Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ka yi rashi babu abin da zamu ce sai Allah Ya jikan sa da rahma. Gobe jana'iza da misalin karfe goma na safe, sai mu shirya ka isa wurin ka.... Ya dakatar da shi da yatsa daya domin ya gaji da sambatu, ji kake dif ji "Wilson a cikin Kalmar koyar da darasi ina kа an ce kisa? Yaushe na ce ka kashe wani? Wannan aikin naka ban so ba don ban sanya ka ba יי Ya sake yin murmushi. "Ranka ya dade ai damuwarka ita ta sanya ni, domin na ga kamar a na son cin maka a bango abin da kuma ba zan taba bari ba. Dole na motsa ta yadda zan karar da wannan wasa har karshe. Ni dai kawai ka huce fishinka mu dan jira sararawar komai ka ga yadda za mu ci moriyar wannan yanayi" "Na ji, fita ka ba bani wuri ban son ganin ka yanzu יי "Yadda ka so haka za a yi ranka ya dade" ya juya da sanda ya fice. Sama da mintuna hudu Na`ibi Bici tunani kawai yake shararawa da ganin abin da ya faru bai dace ba har må da jin tausayi, amma fa da nasa kuskuren, shi ne yace a koya darasin da bai ce ga bakaken ba, sannan sau tari Wilson kan yi amfani da wannan kalma ta mummuniyar hanya, yaya za a yi yayi haka?Amma kuma shi ma Wilson ya kamata ya san cewa babu yadda za a yi hukumcin AlHadi ya zamo daya da hukumcin kananan arna. Farida da ta bangazo kofa ta shigo ta bangaje tunanin sa 189Man Masoya Rahma AbdulMajid inda ya kalli fuskarta a tsanake don ya san me yake tafe da ita. "Thanks father! Na ji kuma na ga shirinka. Ка so ka kashe mijina shi da ubansa, baka yi nasarar kashe dan ba, amna ka yi nasarar kashe uba. Amma fa ka sani.... "Shut up!" Ya daka tsawar da ta jima ba ta ji ya taba yi wa kowa ba koma tace bai ta6a yi mata ba, don haka ta girgiza ta tsaya kallon sa tana jan nunfashin fishi har ya taso. "A me kika san ni? Me kisa ko me sana`a? gaya min.... kin taba ji na yi kisa?" Ba ta tanka ba ta yi inasa kur da ido domin amsar ba ta dace da yanzu ba, fishinta ba zai bari ta ce masa baya kisa ba đuk da ta san a harkar kasuwancinsa kamar babu jini. yayi ajiyar zuciya sannan ya girgiza kai ya karaso inda take ya dafa kafadarta yana son yin maganar hankali kuma hankali. a "Farida. Mutuwar AbdulHadi zan iya tabbatar miki cewa mutuwa ce irin kowace mutuwa mai dauke da kaddara, kuma ni ma da nake zaune a nan ina jin zafinta domin ko ba komai ya taбa zama abokina. A yanzu zan rayuwar babu aboki babu kishiya. Kin san manufar haka gare ni? Farida na taba yi miki karya kuwa tunda kika wayi gari da ni?" Ya gyara tambayar bayan ta Kura masa ido. "Yes, na san kan batunku ke da Ibrahim na boye miki wani abu, amma sai dai 6oyewar ba wai in yi miki karya ba. Farida ki yarda da ni ba Gath 189 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid zan miki karya ba, ina duban cikin kwayar idonki ina gaya miki cewa ban kashe kuma ban yi yunkurin kashe AlHadi da dansa ba" Ya dan jima suna kallon juna cikin kwayar ido sannan ya juya ya bar mata filin. * Ta sami isowa har kofar dakin da Ibrahim ke kwance cikin sassarfa sauranta budewa, amma sai wata mai aikin jinya ta tare ta. "Ina za ki?" "Nan aka kwantar da Bally... sorry Ibrahim Hadi?" "Eh nan ne, sai dai ya ce a dinga sanar da shi ko waye ya zo kafin ya shiga masa daki" "Ok. Ki ce masa matarsa ce Farida" Ta ambata cikin zumudi a yayin da ma`aikaciyar ta mai da kai cikin dakin da Faridar ke kokarin lekawa don zumudin ta ga Ibrahim. Bayan 'yan sakwanni kofar ta bayyana, maimakon ma`aikaciyar ta fito sai wata me ban mamakj/ta bayyana. Kawarta Merry ta fito tana takí da yanga. "Farida ce kuwa! Ki yi hakuri majinyacin yace ba ya son ganin ki" Tuni ta daure faduwar gaba da mamaki ta ari karfin zuciya mai famar kubucewa. "Me ya kawo ki nan?" Tayi dariya sannan tayi rausaya. "Me ya kawo ni nan? Nice nake jinyar saurayina Bally, ko yaya kika gani? Ba dai kin zarge ni da karuwanci ba, shi ne nake nuna miki Mayran Masoya Rahma AbdulMajid zan iya shigar ki ta ko ina ba ki ga ma komai ba Farida ta daga hannu domin ta mare ta amma ta rike tana kada kai daidai lokacin da mai aikin jinyar ma ta fito. "A'a! Kada ki jawo masoyina ya nuna miki fishinsa don kin mari mafificin wurin da ya fiso a jikina. Kumatu fa kusa da baki yake kada ki manta" Mai aikin jinyar ta dan tsaya kallon su cikin mamaki har suka sarara sannan ta waiwayi Farida. "Malama mai jinyar yace ki yi hakuri ba ya son ganin ki" Farida ta kura wa mai maganar ido duk da idanunta na yi mata nisa da ita. Ta so bude baki tayi mata tambayar da ta dame ta, amma bakin yaki buduwa. Tana son cewa Bally ne yace baya son ganin Farida, amma wani sa` in bakinta rawa kawai yake. Me aikin jinyar ta bar wurin da sauri a yayinda ita ko Merry ta sake buga rausaya da dariya, ta juya don komawa cikin uwar dakin. "To kin ji a bakin da baya karya, tunda ba za ki yarda da nawa ba. Yanzu sai a koma ko?" Ta shige ta bar Farida tsaye kan gwiwoyin da ke shirin kasa daukarta. An yi jana`izar AbdulHadi cikin yanayi na ban tausayi musamman ga wanda zasu kalla daga nesa. Akwai dimbin 'yan uwansa amma babu wanda ya fi daukar ido kamar dansa daya tilo dake tsaye bisa sandar guragu biyu yana sharar kuka babu kafkaftawa har ya kasa rike kansa. 191 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ministoci da manyan jami'an gwamnati sun halarta sai dai Na'ibi Bici bai sami zuwa sahun gaba a masu sallar gawar ba, wannan kuwa ta biyo bayan umarnin da Ibrahim ya bayar na kada a bar shi ya zo kan gawar mahaifinsa bayan ya sami labarin isowarsa mukabirar. Sai dai a lokacin da yan jarida suka yi masa tambaya kan hakan, shi Na'ibi ya ambata cewa latti yayi sanadiyyar ruwa da ake a hanya wanda ya haddasa gosilo, ya kuma kara da cewa shi ne na biyu a rashi in aka yi la`akari da yadda zai kare rayuwarsa babu aboki babu kishiya a harkar sana`a sakamakon kawuwar AbdulHadi. Ko da aka tambaye shi kan sabaninsu ya bayyana cewa ya ji dadi da ya zamnto ta kawu kafin barin dayan su duniya, domin kuwa ko kwana uku da suka wuce yana tare da AbdulHadi suna tattauna wasu muhimman abubuwa da suka shafi rayuwarsu ko da bai bayyana wannan abu ba. Sai dai ya fadi cewa marigayin ya ambaci su kawo karshen adawarsu kasancewar in sune yau ba sune gobe ba, kamar wanda ya hangi karatowar lokacinsa. Yayi fatan Allah Ya jikan abokinsa ya silale daga hannun 'yan jaridar. Duk wannan lamari ya faru kan idon Farida wadda ke kulle a dakinta tun jiya da ta je wurin mijinta ta kasa samun shiga. Duk da hoton yadda yake tsaye kan sanda da kukan da yake ya makale a zuciyarta kamar yadda ya sanya ta zubar da hawaye maras iyaka, hakan bai kau da hoton yadda ya kasa mika wa mahaifinta hannu yayi kamar bai gan shi ba a yayinda suke ficewa daga makabarta. Ta san ma'anar haka kuma nauyi ne 192 Maflyan Masoya Rahma AbdulMajid ke karuwa a kanta. Hakan na nuna wata sabuwar rugujewar alakar aurensu da ba ta san ta inda za ta gyara-ba. Sai dai ko ma me nene a yanzu tana jin matukar bukatar kasancewa da shi ganin halin da yake ciki. Babu yadda za a yi ta bar shi haka. Ta mike ta dauki Jakarta tana share idonta da hankici a yayin da ya zo daf da shigowar mahaifinta falonta suka ci karo. Ya kalle ta cikin ido da nuna tausayi. Yana dauke da labari mai dadi ga zuciyarsa shi ne na yadda Ibrahim ya kulla da shi wanda hakan na nufin samun nasara mai sauki kan alakarsu da `yarsa. "Zan je wurin Bally. Babu dama na bar shi shi kadai a wannan yanayi...yana bukatar kasancewata tare da shi" Ta furta da sauri cikin kuka don kada mahaifinta ya sami damar tare ta. Shi ma bai yi niyar haka ba duk da yana yi mata kallon tausayi. Ya dai bar mata magana kamar haka. 'Watakila ke ya tanka ki, amma ni ko hannu ya ki yi da ni...Ibrahim na tuhuma ta da abin da ba zan taba yi ba, amma ki je yana bukatar ki" Ta dafa kafadarsa tana shirin fita da sauri. "Zan wayar masa da kansa ko ta yaya" * Ya kaurace wa zaman makokin don ya kasance a falon mahaifinsa shi kadai. Ya shigo babban falon wanda babu yawan kujeru da kayan ado sai jifa-jifa masu dan karen tsada da satar ido. Yana dubansu ba wai don suna dibarsa ba sai don wannan falon ne yayi fitar karshe da mahaifin a 193 Mafiyan Masoya Rahma AbduMajid nasa wanda a yanzu yake jin kamar shi ya kai shi ga mahalakarsa "...baka yi rokonka na karshe ba ... zamu fita neman babbar sa`a, ka san yaya zamu dawo?" "...Ni da Na'ibi ba mu yarda da juna ba, komai zai fito daga hannun junan mu mu kan sanya shakku da zaton akwai makirci, wannan ne ya sanya muka kasa shiryawa tun tsawon lokaci duk kuwa da kowa ya wadata da sharrin kowa, kuma da ba haka muke ba. Abokai ne na gaske masu kishin kauyensu. Gaskiyar lamari ita ce ni na haddasa matsalar, amma Na'ibi ya fi ni zakewa bayan da ya sami amintattun kwararru a bayansa kamar Wilson, da Adamu, da Farida 'yarsa da ma wani sabon yaro Farid... tun a da ya fi ni iya zaben ma`aikata da kashe kudi a kansu....Sai dai Alhamdulillahi ga ni a hanya zan je karar da abin da na fara. Fatana Allah Ya sanya Na'ibi da gaske ya shirya ya kare... Allah Ya sa wannan lamari na ku ya kawo karshe ta hanyoyi da dama... Kalmomin mahaifinsa da zai iya tunawá na Karshe ke nan da suke amo a kunnensa kowacce na ba shi fassara da aibata shi da wauta na rashin samun fassarar tun a farko. Yayi jifa da duka sandunan hannunsa ya tsaya kan kafafunsa yana girgiza da rurin ciwo, amma bai jin na ciwon sai na duk abubuwanda ke nuna masa cewa Na`ibi kungiya ne da babu rahama ko kauna a cikinta. Babansa ya nusantar da shi amma ya kasa ganewa saboda kaunar Farida. Yanzu ke nan ya janyo wa mahaifinsa asarar rayuwarsa. Alamunta ya gani 194 Mayan Masoya Rahma AbdulMalid kamar tana yi masa gizo, amma fa da gaske ta shigo falon kuma shi take kallo kur da ido. "Me kika zo yi min kuma Farida?" Ya ambata Kalmar cikin murmushin zafi. Ba ta daina kallon sa ba duk da zafin tambayar gare ta. Ko dai da tayi ajiyar zuciya a yayinda za ta ce. "Kana bukata ta a wannan lokacin domin babu dalilin da zai sanya ka kasance kai kadai cikin wannan yanayi da muka samu kanmu" Ya yi karin mumushi sannan ya dubi gefen damarsa. "Ina bukatar ki Farida? A wane matsayi za ki yi min wannan aiki ke nan?" "A matsayina na matarka masoyiyarka kai da zuri`arka. Ji nan Bally na san kana cikin matukar zafi da rashi, amma haka baya nufin mu zubar da hankalinmu mu fara abin da ba zai yi mana dadi ba. Na san ka yarda da ni da abin da zan iya...Bally ba zan cutar da kai ba ba zan taba goyon bayan mai cutar da kai ba. Bally ina son ka ina dauke da danka yaya za a yi in yi tunanin hallaka ka ko mahaifinka?" "Ba za ki goyi bayan mai cutar da ni ba...har ubanki da kuka gina sana'ar hallaka abokan gasar ku har lahira?" "Har ubana Bally ba zan yi tarayya da shi in zai cutar da kai ba, kuma ka san haka. Ina tare da mahaifina ne har yanzu domin na sani kuma na tabbatar bai da hannu a abin da ya same ku.... Bai tabe yi min karya ba kuma na san abin da zai iya babu kisa a ciki, mun dade muna aiki da shi....na san ba lokacin wannan maganar bane yanzu, 195 Mafiyan Masoya Rahma AbduMajid amma ka daure ka saki ranka ka bar ni na yi aikina na kasancewa da kai a matsayin matarka kuma.... Tunda take magana murnushi yake yana laluben wani abu a aljihunsa, can kuwa sai ga shi ya samo wata takarda a dunkule ya kwance ta sannan ya nufo ta da murmushi ya muna mata. Katin shaidar aurensu ne "ina jin wannan ce ta hada ni da ke da kike kiran kanki mata ta ko?" Bata iya cewa komai ba don fargabar abin da yake shirin yi. Ya keta ta gida hudu sannan ya watsa mata a fuska. "Yanzu sai ki huta da cewa na kawo karshen auren. Dama ba mu da shaidu a nan sai ita, a musulunce ina gaya miki cewa ke Farida na sake ki saki uku.... Sannan abin da ke cikinki na ba ki ki kashe shi ko ki raya shi....Abin da nake so ya hada mu ni dake yanzu shi ne kiyayya! Mafiyanci kika iya ko? Ina so mu san juna a MAFIYAN MASOYA. Ba dai mafiyanci kuka iya ke da Na'ibi ba? To ina so ku gwada da ni.... kun yi da babana kun kashe shi ina so mu gwada ni da ku it ga waye me nasara. Farida ina neman alfarmar mu yi wasan MAFIYAN MASOYA ni dake" Ya kura mata ido kamar yadda ta kura masa tana kada kai. "Ni Ibrahim?" "Ke Farida" Ta kwashi yankakkun kwalayen a hankali ta dube su sannan ta dube shi. Har yanzu idanunsa babu walwala kamar yana jiran me za ta yi. Dа MARASMBOUNAK sauri ba sauri ta juya za ta fita a yayin da zuciyarta Re Zaizay 9yNC "Şai mun hadu a fagen daga. Gara ki yi sauri fkafin Ki kathi MRcin Garawo a gidan nan ongaca uyd Bf har tafalon zuwa cikin hotarti wadda ta taka da gadu kada ta rasa mai kai ta gida n abuEUEU m st aids redagial mob sd ismol swo avi a EY REMISE busbig & EION BY inde morered ows st swas sb sud it ise nE Y sti is a subisd sb um 6d கா sase sa abriel sil swas ilim sysy sri mel il sd sa iknikic ek sb nids nku i λα 20 U9KE q9 2μ 19λς Xι κо 2μ! κπάμε 1 tonsyits !SVYEVINON ide usrisy ors in m KAYTAM s επυ πε2 um or En! Sod sgi u sb 3x svi sud ioπsvilem isb s AYO2AM sb iy nuk..in sb sbewg ux or en oT Yed idi ni ud sb in sbswg um oг aл ide edesk uuk snadad பாமா bre STERN ON SVEW "edsb in AYOZAM WAYAM ПЕКЕ seem swal 61 sbbsy ismed obi sent Erua KI பான்வு "midaidliv tenibs" .KG ε μελακό 8 πsslw πυλλελον ideεwd senunsbi SASY TH ide dub BI NERGET do 50. அj Gasy isrisa Biew a Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid MAFIYAN MASOYA Tana ta tirje-tirje da mutsttsuka har Allah Ya ba ta damar abin da take so wato farkawa daga wannan bacci ko dogon suma, ta kalli dakin da sauri. Karo na biyu ke nan a rayuwarta da ta kan farka ta sami kanta a asibiti. Sai dai wannan karon da alamar ba a gida Najeriya take ba. Ta san wannan asibitin in za ta iya tunawa tayi jinyar mahaifiyarta wadda asibitin suka yi bikin zamowarta mace ta farko da tayi nasarar warkewa daga barazanar kyansa ba tare da an yanke mata nono ba. Kusan a wannan dakin suka yi hoton tuna wannan rana. A birnin Moskow ta kasar Rasha ne. to yaya aka yi ta zo har Rasha ba ta sani ba? Daga gidan Ibrahim ta fara tuna ta iso gidansu amma da alamar bata shiga ba don ba ta iya tuna inda ta shiga illa zamanta a mota tana jinyar zafin kirjinta. "Sannu da farkawa" Muryar babanta ce ta gefen hannunta na dama. Ta juyo gare shi, ashe ma yana rike da hannunta ba ta sani ba. Yayi mata murmushi. "me nake yi a Rasha?" Ta bukata. Ya dan kau da kai. "Kin suma ne a kofar gida kamar kina dawowa daga wurin Ibrahim. Likitoci sun nuna cewa bai yi miki wani abu ba sai dai kin sami fargaba wadda ta so taba zuciyarki" Ta kura masa ido tana jin abin da yake fada tana tuna yadda komai ya faru. Lallai Ibrahim bai yi mata komai da likita zai iya gani ba, amma ta 198 Mayan Masoya Rahma AbdulMajid gwammacece abin da likita zai iya gani yayi mata. Ta tuno cikinta da ta san yanzu ya zama mallakinta kuma kamar Ibrahim zai so yin amfani da shi nan gaba wajen takura rayuwarta. Sai ta ji kamar bata dauke da wani nauyi. Kuma marar tana masifar ciwo. Ta taba cikin nata zuwa kan mararta. "Am sorry Parida We lost your Baby" Ta kura masa ido, cikin wani cakudadden yanayi take. "Ko dai ka sanya an kashe shi ne Father?" Ya sunkuyar da kai "Ba zan yi miki karya ba Farida, na sami labarin yadda kuka yi ke da Ibrahim don kina ta maimaita yace ya bar miki dan nan a cikin magagin sumanki. Hakan ya sanya na sanya hannu kan a cire cikin nan daga Ibrahim ya bar miki wani abu da zai dinga damun rayuwarki da shi. Ba sona ne in rasa jikana ba kuma ba sona ba ne in hana uwa samin danta ba, amma wannan za mu cuce shi ne in ya zo duniya, zai zamo cikin duniyar kiyayya da gasar da ba za ta bar shi ya iya tasiri ba ban da bakin ciki. Zai zargi dalilin kawo shi duniya da kika yi nan gaba. Gara baya nan ku yi rayuwa irin wadda kuka shirya ke da Ibrahim nan gaba" Kallonsa kawai take yanzu ba ta da sauran tunani da za ta iya illa mika wuya ga duk abin da ya zo don ba za ta iya kare kanta ba. Ta yarda za ta iya ci gaba da rayuwa, amma ba ta san ta ina za ta fara ba. 199 Mafiyan Masoya Rahma AbduMajid "mun kashe me rai ke nan Father? Ya fara samun rai yana motsi a cikina" Ta furta haka tana shafar cikin a cikin karaya da kewa. Ba mu kashe me rai ba mun zabar masa rayuwar da ta fi wadda zai yi ne a nan duniya. Farida ba ki da wani laifi kan abin da ya faru illa tsarin rayuwa, kuma haka za ki ci gaba ba tare da ta sami tangarda ba. Duk abin da Ibrahim ke shiri zan iya masa in kin bar ni da shi..." "Father ko za ka ba ni wuri ina son yin magana a waya" "Sure" Ya mike ya fita. * Ibrahim na zaune gefen matattakalar falonsa yana yin abin da bai saba ba wato zukar taba sai ya ji waya. Ya duba lambar Farida ce ba ta wani ba. Ya jima yana kallon ta, amma sai ya ji yana bukatar dauka, domin bai ga abin da ya saura da zai hana shi daukan wayar Farida ba. Babu tsoro babu tausayi tsakaninsu. Ya daga yace hello "Ibrahim Ni ce Farida. Ina son gaya maka abu biyu ne kawai. Daya shi ne, kyautar da ka bar min ni ma na mayar wa Allah abinsa. Ke nan babu wata igiya da ta hada mu babu wannan da da zai zo da bakin cikin iyayensa ya dame shi don haka muna da damar cin karenmu babu babbaka. Na biyu shi ne ina tabbatar maka cewa na karbi tayin ka na zamowarmu MAFIYAN MASOYA. Kana so ayi wasa ni da kai, na amince da mu yi wannan Game da kyau. Ba iyayenmu ne zasu gwada sa`ar Mafiyan Masoya Rahma AbdulMalid su ba ni da kai ne zamu gwada. Hakan bai hana mu zama masoya ba, amma mu nuna wa juna cewa ba masoya ne irin zallar sauran masoya ba. Don haka duk wasan da ka shirya Farida ta shirya, bana gari yanzu,amma zan dawo don ba ka damar bude fage nan ba ba da jimawa ba HUM! TAFDIJAN! Yanzu za a soma mafiyanci a soyayya, duk na baya wasa ne domin ba masoyan ke yi ba iyayen su ne suke yi, amina yanzu sun janye iyayensu gefe, sune zasu yi, mu hadu a littafi na gaba makaranta. Ku yi hakuri nayi alkawari in dai da rai da lafiya ba zai dade ba zai fito Rahma A.Majid Maman Ahlaam Fatima Prints MACE MUTUN Rahma A. Majid Mafiy MASO MACE MUTUM BOOKSHOP Block .No 121 lay uku Bayan Gadar Yan Kur Kasuwa Sabon Gar Kano 08063800300. 0806453357, www.mamuwa.com 978-978-081-870-3 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 11 of 11