Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
inda firij yake yana dariya, ya dauko ruwa ya tittila a kofi, sannan ya dawo falo ya zauna yana ccwa, "Abubuwan ne da yawa, Momy sai yanzu na fito daga gidan". Ta yi dariya ita ma tana zama, ta ce, "Ah lallai masha Allah, komai ya yi daidai tunda ana kai kamar yanzu ba a fito ba". Ya ce sanda yake aje kofin, "Bako muka yi yau tun safe shi ya sa. Та се, "Вako kuma, wane bakon?" Ya cc, "Babanmu mana". Daf! Wuta ta dauke mata, sarai ta fahimci wa yake aufi. ta dube shi da kyau, ta cc, "Lallai kun sha baki, wannan bakon ba na kunya ba ne, na san ka ga abubuwa, ita dai da man ta sani". Dariya ya yi kawai tare da daukar remote yana cewa, "ke kadai Mommy, Daddy fa?" lafiya". Ta ce, "Yau ya bar kasar da yammacin nan". Ya jinjina kai alamar gaisuwa, "Allah dawo da shi Ta се, "Amin, bari na duba abu a kan wuta". Ta mike la wuce. Labari shi da Mommy ba sauki, ba sa ganin wai su surukai ne, kailon mahaifiya yake mata, haka zalika kallon 102 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna da ta ke masa ko irin kunyar nan tsakani babu, don tun yana yaronsa kan ya san waye shi ta ke tare da shi, har girmansa, to ko me ye abin kunyarsa? Haka shi ma ita yake gani matsayin mahaifiyarsa mai ba shi shawara a kan duk abin da zai yi, sai ta amince wani lokacin ita za ta sani kan Daddy, sai dai ya ce ta sanar mishi. Ana magriba ya baro gidan ya yi alwala ya wuce masallaci, sai da ya kammala sallolinsa na ranar sannan ya dawo gida. Zulluminta dare yau a ya za ta kwana? Tuni ta ke a daki har ta kwanta, amma ba bacci ba waya na hannunta tana buga game, in ta gaji ta tabo wannan kawar ta kashe, ta nemi wannan aikin kenan. Duk da ba wai cikin fara'a ta ke ba. Ko da ya dawo bai neme ta ba, ya shige dakinsa ya rage kayan jikinsa ya fito da boksa a jikinsa. A kasan kafet ya mike falo ya dauko sauran abincinsa na rana ya jawo remote yana kallon news. Ya dade yana kallo har sha daya na dare, sai da ya fara jin bacci sannan ya mike dakinta ya nufa. Ya tura kofar, da iyakarsa bakin kofa zai tsaya ya mata bankwana, amma abin da ya gani ne ya sa shi sakin kofar ya shigo. Kwance ta ke ta yi faidai a tsakiyar gadon ba wata rigar kirki ba ce jikinta, ta bacci mai laushi da santsi, fara sol duk ta yaye ta koma sama saboda dadin bacci ne. fararen cinyoyinta santala-santala sun bayyana ba ko alamar tabo a jikinsu tamkar budurwar Turawa. Ta yi d'aidai da su har pant dinta a waje. Ya bi samanta da kallo, kanta ba fankwali mai yiwuwa ya cire ne, gashin ya bazu saman filon. 103 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Wuyanta shamfal har saman kirjinta, ta yi wani fresh, tuskarta har wani sheki ta ke masa ba kurji ko kadan, bacci ta ke sosai ba ta san waye saman kanta ba. Gwiwoyinsa suka yi sanyi, ya kasa dauke kansa daga kallonta. Ta yi masa kyau matuka, bukatar matarsa ya taso masa, ya rasa sukuni da kuzari, kafarsa ta yi nauyi bare ya daga ya bar dakin ko zuciyarsa ta huta da ingiza shi da ta ke. Ya dade a haka yana kallonta, da kyar cikin mutuwar jiki ya ja jikin ya bar dfakin, hotonta da Kwakwalwarsa ta dauka tana kara nuno masa surarta mai ban sha'awa da dadin kallo, ya zauna dabas! Kan gadon yana tambayar kansa, "Sai yaushe ne to zai kasance da matarsa? A haka za su ci gaba da zama yana kallonta ba wani abu da zai shiga tsakaninsu alhalin yana son matarsa, yana bukatarta? Ta ya ma za su samu fahimtar juna alhalin suna nesa da juna, anya bai sakaci ba, kar fa damarsa ta wuce ta wannan hanyar ne za su daidaita da juna, ba wai suna nesa-nesa ba. Ya tuno da alkawarin da ya yi wa kansa, a kan ba zai neme ta ba idan bai manta rotsa da ta yi masa ba. Anya ba zuciya ba ce da shaidan ta debe shi ba ya yi wannan alkawarin ba? Ai ibada ce ta ya ya zairana wa kansa abin da Allah ya halatta masa, yake so ba sunnar Annabi kuma to in ba yau ba sai yaushe? Sannan haka za su ci gaba da zama cikin kunci? Kansa ya dau zafi, ya rasa me zai ji ya fisshe shi, matuka ya kai kololuwa kan bukatar matarsa kar fa ya kwari kansa. Ya dade kan gadon yana juye-juye da tilasta wa kansa lallai sai ya hakura, daren nan. Karshe dai mikewa ya yi ya yo alwala ya zo ya yi sallah, yana kara 104 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna gaya wa Ubangiji damuwarsa. Tun kan ya idar ya ji ya samu nutsuwa, don haka yana idarwa ya fada gado, nan da nan bacci ya dauke shi. Yau kam ba laifi, don ta yi bacci a dakinta, sam ba ta farka ba tunda ta kwantan, haka ma katnukan ba su haushin kullum ba, sai gab da asuba uku da rabi an fara kiran sallah sannan ta farka, ta yi tsuru ta ja bargo ta kudundune, har da fuska ta runtse ido gam, ta alkawarta wa kanta yau ba inda za ta je, ba zai sake raina ta ba, tana nan har wani baccin ya sake faukarta. Sai dai ta farka ta ji ana sallah. Shi kanshi ya yi mamakin rashin zuwanta, yai ta sa ido amma bai ganta ba, don haka ko da asuba da zai tafi masallaci ya buga mata kofa, ta tashi ta yi salla. Ba ta ji ba, saboda baccin da ta yi, ta ji dadi sosai yanda ta kwanta ita kadai ba ta je gurinsa ba, don haka tunda ba abin da ya same ta, to insha Allah kullum ma ba abin da zai same ta, za ta dinga kwanciyarta har ta bar gidan. Yau ma lahadi ba aiki, ya yi kw anciyarsa yana bacci, musamman da bai kwanta da wuri ba. ita ko tuni ta tashi ta yi wank-nta da kwalliyarta, kamar kullum har abinci ta ci, ta loma gado ta harde. Kamar daga sama ta dinga jiyo salamar Rafi'a a falo, ta daka tsalle ta yo waje tana murnar zuwanta, ta fada jikinta suka rungume juna suna dariya. Rafi'ar ta ce, "Na shiga uku Mabaruka, sai kin karya ni wannan tsalle da ki ka yi kaina?" 105 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Suka zauna tana cewa, "Dole ne na yi murnar ganinki Rali'a, kwanana nawa ban ganki ba? Ina kewarki wallahi Ta ce, "Ni ma Mabaruka haka kawai ina tashi yau na ji ke nake son gani, ko ya ki ke duk da duka kwana uku ne ina ga ko hudu rabona da ke, ga shi nan na yo sauko goma da rabi fa? Та се, "Тo mene ne? Kin san tun yaushe na tashi ai? Tun bakwai fa, ba abin da nake sai dai buga game" Ta kalle ta da kyau, ta ce, "Ban gane ba sai buga grame, ba ki nemar muku abin kari ba?" Ta tabe baki, ta ce, "na karya mana, kin san ni sai in dafa lipton in ci ragowar abincin jiya". Ta ce, "Ban gane ba, shi fa imran din me zai сi?" Ta ja tsaki tare da harararta ta ce, "Ina ruwana? Can shi ya sani, me zai ci ni dai bana ci ba?" Ta juyo sosai tana kallonta, ta ce, "Mabaruka kina son ki ce min har yanzu kina nan kan ra'ayinki?" Ta ce, "Sosai ba abin da ya sauya, ina nan kuma ba zan sauya ba har sai sanda na bar gidan”. Ta ce, "Kina tunanin barin gidan ke nan?" Ta ce, "Sosai akwai iyaka, kwanan nan kuwa". Tsaki ta ja tare da cewa, "Ina ganin ba ki da hankaii. An Caura miki aure ba don rabuwa ba, Imran mijinki ne na har abada, kin shigo kenan cikinsa, daga nan sai kabari..." Ta katse ta, "Allah sauwake, wallahi rayuwata ba za ta kare a kunci ba da rashin walwala, dole ne in sakc in ji dadin rayuwa kamar kowa". 106 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Та се, "Mabaruka, ki nutsu ki san me ki ke. Aure fa ba abin wasa ba ne ki karbi hukuncin Ubangiji, ki rungumi mijinki ku zauna lafiya. Wallahi na san za ki ji dadin zama da shi, Imran mutum ne mai hankali da tunani, yana da ilimi, ya san hakkokin aure, zai ba ki hakkinki, ya kiyaye damuwarki wallahi ba zai taba muzguna miki ba. Sannan yana sonki so mai tsanani, a rayuwata ban taba ganin wacce mijinta ke so irinki ba". вні Та ce, "Ni kuma bana sonsa, duk abinsa ba ya burge ni, ba zan taba farin ciki da auransa ba. Ina jina kamar a kabari nake, a kuntace, na takura sosai ba abin da ke min dadi a gidansa, kawai so nake na rabu da shi ko ba don na auri Sulaiman ba, ko don zuciyata ta yi sanyi in yi walwala, in bar kuncin da nake ciki". Та се, "Тo in ba ki labari, matukar ki ka bar gidan nan ba za ki taba farin ciki ba, kunci, nadama su za su baibaye ki. A yanzu ba komai ki ke ba, wallahi kin faye naci da kafiya Mabaruka, ba kowa yake sa'ar samun miji irinki ba, amma kin runtse ido kin ki karbarsa, ina guje miki ranar da na sani, ranar da za ki kuka idan ki ka bari ya kubce miki, hankalinsa ya bar kanki ya koma kan wata wallahi. sbigCikin ko'in kula ta ce, "Da hakan ya fi min farin ciki da walwala, zan so a ce ga ranar da ya daina sona wailahi, can wata ta kwasa". sb edrg Ta jinjina kai, ba ta san ta ya za ta gane ba tun ba yau ba ta ke nuna mata, amma ta kasa fahimta. Ta nisa tare da cewa, "To na ji, yanzu dai ni me zan samu, ban ci komai ba, ina gama wa Mama aikinta na fito na ce inina zo nan na karya". 107 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Ta cc, "Ki shiga ki duba abin da ki ke son ci. Ta mike tana cewa, "Zo mu je ga masu shara can ina jin sun zo, zo mu je ciki". Ta ja ta zuwa bedroom dinta. Ta yi tsaye sake da baki ganin yanda ta cika dakin da kayan girki tamkar kicin, ta cc, "Me zan gani haka, ba dai a nan ki ke girki ba? Wanc irin hauka ne ya same ki Mabaruka?" Ta zauna tana cewa, "Za ki ga abin da ya fi hauka, in dai na ci gaba da zama gidan nan". Ta karaso tana cewa, "Amma me ya sa ki ke girki daki bayan ga kicin can?" Ta ce, "Kawai bana son shiga kicin din ne". a Ta ce, "Wallahi ba ki nema wa kanki mafita ba, ban ga dalilin girki a daki ba ga kicin". a Ta fara bude-bude, ta ga himilin kayan abinci cikin wardrobe, jinjina kai kurum ta yi har ta gaji da maganar ko ta fada ba jinta za ta yi ba ta bari, to ba ma amfanin maganar gwanda kawai ta yi shiru ta nema wa kanta abin da za ta ci, suka hau zuba labari. Tun daga dakinshi yake jiyo maganganu lokacin da ya tashi, matuka ya yi mamakin jiyo harshenta ko ita da waye ne haka? Abin da bai taba ji ba tun sanda ta zo gidan, da alama tana murna da bakon ko bakuwar. Sai da ya shiga wanka ne ta bayi ya gane Rafi'ati ce, saboda maganarta. Ya jinjina kai kurum ya ci gaba da wankansa. Sai da ya shirya tsaf cikin dogayen kaya, farare sol ya dan sa tabaransa mai kyau, kamshi ko ta ina fitowa yake, ya yi kyau sosai ya dauko wayoyinsa ya fito. 108 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Kai tsaye dakin ya nufo tun kan ya iso kamshinsa ya sanar musu. Ita da ji ta gane shi ne, amma Rafi'a ta yi luf har da lumshe idanuwa tana shakar kamshin, ta dube ta ta ce, "Wayyo Mabaruka kin ji wani irin kamshi mai dadi ya buga? Wannan da ji na mutanen boye ne, ina mutum zai samu wannan turaren kamar ba a duniya ba? Wallahi ya hadu". Tsaki ta ja tare da dauke kai tana jin haushin Rafi'ar, sam kamshinsa bai taba burge ta ba, da dama yana sa ta tashin zuciya tamkar z ta yi amai. Kan ta ce komai ya fara buga kofar, Rafi'atun ta ce, "Waye?" Ya turo kofar yana murmushi, "Ni ne da kaina". Ta yi dariya tana kallonsa, ta ce, "Ashe kana gidan muna nan muna ta zuba surutu?" Ya ce, "Ina ciki ina jiyo ku, na ce ke ce kadai za ki zo in dinga jiyo harshenta sama har da dariya". Ta yi dariya sosai tana kallon Mabarukar, ganin yanda ta turbune fuska. Ya sake cewa, "Rafi'atu manyan mata, ke ce dai ga ki ga aminiyar?" Ta yi dariya, ta ce, "A'a ko dai kai, kai da ka ke tashi yanzu karfe sha biyu, ni kwa tunakwas idona biyu". Ya yi murmushi, ya ce, "To sa zan yi, wa ya hana ni bacci jiya in ba kawarki ba?" Ta kalle shi da sauri, "Kawaia kuma?" Ya daga kai aiamar eh, yana kallon Mabarukar ya ji ko za ta ce wani abu, idonta ba kanst vakeba. Ta juya can gefe tana kumburi, Rafi'ar ta juya lanr larnbayarta, "Wai haka Mabaruka?" 109 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Juyowa ta yi tana harararta tamkar za ta kai mata duka, ba shiri ta kyale ta. Za ta yi magana ya tare ta yana cewa Mabarukar, "Barka da safiya my princess". Ta yi masa banza tana kara jin tsanarsa. Ya jinjina kai yana dariya, ya cc, "Sarautar ce ta-motsa kenan?" Ba ta dai ce komai ba. Ya dubi Rafi'a yana cewa, "Bari in dan fita, zan dawo yanzu". Та се, "То a dawo lafiya". Ya ce, "Amin". Tare da juyawa, fitarsa juyowarta tana harararta tare da cewa, "ke dai wallahi yar wulakanci ce, kina jin yana miki magana kin masa banza, anya Mabaruka daidai ki ke? Mijinki ne fa karkashinshi za ki shiga aljanna". Ta juyo cikin bala'I, "Eh din, na yi, sai me? Kar ya daga din an gaya mishi ina nema gurinsa ne? Bana so ya take, kar ya daga, mugu kawai". Ta zaro idanu tana kallonta a tsorace, abin nata gaba yako. Wannan wace irin tsana ce? Ta ce, "Kina ba ni mamaki Mabaruka, idonki gabadaya ya rufe, kin manta Imran da matsayinsa, kin manta alkhairansa gare ki kawai saboda an miki gatan aura miki shi, sai iskanci ki ke kalakala kina bijire wa kyautar da Allah ya miki, wallahi ki ji tsoron Allah ki nutsu ki san me ki ke, ki tallafi mijinki da auranki ku zauna lafiya ya fiye miki abin da ki ke son banza za ki je ki halaka kanki". Ta dube ta da rinannun idanunta da suka fara canzawa na kuka, ta ce, "Har yanzu kin kasa ganewa Rafi'a, tsana, kiyayya babbar ciwo ce da kunci, in ba ka son mutum ba zai taba yin abin da zai burge ka ba ko da 110 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna sau daya. IHaka nan ba ka san sanda za ka dinga kuntata masa ba, saboda zafin da zuciyarki ta ke miki. Ban ga amfanin a nace lallai sai na zauna da wanda bana so ba, duk ko abin da na yi kar a ga laifina saboda ba daga ni ba ne, zuciyata ce ba ta sonsa, ba ta iya zama da shi, mafi a'ala a sauwake min auransa sai kowa ya huta, ni ma na samu saukin radadi da zafi da zuciyata ta ke min". Та се, "Кarya ki ke wallahi, ke ki ka sa wa kanki tsanarsa. Imran bai zamo makiyinki ba, masoyinki ne idan har za ki tuna baya zuciyarki kuma ta fi karfinki, ba ki iya sarrafa ta sai dai ita ta sarrafa ki, amma wallahi babu kiyayyarsa a ranki wallahi Mabaruka". Zuwa yanzu ta fara kai wa bango a kan Rafi'a, maganganunta suna mata kaushi a ranta, don me ba za ta fahimce ta ba, sai ta dage a kan lallai ita ce mai gaskiya tana goyon bayansa, akwai abin da zai iya sa wa kansa tsana ne haka kurum ba tare da an jarabce shi da hakan ba? Ba ta sonsa ta fada ta sake fada, dole ne sai ta so shi? Ta ce, "Ya isa Rafi'a, mu bar maganar nan ranki da nawa duk za su baci, ba za mu taba fahimtar juna ba, ke ki tsaya a kan naki ra'ayin, ni ma in tsaya a nawa kafin lokacin barina gidan nan ya yi, ni ma in zama mai 'yanci kamar kowa". Ta numfasa ta ce, "Shi kenan na kyale ki, maganganuna ba su ne za su fahimtar da ke ba na lura babban abin da zan miki addu'a, ke ma ina shawartarki ki ringa addu'a kina gaya wa Allah, sai Ya kawo miki sauki a lamuranki. Sannan zan shiga kasuwa in duba miki wasu littattafai na marubutanmu wadanda aka rubuta a kan irin matsalarki, ki karanta ki ji yanda matan suka yi har suka 111 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna samu riba, ko kuma wadanda suka Ki karshe suka dawo suna kuka da nadama. Ina ganin abin da zan miki kenan in Allah ya taimaka sai ki ga kin yi maganin matsalarki ta nan, sannan ga addu'a da man kina yi, sosai za ki rage Kunci da damuwa da kadaici don ina da tabbacin za ki nishadantu da ilimantuwa inshaAllah, a hankali damuwarki za ta ragu har ki neme ta ki rasa". Ta nisa cikin gamsuwa da zancenta, ta ce, "Shi kenan ina jiranki". Ta ce, "Zan duba miki insha Allah, sannan gobe fa school kuma lecture ta farko test ce, har da haka na zo tuna miki". Ta zaro ido tare da mikewa zaune, ta ce, "Da gaskeе Rafi'a, "Har mun cinye hutun?" Ta ce, "Wallahi ni ma na ga saurinshi". Ta ce, "Tabbas haka ne, daman ya ce ranar da aka dawo da test za mu fara. Ki ce yau in kwna karatu?" Ta ce, "Sosai, tun jiya na fara wallahi". Ta yi farin ciki sosai da komawa school, ko ba komai ta fita ta huta da zaman gidan, ta yo karatu watarana ma a school ta ke wuni, sai yamma lis sosai za ta ji dadi dogon hutu ne tun kafin auran. Rafi'atu ta dubi agogon hannunta, ta ce, "Ke ni fa yunwa nake ji, kin san ni indomi ba ta rike min ciki, mu tashi mu girka wani abu". Cikin farin cikinta ta mike suka hau kiciniyar girkin. Dawowar da zai yi ya tarar da gida ya turnuke da kamshin girki, miyansa ya tsinke sosai yunwa ta taso masa a falo ya tarar da Rafi'atu, ya ce, "Ina Mabarukar?" 112 WAYE ANGON?-3 Б 362 69 nawa Maryam Jafar Kaduna Та сс, "Тana ciki, wanka ta ke"! Ya cc, "In dai ita tai girkin nan?" Ta ce, "Sosai ma6 Ya kada kai cikin farin ciki, Da kyau, zubo min Ya wuce dakinsa da sauri Ita kanta ta yi dariya, ta mike ya sani idan zai cе wa Mabarukar ta zubo masa ba za ta zubo ba, sai ranshi ya baci dơn haka dama ce ta same shi Raff'a ta zubó din. SHBY YG7 'Ta yi yanda ya ce, ta jere masa a falo, ya fito daga dakinsa ya karaso da gudu-gudu yana cewa "Ba ni nan, ai daki zan je da shi, ba ta dai saní ba ko?i Ta kalle shi da mamaki, sai da ya sake nanata mata, Bb d Yce, To Karki sanär mata kin ji ko sgb Ya wuhn SLO Daga kai kurum ta yi, ya wkashe kayansa ya shige dakinsa da gudu cike da murnar yau ma zai sake cin girkinta mai dadi. Ta juya ta shige dakin daidai fitowar Mabarukar ashio daga wanka, tana cewa."Ke'da waye ki ke magana?g BAs TuSVa 5 co! Imran ana"d siek tnisi si iRD 133 ta ce komar ba, sai ma jai tsaki da ta yi ta wuce ta dauko darduma ta shimfida da sallah. RafFa ta dube ta kurum, ta co"Allah ya shirya kionuх влиа ок яa ma ba ta ce komar ba,a. ta kabbara sallartasdes Inna Binto ko tun safe ta ke ta sauri taa gama saida alalarta ta tafi ko ita ma ta samo nata rabön Ga shi dai jiya sun sha dage-dage, yara sai santi ake an kwan biyu ba a lasa ba, Bare shi margidan yana ci yana sa wa Mabaruka da ved ib syilst sums moyog olas ST 13 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna mijinta albarka, ba abin da yake cewa, sai, "Haihuwa ta yi rana. Sai daa ta saida alalarta tas! Sannan ta fito, tana tafe tana lissafin kasafin kudin, kowanne ga abin da za ta yi da su. Ta iso bakin gate, leke ta hau yi tsoronta kar a kuma hana ta. Ta yi sa'a kam ba kowa, a guje ta shigo tallafe da goyo ta hau wuri-wuri da idanu, ina ne kofa ko ina kallon kanta ta ke ta madubi, ba ta ga alamar kofa ba, da wacce ta sani sai ta yi nan ta yi can, ta rasa inda za ta bi ta sadu da masu gidan. Tun tana ganin abin wasa har yana kokarin zama gaske. Ta birkice ainun, cewa ta ke, "Ina nake, nan ina ne? ina na shigo? Ko dai gidan yankan kai na kawo kaina, gidan ne kuwa?" Ta hau zagayen gidan duk girmansa har ta kai inda ta daga kai, wani dogon gini mai tsini ta gani ba shi da iyaka, karshe katanga ta tsorata sosai a guje ya baro wurin goyo na shirin sullubea cewa ta ke, "Na shiga uku, ina nake jama'a? Ku taimaka min". Ba abin da ta ke gani sai kanta kurum ta jikin gilassan. Wata kofa ta gani a tunaninta za ta fita daga gidan ne, sai dai ta tsinci kanta tsakiyar falon tamkar wacce aka jeho, ta yi wuri-wuri sai waige-warge ta ke da ka gani ka san a tsorace ta ke, tak! Za ka ce ta arce da gudu. Suna zaune falo da fara'a, tsulum suka ganta gabansu, Mabaruka ta mike da hanzari tana cewa, "Inna ke ce? Lafiya dai ko?" Muryar Mabarukar ne ya dawo da ita hayyacinta, don ko gani ba ta yi daidai, saboda firgita da ta yi. Mabarukan ta lura da ita ta taho inda ta ke tsayc ta bayanta, lana cewa, "Kwanto goyon, amma lafiya dai ko?" 114 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Ta kwanto tana cewa, "Bar ni in dawo hayyacina Mabaruka, ban maheci in fifita duk na jike da zufa kamar an watsa min bokitin ruwa, ke ina ma makewayi in zaga, don marata dam ta ke saboda firgita". Ta yi mata jagora zuwa bandakin, a can ma a rude ta ke, ta hau lalube ta rasa inda za ta tsugunna sam gurin bai mata kama da makewayi ba, ko ina tartar kal! Anya akwai gurin fitsari gurin nan? Ga madubi nan da kayan kwalliya kila dai daki ne? Ba shiri ta fito tana cewa, "Kina ina? Ni fa ban ga makewayin ba, yana ina?" Ta ce, "Ga shi nan inda ki ka fito Inna". 'Ta juya tana waige, "Nan shi ne makewayin?" Ta ce, "Eh mana", Та се, "Тo amma zo gwada min inda zan tsugunna in yi fitsarin, kar na muku barna". Ta wuto tana dariya, "Inna ho! Mu je ki gani". Suka wuce ta nuna mata inda za ta zauna ta yi fitsarin, ta ce, "A kan wannan tukunya-tukunyar?" Ta yi dariya tana kallonta, ta ce, "Eh”. Ta wuce tana kunna mata famfo, "Ga famfo nan in kina da bukatar ruwa ga buta nan". Ta jinjina kai kurum, Mabaruka ta ce tana murmushi, "Hakan ya yi, ko akwai wani abun?" Ta сe, "A'a je ki ya yi”. Ta fice tana mata dariya. Sai da ta yi fitsarin har da wanke kafafuwa da suka yi kura, sun kwaso jar kasa aka wanke fuska, ta fito tana cewa, "Wannan gida Mabaruka a cikinshi ki ke rayuwa?" Ta yi dariya tana kallonta, "Eh mana Inna". 115 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Ta zauna tana jinjina kai, "IHodijam! Na ga kokarinki ni kam ba zan iya ba, a kullum na san sai na bace, wannan gida da ya yi kama da na masu satar mutane?" Suka yi dariya gabadaya, Rafi'a ta ce, "To Inna, ina ki ka san yanda gidan masu satar mutanen yake?" Та сс, "Кe bar ni Rafi'a, yau na tsorata ban taba irin na yau ba. Gabadaya fa na rude. Cewa nake ina nake a taimake ni, duk na firgice duk inda na juya kaina nake gani, ko'ina ya zama madubi na rasa kofa". Dariya ita da Rafi'a har suna fadowa daga kujera, ita ko fade ta ke ba ta ko dariya. Aka kawo mata abubuwan sha da na tauna zuwa abinci, ta mike kafa ta dinga aikwa tana yi tana zuba hira, tun abin yana ba Mabaruka dariya, har ya koma ba ta haushi, tsoronta kar Imran ya dawo ya tarar da ita a gidan, jiya Babanta ya zo ya matarshi ta zo? Ai abin zai yi yawa ba hauka ake ba, da ganinsu ka ga makwadaita ita kam kowa ya kalle ta zai ce kwadayi ya kawo ta, don ta ga jiya abin arzikin da ya koma da shi shi ne yau ita ma ta zo ta karbi nata. Ta dade fa ba alamar tafiya har yamma. Ganin har lokacin bai dawo ba ya sa ta сe, "Ke Mabaruka mijinki ba ya dawowa da wuri ne?" Ta hade rai, ta ce, "Lafiya, wa ke nemansa?" Ta yi dariya tare da sosa kai, "Ah daman ni ce wai ya zo mu gaisa, sai in tafi. Kin ga ba dadi har in zo in tafi ba mu gaisa ba". Ta ce, "Sosai kam, sai dai kin taki rashin sa'a, don yau ya yi tafiya tun safe". 116 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Ta zaro ido tamkar wacce aka gaya wa mugun abu, ta ce, "Ke 'yar nan sai yaushe zai dawo ke nan?" Ta сe, "Cabdi! Ni kaina ban sani ba, don ya ce zai kwana biyu, sai an ganshi". Ta yi shiru tana jin takaici a ranta, me ya sa ba ta zo tun safe ba ta riske shi kan ya tafi? Ta ja tsaki ta ce, "To ki dan kira min shi ko ta waya ne mu gaisa ya san dai na zo, ina gidan". Suka haďa ido ita

Chapter 7 of 11