Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels MAFIYAN MASOYA 1 RAHMA A. MAJID HAUSABOOK.COM Rahma A. Majid Mafiyan MASOYA 2 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Copy right © Hakkin Mallaka (M) Rahma Abdul Majid An fara bugaawa: 2011 Gargadi: Ba a yarda a sarrafa ko a kwafa ko a juyi wani angare na wannan littafi ba tare da rubutaccen izinin mai hakkin mallaka ba. Kazalika wannan littafi ba labarin wani ko wata ba ne illa kagen nishadi daga basirar mai shi. 3 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Gabatarwa Hanyoyi da musabbabai na rubuta labara sun bambanta kuma sun yawaita da ba za a iya kirgawa ba, akwai masu rubutu don fadakarwa ko nashadantarwa ko rikitarwa ko tsoratarwa ko ban tausayi ko ban dariya, kana akwai masu bayar da labari don habaici ko zagi ko yabo ko fallasa ko girgiza sha`awa ko kashe ta. Har ma da masu rubutu don daukaka wani addini ko wata akida kо wani imani. Gasu nan babu iyaka. Sai dai Rahma Abdul Majid a wannan karo ta zo ne ba da daya daga cikin wannan dalilai ko wasunsu ba, dalilina daya shine taya makarantana hira wadanda sau tari sukan yi kewar rubutuna saboda dadewa da akan yi ba a ji duriya ta ba. don haka mai karanta littafin MAFIYAN MASOYA ya shirya yin hira ne da Rahma AbdulMajid a majalisar hirarta ta alkalami da takarda. A bangare guda kuma ina son yin amfani da damar nan in bai wa masu jiran DA HANNUN MAZA 2 hakuri na rashin ganinsa. Hakika labarin yadda hannun mazan yake yana cikin na biyu kuma shine ma ginshikin littafin. Sai dai wasu dalilai sun sanya ba zan ci gaba da labarin kamar yadda na so ba, maimakon haka na bar masu karatu su zana yadda suka so karshen littafin ya kasance wa zukatansu. Ina mai bayar da hakuri bisa faruwar hakan kamar yadda nake bayar da hakurin kan rashin jin filin masoya a wannan karon, wannan ya biyo bayan yawan da shafukan littafin ke da shi wanda ba zan so na Kara muku nauyi bisa kudin sayar shi ba. Ga masu jiran jerin labaran DUHU kuwa kada a karaya. inshaAllah in da raid a lafiya zasu ga guzirinsu bayan wannan hira ta kare. Da fatan zamu yi hira lafiya mu kare lafiya. -Rahma AbdulMajid 4 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Daya Ya sauka daga kan babur din cikin nawa sannan ya mika masa dunkulalliyar Naira hamsin din bai tsaya ba ya wuce ya bar dan acaban ya na kwance kudin don ya tabbatar da lafiyar su. Dakin da yake kusa da kofar fitar ya tura ya shiga a gajiye, sai da ya fara jifa da takardun hannunsa kan katifar ba tare da ya dubi wurin ba sannan ya soma kwance igiyar tai din wuyansa. "Yaya ka zo kana watsa min takardunka kana tashi na?" Inji wanda yake dunkule cikin wani kodadden zanin rufa. Bai ko kalle shi ba ya ci gaba da cire kayan jikinsa. "Mene ne a gidan nan na abinci ne, yunwa nake ji" Ya bukata, Mahdi ya gyara kwanciya ya juya kansa dayan barin kafin ya amsa. "Indomie ce na rage maka in zaka ci, babu ashana ne na jika na ci nawa. Da dadi ka ci ka ci ka ji" Tuni ya bude kafin ya gama jin bayanin ya kalle ta a wulakance. Bata fi loma hudu ba. Kamar ya fasa kuka, yunwa yake ji, tun safe 5 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid bai karya ba, ga shi abin da zai ci ba zai ishe shi sunan kari ba. "Mene ne haka Mad? Me zan yi da wannan?" Sai da ya dauki lokaci sannan ya dago a fusace. "ji nan, ba aiki ka je nema ba? Da ka samo ba sai ka nemi abinci ba, ni zan ci da kai? Idan bai ishe ka ba ajiye ka siyo wani ka ci, dama ban koshi ba" A lokacin da yake wannan sambatu lomar da ta rage a kwanon bata wuce daya ba, don haka Farid bai ga amfanin tanka wannan maganar ba. "Kai mene labari ka dawo gida sai bacci kake da nauyi a ka? Kai ka samo aikin ne?" a A yanzu ya sallama ba zai koma bacci ba, tuni ma baccin ya kare a idonsa. Kuma yana son ya ji tsaigumin fitar abokinsa. Ya tashi zaune tsakiyar katifar sannan ya dauki filon ya rungume kafin ya dubi takardun da Farid ya watsar sannan ya fashe da dariya. "farin mutum kenan...baka samo aiki ba " Ya sake rikicewa da dariya har da kwanciya. "Na gaya maka baka yi serious da neman aikin nan ba...Dubi takardun da ka fita da su...Fotokwafe? hahaha! Na gaya maka ni jiya da original na fita da na ga kallon da a ke yi wa fotokwafe na wulakanci, amma ka ki yarda. Ka zo kana watsar da su. Ji malam ka ma tattara su wuri guda don baka da kudin sake bugo wasu" 6 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Ya ture kwanon abincin gefe guda sannan yayi ajiyar zuciya ya jingina da wata likakkiyar kalandar mawaka da ke bayansa. "Oh boy! Na dena neman zabi a aiki, ko wanne zan yi... kai! Mad a na neman aiki fa. Ka san tun safe nan muna layi a ofishin INEC wai an ce suna neman graduates da za su yi musu aikin zabe, shine na ce bari na je na gwada sa'ar wucin gadi, wallahi har karfe shida layi bai zo kan mu ba, ba ci ba sha, ta maza kawai muke yi. Baka isa fa ka motsa ka bar wurin ba sai a yi ba ka. Amma Mad duk wannan wahalar saura mutum hudu a gaba na aka ce wai mu dawo gobe an tashi aiki. Kai ni zan koma kuwa gobe?" Ya saki filon da ya rungume sannan ya ja tsaki. "Ba za ka koma ba? Gara ma ka koma fa, don wannan watan me gida zai zo. Kai ne ko zaka biya wannan sabon hayan. Tun yaushe na ke gaya maka mutane na murna in sun yi na daya ko na biyiu a jami'a wai su sun tabbatar sun sami aiki sun gama. Now ni matsala ta yin na dayan ne. Duk inda na je neman aiki sai a cе zan yi tsada basu da kudin biyan albashina, yau ni roko nake ma a dauke ni daidai da wadanda suka fadi a jarabawa ko ba komai ai a na biyan su wani abu da bana samu yanzu da kwali na amma na kasa samu. Shine kai da kayi na daya kake neman ba zaka neman..." 1 7 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid "ban ce ba zan je neman aiki ba... cewa nayi ba zani layin INEC ba, kenan zani wani wurin" Ya tashi ya dauko wandonsa ya soma sanyawa. "Ka je fa ba ruwana. Ka je ba mu da kudi" Ya gama sanya kayansa ya fita ba tare da Farid ya ce masa kanzil ba, sai da ya rufe kofa sannan ya maye gurbin da Mahdi ya bari kan katifar domin yayi baccі. 本 Tuni kamar jiya Farid ya shirya Mahdi na bacci, ya mayar da kayansa na jiya ya hada takardunsa, sannan ya dada wa Mahdi duka. "ka tashi, ai ba ni kawai aka ce na yi ta neman aiki ba. Tashi kai ma ka fita" Ya nannade kansa a zanin rufa ya kawo matashi ya kara. "Kyale ni mana Farid wai me na tsare maka ne?"" Ya fita yana dariya. "Ni zani neman aiki, kai kuma sai ka nema mana na karyawa yau ba zan dade ba" * Kamar yadda Farid ya zata bai dade a gaban ofishin hukumar zabe ba ya baro wurin ba don ya sami aiki ba sai don kafin ya iso tuni an riga an hattama jera sunayen wadanda za a dauka kuma sun cika. Don haka ko da aka duba takardunsa, jami'in dariya yayi ya gaya masa cewa ai abin da ake neman ma`aikatan a kansa baya da alaka da wata kwarewa mai nasaba da 8 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid cin jarrabawa, don haka shaidar yin na daya bata da wata rana a nan. Jan kafa yake a kan titin don gajiya har ya iso gaban wani dogon gini da ya kawatu nesa da katangarsa. Bai zo wurin don komai ba sai don ya huta kafin ya сi gaba da tafiya, amma sai ya ga sunan dake manne gaban wata hasumiya ta ginin ta ja hankalinsa. Ya taba karanta tallan neman ma`aikata na wannan ofishin a jarida da cewa suna neman jami'ìn tattara bayanai da na sadarwa da ma`aji, amma a wancan lokacin yayi yawon neman wannan wuri ya kasa samu, saboda irin wannan manyan ofisoshi ba a cika lika sunayensu da manyan baki a babban allo don son a sani ba, kasancewar irin wadanda ake gayyata basa son zuwa kowane wurin yakamalam. Ya kara mikewa ya fasa zama a yayinda r bai musa wa zuciyarsa da ta so ya shiga kai tsaye ba. Bai sa ran zai sami aiki ba kamart yadda ya sa ran za a koro shi ganin yadda sama da wata daya bai taba dacewa da sa'a ba. Ya shiga kofar mai duba ilahirin mutum cikin mamaki, sannan ta bude masa zuwa wata faffadar kofa wadda da ka iso gabanta take bude kanta. Ya shigo wani faffadan falo mai kujeru da tebura jifa-jifa. Shiru kake ji kamar babu kowa mutane hudun da suka dukufa suna aiki kan kwamfuta kamar kurame ko makafi, babu wanda ya kalle shi a yayinda a rude yake zaben wanda zai je ya tunkara cikinsu. Wata kofar ta bude irin wadda ya shigo, wani dogon 9 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid mutum kyakkyawa kakkaura fari ya doso shi tun daga ido har kafa, shi ma ya danne zuciyarsa mai bugawa ya fuskance shi. "A kwai wani taimako da žan yi maka?" "Na zo neman aiki ne, domin tun satin da ya wuce na ga tallan daukan ma'aikata da kuka buga a jarida shine na ce bari na zo na gwada sa'a ta" Yayi murmushi da kada kai. "Aiya! Abokina kamar kayi latti. Tuni mun cike gurbin ma'aikatan da muke son dauka tun a wannan satin don.... Wata kofa da ta bude da karfi kamar fashewar gilasi ta ja hankalin dukansu suka yi shiru na razana. Wata yarinya ce ta fito. doguwa ce har karshe, fara ce tas. Babu abin da ba shi da kyau a iya jikinta har tafiyarta. Kanta dauke da kitso kanana sun haura dari biyu, tsayinsu ya doshi gadon bayanta, amma babu ko kyalle na rufewa, gajeren siket baki da rigarsa mai yankakken hannu da matse jiki dukansu, sun ji zif kamar mai ajiyar kudin adashi. Takalminta an daddaure shi har kusan gwiwa. Tana tafiya duk da sauri take kamar tafiyar masu tallan kayan sawa. Fuskarta babu walwala. Ba tare da tana kallon gabanta ba ta bangaje Farid, bata juyo tace sannu ba ta fice a yayinda wata murya ke ihun kiran ta da nuna isa. Farida! Farida...Dawo nan na ce. In kika bar wurin nan..." 10 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMajid Farid ya bi ta da kallo na mamaki, ya manta da wadanda ke bayansa, bai san dalilin kallon ba, shin don tunkude shi da tayi ne ko don kyawunta da sunanta Farida, ko kuwa don fishin da take ciki. Mutumin da ke yi masa magana ya dawo da hankalinsa cikin murmushi. "Da Allah ka yi hakuri, tana cikin fishi ne yar shugaban mu ce. Kamar yadda na ce maka sai dai wani lokaci, amma yanzu muna da ma `aikata" Ya juya ya bar wurin Farid zuwa ga wani ma àikaci da ya bukaci da ya ba shi hankalinsa. Farid ya dan jima a tsaye, amma bai san mai zai ce ba, bai ji daban ba da bai sami aiki ba. Amma ya ji daban a ganin Farida. Wacece Farida kuma me ta ke nufi da zuciyarsa. Ya juya a hankali ya fita. Bai tsira ba domin a wajen ofishin ya sake cin karo da wulakancin yarinyar wadda ta busa masa yashi da motarta mai cin taya. Ya sake kalmashe idanuwansa bayan da ya ture abincin wuri guda ya mike kafa, abokin tafiyarsa bai dena kai tasa lomar ba har ma kada cokali yake a kwanon saboda sanin amininsa ba zai so ya cinye ya bar shi bai koshi ba, amma a yanzu kamar bai damu ba, bai yi loma ta fi uku ba a abincin amma ya ji duk ya ishe shi, ya dan yi ajiyar zuciya sannan ya kada kai zai yi magana amma kwatsam sai ya ga ya bude idanu rai a bace. 11 Matiyan Masoya Rahma Abdull.la jid "Ba ka ga fa yadda take tafiyar jin kai ba, ba ka ji yadda ta cika ofishin da kara ba wai duk da ubanta mahaifi take, wannan wane irin raino ne?' Mahdi ya ci gaba da gyada kai yayinda zai yi magana. "Farid duk na ji ka ba ni labarin nan daga shigowar ka, sau uku ke nan har na haddace, yanzu mene ne naka a ciki har da yin lomar abinci uku. rumbu kamar ka..Farid kada ka sanya kanka a uku, kada fa ka ce min son yarinyar nan kake ?" Da gaske Farid ya ji an rikita masa zuciya, shi ya so wannan mara kunyar? Bai taßa zaton kiyayya tana sanya wa mutum ya shiga ranka tamkar soyayya ba sai yau, baya da tababa ya san kin jinin yarinyar nan yayi. "Ni...So?" "Zaka iya ji kana son ta ka tsaya tsaginagini mana, to ni tunasarwa ce tawa, Farid ko yar tallan gyada aka kawo maka baka isa soyayya da ita ba ballantana wannan mahalukiyar, kada ka sanya mu a uku, bukatar mu a nan bata wuce ta neman aiki ba" "Ban gane me kake son cewa ba, Ni zan so irin wannan futsararriyar? Ai talauci ba rashin ka`ida ne a rayuwa ba" Ya sake kai loma a abincin. "Zaka tashi mu ci gaba da ci ko sai na cinye?" Ya mike da sauri ya kalli kwanon. 12 Mafiyan Masoya Rahma AbdulMa jid “Ai ka ma cinye me ka rage, gafara" Ya dauke kwanon a yayinda ya bar Mahdi da cokali yana dariya * Ya taho da yar guntuwar zazzafar citta dafaffiya da aka hada da sikari a wasu siraran kofina da ake rike su a tsakanin yatsu. Har ya iso inda take bai dena kallon ta ba yayinda ita babu abin da take baya da yamutsa yatsunta cikin gashin kanta idanuwanta lumshe tana hucin takaici. "soma kora wannan sannan mu yi magana" Ya ankarar da ita da zuwansa a yayinda ta bude idon ta kalle shi sannan kofinan hannunsa ""Me kake cewa?" "Ki sha nace ki dan gasa cikinki mu yi magana Ta ture hannunsa cikin kada kan takaici sannan ta mike ta bar kujerar ta fuskanci inda wasu masu rawa ke ta cashew can nesa da su. "Kamar fa ni nake cikin wannan matsalar ni kadai ban da kai Ibrahim" Ya sake biyo ta inda ya tsaya a bayanta yanzu, ya dai kware cikin kallon ta, "Ban gane ke kadai ce a ciki ba?" Ta juyo bayan ta galla wani fari. "ka ji abin da nake cewa?...Baba ubana mahaifi ya ba ni kwana uku cewa in shirya barin kasar nan saboda kai... kuma ka ji inda yake nufin in je...London inda dan chairman yake mu je mu fahimci juna... kuma ka ji yace idan 13 Matiyan Masoya Rahma AbdulMajid na kasa yin haka zuwea jibi, in tabbatar na ajiye duk abin da ya mallaka min, in yi yawo ko da da tsumma ne...1 ko?" "Duka kin gaya min" "kuma shine kake ba ni ruwan citta in sha "To me zan yi kashe ki zan yi Farida?" "Zan rabu da kai fa nace... ka san abin da hakan take nufi?" kai. Ya ajiye kofinansa a gefe sannan ya karkata "To Farida na san wannan ba zai sanya ki rabu da ni ba ko na rabu dake... to me nene zaki kara wa kanki damuwa?" Ta kura masa ido a yanzu ta rasa na cewa. "Farida... babu abin da ya saura su Baba zasu yi a duniyar nan da zai raba mu na riga na gama tabbatar da haka...Farida jiki na na ba ni cewa a jinin ki akwai jini na, karewar aure ina da da da zamu haifa tare dake, ban taba samin kokwanto a cikin zuciyata ba, ni ne mijinki...Tun kafin na san me nene so nake mafarki masoyiyata me zanen rayuwarki tun ban san ki ba...to me zai dame ni a yayinda wani mahaluki ya kawo wa zuciyarsa tunanin 99 raba mafarkina da gaskiyar rayuwata ina...." Ta daga zara-zaran yatsunta duka guda goma tana nuna masa sallamawa don ya bata dama ta fadi wani abin da ya dame ta. "Na ji kana da aure na har ma da danka a jiki na yaya za a yi hakan ta faru?" 14 Matiyan Masoya Rahma AbdulMa jid Ya turo nunfashi ta bakinsa. "aure zamu yi na sunna...aure in har kin yarda da tsarina" "Wane tsarin? Na mu zauna kamar wawaye muna jira har ranar da su Baba zasu gama gabar da kullun karuwa take? Balala baka so na ka gaya min and I promise that you will never find me in your life again" Ya kara zuwa taki daya gabanta. "Farida idan bamu bi wannan tsarin ba me zamu yi? Farida na bi duk abin da zan iya bi, na tura mutane da baba na ya ki zuwa, na je da kaina na cewa mahaifinki idan yana so in bar nawa uban zan bar shi muddin zai hada ni da ke aure duka ya ki.. to me zan yi bau da jiran ikon Allah? Wani abu daya da na sani shine ba zan taba rabuwa dake ba... duk abin da zai faru sai dai ya faru tunanin rabuwa dake ba zai taba zuwa min ba...kuma da fadan su ba za su tabа יי bari mu yi aure ba to... "Sai mu fita daga rayuwarsu mu nisance su mu bar rayuwar su mu tayar da ta mu, idan har muna son juna” "Farida abin da nake goyon baya kin san shi kin san wanda bana goyon baya, na san ba zaki zarge ni da rashin kaunar ki ba a kai idan na sake tunasar dake...Farida ku biyu mahaifinki ya haifa, ni kuma ni kadai. Duka duniya sun san su da 'ya'yansu kamar yadda duka aka san su da gabarsu, suna da suna da duk abin da ya faru kan su sai duniya ta dauka caa duk kankantarsa, 15 Matiyan Masoya Rahma AbdulMajid idan har su basu da niyar fahimtar hakkin kare zukatanmu, mu mu san hakkin kare sunan su... Daf da ya gama ta wawuri Jakarta daga kan dan siririn dogon teburin ta rataya sannan ta kalle shi a yayinda yake mata kallon rikita. "zaka jira ko? Ka jira Ibrahim... ni kuma zan yi abin da ya dace a nawa bangaren kafin jibin tayi" Ta juya zata tafi, amma yayi mata burki da karfi bayanda ya ruko kafadarta, ta juyo ta dubi kafadarta sannan fuskarsa. "Me nene haka Bally?" Ya kada kai ba tare da ko kiftawa yayi ba. "Ki yi komai, amma kada kiyi abin da zan rasa ki...In kika yi haka ba zan yafe miki ba ba zan yafe wa kai na ba haka ma su Baba...Kuma kin san me zan iya yi in ban yafe ba, bana son rayuwar da baki a cikinta Farida kuma kin san ba zata same ni ba, domin na sanya rai a יי tarayyar mu" Sai da ta kare masa kallo sannan ta ja tsaki ta fizge kafadarta ta yi gaba, bai kira ta ba ya bi ta da ido har ta bata, sannan yayi ajiyar zuciya ya dubi sama da kasa gabas da yamma kudu da arewa, babu inda yayi masa sanyi a duniya ya yamutsa hannayen sa cikin gashin kansa na wani tsayin lokaci yana fadin. "Ki yi hakuri Farida nine mijinki don ina son ki...Ahh! Allah Ka san ina son yarinyar 16 Mofiyan Masoya Rahma AbdulMa jid nan, Allah Ka da ka sanya ta yi min mummunar fahimta" A haka yake har ya ba66alla maballan gaban rigarsa bai sani ba bai kuma bar wurin ba * Ibrahim Balala da Farida ya'yan wasu mutane ne da ba masu arziki bane kawai ba, a tarihinsu basu taba jin labarin rashi ko karanci ba tun daga kaka da kakanni, tun daga iyayensu a ke musu rainon turawa kasancewar duka iyayen na da shaidar zama 'yan kasar Birtaniya har kan `ya'yan duk abin da ke hada su da Najeriya itace tijara da kasashe masu tasowa da yawancin turawa kan wakilta su saboda samin riba mai yawa. Duk da da fari mahaifin Ibrahim wato Zakari Abdul Hadi Bici da mahaifin Farida Muniru Na'ibi Bici aboakaine na samartaka kuma masu takamar'sun zo daga asalin kauye daya bacci ne kawai yake raba su, sai dai babu dadewa da aurensu da ma fara wakiltar dukiyar iyayensu sai gasar kasuwa ta fara hada su husuma, koda yake þasu fara fitona-fito da cin dunduniyar jupa ba sai a lokacinda shugaban kasa ya so sanya Na'ibi Bici ministan makamashi a matsayinsa na injiniya, inda Abdul Hadi ya dauki nauyin `yan adawa masu zagon kasa wa hakan da cewa Na'ibi Bici ba shi da kwarewa da kishin kasa kasancewar shi da iyalinsa basu taba zaman kasar sama da na wata daya ba. Tun bayan rasa wannan makami ne Na'ibi Bici ya dawo gida 17 Matiyan Masaya Rahma Abdul Majid don kafa kansa inda ya kafa masana antar samar da wutan rańa mai zaman kanta da gwamnoni ke haya daga wurinsa bayan da gwamnatin tarayya ta gaza karade kasar da wutan lantarki. Wannan sana'a ta zo masa da tagomashi matuka fiye da na zamansa a turai, abin da ya ja hankalin abokin hamayyarsa da shi ma ya dawo ya kafa kamfanin sadarwa wanda babu irinsa a kasar ta hanyar sarkafa yanar gizo mai sauri da saukin kudi, amma a nan ne Na'ibi yace ga ranar sakayya da wa Allah Ya hada shi, yayi alkawarin yin amfani da dadewarsa a kasar fiye da Abdul Hadi da sanin manyan kasa har ma da shugaban kasar wanda ya na cikin wasu tsaffin gwamnoni da jiharsu ta taßa cin moriyar wutan lantarkin hayan da ya basu a fitilun kan hanya inda yake tabbatar da duk wata kwangilar da zata zo ga kamfanin Dot Connect na Abdul Hadi Bici sai ya janyo mata hasara ko rashin karbuwa ko ma ta kubuce baki daya. Duk wani kokari da Abdul Hadi zai yi ba tare da ya bayar da gari ba yana yi amma ya kasa kubuta yayinda tuni na`ibi ke ta kokarin fadada nasa kamfanin na High System zuwa wanda zai maye har da aikin AbdulHadi inda ya fa fitar da tsangayar connection Matrimony, a wannan lokaci dukan su basu tsaya amfani da hanyoyin gasar kwarewar aiki kawai ba, tuni wannan gasar ta haifar da amfani da manyan kudaden cin hanci, amfani da dogayen kafa, da hanyoyin leken asiri masu hatsari kan juna. Sai dai a duk 18 Motiyon Meroya Rahma Abdul Majid lokacinda suke wannan basu da labarin ya`yansu sun fara soyayya da juna bayan haduwarsu a karshen shekarar karatu a wata jami`a dake Kasar Canada. Hakan ta faru ne sakamakon barin yaran da suka yi a turai yayinda suka zo bude harkokin kudi a Afurka domin yayan su kara samin kwarewa,.Shi dai Na`ibi Bici ya baro `ya yansa biyu Farida da shafik a birtaniya tare da mahaifiyarsu Salma `yar asalin kasar Eritirya wadda ke shugabantar wata kungiyar mata makiyaya na zamani, yayinda shi Abdul Hadi Bici ya baro dansaa can Kasar Canada tare da kakarsa ta wurin uwa dake da asalin Kasar Ghana har zuwa rasuwarta a yayinda ya isa shiga jami`a kamar yadda itama Farida mahaifiyarta ta tura ta kasar Canadan domin ta sauya yanayi bayan wanda tuni ta saba da shi a kasar Birtaniya inda kaninta ya saura tare da mahaifiyar tasu. Bayan soyayya tayi nisa tsakanin wannan 'yan makaranta kusa da ləkacin fitarsu ne suka fahimci ko su 'ya'yan su wanene kuma sun san menene tsakanin iyayen nasu, abin yayi matukar damunsu ta inda sai da ya so shafar karatunsu, amma daga bisani bayan kowane fangare ya tabbatar wa zuciyarsa da ba zata iya rabuwa da masoyinsa ba sai suka kulla yarjejeniyar kokarin shawo kan kan mahaifan nasu kuma koda hakan ya gagara ba zasu tabа rabuwa da junansu ba,Farida tayi aiki karkashin mahaifinta na dan lokaci a yanayin da ya ji matukar dadinsa, kasancewar ta yi amfani da 19 Matlyan Masoya Rahma AbdulMa

Chapter 1 of 11