Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
mikinfa       Murmushi takaici tayi tare dafadin Ya Haydar dama Kai a tunanika nicema zamuku breakfast ita wace kakwana a gunatan bazata muku breakfast diba      Ya Haydar kafitamin daga d'akina bana son ganika ai dama nafadama turanar da nashigo gidanka bazan iya hada mijin dawata yan'maceba  Rashine yabaci take yanayisa ya canja  idanuwasa sukayi Jan      Yace Rukkayah nikike d'agawa murya kike fadamin bak'ake magaganu saboda nakara Aure         Too inason sanar dake Ummeey itace zabin Raina Ummeey itace mace da nafara son a rayuwata   har gobe banida Kamar ta Kuma banajin zan inyayiwa wata yan'mace son danakewa Ummeey kema shedace akan hakan      Dan haka kishiga hankalinki kishi ba hauka bane  wlh idan kikace Zaki rainani a gidana  bazaki taba jin dadi a gunaba     Mikewa tayi tsaye cikin masifa tace Ya Haydar kayi duk Abuda zakayi wlh dadai nake dakai  tudaga Ranar daka Bude baki kace an daurama Aure da Wana figagiyar yariyar kafita daga Raina Daga hanu  yayi zai mareta saikuma ya tsaya cak      Girgiza Kai yayi cikin bacin Rai yabar dakin yanufi bangare Ummeey Yana shiga ya tarda ita zaune a fallo Tana ganisa tamike tsaye fuskarta dauke da Murmushi tace barka da dawowa Habibi      Murmushi karfin halin yayi yace Habibty Ina Kika shiga d'azu natashi bangankiba      Murmushi tayi tace Habibi ina can kitchen Ina had'a Mana breakfast Cikin mamaki Haydar yace breakfast Kuma kina Amarya Kika shiga kitchen Murmushi tayi tace muje mukarya ko Habibi Tudaga Wana lokaci  kullu Ummeey ita takeyin girkita har lokaci data cika sati guda a gidan Hayda    Haydar yasanar da Adam iri Abubuwa da Rukkayah take Masa Adam dakansa ya zo har gidan yasameta yamata fada sosai  Ammmy itama tazo gidan  tahadasu tayi musu nasiha akan sujin tsoro Allah suzauna da junasu tsakani da Allah            GOMBE         Tuda Muhammad yasanar da Meenat Abubuwa da suka faru  Meenat tace  bazata zauna dashiba yazamo dolle ya saketa  Rashi mutunci take zuba Masa na yau daban nagobe daban Da Abu ya Ishesa yaje yasamu Dad dinta yasanar Masa halin dasuke ciki    Dad yace Kai dama kasan Mahaifin naka matsiyacine shine kazo ka Auri Yan,tah Too yazamo maka Dole karabu da Meenat Dan ba ajinka bace nifa dama na Aurama Meenat ne saboda Naga Mahaifika sananeni a garina    Too ama tuda Har Arziki banasabane too wlh yazamo Dole kasaki Meenat        Dan bazata zauna da matsiya ciba Babu irin cin mutunci da  Dad din Meenat bayiwa Muhammad ba    Haka Muhammad yabar gidan cikin takaici da danasani Aura Meenat gidasu Muhammad yawuce ya Taran da Momy da Abba zaune Durkusawa yayi a gabasu yace_*ZAƁIN🤵🏻‍♂ABBANA👳🏼‍♂*_ _*NA*_ _*UMMEEY MUHAMMAD LAWAN*_ _*(UMMUH AFNAN)*_ _*"YAR AUTAR💃🏻DASHEN🌲 ALLAH*_ https://www.facebook.com/profile.php?id=100087451774783 https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=2192729347574173/?ref=share _*FACEBOOK LINK*_ https://www.facebook.com/groups/2192729347574173/?ref=share_group_link _*WHATSAPP LINK*_ https://chat.whatsapp.com/CnAupcS3i8c4y3JHVuXYXA _*DASHEN🌲 ALLAH*_ _*WRITER'S ASSOCIATION📚📚*_ _*ALLAH SHINE GATAN MU*_ _{ƙungiyar dashen allah ƙungiya ce ta jajurtattun marubuta kuma tsayayyu masu aiki da ilimi wajen rubutunsu dan ganin sun kawo muku labari wanda zai wa'azantar daku ilimantar daku, faɗakar daku.}_ *Alƙalami✍🏽 yafi takofi🗡️* For more information 08140801885 Page 101 & 102 Barkaku da hutawa  Abba  dago Kai Abba yayi ya kallesa tare da fadin  yauwa barka de Muhammad   dafatan kuna lafiya ya iyalin       D'ago Kai Muhammad yayi tare da sauke idanuwasa akan Abba cikin sanyi jiki  yace Abba Babu lafiya tun  Ranar da Meenat tasamu  labarin  dukiyarka ta Ummeey ce          Tudaga Wana lokacin tabi tad'agamin hankalin Wai ita bazata zauna daniba saide narabu da ita             Yazu hakama daga gidasu nake nasanar da Dad abuda kefaru saide shima Dad yace Meenat bazata cin gaba da Zama daniba           Mikewa tsaye Abba yayi yace Wana ai matsalarkuce Kai da Mahaifinyarka                       Kafun yayi wata magana. Abba. Yabar gun ya wuce d'aki                 Momy nagani Abba ya shige. daki  takalin. d'anata ciki tausayawa tace My Son yaushe raboka daxuwa gidanan  kaga yada duk kabi karame sai kace wada yayin jiya            Shima kallon Momy yayi tare dafadin Momy ai komai jinya baikaini shiga cikin tashin hankalinba Momy inason Meenat banason rabuwa da ita Dan Allah  Momy kitemakeni muje kibata hakuri tayi hakuri mucigaba da zamamu   Momy idan narasa Meenat zanshiga cikin tashin hankalin          Hararasa Momy tayi cikin k'unar Rai tace My Son  kokaki ko kason yazamoma dolle karabu da Wana yar'iskar yariyar     Yariyar dabata San mutuncin kaba bare har kayi tunanin zata mutuntani a matsayina na Mahaifinyarka kaduba iri cin mutuncin da yariyarna tamin  ama wai kana ikirarin cewa bazaka iya rabuwa da itaba saboda ita tahaifeka          Wacece Meenat da har kake tunani bazaka iya rabuwa da itaba akwai Mata kyawawa a duniyarna wada sukafin Meenat  My Son kana da kyauwun da kwar jini wada duk wata Yar Mace zatason kakasance  Mijinta                       Tashi zakayi mutafin gidanka a gabana nakeson kadan k'arawa Meenat saki d'an d'an har guda uku                        Sana narama irin wulakanci da tayimin  tashi mutafi  nasan Abbaka bayazu zai fitoba zanje har nadawo batare da yasaniba       Mikewa Muhammad yayi jikinsa a sanyaye suka nufin gidanasa           Suna shiga sukatara da Meenat zaune a fallo  Tana gani Momy tamike tsaye cikin tsiwa.  tanuna  Ta da yatsa 👉tare dafad'in      Wakekan wace iri  maran zuciyace nace bana buk'atar ganiki a gidana Ama saboda naci sai kizo  too wlh idan ke manyace saide kicin kanki Dan nikan nafin karfin...Bata karasaba tajin saukar Mari a kan fuskarta         Kafin Momy tasauke hanuta daga kunci Meenat itama Meenat din tashararawa Momy Marin  jikake Tasssssssss                Wani hucin Muhammad yayi ya danko  Meenat ya fara dauketa da Mari Yana dukanta keeee Dan Ubanki Mahaifiyata Zaki Mara saboda baki da kuyan tooo wlh yau sana kusan kasheki a gidanan       Bai bartaba Saida yamata duka lilis  sana ya kyaleta  tare da hada Mata da tukwuncin saki har guda uku      Dakar Meenat ta iya daga kafafuta tanufi daki saboda dukan da Muhammad din ya Mata bana wasa bane     Momy ko zuciyarta tayi fari kyal take  tanemin duk wani bacin Ranta tarasa         Momy batabar gidan ba har Saida taga tafiyar Meenat Muhammad dakasa ya maida Momy gida  Abba barcisa yakesha Dan baimasan bata gidan ba      Meenat Tana insa gida tasanar da Mom irin dukan da Muhammad yayi Mata  masifa Mom tadigayi tace baza yardaba yau saitaga waye gatansa a garin Gombe Kiran Dad tayi a waya tasanar dashi  ran Dad bakaramin bacin yayiba  a ransa yake ayyana irin wulakanci da zaiyiwa Muhammad                                       GIDAN  HAYDAR Haydar  nanunawa Ummeey Tsatsar kauna wada har baya iya boye iri Son dayake  Mata  gawani irin  kullawa da yake nunamata          Itama Ummeey bata dawani buri da yawuce taga tasanya mijinata cikin farin ciki  duk wani abuda tasa zai farata Masa shitakeyi         Tana bashi kullawa tamusaman Tana riritashi  takar jariri  shikansa Haydar jishi yakeyi tankar wani sarki sai  a  yazu ya Kara tabatarwa Ummeey itace farin cikinsa   musamama gani irin kullawar da take nuna Masa Tare da Yar,sa  Ummeey k'arama   gawani irin shakuwa data shiga tsakanisu  Ummeey Bata samu nutsu idan bataga yariyar a kusa da itaba duk da irin wulakanci da Rukayyah kemata akan yariyar ama hakan baisa tayin zuciyaba  Dan jin yariyar take a rain tankar ita tahaifeta            Wani lokaci idan taje daukarta haka Rukkayah zata hanata taita fada Mata bakaken maganganu itama yariyar Tana ganita zatafara zillo Tana kuka sai taje gun Anty nata      Takaici ya Kama Rukkayah  duk kuka da Ummeey k'arama zatayi bazata barta taje gun Ummeey ba saide idan Haydar dine ya dauketa ya kaita gun Anty nata shikasa Haydar Yana mamakin sauyawar Rukkayah lokaci guda takoyo  wasu munanan d'abi,u marasa kyau         Haka rayuwa taci gaba da tafiya duk Ranar da Haydar yake d'akin Ummeey to a Ranar daga ita har Haydar din suna cikin fari da Anashuwa  idan Kuma zai koma d'akin Rukkayah  da kuka suke rabuwa wani lokacin saboda kewar mijinata har kasa barci takeyi  Dan bakaramin shakuwa sukayi a Soyayyah ba wada takai takawo basa son  suyin nesa da juna       Shima a bangare nasa hakane take kasancewa  duk Ranar da yake d'akin Rukkayah jishin yake tankar maraya  Dan Bata da Aiki sai mita da k'anana magaganu  Kuma hakan nafaruwane tadalilin zafin kishin datake dashi Zaune take tanayiwa Ummeey k'arama wasa sai kyalkyalle Dariya sukeyi  Mikewa Ummeey tayi zubu sakamokon tunowa da tayin da photuna da Mama tabata  na Mahaifiyarta  wada kwata kwata tamata dasu sai yazu tatina dasu  d'aki tanufa  tadauko jakar dawo Fallon tayi Tazauna   kusa da Ummeey k'arama            Bude jakar tayi tafara fito da photuna idanuwata suka sauka akan photo wata farar Mata kyakyawa  Tana murmushi aka dau photo ga hakworin makka sanye a bakita        Tsirawa photo idon tayi tanajin kaunar Mahaifiyarta nashigarta Hawaye sukafara zirya akan fuskarta                   Zuciyarta namata rad'ad'in tausayi Mahaifiyartane ya cika Mata zuciya cin gaba da kallon photuna take   kallon photon  Mahaifinata Dana Mahaifiyar Tata  take kuka tasa tare dafad'in Allah yajikanki Mahaifiyata   Allah ya Kai Haske cikin kabarinki  inama  ace Mutuwa batayin gagawar rabani dakeba  Dana kalin wanan kyakyawar fuskarna taki  dana kwanta akan ciyarki nima najin d'umin jinkin Mahaifinta wayoo Allah  mutuwa tarabani da Mahaifiyata batare da najin dumin jikintaba Kara fashewa tayi da kuka Mai sauti              Shigowa Fallon yayi bakisa dauke da sallama a rude ya yakarasa Ida take  yace Subbahananllah Habibty Mai yafaru kike irin Wana kuka sanar dani cikin gagawa tukan zuciyata tabuga       Sai a lokacin Haydar ya lura da photuna dake gabanta  gabansane ya fadin hanu yasa ya dauki photuna zare idanu yayi yace Habibty.... Ina kikasamu photo Anty Aysha    Kukan tane ya tsaya cak idanu tazira Masa tace  Wana itace Mahaifiyata  sune photuna da   Abba kefadin Mahaifiyata tabashi a lokacin da take Shirin barin duniya         Zare idanu Haydar yayi yace Ummeey karde ace kee. Yar' uwatace  Wana ai Anty Aysha ce k'anwar Dadynace   Uwa  daya Uba daya  kimanin shekaru Ashirin kenan da b'acewarta Babu Ida Dady bai nemin Anty Aysha ba ama bai sametaba idai hakan takasance sainafi kowa farin ciki            Ummeey k'aramace tasa kuka sai a lokacin Haydar ya lura da ita daukarta yayi tare da Ciro wayasa a Aljihusa Kiran Dady yayi Dady dake gida zaune suna hira shida Ammmy yajin wayasa nakara d'agaawa yayi yace Assalamu alaikum...       Cikin zumud'in Haydar yace wa,alaikumu sallam Dady Albishirika  dariya Dady yayi yace yau Kuma nazamo kakanka kenan       Haydar yace wlh Dady yau nazomaka da Albishi  wada zai dawo maka da farin cikinka wada ya dad'e da gushewa             Dady yace kayya  kaide Haydar fadin duk Abuda kakeson  fad'a Ina sauraronka amani Babu abuda zai dawo min da  farin cikina Haydar yace koda sanar dakai nayi nasamu Labari Anty Aysha Zaro idanu Dady yayi tare da mikewa tsaye yace  Haydar Ina wasa dakaine ko son kake kafamemin tabo daya dad'e a zuciyata        Haydar yace wlh Dady dagaske nakema  Ashe Ummeey yar' Anty Aysha ce dazu Naga photo  Anty Aysha a gun Ummeey      Dady yace katabata Haydar photo  yar'uwata Aysha kagani  Wlh Dady Anty Aysha ce tun lokacin da Abba Ummeey yasanar damu Labari Iyayyan Ummeey  sai nake gani kamar Anty Aysha ce Mahaifiyar Ummeey ama sai zuciyata takasa gaskata hakan     Ajiyar zuciya    Dady  ya sauke Mai k'arfin tare da fadin  Ganinan zuwa gidan naka yazu kashe waya Dady yayi   Haydar nagama waya da Dady Kiran Adam yayi yake sanar dashi  komai Adam bai bata lokaciba ya inso gidan Kallon Ammmy  Dady yayi yace tashi mutafin gidan Haydar yazu yake sanar Dani Matarsa  Ummeey yar' Aysha ce        Mamakine ya Kama Ammmy  tayaya Haydar yasa  Ummeey Yar Aysha ce Mayafin Ammy tadaka suka nufin gidan Haydar din suna insa  Dady ya kurawa Ummeey idon  sai a lokacin Dady ya lura da komai nata na Aysha ne  turanar da ya fara ganin Ummeey yaga taso tayi Kama da Yar,sa fatima      Dauko photunan Haydar yayi ya nunawa Dady da Adam kallon  photuna Dady  yayi sai yafashe da kuka Mai tsuma zuciya yace  Tabbas Wana koshaka Babu  Aysha ce   taho gareni  Yan'tah kizauna kusa dani Dan najin kamshi Yar, uwata atare dake Ashe kedin jinace Karasowa tayi ta dukusa agaban Dady tace Dan Allah kadena zubar da hawayenka akan Abuda Allah yarigada ya tsara Mana          Karasa K'anwarka a lokacin da bakayi zatoba sai gashi cikin rahamar Ubangiji Allah ya hadaka da jinita a lokacin dabaka taba tsamaniba Share hawayesa Dady yayi ya Ciro wayasa yakira Abba Ummeey yasanar dashi cewa shine yayan Aysha Abba yayi farin cikin sosai  dajin Wana dadad'an labari yace Suma gobe Insha Allah zasuzo  Kano A Ranar Dady yayi kukan farin ciki godiya yayiwa Allah daya kaddara haduwarsa da yar' Aysha itama Ammmy farin cikine ya cika Mata zuciya tare da Taya  Dady murnar haduwa da yar' Aysha Dan ita kanta tasan irin  kaunar dake tsakanisa da yar'uwar tasa Adam kaga ikon Allah ko Ashe Ummeey yar' uwatace nikaina Ina mamakin irin zazafar kaunar danakewa Ummeey  har nakejin a Raina dana rasata gyara narasa Raina         Murmushi Adam yayi yace HAYDAR ai jini daya ya wuce wasa                    WASHE GARI Da sasafe Su Abba sukaka dau hanyar Kano  Muhammad shikejan  Motar sai Abba dake kusa dashi Mama  Abba suna gidan baya       Sushigo Kano kicin kwoshin lafiya Haydar  da Adam susuka tarosu A Wana Ranar bakin Ummeey yakin rufuwa saboda murna gani iyayyenata  a Wana Rana su Abba suga karamci da girmamawa daga gun Haydar da Iyayyesa        Bayan su Abba sunci abinci suhuta   Abba yace Yaya Abdallah ya kamata muyi Abuda ya kawomu Dan a yau mukeson komawa Gombe      Dady yace yakamata kubari zuwa Gobe sai kutafin Dan a yau inason Muje har Bauchi Muhada Ummeey  da Mahaifita Alhaji Sadiq Abba Muhammad yace  badamuwa da yau da gobe duk dayane a guri Ubangijin      Abba yadubin Dady yace Alhaji  kaga yarda Allah yake ikonsa   Aysha Tasha yawo bulayin Neman kan ama Batasamekaba      Harta koma ga Allah Tana Mai mararin gani fuskar yayanta Ama Allah bai nufaba       Abba yasanar da Dady komai tudaga Ranar da ya fara ganin Aysha a bakin shagonsa         Kuka Dady keyi Kamar wani karamin yaro Yana tuna irin shakuwar da sukayi da yar' uwarsa  cikin Kuka Dady yace  inata Kiran wayan  Aysha ba,a dagawa daganan jikina yabani da Akwai matsala nakira wayan mijinta anane yake sanar Dani an nemin Aysha ba a gantaba nashiga tashin hankalin da rudani bad'an kad'anba A Ranar natafi  Bauchi nabada cikiya gidajen Redio da Talevion Ama ba a daceba Aysha ita kada'nce Yar Uwata bani da kowa sai ita haka itama Bata da kowa saini  tsawan Wana lokaci kullun zuciyata da tunani Yar uwata take kwana take tashi har nakamu da cutar hawan jini        Gaba daya wada suke gun Saida suka tausayawa Dady  rabuwa da d'an uwa akwai zafin  Dady shikadai yasan irin rad'ad'in dayakeji a ransa  shima Haydar kuka yake tare da tausayawa Mahaifinashi Dan tuda yake da Dady nasa bai taba gani kuka Shiba sai yau    Dakar Su Abba suka samu suka rarashi Dady sana yayi shuru  ama yanajin ciwo rabuwa da Yar,uwarsa       Ammy itama kuka take Dakar Akasamu sukayi shuru       Rukkayah jikintane yayi sanyi nadama da danasani suka shigeta Ashe Ummeey yar' Uwar mijin natane. Kiran Alhaji Sadiq Dady yayi yake sanar dashi gasuna zuwa gidan nashi Tashi sukayi gaba dayasu suka dau hanyar Bauchi   suna insa cikin garin Bauchi Kai tsaye gidan Alhaji Sadiq suka nufa  Suna insa gidan  Alhaji Sadiq Da kasa ya fito ya tarbesu cikin karamawa Cikin suka shiga ya kaisu katafare Fallosa na Alfarma  wata datijuwa ce tashigo hanuta dauke  da Fruit  ta anjiye a gabasu  Sana tagaishesu Hajiya Saratu ce tafito cikin takun k'asaita tazauna kusa da Mijinata ko kallonsu  Batayiba barai susa ran ran zata gaishesu       Bayan sugama gaisawa  Dady yace Alhaji Sadiq  yau muzo maka da babban Albishin   wada zai sanyaka cikin farin cikin maran yankewa  farin cikin da bazai taba gushewa daga garekaba  har Ranar da zaka koma ga mahalincinka Alhaji Sadiq kakalin Wana yariyar da kyau dawa tamaka maka  Dady yanuna Ummeey  d'aura idanusa yayi akan Ummeey sai yazabura ya Mike tseye   tare dafadin Alhaji Museen Wana yariyar Bata da maraba da Aysha Gani Wana yariyar danayi ya famenin tabo dake zuciyata  Allah sarki Aysha kitafi kibarni cikin tunaniki                     Alhaji Museen kahaifin yariyar Mai Kama da Aysha Dady yace Alhaji Sadiq bani nai haifintaba Wana yariyar Yar,kace  Yar,da Aysha tahaifa  cikin rudun Alhaji Sadiq yace Dan Allah Alhaji Museen kada kamin wasa da zuciyata Dady yace Alhaji Sadiq tsakanina dakai Babu maganar wasa Ummeey Yar,kace  take Dady yasanar dashi duk Abuda ya faru hata Labari haduwarsu da Haydar hazuwa Aure Dady bai boye musu komaiba Alhaji Sadiq jiyayi tankar Amasa bisha da Aljannah  rike hanu Ummeey yayi tare dafadin Museen kayi gaskiya Wana yariyar jininace Allah sarki Aysha Allah ya jikanki Allah yasa mutuwa tazamo hutu a gareki      Durkusawa yayi a gabansu Abba yace Alhaji nagode nagode Allah yasaka maka da mafifincin alkairi  kirikemin Yar,ta riko nagaskiya duk wada yaga Ummeey yasan tasamu tarbiya Tagari  kallon Mama yayi yace Hajiya nagode Allah ubangijin yasaka muku da Alkairi Abba yace Dan Allah Alhaji kadena Mana godiya wlh duk abuda mukayiwa Ummeey bamu fadinba Ummeey Takasance Yan,Tagari wada muke Alfahari da ita tuda muke da Ummeey Bata taba tsalake Umarnimuba K'arrra Hajiya Saratu tasa Tana tsale tanafadin shikena tawa takare dama boka yace duk sanda nabari Wana yariyar tazo duniya ide sukayi idon biyu da Alhaji shikena duk wani kullin danayi zai warware shikenan       Sai Kuma tafara dariya Tana fadin. Alhaji Nina maka asiri narabaka da danginka nice nasa Aysha tabar  gidanka Nina turo Yan,daba  akan sukasheta shine tagudu wayo nacuci kaina dariya Saratu take iya karfita Tana fadin tacuci kanta cire Dan kwalin tayi tabaza gashita tabar gidan aguje   Kowa nagun sai Allah wadare yake da halin Saratu shikasa Alhaji Sadiq jiyayi Kamar an sauke Masa kaya Mai nauyi  akansa saka makon Asiran da suka warware atare dashi     Ummeey kuka take tare da tausayawa iyayyenata Hirace tabarke a tsakanisu  Alhaji Sadiq yakira Yan uwa da dangi yasanar dasu haka suka diga zuwa suna gani Ummeey  dagi gaba daya sucika   da farin cikin gani jini Alhaji Sadiq din Dan dama Yana fama da rad'adin rashin Haihuwa Kyautuka masu yawa sufito daga hanu Alhaji Sadiq.  Daga cikin harda kyautar kujera makka ya bawa su  Abba hada Dady da Haydar da Adam harda Rukkayah da Mama da Muhammad          Sanan kowane su ya hada musu da  mukulin Mota  godiya sukayimasa Mai tarin yawa tare da Aduoin samu nasa a rayuwa Alhaji Sadiq ya rokin Alfarma agun Haydar akan  yabar Masa  Ummeey tayi Koda  sati guda   sanan yayi Masa Alkawari  da kansa zai maidata har Kono Haydar de ba a son ransa ya Aminceba  Dan a zahiri gaskiya baya kaunar yayi nesa da Matarsa  ama Babu yada ya inya haka suka bar Bauchi batare da Ummeey ba Sun Abba sukoma Gombe cikin farin cikin  da murnar sada yar'tasa da Mahaifinata Ummeey nagani soyayyah da kullawa daga gun Mahaifinata   harma da dangisa  kowa nahaba haba da ita Kullun suna tare da Mahaifinata  yana   Bata Labari irin Zama dasukayi shida Mahaifiyatata itama tasanar dashin iri rayuwar da tayi da irin gata da Abba da Mama suka nuna Mata A Ranar da tacika Sati a Ranar ne Mahaifinata ya maidata har gidanta  tare da daleliyar sabuwar  motar  Haydar yayi murna da dawowar Ummeey  Dan bakaramin kewar juna sukayiba            BAYAN WATA UKU Jirgisu ya  tashin zuwa kasa Mai tsarki domin gudanar da aikin hajjin tun acan Ummeey take fama da kasala da rashin jin karfin jikin Tun bayan tafiyarsu Abba aiki hajjin Alhaji Sadiq  yaje Gombe yasa aka rushe gidan Abba akamasa gini zamani    tare da zuba masa kayan Alatu a gidan Saida Aka Gama komai Sana Alhaji Sadiq yasanar dasu Abba             Godiya Abba yadiga Masa tare da  Adu,oi masu tarin yawa      Bayan sugama aikin hajin su dawo kasarsu Nijeria su Mama da Abba suka wuce Gombe           Abba yacika da mamakin gani yanda gidansa ya koma tankar nawani hamshakin Mai kudin   farin cikine ya Kara lulube Abba da Mama lalai Ummeey Alkarice a garesu  godiya suka Kara yiwa Alhaji Sadiq Rukkayah tanemin yafiyar Ummeey akan Abubuwa data aikata Mata take Ummeey tayafe Mata sun hada kansu suna zaune lafiya hata girki  tare sukeyi  renon Ummeey K'arama ya koma hanun Ummeey                  BAYAN WATA SHIDA Ummeey tahaifin Dan,ta namijin Ranar suna yaro yacin sunna Abba Ummeey wato Muhammad za,Ana cemasa Shurabeel Abba yayi farin cikin dasamu Mai suna  Ummeey  Takoma   wankan  gida nama dak'ar  Haydar yayarda  Saida Ammy tasa baki sanan ya yarda suka tafin da Mama Mamace tace Ummeey kiga muma mun dawo Yan,gayuko Mahaifinki Alhaji Sadiq shine ya canja Mana rayuwa ya Mai damu Yan,gata Anane Mama take sanar da ita irin Abu alkairi daya musu harda su Gwogwo Asabe        BAYA    KWANA  ASHIRIN Haydar yazo dubasu shida Adam Kuma Alokacine Adam Yaga Hauwa  yaji takwanta Masa a Rai Ya Muhammad Kuma tuda Ummeey tadawo wankan gida yake zuwa gidan suta hira Kamar ba muhammad din daya tsanetaba           BAYAN SUN GAMA WAKA Ummeey taje har gidasu Hauwa tagaishe Da Umma Sana tabata kudin masu tarin yawa  Umma taita godiya sosai Ummeey tace Umma kidena godemin wlh bazan taba manta alkairiku gareniba            A Ranar da zata koma gidanta Saida tayi kukan rabuwa da Iyayyenata Haydar dakansa yazo ya daukesu  suka koma Kano Hauwa da Adam soyayya  suke zubawa bana wasaba                BAYAN SHEKA BIYU Rukkayah tahaifin d'an namijin yaro yacin suna Dady Museen za Ana kirasa da Shaheed Baya haihuwar Rukkayah da wata biyu Ummeey tasake Haihuwar d'an namijin yaro yacin sunna Adam za Ana kirasa da Shureen Momy har Kano tazo neman yafiya agun Ummeey  Ummeey tace aini Momy nariga da nayafe Miki tuda jimawa godiya Tadigayimata Tana samata Albarka Ummeey tajin dadin zuwa Momy tahad'a Mata Tara ta Arziki Sana tayi tafiyarta An  daura Aure Hauwa da Adam sutare a gidansa dake kusa Dana Haydar  Fatima ma sudawo uguwar da Zama Alhaji Sadiq Mahaifin Ummeey ya Aure Gwogwo Halima dama mijinta ya dade da mutuwa suna zaune lafiya  Hajiya Saratu kan hauka muraran sai bin jujin takeyi Mahaifin Meenat  nakan hayarsa  tazuwa gidasu Muhammad daniyar ya wulakantashi yayi hadari Mota yasamu karaya a  ciyoyisa guda biyu gashi bayasa ya bugu baya iya komai saide Amasa Meenat tayi bak'in tarame tadawo Abu tausayi taje tasamu Muhammad akan yayi hakuri ya Mai data d'akinta ama shin Muhammad yakin kuka take Tana danasani kashe Aureta datayi Su Abba sucigaba da kasuwancisu Kuma Allah yasawa kasuwanci Albarka dukiya sai habaka takeyi idan kukaga Abba da Mama Bazaku ganesuba Muhammad yasamu wata yariya Mai suna Hafsat ya Aureta suna zaune cikin rufin Asirin       BAYAN SHEKARA DAYA Hawa tahaihu tahafin Yar, mace yariya taci sunata zainab Ummeey k'arama tagirma tayi wayo sosai yariyar Mai shiga Rai mutane Rayuwa tayiwa Haydar dadi Haydar yazama d'an gata a gun matan nasa Sumai dashi tankar wani Sarki ALHAMDULILLAH. ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH DUKAN YABO DA GODIYA SUTABATA GA ALLAH MADAUKIN SARKI WADA YA YONI YA YON KOWA ALLAH MAI DARE MAI RANA ALLAH KAYIN DA'DIN TSIRA GA SHUGABAMU ANNABI MUHAMMADU SALLAHU ALAIHI WASSALLAM INA KARA GODEWA ALLAH MADAUKIN SARKI DA YABANI IKON GAMA WANAN LITAFIN MAI SUNA ZABIN ABBANA CIKIN KOSHIN LAFIYA  ABU DA NARUBUTA DEDE INA ROKON ALLAH YASA YA ANFANA MUTANE WADA KUMA NAYI KUSKURE ALLAH YA YAFEMIN INA MIKA SAKON GODIYA GAREKU MASOYAN WANAN BOOK NA ZABIN ABBANA MUSAMA MASU COMMENTS INAYIN KU SOSAI DINA💞💞 ALLAH YABAR KAUNA ❤️ MUHADU A SABON LITAFINA MAI SUNA SHAGALIN AURE DATIJO ZAIZO MUKU NAN BADADADEWABA                      An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura

Chapter 13 of 14