amma a yanzu ya soma yi masa sannu da yi masa alkawarin tashi musamman da ya ga mahaifin nasa zai kame zuwa wani halin sharafa, mai jinyar ta shigo a guje ya daka mata tsawar ta nemo likita, fitarta da minti kasa da daya likitoci da dimbin masu taimako suka afko cikin dakin yayinda wasun su suka tilasta wa Ibrahim barin dakin domin kwantar da shi a nasa dakin. A kofar dakinsa... ta bayyana rataye da jaka fuskarta cike da tausayi. Cikin hanzari ta miko hannun taimako inda ita ma ta rike kafadarsa tana 'sannu' don hakan ya ba ta damar shigewa dakinsa. 186 Малyan Masoya Rahma AbdulMajid Ita kadai ta ragu a dakin bayan an sassarkafe shi da kayan magunguna tana rera masa sannu. Ya dago da rurin kuka ya kalle ta, a yanzu babu zafin Kiyayya da tuhumar da ya saba nuna mata a idonsa. "Baba na zai mutu" Kwalla ta kubuto daga idanunta ta dafa shi. "Allah ba zai sanya haka ta faru ba. Likitoci zasu cece shi.... Sai dai bana ka daure ka yarda da abin da nake gaya maka. Idan a ce ka ba ni dama tun a wancan lokaci na kwance maka wannan yaudara da haka ba ta kai ga faruwa ba. Farida kawata ce kuma makusartiya amma na san me za ta iya na san yaddaa gaji ubanta wajen hada makirci da iya daure soyayya. Ban ce Farida ba ta son ka ba, amma za ta iya daure wannan domin ci gabansu. Farida da babanta sun shirya kashe babanka ta hanyar zuwa baiko sai ka saura a duniya ku yi aure, sannan su mallake ka ta hanyar dan da ke cikin Farida bayan kai ma sun kashe ka. Na`ibi Group zasu huta da ku da kuka zame musu karfen kafa" Tunda take babatun kallon ta kawai yake baya ko kiftawa duk da yana hawaye. Sai dai ba ta gaza ba domin kuwa wannan karon ko ba komai ya saurare ta sabanin wancan kora da ta sha kaye.... * Wilson ya fado ofíshin mai gidansa cikin farin ciki yana bayyana murmushi. "Me gidana ka kira ni ina daf da shigowa wurin ka....Karshen tika-tika-tik! Allah Ya'yanke mana jayayya da hasuma da gasa. Allah Ya karbi Rahma AbduMajid 187 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Malam Abdul Hadi zuwa wurinSa. Na san

Chapter 10 of 11