Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
gani yanda tayin wani mugun rama gaba daya yanayinta  yaacanja               K'asa tayi da Kai Hawaye nakokarin zubowa daga idanuta muryarta narawa  tace Abba   akwai kudi a gunka kabani nasalamin Mai Naffee    Abba yace kishiga ciki zanje nasameshin  shigewa ciki tayi  Dakar ta inya bude baki tayi sallama Mama dake shara sake tsitsiyar dake hannuta  tayi kallon  Ummeey  tayi cike da tausayawa  hawayene suka zubo daga idanun  Mama Karasawa tayi Ida  Ummeey take Kama hannuta tayi tazaunar da ita a kan taburma  cikin murya Mai rauni Mama tace Ummeey  lafiya  Naganki da akwati kiga yanda Kika dawo saikace wace tashekara Tana jinya  Kode kiyin rashin lafiyane Abba nasalamar Mai Naffee din gidan ya shigo Dan bazai inya fita ko inaba  gani Ummeey dayayi bakaramin tayar Masa da hankalin yayiba Zama yayi a gefenta.. Kallo iyayyen nata tayi taga gaba dayasu fuskarsu dauke da   damuwa  A Ranta tace kowane halin zasu tsici kansu idan sukaji  ya Muhammad ya sakeni tausayinsune ya kamata Abba ne  ya dubeta cike da kullawa yace Mamana lafiya kuwa Naganki cikin irin Wana yanayi Hawayene suka zubo daga idonta a hankalin tabude bakinta  tace Abba ya Muhammad ya sakeni  yamin sakin uku Abba tuda ka Aura dani ga ya Muhammad  yake azabtar Dani  haka nake rayuwa a gidansa kullu cikin duka da zagin An wayi gari abuda zanci yafi karfina a gidansa saka makon kwashe kayan Abinci da Momy tayi    "Umma Hauwa itace  tasai da wayanta tamin cefane kayan Abinci ta aika Hauwa takawomin  hata magani  dazan sha. Hauwa ce tasayamin "Wlh Abba nason ace mutuwa ce zata fitar Dani daga gidan ya Muhammad  kodan gani daurewar farin cikika  Abba naki sanar daku halin danake cikine  saboda banason hankalinku ya tashi   fashewa tayi da kuka Itama Mama kuka tasa tace kagani ko Mallam  yariyarna babu iri rok'oka da batayiba  akan kabarta  ta Aure wada take Son ama kaki kace lalle sai zabinka Gashina Kuma zabin naka Yana Neman kashemin Yar, kaduba yada Muhammad ya dawo min da Yar,  wlh daga shin har mahaifiyarsa bazan ya femusu cutarmin da rayuwar Yar,ta da sukayiba" ! Tsantsar bacin Rai ya bayana a fuskar Abba   yace  Mamana kuka ya Isa haka kishare hawayeki   kidau Wana abuda ya faru a matsayin kaddara  wada bamu isa mutsalakeba     Mamana akwai wani Siri dazan sanar dake nangaba kad'a  Anane Zaki gane dagani har yayana Abdallah  mun Aura mikin Muhammad ne don gani mun inganta rayuwarki        Sai gashi abuda muke gudu shine ya faru Share hawayenta tayi  tace Abba kadena bani hakuri nasan bazaka tabayin abuda zai cutar daniba Kuma wlh nadau hakan a matsayin kaddarata  kallon Mama tayi tace Mama Dan Allah kidena kuka banason kisaka damuwa a ranki   komai ya riga da yawuce   Kallonta  Ummeeyn tayi Tanajin radadin a zuciyarta Shikasa Abba    daurewa yake  danji yake Kamar ya zubar mata da Hawaye musama idan ya daura idanusa a kanta              Yakanji zuciyarsa namasa k'una Anya kuwa zai inya yafewa muhammad   iri cutar da yayiwa Ummeey Wayasa ya ciro ya Kira yayanasa  yake sanar dashi  sakin da muhammad din yayiwa Ummeey   shima Abba bakaramin firgici ya shigaba saka makon  jin Wana mumunar labarin yasanar dashi yayi  gashina zuwa gidan yazu, sana ya kashe wayansa ...............Fitowa Abba yayi daga d'akinsa ya Taran da Momy zaune a fallo  tadaura kafa daya kan daya karasawa Abba yayi Ida take fuskarsa babu annuri  yace d'anki ya sanar dake  abuda ya aikata....... Ya mutsa fuska Momy tayi tace  Alhaji in bada abunka akwai abuda My Son zai aikatane batare daya nemin shawarataba     Inade akan sakin Wana yariyarce to  ya sanar Dani ya mata sakin uku saboda bata da kunya batasan darajar  manyaba hanufa tad'aga tamari Meenat  saboda raini  Meenat sa,artace   to ko Mai Aiki gidasu tafi Ummeey daraja da kima shikuma My Son yaga bazai inya Zama da itaba shine ya kad'ata gidasu sana yahada mata da tukunci duka  aini sonayi daya karya banza Cikin bacin Rai Abba yace kun tafka babban kuskure daga ke har d'anki    zakuyi danasani a kan Abubuwa da kuka aikata Fita yayi daga gidan ransa a bace Kai tsaye gidasu Ummeey ya wuce Yana insa ya Taran da Abbata a kofar gidan Shiga cikin gidan sukayi Mama ta shifuda musu tabarma takawo Masa ruwa da Abinci    Itama Ummeey fitowa tayi Durkusawa tayi  a gabasu tagaishe da Abba Shikasa Abba bakaramin tsorata yayiba gani yada tarame talalace  gawani baki da tayi kiyi hakuri Mamana Allah baya barin zalinci shine zai bimiki hakinki akan wadanda suka zalinceki      Shima Abba nasiha ya mata sosai  kudi yabata masu yawa da kyar Ummeey takarba nama Saida Abba yabata Rai sana takarba babu Abuda zatace da Abba saide San barka tutana karama Abba ke da'wainiya da ita harzuwa girmata ................. Meenat nasamu kullawa daga gun Muhammad din komai take bukata Tana samu daga gareshi    Momy tanemo musu Mai Aiki ita takeyi duk wasu ayukan gidan             Abuda Muhammad ya lura dagane da ita batasan komaiba dagane da abuda ya shafin addini  batason yin sallah idan Kuma ya takura mata sai tasaka kuka  gashi shikuma  bayason bacin Ranta haka zai hakura ya kyaleta  ama Abu Yana damusa  gashi   ko wankan tsarki batayin saide  tayi wankata da sabulu  Zaune suke a fallo suna kallo, tadaura kanta a kan cinyarsa sallama sukaji dago Kai Muhammad yayi  yaga Ashe Momy ce Murmushi yayi yace  Momy barka da zuwa Zama tayi a kan kujera tace yauwa My son Kallon Momy  Meenat tayi tace  Hy !! Momy y kk? Momy tace lafiya Lou Meenat y gida ?  Yatsina fuska tayi tace normal!!    Ama Momy ya kamata idan zakizo kina  sanarwa Dan gaskiya banason Ana zuwa min gida batare da nabada izziniba Daure fuska Muhammad yayi yace baki da hankaline Meenat  Momy nawa kike fadawa haka to kishiga hankalinki  Kuka tasa tace baby nikakeyiwa hayaniya kasanfa banason anamin fada... DAGA ALKALAMIN Ummeey Muhammad Lawan      Yar Autar dashen Allah_*ZAƁIN🤵🏻‍♂ABBANA👳🏼‍♂*_ _*NA*_ _*UMMEEY MUHAMMAD LAWAN*_ _*(UMMUH AFNAN)*_ _*"YAR AUTAR💃🏻DASHEN🌲 ALLAH*_ https://www.facebook.com/profile.php?id=100087451774783 https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=2192729347574173/?ref=share _*FACEBOOK LINK*_ https://www.facebook.com/groups/2192729347574173/?ref=share_group_link _*WHATSAPP LINK*_ https://chat.whatsapp.com/CnAupcS3i8c4y3JHVuXYXA _*DASHEN🌲 ALLAH*_ _*WRITER'S ASSOCIATION📚📚*_ _*ALLAH SHINE GATAN MU*_ _{ƙungiyar dashen allah ƙungiya ce ta jajurtattun marubuta kuma tsayayyu masu aiki da ilimi wajen rubutunsu dan ganin sun kawo muku labari wanda zai wa'azantar daku ilimantar daku, faɗakar daku.}_ *Alƙalami✍🏽 yafi takofi🗡️* FOR MORE INF... 08140801885 Page 77 & 78 _______________" Rugumeta yayi a jikisa I,m Sorry Baby  rainane ya b'acin  banji dadi maganar da Kika fadawa Momy ba Momy zata inya zuwa gidana a duk lokacin da taga dama  Turro, bakin tayi tace  nifa Baby banason a yawaita zuwamin gida  in Kuma Momy tanace sai tazo to gaskiya saide nabarma  gidanka ' Kallon Momy tayi tace , Sorry Momy  kizauna a gidanki Ida kina bukatar gani Baby  sai kikirashi a waya zaizo har gida ya sameki                Dan banason ganin tarkace a gidana mikewa tsaye Momy tayi  cikin b'acin Rai tace amade yariyar nan baki da kunya          Nida gidan 'Da,na  zakice sai nanemin iziniki agunki  kafin nazo to wlh kiyin kadan yariyar kibin a hankalin in kuma  bahakaba yazu , yazu zansa ya sakeki tuda baki da mutunci         Kuka Meenat tasa tafara buga k'afafu  Baby kanajin   abuda take fadamin wlh bazan yardaba sai kadaukamin Matakin a kanta                  Muhammad ' kasa ya kullule yarasa ya zaiyi da Wana lamari   ga ran Momynsa  ya b'acin sai banbami takeyi Ga Meenat sai kuka take jin kuka nata  yake har cikin ransa   please....Baby   kidena Wana maganar  tayaya Zan dau mataki akan Momyna  kikwantar da hankalinki yazu zata barmiki gidanki share hawayenki  kiga banason gani bacin ranki Share hawayeta tafarayi tace to Baby tatafin yazu Dan nagajin dajin hayaniyar nan                  Kallon Momy yayi yace Momy kiyi hakuri Meenat yariyace karama yarintane yake damunta  muje namaidaki gida            'Momy tsabage b'acin Rai kasa yin magana tayi   Fita zasuyi daga Fallon Meenat tace Baby Ina zaka Kuma ? Juwowa yayi yace zankai Momy gidane ama bazan dadeba Ina kaita zan dawo         Kallonsa tayi karmar Mai Shirin yin kuka  cikin shagwaba tace  nifa babu idan zaka kabarni nikad'an a gidan   gulma da ya kawota shizai Mai data              Muhammad yace Momy kiyi hakuri kije gida nima inaxuwa anjima takaicine ya Kama Momy masifa tadingayi  zagin Meenat Muhammad sai hakuri yake Bata Fita tayin daga gidan Rai a bance shikuma Ida Meenat din take yanufa sai wani cin magani takeyi rarashita yafarayi Dan a duniya babu Abuda yatsana sama da bacin Ranta ................... Yau kimani wata biyu kena da dawowar Ummeey gidasu tafara murmurewa kyauwuta ya fara dawowa Dan   Tana samu kullawa daga gun iyayyenata   Fitowa tayi cikin shirita  ta iske Mama a tsakar gida  Tana wanke wanke tace Mama sanu da Aiki  dama Ina son zanje gidasu Hauwa ne   bata masan nadawo gidaba Kallonta Mama tayi tace aiko da kinkyauta kigaishesu. Ummeey tace to zasujin insha Allah Tashi Ummeey tayi tace Mama sai nadawo Mama tace a dawo lafiya Tana fita gidasu Hauwa  tanufa   Tana shiga gidan tatara da Hauwa a tsakar gida Tana wanki  karasawa tayi tarugumeta tabaya tare da fadin nayin kewarki Yar,uwata Murmushi Hauwa tayi tace nima haka Sister wlh kulun cikin tunaninki nake  d'azuma Saida mukayi hiranki da Umma take Tabayana yaushe zanje nadubaki  Ummeey tace Allah sarki Umma ai wlh sisters babu Abuda zace daku  saide Adu.ah Keni banji motsin Umma ba kode batanane  Hauwa tace eeeh wlh Umma tafita unguwa gashi sai yamma zata dawo Wai nikan Sister meye sirrine Naga kincanja bakamar Ranar danaje gidanki nagankiba wlh sister dana dawo gida kasa barci nayin  sai tunaniki nakeyi Murmushi Ummeey tayi tace kiyin hakuri sister nasan namiki laifi ban sanar dake cewa nakai kimani wata biyu Ina gidamuba Aurena ya mutu  ya muhammad ya sakeni batare da wani Abu ya shiga tsakanina dashiba Farin cikine ya lulube Hauwa tace Alhamdulillah  Allah nagodema daka cire k'awata daga cikin wanan k'angin   Ina rok'on Allah daya gagauta saka Miki  iri zalincin da ya Muhammad ya Miki                  Murmushi Ummeey tayi tace sister  zaifi kyau  mumanta da baya mutinkari gaba Allah Dee yasa inya bakin  wahalar kenan Hauwa ta Amsa da Ameen Cigaba sukayi da hiransu cikin kwanciyar hankalin kamar karsu rabu   Ummeey batabar gidasu Hauwa ba saikusan yamma                   BAYAN. WATA HUDU ..................Yau kimani wata hudu da mutuwar Auren Ummeey   kwance take a kan gaddo    zuciyarta cike da tunanin Haydar din  tunani take ta Inna zata fara nemansa  Dan a yazu bazata inya rayuwa  da kowane dan, namijiba idan bashiba Zubur tamike sakamokon tu,nawa da wasikar da yaturo Adam ya kawo mata a cikin wasikar yasaka number wayasa  Ida yace idan Tana bukatar temako tasanar dashi tashi tayi tabude wata jakar litatafai Ciro wasikar tayi hamuta na rawa tafara daukar number   Kiran layin tayi tajin ya danga cikin zazakar muryarsa Mai narkar da zuciyar yace..... DAGA ALKALAMIN Ummeey Muhammad Lawan Yar Autar dashen Allah_*ZAƁIN🤵🏻‍♂ABBANA👳🏼‍♂*_ _*NA*_ _*UMMEEY MUHAMMAD LAWAN*_ _*(UMMUH AFNAN)*_ _*"YAR AUTAR💃🏻DASHEN🌲 ALLAH*_ https://www.facebook.com/profile.php?id=100087451774783 https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=2192729347574173/?ref=share _*FACEBOOK LINK*_ https://www.facebook.com/groups/2192729347574173/?ref=share_group_link _*WHATSAPP LINK*_ https://chat.whatsapp.com/CnAupcS3i8c4y3JHVuXYXA _*DASHEN🌲 ALLAH*_ _*WRITER'S ASSOCIATION📚📚*_ _*ALLAH SHINE GATAN MU*_ _{ƙungiyar dashen allah ƙungiya ce ta jajurtattun marubuta kuma tsayayyu masu aiki da ilimi wajen rubutunsu dan ganin sun kawo muku labari wanda zai wa'azantar daku ilimantar daku, faɗakar daku.}_ *Alƙalami✍🏽 yafi takofi🗡️* FOR MORE INF 08140801885 Page 79 & 80 _____________"HELLO!!!!! HELLO!!!!! Sauti muryarsane ya dakin dodon kunanta wada hakan ya hadasar mata da farin ciki a zuciyarta Ajiyar zuciya tasauke Mai karfi hawayen farin cikine suka zubo daga idanuta cikin muryarta Mai sanyi  tace  Haydar........ Ummeey ce sai Kuma tafashe   Mikewa yayi tsaye ciken da mamaki yace Ummeey  Ashe dama zank'arajin  wanan zazak'ar muryarna taki wace take sani farin ciki Koda Ina cikin bacin Rai Kukan Mai kikeyin kidena kuka   kukaki nad'agamin hankalin kunuwan Haydar bazasu inya jure jin kukan  Ummeey ba Share hawayenki Ummeeyna kisanar dani maike faruwa Share hawayeta tayi tace Haydar nakirakane domin nasanar dakai  Aurena ya mutu nakai kimani wata hudu Ina gidamu Lumshe idanu yayi ya budesu yayi a hankalin zuciyarsa cike da farin ciki Bude bakinsa yayin yace   Alhamdulillah Allah nagodema daka dawomin da farin cikina   dama inajin a jikina duk da anyin sanadiyar rabani dake watarana dolle Zaki dawo gareni Allah bazai taba barisu suk'wacemin keba sai gashi cikin ikon Allah kin dawo gareni Wani dadi Ummeey tajin Yana ratsa dukan sansan jikinta Murmushi tayi gamin da fadin hakika Kai masoyin gaskine   bayin gangancin baka   Amanar zuciyataba  Yaushe zakazo Gombe  danyin bayin ga shukar da tadade Tana  bukatar ban ruwa Ummeeynka  namararin kallon Wana kyakyawar fuskarna taka wace ke dauke da annuri a Koda yaushe Murmushi yayi yace gobe Insha Allah Zan shugo Gombe !!!  Gombe  gari masoyiyata                       Lumsheee idanu tayi tanajin wani sanyi a cikin Ranta budesu tayi fuskarta dauke da  Murmushi tace Allah Ubangijin ya kaimu gobe da Rai da lafiya              Amsawa yayi da Ameeen sana sukayi sallama zuciyoyinsu  cike da son ganin junnasu  k'urawa waya dake hannusa yayi idon    gani  lamari yake tankar a mafarki daga hanuwansa yayi sama ya Allah idan mafarki nake ya Allah kada kabani ikon farkawa yazu            Murza idonsa ya farayi yaga abun a zahiri yake faruwa   murmushi yayi gamin da fadin koyanzu  Naga ribar hakurina  yau ga Ummeey a  hanuna Ya Allah kaji Tausayina kada kabari tasake kufcewa daga gareni                              Kiran wayan  Adam yayi  Adam dake kwace a d'akinsa yaji wayasa na ringing daga wayan yayi dauke da far,a akan fuskarsa  hello, Haydar kana lafiya ?           Lafiya lau nake Abokina Ina cikin farin ciki wada ya mamaye dukan sansan zuciyata   Adam Ashe rabon mutun bazai taba kubce masaba  Auran  Ummeey  deee baiyin Rai ba  yazu take sanar Dani takai kimani wata hudu a gidasu babu  Aure a kanta Mikewa Adam yayi zaune cikin mamaki yace Haydar  kana nufin Ummeey bata da Aure Auran Ummeey ya mutu                     Alhamdulillah duk da ba,a farin ciki  da mutuwar Aure ama  a wanan karo nakasance cikin jin dadin  dajin mutuwar Auren Ummeey                             Ina tayaka murna Abokina  da dawowar masoyiyarka gareka  yanzu yaushe zamu Gombe              Haydar yace nariga nasanar da Ummeey gobe Insha Allah muna hanya Adam yace to Allah ya kaimu gobe           Haydar yace Amiin ama Dan Allah banason Rukkayah tasan  da maganar mutuwar Aure Ummeey Rukkayah Tana da kishin  sosai wlh mudin tasan Aure Ummeey ya mutun  to daga ranar nayi bankwana da farin ciki  a cikin gidana har yazu Rukkayah bata Dena fushi daniba saboda suna Ummeey danasawa yar'ta   Taki tafitar da Wana Abu a rainta.               Wlh kishin Rukkayah har tsoro  yake bani Adam yace   kwantar da hankalinka Abokina  dazaran mun dawo daga Gombe zansamu Rukkayah zan mata bayani insha Allah komai zai tafin daide Haydar yace nagode Abokina gobe karfe 8:00 zamu tafi Adam yace Allah yakaimu gobe kashe wayansa yayi  yanufin  gidan Koda ya insa gida ya Taran da Rukkayah zaune a fallo tanayiwa Ummeey wasa itako sai kyalkyallewa  da dariya takeyin Zama yayi a gefenta sanu da dawowa tamasa Amsawa yayi dauke da far'a akan fuskarsa  hannu yasa  dauki Ummeey       Kallon Rukayyah yayi yace Momy Ummeey gobe inaso zanyi tafin  kallonsa itama tayi tace Allah yakamu gobe ama wane gari zaka  Haydar yace Gombe zani           Gabantane ya fadin kallonsa tayi cike da tuhuma  mezakayi a Gombe bayan nasan baka da yan'uwa a can        Ina da yan'uwa a Gombe Mana ko kin manta Kakarmu Inna  nacan tare da Adam zamu tafin Zamu kaiwa  Inna ziyara kiga ai zataji dadin ko  Kallonsa take batare da tayin maganaba zuciyarta naraya mata Abubuwa daban daban                                   WASHE GARI Damisalin karfe 8:00 Adam ya inson gidan Haydar Rukkayah gaishe da yayannata tayin fuska a hade Dan ita bata yarda dasuba gaba dayasu haushi yayan natane ya kamata       Musamama da takalin  fuskar Haydar din taga sai murmushi yake sai kace wani sabon ango Haydar yace Rukkayah zamutafi kikulamin  da kanki kikulamin da  Ummeey na  zamu wuce sai Allah ya dawo damu lafiya  Dak'ar ta inya bude baki tace a dawo lafiya Allah ya kiyayye hanya  kwana nawa zakuyi        Haydar yace kwana biyu zamuyi    shuru tayi batare da tace komaiba  Fitowa sukayi daga gidan suka shige mota suka dau  hanyan Gombe Haydar sai far'a yake bakisa yaki rufuwa Damisalin karfe 12 :30 suka in son cikin gari Gombe  tsayawa sukayi a masalacin sukayi sallah Anguwarsu Ummeey suka nufa          Ummeey sai shirye shirye tarbar Masoyinata takeyi girki tayi musu shikafa da wake da Mai da yajin  sai kunu ayyah Dan tasan Haydar din nata dason Abinci gargajiya zuwa tayi tashiya ciki shigar doguwar riga  kayan bakaramin kyau suka mataba  wayatane tayi Kara dauka tayi takara a kunenta  fuskarta dauke da murmushi Sallama tayi Amsawa yayi yake sanar da ita suna kofar gida  kashe wayan tayi cikin sauri tanufi hanyar waje Tana fitowa tatar dasu  tsaye jikin mota kallon kallon sukeyiwa juna zuciyoyinsu cike da shaukin So  wani kyau yaga tagara Masa duk da rama dayaga tayi hakan bai hanashi gani kyautaba  sallama tamusu sana tagaishesu Amsawa sukayi gaba dayasu suka Amasa. a hankalin tabude bakinta tace  Haydar.... Ashe Idanuwana zasu Kara ganika" Allah nagodema  daka dawo min da masoyina a Lokacin Dana cire Rai dasamusa Murmushi yayi yace Ummeey ai Mai Rai baya fitar da Rai daga rahama Ubangiji  kullun  inajin a jikina watarana Zaki dawo gareni burimu Zai cika namalakar junamu      Saide akwai maganar da nakeson sanar dake Ummeey.... nayin Aure dago Kai tayi da sauri tadaura dara daran idanuta a kansa tace  Haydar kayi Aure?        Eh nayi Aure Ummeey har Allah ya azurtani  da samun karuwa yar'mace   Ummeey tace  natayaka murna   lale wanan matar takasance Mai sa,a a rayuwa tasamu mijin daya tankar ya dubu  dazan ganta Dana Bata shawara tarike mijinta hanu biyu  Dan samu irinsa a fadin duniyarna sai Ansha wuya Mamakine ya Kama Haydar  gani yada bata nuna damuwarta akan Auren da yayiba  lalai Ummeey tadabace a cikin mata      Kallon Adam Ummeey tayi tace Adam Naga kayi shuru bakace komaiba murmushi Adam yayi yace  Mai zance Amaryamu ai Wana zance namasoyane            Saide namiki wani albishin wada shi Haydar din ya manta bai fadamikiba  Itama murmushi tayi tace Ina sauraroka  Adam yace Ummeey  saboda irin son da Abokina yake Miki  ya dau alkawari idan Allah yabasa yar' mace zaisa mata sunaki Sai gashi  Allah ya azurtashi da samu yar' mace Kuma yasamata sunaki Wani dadi Ummeey tajin Yana ratsata tace  Haydar  Ashe kaunar  dakamin hartakai haka kasawa Yar,ka sunana wayo dadin  zanso Naga Wana yariyar zason gani yar' masoyina   Allah yarayamin Mai sunana Haydar Kai masoyine nagaskiya Ina Alfahari dakai Haydar Mushiga cikin gida kucin Abinci kuhuta shiga sukayi cikin gidan Ummeey takawo musu Abinci  zuba musu tayi a plate         Basu wuri tayi Dan susamu sucin Abinci Suna gama cin abincin sai ga Abba ya shigo mamane take sanar dashi zuwansu Haydar din  karasawa yayi Ida suke gaishesa sukayi cike da mutuntawa. an wanan karo Abba yajin dadin zuwasu Haydar din   Adam ne yace Abba yauma  de musake  dawowane a kan maganar Aure Ummeey dan Allah Abba katemaka kabawa Abokina Auren Ummeey Kallonsu Abba yayi yace na'amince zan bawa Haydar Aure Ummeey Ama Ina da sharadin  zaka turomi mahaifinka a gabansa  zan fadamuku sharadina  idan kun Amince to Zan Baku Aure Yar,ta zufane ya karyowa Haydar Abba yace kakwantar da hankalinka Haydar Wana karo bazan hanaka Aure Ummeey ba saide idan kune kukaga bazaku inya Aurentaba... DAGA ALKALAMIN Ummeey Muhammad Lawan Yar Autar dashen Allah_*ZAƁIN🤵🏻‍♂ABBANA👳🏼‍♂*_ _*NA*_ _*UMMEEY MUHAMMAD LAWAN*_ _*(UMMUH AFNAN)*_ _*"YAR AUTAR💃🏻DASHEN🌲 ALLAH*_ https://www.facebook.com/profile.php?id=100087451774783 https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=2192729347574173/?ref=share _*FACEBOOK LINK*_ https://www.facebook.com/groups/2192729347574173/?ref=share_group_link _*WHATSAPP LINK*_ https://chat.whatsapp.com/CnAupcS3i8c4y3JHVuXYXA _*DASHEN🌲 ALLAH*_ _*WRITER'S ASSOCIATION📚📚*_ _*ALLAH SHINE GATAN MU*_ _{ƙungiyar dashen allah ƙungiya ce ta jajurtattun marubuta kuma tsayayyu masu aiki da ilimi wajen rubutunsu dan ganin sun kawo muku labari wanda zai wa'azantar daku ilimantar daku, faɗakar daku.}_ *Alƙalami✍🏽 yafi takofi🗡️* FOR MORE INF 08140801885 Page 81 & 82 ______________Adam yace toshikenan Abba  babu damuwa insha Allahu zamu sanar da Dady sak'onka  Kuma nasan Dady zai yarda da duk wani sharudanka matukar bai sabawa addiniba Zamu tafin masaukimu zuwa gobe zamu dawo wata killama tare da Dady zamu dawo Abba yace Allah ya kaimu gobe Atare suka Mike tsaye    sukayiwa Mama sallama Ummeey fitowa tayi daga d'aki domin tayi musu rakiya Kallon masoyin nata tayi taga yanayisa gaba d'aya ya canja  gabantane yafadin cikin tashin hankalin  tace  Haydar  Wana karoma Abbana yakin Amince da maganar Auremu  koh wayooo Allah nashiga Ukuna  sai Kuma tafashe da kuka Mai cin Rai Kallonta Haydar yayi gamin da fadin menene abun kuka anan bafa abuda kike tunanibane Abba ya Amince zai bani Aurenki. Ummeey tace Adam dagaskene abuda yake fada kode akwan wata matsallane kuke boyemin Murmushi yayi yace  gaskiya Haydar ya fada mikin  Ummeey tace tomeyasa naga yanayiku gaba daya  ya canja  bayan ba a haka kuka shiga  gidamuba kushiga gidamu   dauke da far,a akan fuskarku Kun fito Kuma fuskarku dauke da damuwa        Dan Allah kusanar Dani Mai Nene dalilin canjawarku    Murmushi Haydar yayi yace Ummeey Abba yace zai bani kee naturo Dadyna  ama Kuma akwai sharudan dazai kafa Mana              Hankalina yatashine saboda bansa wane irin sharadin Abba zai kafamanaba yazu kishiga gida zamuwuce gidan Inna idan muhuta zankira Dady nasanar dashi  duk yada mukayi  da Dady zakijini zuwa dare  Ummeey bazanbar Gombe ba har sai Abba ya baniken  An tsai da Ranar bikin sana Zan koma Kano      Murmushi tayi tare da fadin Allah ya Amince zanso gani Wana Rana Mai cike da dinbin tarihi            Ranar da muka Dade Muna mafarkin zuwata Murmushi yayi yace Zan wuce Ummeeyna saimuyi waya Toh Allah ya tsare Ango Ummeey Dady  Ummeey  dariya yayi Dan har cikin ransa yajin dadin Wana suna data kirasa dashi                Shigewa Mota Adam yayi tare da fadin idan nabiyema  Haydar saimu akwana anan batare da kasaniba Dan Naga kuna cikin shaukin son             Kallonsa yayi gamin da fadi wlh Adam Idan inatare da Ummeey mantawa nake da komai a cikin wanan duniyar                 Subar kofar gidasu Ummeey batare da son ran Haydar ba  gidan Inna suka nufa  Inna tayi farin cikin daganinasu susamu tarba tamusama daga gun Inna       Haydar ya Kira Dady yake sanar dashi  duk abuda ya faru bai Boyemasa komaiba   Dady ya Masa Alkawari gobe zazo yasamu Mahaifin Ummeey   farin cikine ya Kama Haydar  wada ya bayanna a kan fuskarsa             Yasanar da. Adam yayi  yada sukayi da Dady shima Adam yajin dadin da Dady ya  amince zaizo gobe     Dady yasanar da Ammy mutuwar Aure Ummeey Kuma gobe zaije Gombe nemawa Haydar din Aure Ummeey Ammy tayi farin ciki sosai tayi musu Allah yasaya alkairi.                 WASHE GARI Damisalin  karfe 1:30  Dady yashigo cikin gari Gombe kira Haydar yayi yasanar dashi insowarsa Haydar da Adam  ne sukaje Taran Dady Basu bata lokaciba suka nufin gidasu Ummeey dama Kuma Ummeey  tasanar da Abba Mahaifin  Haydar din nazuwa yau shima Abba yasanar da yayanasa   zuwasu       Abba da yayanasa suyi matukar farin ciki da zuwan Dady sun karbesa cikin girmamawa da karanci shikasa Dady yajin dadin irin karamawar da yasamu daga gun su Abba            Dady yace Alhaji  nide  sunana Alhaji Museen nine Mahaifin Haydar  Allah ya jarabin Haydar da son Yar,ka  wada kaddara tazo lokaci guda tarabasu    Haydar yashiga cikin mawuyacin halin sakamokon rasa Yar,ka da yayi   Dan bakaramin son  yakemataba  sanadin hakan   ya harfar Masa da ciwo zuciya mutsici kamu cikin tashin hankalin         Musha wuya sosai kafin musamu Haydar ya dawo hayancinsa              Jikin Abba yayi Sanyi tausayin Haydar din yakamasa lalai bai kyauta musuba yayi sanadiyar shigarsu cikin wani halin ya jefasu cikin garari to Yaya zaiyi dolle sumasa Uzuri shima ba,a son ransa ya aikata hakanba yayi hakane domin inganta rayuwar Yar,tasa  kallon Mahaifin Haydar din yayi yace... DAGA ALKALAMIN✍🏻 💞Ummeey Muhammad Lawan💞      🥰Yar Autar dashen🌲 Allah. _*ZAƁIN🤵🏻‍♂ABBANA👳🏼‍♂*_ _*NA*_ _*UMMEEY MUHAMMAD LAWAN*_ _*(UMMUH AFNAN)*_ _*"YAR AUTAR💃🏻DASHEN🌲 ALLAH*_ https://www.facebook.com/profile.php?id=100087451774783 https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=2192729347574173/?ref=share _*FACEBOOK LINK*_ https://www.facebook.com/groups/2192729347574173/?ref=share_group_link _*WHATSAPP LINK*_ https://chat.whatsapp.com/CnAupcS3i8c4y3JHVuXYXA _*DASHEN🌲 ALLAH*_

Chapter 9 of 14