Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
"Sai Innarmu, wannan baka ne ."kam יי Ta yo wankanta fes bayan ta yi sallah. kamar yanda ta ke ita dai tana son gayu ko ba inda za ta je za ta yi kwalliya ta dauko kayan da ta fi so ta sa, ta yi kwalliya sosai, don haka ko a nan ma haka ne, ta fsto abinta fes. 85 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Abin da ta gani ne ya sa ta ja ta yi tsaye idonta a waje ta rike kugu ta lada daidai yanda ita za ta ji, "Kan bala'in nan, wa ya ce ka ci min abinci?" Ta karaso inda suke shi da Baba,. Sun baje saman kafet da Baban da Imran suna kwasar girki, kowannensu na santi a cikinsu ban san wanda ya fi wani ba, shi kam Imran tunda yake bai taba cin irin watuan girkin ba sai kada kai yake yana jinjina mata, ashe ya bar gara na tafiya? Cikin tsananin fushi ta zauna tana hararsa tamkar za ta shake shi, takaici da bakin cikin ci mata abinci ta ke kamar ta fasa kuka. Kai ta gagara daurewa, ta tura masa sako ta wayar da ke kusa da shi. “Allah ya isa abincina da ka ci". Ta tura ta ci gaba da satar iddon Baban ta dalla masa harаrа. Ko da ya karania murmushi ya yi, da yake shi ma da hannun yake ci ya biye wa Baban ya cika hannu da abincin bar yana nuna mata ya sa baki, har da lumshe idanuwa yana motsa kunne, ya ce, "Umm..." Takaici ya turnuke ta, ta kauda kaina sake jin tsanarsa, don me zai ci mata abinci? Ya maido mata da amsa, "Ba tarbiyyarki ba ce Mabaruka, bau sanki haka ba. Kada ki sauya kanki, abinci kuma na ci sai dai ki kwana kina min Allah ya isa". Ko da ta karanta ta yi wurgi da wayar tana harararsa. Yana kallonta ya'yi dariya tare da sunkuyar da kai, shi ko Baba bai san me ake ba, gabadaya ya ba da baakalinsa kan abincin yana ci tare da lumshe ido. 86 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Tana nan zaune har suka gama cikinsu ta rasa wa ya fi ba ta haushi, Baban ko ko Imran din? Sam ta ji abincin ya fita ranta, ba ya ba ta sha'awa duk da yunwar da ta ke ji ba don komai ba sai don ya ci abincin da kuwa ta ci abincin da ya ci gwanda ta kwana da yunwa. Zai tafi? Zai tafi? Shiru! Sam ba ta ga alama ba, shi ko lmran ya mike kafa yana biye wa Baban yana canja masa channel, duk fadin duniya duk inda aka nuna da Turawa yanzu zai cafko maagana, musamman in ya gansu tsirara. Takaici da haushi suka cika maata rai, tamkar yana zaune a gidansa. Sam bai yi kama da ya zo gidan suruki ba. Sai yamma lis! Sannan yai shirin tafiya bayan ya sa Mabarukan ta kawo masa dan soyen da ya ci ya tafar wa da yara. Kamar ta fasa ihun takaici, musamman duk a gaban Imran din a ke. Haka nan dai ta zubo masa a leda ta kawo masa, hade da dubu uku tana cewa, "Ga shi Baba ka dan rike kwana biyu kafin na zo". Ya hau washe baki yana kirga kudin ya ce, "Kai Allah miki albarka rabon da na rike irin wadannan tun ki... nan sai yau, lallai yau akwai cin balangu a nono". Ta kauda kanta gefe, tana kumburin haushinsa. Imran ya yi dariya tare da ciro keyn motar, ya wuce gaba yana cewa, "Ina waje Baba". Bayan fitarsa ta dube shi tamkar za ta yi kuka, ta ce, "Me ya sa haka Baba? Me ya sa ka ba ni kunya, ka riga ka gama zubar min da mutunci aa gabansa Baba, surukinka fa ne?" 87 VAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna out SV Ya kalle ta da kyau yana gyara tsayuwa, уa сe, To to lyar masu bakin ciki an sha nono. Me na yi da ki ke Kokarin mın sharci? Gaishe ku fa na zo yi' Ta ce, "Ba wata gaisuwa, nan ba ita ta kawo ka ba, taka ta kawo ka. Ni ba za ka bari na zo na gaishe ka ha sai kawai ka wanko kafa ka taho, ka zo ma din kana da kunyata ni ka zubar da girmanka a idonsa? Wallahi na san ya riga ya gama raina ka Ya ciro kudin cikin fushi yana mik mata, hade da ledar, "Ke amshi kayanki uwar 'yan tsogumi, tun kan ki tara min jama'a. da ma 'yan kudin da ki ka ba ni ki ke wa, to amshi ban so Ta dube shi cikin kunar rai, ta KSMO ce, "Amma ka san KULsRI a yau na saba ba ka ba ko? In su naake wa tuni me ya sa ban maka ba tun ina gida? Ina son ka fahimce ni, ni kaa kiyaye gaba kar ka sake, masa fuska, sama-sama kana nuna kai ba ka damu da shi ba bare abin aljihunsa, HASWK on nsDds don kar ya raina mu Ya ce, "Na ki, na, yi din ba ni da kwandala ki ZIL RD E BOST xim delШA sani fadin rai talaka ina ya ga ji da kai?" Ganin ba zai fahimce ta ba sam, ya sa ta ce,Shi 023 ke nan ka je to in da matsala ka dinga kirana ba LG AIAR VB ba !uISE sai ka vo ba, zan zo ni ka ji Baba?" Ya kalle ta tsawon dakiku ya ja tsaki kawar tare da wucewa yana cewa, "Gabadaya kin kwaso mugun halin uwarki na bakin ciki da hassada. Sam ba ta son ta ga na ci gaba, ke ma haka ne. Allah shirya ku Ta bivo shi da sauri tana ba shi haku kr ya karasa gurin Imran din da yake jiransa yana surutan. Bai WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna saurare ta ba ya wuce abinsa, har bakin motar. Da zuwa ya kama washe masa baki, yana cewa, "Sannu dan nan, kana ta jira ko?" Ya yi murmushi kawai, ya ce, "Ba komai Baba, shiga mu je. Ya kama motar ya shiga yana cewa, "Ta tsayar da ni tana gaya min maganganu na bakin ciki. Sam ba ta son in dan ci arziki halin uwarta ta gado". Ta dafe kai tare da dade kunnuwa ta wuce ciki da sauri, har tana runtse ido duk don takaicin Bbanta, ta gaji da surutansa na dattijon banza. Allah kadai ya san inda surutansa za su tsaya kan su sauka. Imran yana kallonta, sam ya ji ba dadi a ransa ganin damuwarta karara. Ya yi shiru, sam ya daina jin me Baban yake cewa. A haka ya ja motar suka fice cikin mutuwar jiki da tunanin Mabarukansa. Tun kan su isa yake cewa, ya tsaya da shi ta kasuwa ya shiga ya yo cefane, tunda ya samu kudi kar ya shiga gidan haka nan ta kusan cinye shi saboda bala'i. Bai musa ba ya biya ta kasuwar ya sauke shi, ya sa hanad inda yake ajiyar kudi a motar ya ciro adi, 'yan dubu sabbi kar! Ba ko lankwasa har guda goma ya mika wa Baban yana cewa, "Ga shi Baba ba yawa saboda yau weekend, kuma ba na aje kudi da yawa gida, ka dan rike tukunna". Ku zo ku ga buda baki wajen fara'a, ya dưbi kudin ya dube shi, ya ce, "Duk haka yaro, ba su yi yawa ba?" Ya ce, "Ba komai Bab ka rike dai", 89 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Yana Kirgawa ya ce, "To madallah, Allah yai maka albarka dan nan, wannan ai sai jari, yau ba sai gobe ba". Ya cc, "A'a Baba, ba da haka na ba ka ba, na ba ka ne don ka yi cefane, zan san me zan yi na sana'ar naka, kar ka sai komai". Har yana feso ruwan goro, "To... to... to shi kenan, Allah sa albarka, na gode ka ji ko?" Ya ce, "Ba komai". Ya murza key, shi kuma ya fita yana kara lankwashe kudi aljihu yana washe baki, ya shiga cikin kasuwa, shi kuma ya ja motarsa ya koma gida, dole ne va je ya lallashi 'yar matarsa, sam bai ji dadin ganinta cikin damuwa ba tamkar za ta yi kuka. Duk jikinsa ya yi sanyi, da kyar ya isa gidan, hankalinsa na kanta. NAFEESA FA? Tunda ta shiga adaidaita sahun ta ke share hawaye ba sauti, tana gogewa da hijabinta babban bakin cikinta da za ta koma gidansu gurin matar Babanta, ko kan ba ta jin dadinta, dama-dama ma id Babanta yana gida. A haka dai har ta isa, ta yi sa'a kam Baban na gari ya ga tsayuwarta ta fito bayan ta biya mai motan kudinsa, ta dauko bakaken kaya ta tsugunna kanta kasa cikin ladabinta da kunyarta tana boye idonta ta gaishe shi. Dattijon kirki mai kyawun zuciya da fahinta ya dube ta da kyau, bayan ya amsa gaisuwar ya се, "Mai WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna sunan Inna lafiya dai ko? (kasancewar sunan mamansa ne da ita)" Ta dan dago tare da kakalo murmushin dole iya fuska ta ce, "Alhamdu lillah Baba". Ya ci gaba da kallonta yana son fahimtarta, ya santa sarai, ya san halinta ba za ta taba fadin sharri ba, ko inasifa a bakinta ko da ita ce tare da ita ta kan saya cikin ladabi ba tare da ta fade ta ba yanda hankalin wanda ta ke fada masa ya tashi ba. Cikin hikima ta ke fada, ya ce, "To shi kenan, shiga ciki ga ni nan zuwa kin ji ko?" Ta сe, "To Baba sai ka shigo". Ta mike a sanyaye ta shige da sallama ta shiga. Baba matar Babanta tana zaune tsakar gida ciki rumfa tana kasawa yara kayan miya, ta bi ta da kallo har ta karaso ta samu 'yar kujerar tsugunno ta zauna tana gaishe ta. Kan ta amsa ta ce, "Ashe kwa ke ce din, yara ke ce miu sun ganki kwar gida ashe kwa, lafiya dai ko?" Ta dan yi murmushi ta ce, "Lafiya lau Baba, na zo gidan ne dai". Та се, "То kin zo gaishe mu ke nan, yau an tuno mu?" Ta yi murmushi kawai. Sai can Baban ya shigo hankalinsa tuni na kanta, ya shiga dakinsa yana cewa, "Zo mai sunan Inna". Ta nike cikin nutsuwa tana cewa, "Baba ina zuwa". 91 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Ta shige dakin Baban, ta zauna a kan buzun da yake shimfide tsakar dakin kamar kullum. Ya dube ta shi ma yana daga zaunen, ya ce, "Fada min Innata, na san-akwai abin da ya faru haka nan ba ki zuwa sai kin sanar da ni za ki zo, kuma da ganinki na san akwai damuwa. Fada min mene ne, zan fahimce ki kamar yanda na saba miki" Kalaman mahaifinta sun sa ta dan ji sanyi, da man ta sani za ta samu sauki daga gurinsa, in kowa ya tsane ta shi yana sonta, a kullum yana yabawa da ita, kullum alkhairi yake fada gare ta da sa mata albarka. Wasu 'yan siraran hawaye suka zubo, ta goge cikin nutsuwa da kwantar da hankali ta ce, "Komai yana da iyaka Baba, komai yana da lokaci duk abin da ya samu bawa da sanin Ubangiji, shi ne ya sa shi ciki kuma Shi zai masa magani duk ya jarabta ta zo min Baba na dauke ta ba na fushi da yin Allah, gurinShi zan jira sakamako”. Ya jinjina kai alamar gamsuwa ya се, "Hаka ne, amma me ya faru?" Ta ce, "Aurena da Sulaiman ne ya-zo karshe. Iya inda Allah ya dibar mana kenan ya cika, ya sauwake min auransa". Baban ya yi shiru yana tunani, can ya nisa ya dube ta, ya ce, "Masha Allah, na gamsu hakan da ma Allah ya rubuta, Ubangiji Allah yai muku zabin da ya fi alkhairi da ke da shi, Ya sa hakan shi ne mafi alkhairi gare ku". Ta ce, "Amin Baba". 2 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Ya ce, "To amma nawa ya miki, ko gabadaya ne?" Та се, "А;a daya ne dai". Ya ce, "To idan akwai ci gaban zama tsakaninku in alkhairi ne Allah ya daidaita ku, ku ci gaba da auranku". Ta ce, "Amin". Ya ce, "Allah zaba abin da ya fi alkhairi, amma me ye sanadin kin masa wani abu ne?" Тa сe, "A'a Baba, lafiya muka rabu da shi ba fada bare wulakanci, kawai dai matsalar Innarsa ne, ita ce ta tilasta masa har dai ya yi sakin ba da son ransa ba..." Ta ba shi labarin duk abin da ya faru. Ya gamsu sosai, ya ce, "To Allah ya sauwake, Allah ya shirya mu da ita gabadaya". Ta ce, "Amin". Sun dan taba hira yana kwantar mata da hankali da mata nasihohi, har ta ji sanyi a ranta sosai ta bar wa Allah komai. Ya ba ta shawarar ta gaya wa Allah ya zaSa mata mafi alkhairi. Ta dauki shawarwausa. Ya kara da cewa, "Ga daki can wanda yake kulle sai shirgin kaya, kina iya ciro kayan ki share ki zo ga katifa nan ki dauka kafin mu ga abin da Allah zai yi, har ki gama idda". Та се, "Тo Baba, amma ka bar katifarka zan dai dauki tabarma". Ya ce, "A'a, katifuna biyu, ga wata can a jingine shekaran jiya Aminu ya kawo min ita sabuwa dal! Har 93 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna da bargo wai ya ga ina kwanciya waje kan tabarma, da yake in dakin ya yi zafi na kan sa tabarma da filo in dan kwanta tsakar gida, sai na bar katifar a daki". Ta сe, "To ka ga sai ka yi amfani da ita a wajen zan dai dauki bargon". Ya ce, "A'a, bana son musu, na ce dai ki dauka duk kuma abin da ki ke bukata ki sanar min, insha Allahu ba zai gagara ba, ga babarku nan a dai ci gaba da hakuri da ita kamar yanda aka saba zama da ita, sai hakuri na san kia san ta kanta, ki lallabata har ku rabu 2b lafiya". Tа сe, "To Baba, na gode, zan kiyayeс". Ya ce, "Masha Allah, Allah miki albarkaa rayuwarki, Allah ya yi miki zabi mafi alkhairi gare ki" Ta ji dadi sosai, ta ce, "Amin Baba, Allah kara lafiya". Ya ce, "Amin, amin. Je ki abinki ki huta kada ki damu, ki yi ta addu'a in rabon za ki koma dakinki yau ko gobe sai ki ga kin koma abinki, ki bar wa Allah dai" Та се, "Тo Baba". Tare da mikewa. GIDAN INNA Tun bayan fitarta Sameerar da Innar suka shiga dakin suka hau mata bincike, wai su karya asirin da ta aje. Duk suka birkice mata faki ba su ga wani abu da ya yi kama da sibiri ba. Hakazalika kwandala ba su ci karo da ita ba, ina ma ta bari ya ba ta 'yan kudi idonta na kansu duk ya suka motsa. 94 WAYE ANGON?-3 Maryam jafar Kaduna A haka ya cimmasu a dakin, da ma ya shi raisd d bace ya dawo, kuma ya tarar da wani bacin rai. Ya yi tsayc yana kallónsu cikin kunar rai, duk ba su san yana kallonsu ba, can Samirar ta fago. Ganin kallon da yake mata ya sa ta tsorata ainun, duk ta kama kanta ta dan yafito Inna da ke durkushe tana lalubo. Suka dago suka yi ido biyu da shi, Innar ta dube shi ta ce, "Dukanmu ża ka yi ne da ka ke harararmu?" Ya ce, "Me zai sa in dake ku tunda abin da ku ke daidai ne? Ya dace ku shigo mata daki kuna todid bincike". Ta harare shi son ranta, ta ce, "Ni na kwafde ka, ni za ka gaya wa magana an shigo din". Ya ce, "Ni ma ban hana ku ba, ku ci gaba in kun gama na shigo in dauki abin da ya kawo ni. Ya ja baya tare da samun turmi da ke gefe ya zauna tare da harde hannuwa saman kirji yana jin wani Kuna da radadi a ransa. Ta kalli Samirar ta ce, "Ke zo mu bar masa daki tun kan mu ji saukar duka". Suka fito ta dube shi, ta ce, "Kumaa yanda za a yi da gidana a bar min tarkacen can in na shiga a ga laifina, don haka ina bukatar filin dakina, maza ka sa a kwashe tarkacan can na tsafi, duk an bi an tsafe mana gida da mugun abu". "To". Kawai ya ce ba tare da ya musa ba. A ganinshi doguwar maganar ba ta da amfani, har abada ba za ta taba sauraransa ba. Ta hana masa farin ciki da walwala, duk ta bi ta takura wa rayuwarsa. A yau yanda 95 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna yake ji da ba uwarsa ba ce, da ya rabu da ita har abada. Ba ya jin zai kara wani auren a rayuwarsa, gwanda ya mutu a haka, Allah ya ga zuciyarsa. Ta wuce tana kara cizgar fadanta na ba gaira ba dalili, ya mike ya shige dakin ya kwantar da katifar da suka dage suna duba karkashin gadon. Ya kwanta bayan ya datso kofar. A kasuwar nan ya yi siyayya sosai, tun daga shinkafa, taliya, wake, masara, maggi, mangyada har da dan kwala-dankwalan kajinshi guda uku da cefane ya ciko ledoji dam da kaya. Adaidaita sayu ya yo shata har kofar gida, aka gama sauke masa ya biya ya dauko ya fara shigowa da su jikinsa na rawa, ya rangado sallama. Tana daki ta jiyo muryarsa, tun kan ta fiio ta hau bala'i, "Wallahi yau ba mai raba ni da kai sai Allah, kudina sai ka biya ni kwada..." Abin da ta gani ne ya hana ta magana, ta yi cak! Kalmar ta makale. Ledoji ta gani hannunsa ya tsugunna ya aje, kajin suka leko bankararru, ya juya yana cewa, Maza zo aiki ya same ki": Ya fice. Ta karaso da sauri tana dubawa jiki ya yi sanyi, ya sake shigowa da himilin doya a daure ya dire, ya sake fita ya kinkimo karamin buhun shinkafa ya aje, duk tana tsugunne rungume da hannuwa baki sake da kyar ta iya cewa, "Baban Mabaruka daga ina wadannan garar, ka samu kudi ne?" Ya yi dariya ya fice yana cewa, "Tukunna dai, bari in karasa shigowa da su". Ya fice. 96 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Ya shigo da wasu ledojin ya aje, ta bi shi da kallo, ta ce, "Au har yanzu ba su kare ba?" Ya cc, "Ina?" Yana juyawa. Sai da ya kwaso su gabadaya tas, sannan ya tsaya rike da kugu yana zaro idanuwa, idonsa kan kayan ya ce, "Ho kadi da wuyar samu, amma ba wuyar kashewa. in na gaya nuki kudin kayan nan za ki sha mamaki". Ta buda baki cikin mamaki, "Haba dai?" Ya se, "Sosai, dan samo min ruwa in sha na ci maski yau, sai kora ruwa nake". Ta mike da azana har tana tuntube tana cewa, "Ina ka je ne ka ciyo har ka samo kudi?" Ya ce, "Kawo min dai ruwan". Ta debo a tukunya (randa) ta kawe tana cewa, "Kuma ba sanyi, amma bari in leka in samo yaro ya amso maka ko na leiar nan mai sanyi, ga biyar nan a zanina. Ya yi dariya ya ce, "Ho su Binto manya, an ga ledoji an san bayaniu kwandala ne yau ni ake siyo wa ruwan leda, na randa ma watarana da ya ake ba ni?" Ta wuce tana cewa, "Ba haka b ne Baban Mabaruka, na ga ka shawo rana, duk ka gaji". Ya ce, "Yau ba, sau nawa na shawo ranar ba a ba ni ruwan ba in na ce ki kawo sai ki ce ban san hanya ba ne, ko ban da hannu?" Ta fice tana cewa, "Ina dai zuwa". Karara haka ta siyo ruwan ba tama jira yaro ya siyo ba, ya amsa yana cewa, "Ai ni yau na roba na sha karara mai tsafta" 97 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Ta zauna kasan siminti gabar ledojin, ta се, "Wai ina ka je haka ne?" Ya ce, "Hum ke dai bari, haihuwa mai rana. Gidan Mabaruka mana, ai can na wuni kin ga gida? Gida duk tangaram kana kallon kanka a jiki". Ta rike baki, "Allah Baban Mabaru?" Ya ce, "Abinci kuwa hum uhum ba a magana, nama zako-zako har suna dago hannu ka raba ina sha". Ta ce, "Wai, lallai yau ka shana, in ce su suka ba ka kudi ka yo mana cefane?" Ya ce, "Kudade kai in kin ji kudi 'yan kadan ne, dubu goma mijin ya ba ni, ita kuma dubu uku har da nama ma na ye guzuri, kin ga ledarshi can". Ta hau lalube tana cewa, "Wai wa wai wai lallai yau za mu ci dadi, 'yar Mabaruka daman ba dai kyauta ba. Na san a rina kam, har dubu goma Malam?" Ya ce, "Somin tabi ne ma ya ce zai ba ni abin sana'a, wannan na cefane ne ya ba ni kawai". Ta ce, "Allah Baban Mabaru?” Ya ce, "Wallahi, don haka yau dage-dage za ki ana mu sha ga shinkafa nan da kaji aye su, rabi kuma a yi farfesu, saura a yi miya". Ta ce, "Ai kwa yanzu da ma ba mu ci komai ba". Ya ce, "Ai sai ki tashi yanzu ki yi murhu biyu, ina ma za ki iya irin wanda na ciyo da shi za ki yi, kai yarinyar nan 'yar albarka ce, har mamakin yanda ta iya wannan abincin nake kamar ba hannu yake ba. Shi dai kam ya more, shi ya sa na san kullum yake gida, ga gida duk kamshi ko'ina sanyi-sanyi, dumi-dumi. Ga wata 98 WAYE ANGON?-3 Maryam jafar Kaduna katuwar talabijin a bango, kai! Yau na ga fitsara, mata a zindir ba kaya jikinsu, ka ga mutane kala-kala, kasashekashe hankalinka kwance abinka. Yarinyar nan ta more ta bar ni cikin talauci". Та се, "НHo Malam, ai yau na san za mu sha labari, don kai ba ka iya gano abin labari ba ka yi shiri, dadi dai ka sba, mu ma za mu ci shi yanzu Mabaruka kuma ai ka manta ne, duk randa ta zo in dai tana son cin tuwo za ta ce in barshi ita za ta yi, ta yo cefanenta duk makota sai an jiyo kamshi. Ina lura da kai yanda ka ke sude kwano kana gyada kai, yara ko a hau dambe, ai zakin hannu ne da ita, ina zan iya wannan girki nata?" Ya ce, "To ga shi nan dai ki yi dai iya bakin kokarinki, yau dai na huta da gorinki, kullum bana ba da kudin cefane bayan kin san ba ni da shi in har ina da shi zan yi ko da aljihuna kenan, amma sam ba ki hakuri". Та се, "Нaka ne kuma Baban Mabaruka, in dai kana da shi kana yi tun kan a roke ka. Ka san mu mata sai hakuri da mu'. Ya mike yana cewa, "To ga shi nan dai 'yata ta fitar da ni kunya yau, tun kan mijinta ya ba ni sana'a. ina ma zai ba ni daki, wallahi da na tare a gidan kullum in dinga shan rabar nan, ina asuwaki da cinyar kaza" Та се, "Кai Malam rage dai, kai yanzu sai ka tare din?" Ya juyo yana cewa, "Alkur'an sai na tare". Га се, "Тab! To ba da ni ba wannan abin kunyar, Allah kyauta". Ya wuce yana cewa, "Ba amin ba, sau nawa aka yi?" 99 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Ta ce, "Ban taba ji ba, wallahi kai dai ka tsaya a ba ka sana'ar". Ya wuce yana ćewa, "Sai ki ta yi, ni na fita" Та се, "То a dawo lafiya, Allah ba da sa'a" Ya ce, "Eh tunda kin ga ledoji ba, har dago murya ki ke". Ta tsura wa kayan ido, ta ce, "Tabdijan, ai alkur'an gobe ni ma sai na je, in je in samo nawa rabon. Yaushe zan zauna? Ai mu Allah ya sauwake mana tunda ya kai Mabaruka gidan mai naira, don haka kullum ina can, adashe ma zan shiga". Da wadannan soki-burutsun nata ta tashi ta gangama itace. GIDAN IMRAN A dakinta ya tarar da ita, gidan ya game da Kamshin girkinta. Yar Karaınar tukunyarta akai tana girkawa kanta sabon abinci a kan ta ci wanda ya ci. Ya shaki kamshin tare da cewa, "Hummm dadi". Ta dago ta dalla masa harara, ba ta ce komai ba ta ci gaba da girkinta cike da haushi daa takaici, matar iyaka. Ya tsuguna gabanta cikin kulawa, ya cc, "viy Angel mene ne fushin ne har yanzu? Shi fa Baba ya riga ya tafi tuni ma yana gida". Ta dago tana kallonsa da idanunta da ke nuna tsansarsa karara, ta ce, "Wai ina ruwanka da ni ne ka ke Gamuna? Matsalata ce fa don son Allah ka kyale ni na huta, wailahi na gaji da ganinka kusa da ni, don Allah". Ya yı murmushi, ya ce, "Mabaruka kenan, ke tawa ce haka ni naki ne, don haka mu abu daya ne damuwarki Σ 100 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna tawa ce, za ta dame ni ba zan so na ganki cikin fushi ba, zzan damu ni maa kin ga dai matsala duk tamu ce ni da ke, zama kuma kusa da ke dole ne Mabaruka, saboda kс matata ce, ni kum mijinki ne. ki yi hakuri da haakan" Ta kashe wutar taa mike daf, calander laa dauko masa ta nuna masa, "Ka ga ni yau kwanana nawa gidanka, ga kuma abin da ya rage min na yarjejeniyar da, muka yi da kai, don haka ka daina shige min da yawa, don zan barka ka kuma daina kirana da sunan matarka". Ya yi jim yana kallonta, can ya nisa ya ce, "Well haka ne yanda ki ka fada. Amma a tissafinki idan kin duba ko wataďaya ba ki yi a gidan nan bà bare ki ce kin kusa barinshi, don haka baa yanu bane ya kamata na fara ncsanta da ke ba sai lokacin ya у Ya mike yana kallonta tare da ecwa, "Kin gane?" Ba ia iya juran kallonsa ba ta, dauke kanta zuwa gefe, ya ce, "Bari in tafi in ba ki wuri ko kin samu damar karasa girkinki ki ci zan yi farin ciki da hakar, ba zn so zamanki da yunwa ba". Ba ta jin za ta iya amsa masa, a kagare ta Le ya bar mata daki, ya yi dariya kawai tare da cewa, "Mabaruka manta. Ya budc kofar ya fice gabadaya ma ya bar gidan. mota ya dauka ya nufi gidan Momy. Maigadi ya bude masa get ya shiga da hancin motar tare da mata matsugunni a wurin da ake tanada don haka ya fito, maigadin ya taho baki bude yana masa sannu da zuwa". 101 WAYE ANGON?-3 Maryam Jafar Kaduna Suka gaisa a mutunce kamar yanda suka saba tun yana gidan, ya shige yana cewa, "Zan ganka in na fito" Har da tsalle, ya ce, "To... to... to a fito lafiya, yau na san aljihuna dam". Momy ta fito daga kicin tana fara'a jin sallamarsa, ta ce, "Kai ne da yamma lis?" Ya wuce dinning

Chapter 6 of 11