rai babu daɗi.
Sai bayan sallar isha'i baba ya shigo gida sam innah batai masa maganar ba har sai da yaci abinci ya zauna a tsakar gida yana sauraron labarai a Radio.
Innah ta aje masa kofin Furar data damo masa.
Ya dube ta tare da cewa.
"Hafsatu mai yake damunki ne? gaba ɗaya tinda na shigo gidan nan na fuskanci yanayin ki ba daɗi"
Innah ta rausayar da kanta gefe cike da zurfin ciki tare da danne abin da ke cin ƙasan ranta tace.
"Babu komai Babansu ga furar nan ko sai anjima zaka sha?"
Baba ya fuskance ta.
"Haba Hafsatu bafa yau na sanki ba, wallahi shiyasa inna ga Sadauki ya ɓoyen abin da ke damun shi nakan ce barewa batai gudu ɗanta yayi rarrafe ba, yanzu dai faɗa mini mai ke damun ki?"
Ya faɗa yana maida hankalin shi kaco kam izuwa gareta.
"To inda hali Babansu ina neman alfarma da abar batun haɗa sadauki da wannan yarinya ƴar wajan Amadu wallahi abin babu arziƙi sam kai kaga cin zarafin da maryam taiwa yaran nan yau haba talauci hauka ne shima baya so nima bana so dama dannewa nake kuma nike tausar shi akan auren"
Ta faɗa tana haɗe fuska.
Baba yayi dariya.
"Ikon Allah wato ku dai mata bakwa rabo da cece kuce, To yanzu so kike na zama ƙaramin Mutum ɗan uwana ya bani kyauta nace bana so kome?"
Innah ta kuma haɗe fuska cikin rashin sukuni tace.
"Tinda abin ba daraja ba martaba a haƙura kawai"
Baba ya kama haɓa.
"Haba Hafsatu shifa shaiɗan baya son ƙulla alheri gaba ɗaya bamu san mai ke tattare da wannan aure nasu ba"
Cikin zafin da bai santa da shi ba tace,,,
"Meye acikin auren in ba ta shin hankali ba........
Da sauri yace.
"Kefa uwa ce Hafsatu kada kiwa auren nan mugun baki"
Lokacin hawaye ya fara sauka daga saman fuskar Innah abin da yayi matiƙar ɗagawa Baba hankali kenan cikin kuka! tace.
"Shekaru Kusan Arba'in muna tare da kai Muhammadu baka taɓa saka doka na karya maka ba baka taɓa zuwa da abu na musa maka ba amman don Allah ka janye auren Sadauki da wannan yarinya tinda shima ba sonta yake yi ba kawai biyayya ce yake yi maka"
A ɗan fusace Baba yace.
"Sabida bakya ƙaunar Jinina Haɗin zumuncin ne bakya so shikenan zan gani tsakanin ni da ke waye zaifi rinjaye akan wannan lamari"
Da sauri tace.
"Kai ne zakai rinjaye"
Ta faɗa tana goge hawayenta.
Lokacin Saadik ya shigo gidan wanda sauran ƙarashen maganar ta sauka a cikin kunnen shi.
Ya nemi guri a bakin Ƙofar Kitchen ya zauna ya tsirawa Innah ido wanda idan idon nashi bai masa gizo ba hawaye yake gani a saman fuskar Mahaifiyar tashi.
Baba miƙewa yayi cikin fushi yama fice daga gidan gaba ɗaya.
A hankali Innah ta ɗago tana cewa.
"Kaga ni ko sadauki wallahi bana son auren nan bana so bana so!
Kalmar data firgita Saadik ta hargitsa masa zuciyar shi kenan.
Hannun shi biyu ya saka ya rufe fuskar shi yana jan numfashi gaba ɗaya Jikinsa rawa yake hankalin shi yayi mugun tashi.
Ya kai minti goma a haka kafin ya ɗago manyan idanunshi waɗanda suka sauya launi zuwa jajir ya zubawa Innah yana fesar da Huci zazzafa.
Muryar shi a raunane ya ce mata.
"Haƙiƙa innah nafiki tsanar wannan aure wallahi innah nima bana son shi bana ƙaunar shi ban san meye yasa Baba ya kafe ba"
Sauran maganar ta maƙale masa sabida Jin muryar Baba akan shi.
"Idan ka auri Rabi'atu ka saka wuƙa ka yankanta Abubakar Saadik! daga nan zan san kai cikakken maƙiyinta ne kuma zanyi maganin ku daga kai har uwar taka tinda naga abin babu arziƙi"
Gaba ɗaya Baba ya birkice musu kamar ba shiba faɗa yake ta inda ya shiga ba tanan yake fita ba seda yayi wa Innah da Saadik kaca kaca sannan ya sa kai ya shige ɗaki.
Innah ta zabga tagumi shiko Saadik ta shi yayi yana rangaji yabar tsakar gidan.
Ya shiga cikin yanayi marar daɗi ranar sai bacci ɓarawo a idanunshi amman duk juyi fushin mahaifin shi da ɓacin ran mahaifiyar shi akan auren yake haskowa.
Shi baba idanunshi ya rufe ne akan haɗin zumunci ita kuma innah cin zarafin da akaiwa ƴaƴanta ke cin ranta har taji ta tsani auren.
Zaɓin wa zaibi?
Daya gaji da juyi, sai ya miƙe ya shiga toilet ya ɗaura alwala ya shiga jera sallah yana faɗawa ALLAH damuwar shi yaji daɗin zuciyar shi yaci kashi casa'in da tara na daga cikin damuwar shi ta kau dalilin daya sa har ya sami bacci mai nauyi wanda ya kusan makara a sallar asubahi agurguje yayi wanka yayi alwala ya fita masallaci yana idar da raka'atul fijir liman ya tada Iƙamar sallah ya maida ajiyar zuciya Allah ya taimakeshi ya samu raka'atul fijir ɗin, ba a tada ba hakan yabi sahun sallar bayan sun idar ya zauna yayi azkar sannan ya fito cikin gida ya shiga ya gaida Baba wanda ya amsa mai gaisuwar da ƙyar sannan ya ƙarasa wajan Innah dake damun koko a kitchen ya tsugunna ya gaishe da ita.
Yana saka hannu yana tura mata wutar ɗumamen tuwon data ɗora.
Cikin kwantar da murya yace.
"Don Allah don Annabi Innah ki bar sanya damuwar auren nan aranki nina barwa Allah komai kuma wallahi tinda na barwa Allah in har auren nan babu alkairi rushewa zai yi"
Innah ta maida ajiyar zuciya.
"Sadauki haƙiƙa cin zarafin da maryam taiwa yarannan ya ɗagan hankali da shi na kwana ga ɓacin ran mahaifinka amman tinda ka ambaci Allah magana ta ƙare nima zan cigaba da addu'a akai"
Ya lumshe idon shi dayay masa nauyi ya warasu akanta yana cin tsananin damuwar daya gani a tare da ita.
A hankali yake kwantar mata da hankali harta sake.
Don ya ƙara kwantar da hankalinta yasha kokon yaci ɗumamen tuwon da farar safiyar duk da bai kari a wannan lokacin.
Sannan yayi mata sallama ya tafi ɗaki agurguje ya shirya ya fita kasuwar ƙofar ruwa.
Don kai kaya.
***********
Momi ta sheƙe da dariya tana cewa.
"Tsinannu gayyar tsiya ai nice maganin ku"
Ko kallon kayan batai ba ta barsu a wurin.
Ita kam adaah bata ma san wainar da ake toyawa ba tana can ɗakinta tana kukan takaici.
Abbah da magariba ya shigo gida yadda yaga kayan ne ya bashi tabbacin masu kawo kayan basu sami tarbar arziƙi ba.
Aiko tindaga parlour yake kiran Momi ranar taga tijara domin cewa yayi akan auren zai iya sakinta.
Data ga ba haza shine tahau bashi haƙuri.
Ranar Abbah yayi kwanan takaici washe gari wajan ƙarfe goma ya dira agidan Baba.
Lokacin Baba yana ƙoƙarin fita kasuwa Abba ya ƙaraso haka suka juya cikin gidan haƙuri Abba ya dinga bawa Baba duk da bai da tabbas na abin da Momi taiwa masu kawo lefen amman ya tabbata bata shuka abin kirki ba musamman daya kira Iyah mahaifiyarta tace sam Momi bata faɗa musu maganar kawo kayan lefen ba.
Baba ya dubi Abba yace.
"Amadu wannan ban haƙuri da kake kamar nace maka Sadauki ba zai auri adawiyya ba ka kwantar da hankalin ka akan wannan lamari komai zai tafi yadda bakai zato ba cikin alheri"
Cikin sanyin Jiki Abba yace.
"Hankali na ya tashi da lamarin Maryam haƙiƙa banyi dace da mace ta gari ba, gaba ɗaya Halin Rabi'ah na uwarta ne, In har ta auri bare ba zasu zauna lafiya ba Ina ji ajikina auren rabi'ah kamar wani nauyi ne da zan sauke kafin fitar Numfashi na"
Da sauri baba yace.
"Ka bar faɗin haka amadu ni ban da kamar ka, duk shirme suke itama hafsatu ta damu ko wacce bata son auren mu toshe kunnuwan mu alheri muka nufa kuma shi zai ƙullu Sadauki yayanta ne koba aure shi mai tsaya mata ne da ikon Allah"
Da ire iren wannan Baba ya samu hankalin ɗan uwanshi ya kwanta koda suka fito innah da ƙyar taiwa Abbah sallama muryarta a shaƙe ranar anci sa'a domin a motar Abba suka fita Abba ya aje baba a kasuwa shi ma ya wuce tasa.
Iyaye mazan sun toshe kunnuwan su daga cece kucen matansu domin ita ma innah ta riƙe wuta sosai akan lamarin musamman da Anty nafi ƙanwarta ke ƙara rura mata wutar ƙin auren sai dai Baba da yake yafi ƙarfin gidan shi tara ƴaƴanshi yayi kaf yace bai lamunta wani ya ƙara sukar auren ba da wannan aka samu sauƙi.
Shiko Abba komai na shawarar biki baya tinkarar momi Iyah yake faɗawa hatta kayan lefen ma ya ɗebe su ya kai gidan iyah sabida haka koda biki yayi saura kwanaki bakwai iya ta sayi goron rabo ta saka Mariya ta kakkai gidan danginta sabida ganin take taken matan yasa Baba yace wa Abba ya tsaida ranar biki domin ko Saadik ɗin ma baba bai faɗawa ba, sai da Bikin yayi saura kwanaki bakwai.
Baba ya kira saadik ɗin ya shaida masa duk yadda saadik yaso baba ya ɗaga masa ƙafa amman baba yaƙi yace ko bukka ce ya saka matar shi.
Da damuwa saadik ke shaidawa Innah wadda sam baba bai shawara da ita ba, cewa tai kada ya ɗaga hankalin shi abin da Allah ya hore mishi yayi ita kam ba taro zatai ba tinda abin yazo a ƙure iya ƴan uwanta kaɗai zata faɗawa.
Gaba ɗaya saadik ya shiga busy gidan daya kama suka shiga gyara shida su Nura ƙanin Nura yayi paint a gidan wanda Falo ne guda ɗaya sai ɗaki aciki sai banɗaki da Kitchen duk a falon.
Ɗan ƙarami ne gidan irin na zaman mutum ɗaya.
Bai sami nutsuwa ba sai ana saura kwana biyu daurin aure su Nura ne suka bugo katin ɗaurin aure suka shiga rabo Babawo yayi musu ɗinki shaddar ɗaurin aure duk su huɗun.
Ana gobe ɗaurin aure Iya ta saka Abbas ya kaita gidan Momi wadda ta saki jikinta sam batai zaton da bikin bama sabida Abbah baya bibiyar ta akan lamarin shiyasa ta saki jiki akan aikin malam yaci maganar aure ta mutu zasu yi son ransu ita da lubna shiyasa suke ta ƙulla yanda za'ai Mahir ya turo manyan shi.
Ƙaramin hauka momi ta shiga yi sanda iya ke sanar da ita tazo tafiya da Rabi'ane sabida gobe za'a daura aure a wuce da ita gidanta.
Momi kuka Adaah kuka sai da Abba yayi jan ido sannan Adaah tabi iya domin ko kayanta ma bata haɗa ba, Abba yace a kai mata su daga baya.
Komai na momi ya tsaya cak sai faman zage zage take kuma tace ba zata taka ƙafarta gidan bikin ba Hajiya lubna tafi momi shiga tashin hankali data ji maganar amman data tina zagon ƙasan datai sai taji bata damu da auren ba tasan dole adaah zata fito ɗanta ya aure ta, domin ba burin ta auren adaah ba burinta dukiya.SO DA ALƘAWARI....! littafin kuɗi ne 500 Naira zuwa asusun bankin 0078174806 sterling bank ko kuma 9022260850 Opay bank, Shaidar Biyan kuɗi zuwa 09022260850, Ƴan Private waɗan da ba sai nayi adding ɗinsu a grp ba ta Private kawai zan dinga tura musu 1000 Naira ne in sha Allah.
[12/16, 10:27] Autar Manya: *SO DA ALƘAWARI..!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
*13*
Da tsananin ɓacin rai yake shiga cikin gidan nasu, yadda ya tarar da mutane a tsakar gidan nasu suna ta ɗaga kayan cikin akwatinan abin ya bashi mamaki ba kaɗan ba.
Ya tokare a bakin rijiya tare da zuba hannayen shi a saman ƙirjin shi sabida yadda ranshi ke ɓace baya tinanin ma na tsakar gidan sun ji sallamar da yayi.
Innah ce ta farga da tsaiwar ta shi ta taso ta iso inda yake tana cewa.
"Sadauki! lafiya na ganka a tsaye ka ƙaraso mana, Allah ya sa ƴan uwan naka basu tafi ba dama kai suke jira"
Ya ɗago tare da zuba mata jajayen idanunshi murya a raunane yace.
"Yanzu innah sai da kuka aika azo aga lefen nan fisabilillahi mai iyayen jiddah zasu ɗauke ni?"
Sai ya sunkuyar da kanshi ƙasa yana cije bakin shi, sauran maganar ta tokare a maƙoshin sa.
Innah ta zuba mai ido tana ƙara jinjina son da yake wa jiddah tinda har yana gudun ɓacin ranta da kuma na iyayen ta.
"To sadauki ya za'ayi da ƙaddarar Allah tinda Ubangiji ya ƙadarta ba Jiddah bace matarka a farko ba, yaya zamuyi gaba ɗaya haƙuri zamu yi tare da addu'ar alheri acikin lamarin"
Jinjina kanshi yayi tare da cewa.
"Tin da kika ce Allah magana ta ƙare"
Bai iya faɗa mata maganar da maƙocin nasu ya tare shi da ita ba sabida masifar zurfin ciki.
Ya na ƙoƙarin juyawa ya koma ɗakin shi su Ya minau suka ƙaraso wajan da shirin tafiya gida faridah sai tsokanar shi take yayi mata banza ya wuce ya barsu a wajan.
Innah tai murmushi tana kallon Aunty Hajjo tare da cewa.
"Yanzu goben ƙarfe nawa za a kai kayan? sai na kira Nafi kuje da ita amman ban da abinku da kun bari maza sun kai yanzu yaushe rabon da ku ga mata sun kai lefe?"
Da sauri faridah tace.
"Ban da abin Innah mazan su waye zasu kai? abu duk ɗaya Mu dai ki bari Muje mukai"
Ba yadda Innah ta iya ta amsa musu kamar yadda suka buƙata Ya Minau ce tace.
"Innah ni naga Saadik na haɗe rai wai meke faruwa ne?"
Innah cikin basarwa tace.
"Ke rabu da shi ya ƙarata da Ƙuncin sa"
Har soro innah ta raka iyalan nata tana musu addu'ar fatan gamawa da duniya Lafiya suka fita titi ko wacce ta hau motar gida.
Ba jimawa da fitar tasu Baba shima ya shigo gida lokacin mutanen dake ganin kayan lefen duk sun tafi sai su Khadija dake tattare tsakar gidan.
Baba ya zauna a saman tabarma a rumfa Hasken farin ƙwan tsakar gida ya hasko har cikin rumfar da yake zaune yabi akwatinan da kallo Fuskar shi dauke da maɗaukakin farin cikin haɗin zumuntar da zasuyi da ɗan uwan shi ya dubi Innah dake haɗa masa abinci yace.
"Haƙiƙa Hafsatu naji daɗin wannan aure ina fatan Ubangiji yasa sai mutuwa ce zata raba su, tabbas Amadu ya wanke duk wani laifi da ya min abaya domin duk duniya ba wanda zai iya riƙe Ƴar amadu kamar Sadauki kinga munyi tuwo na mai na"
Ya faɗa yana sakin ƙayataccen Murmushi, Itama Innah Murmushi tayi tana cewa.
"Allah dai yasa ayi lafiya a gama lafiya niko burina na goya ƴaƴan ɗan auta tin da ƙwarina Kuma Allah ya cika min, sai batun kai Lefe kunyi magana da shi Amadun ne? waɗan nan yara fa sun kafe sun ce sai sune zasu miƙa kayan"
Baba ya ɗaga kofin da innah ta cika mai shi da ruwan sanyin randa mai daɗi yace.
"Munyi waya ɗazu yace min Gobe da safe zai sauka kano Wajan yamma sai su miƙa abu duk na gida nida ma niyata ma a bata kayanta ranar ɗaurin aure, to tinda sunce zasu kai kar a katse su duk cikin murna ne"
Ire iren hirar bikin suka cigaba dayi har zuwa Lokacin kwanciya bacci.
*******
Adaah bata san waya bawa Mahir Numbern wayarta ba amman tafi zaton Momi ce ta tura masa shiyasa sanda taga kiran shi cikin dare batai mamaki ba hira mai cike da so da kulawa yake mata har sai da ya tabbatar ya dasa mata son sa acikin zuciyarta sannan ya barta aiko daren bata rintsa ba duk juyi shi take tunani abin ka da farin shiga.
Washe gari sai wajan taran safiya tayi sallar asubah sabida wayar da suka sha da Mahir ta makara ne tasha baccinta ta gode Allah wanka tayo ta shirya cikin Riga da skirt na Jar Atamfa Java bata ɗaura ɗankwaliba a haka ta fito Parlour tana kiran Maimuna da sauri maimuna ta ƙaraso ta rissuna tana cewa.
"Gani uwar ɗakina Barka da asubah"
Cikin halin ko in kula tace.
"Kije ki wanken toilet ki gyaran ɗakina ki kunnan turare akwai undies ɗina da zaki wanken washing machine ɗin toilet ɗina ya lalace"
Har lokacin maimuna bata ɗaga kanta ba har sai da Adaah taja aya sannan maimuna tace.
"An gama uwar ɗakina ga break ɗin ki can na haɗa komai kawai ci zaki yi"
A ya tsine ta amsa wa maimuna da.
"Ok"
Sannan ta wuce dining ta zauna ta haɗa tea ta ɗauki bread tana haɗawa da soyayyen ƙwai tana ci da yake Allah ya ɗora mata ci kamar gara ita Ko irin rashin cin nan ma na ƴaƴan masu kuɗi bata da shi.
Sai da ta share wannan bread da ƙwai tas sannan ta goge bakin ta da tissue ta ƙarasa cikin parlour ta kwanta tana canza channel.
Momi ce ta fito sai baza ƙamshi take.
Ta ƙaraso gaban Adaah tare da cewa.
"Tashin ki kenan na lalleƙa ki naga baki farka ba, Nima fita zanyi yanzun nan zan dawo"
Adaah tabi momi da kallo kafin ta kawar da kanta, ba tare da gaishe da mahaifiyar tata ba.
Momi tana ƙoƙarin fita daga Parlourn Sukai Kiciɓus da Abbah wanda shigowar sa gidan kenan hannun shi riƙe da ƙaramar jaka ta matafiya.
Momi zamewa tai a wayance ta zauna a saman kujera tana aje ƙaramar jakar hannunta dama lefen ƴar ƙawarta zata je gani sam bata kawo Abba zai dawo yau ba shiyasa zatai gaban kanta sabida ana faɗin irin dukiyar da aka laftawa ƴar ƙawar tasu.
"Sannu da shigowa Alhaji, amman dawowa babu sanarwa"
Ta faɗa tana sosa kai alamun rashin gaskiya.
Bai kulata ba sai Neman gurin zama da yayi da sauri Adaah ta diro tana sauka ƙasa har tana ƙwarewa wajan yiwa mahaifin nata barka da zuwa sabida shi tana shakkar shi ba kamar Momi ba.
Abbah ya bita da kallo ba tare daya amsa gaisuwar tata ba.
"Rabi'atu mai kike agida yau baki je makaranta ba?"
Sai ta hau kame kame sabida sarai tana da lecture ranar amman taƙi zuwa.
"Wato asarar kuɗina nake a banza ba karatun kike soba ko da yake ai magana ta ƙare dama abin da yasa na rabu dake na zaci zaki dage ki karatu ne, amman tinda baki son makaranta zan faɗawa Mijin naki ko bayan aure karya barki Fita ki haƙura haka abin da kika samu Allah yasa mai albarka"
Haɗe rai tayi nan da nan ruwan hawaye ya fara firfitowa daga idanunta ta jefa kallon ta ga Momi wadda ta kafe Abbah da ido tana jijjiga ƙafa.
"Wannan wace irin magana kake Alhaji wai shi wannan auren dole ne? haba yarinya bata so nida na haifeta bana so gaskiya ba zan lamunci a cusawa ƴata ƙatoton jahili ba, ce maka akai bata son karatu bayan ita kaɗai Allah ya bamu Tarin dukiyar da Allah ya baka in baka barta tai karatun ba waye zai riƙe mana ita nan gaba"
Abbah ya zubawa Momi ido cike da ɓacin rai, sam tinda lamarin auren nan ya tashi momi bata saurara mai bata masa ta sauƙi hatta ga kalamanta kawai yana kai zuciyar shi nesa ne yana duba wasu abubuwan jiba yanzu yadda take masa magana agaban ƴarta ba ladabin harshe ko tauna magana.
"Maryam sai fa Rabi'a ta auri Saadik koda gawarta ce wallahi zan kai gidan ƙarewar ƙiyayya in an aura masa ita tasa Ashana ta kunnawa kanta ta Ƙone ta mutu Ki sanar da ƴan uwanki anjima Za a kawo lefe"
Daga haka ya miƙe yabar Parlourn zamewa momi tayi daga saman Kujerar tana yarfe Zufa.
Da sauri ta ɗaga waya tana Kiran Hajiya Lubna.
Daga ɓarin Lubnah dake kwance domin har Lokacin bata tashi daga baccin safe ba.
Ta ɗaga wayar tana jan ƙaramin tsaki.
"Maryam yaya akai wannan wayar da farar safiya?"
Momi ta yarfe zufa a karo na barkatai kafin tace.
"Kinji wata sabuwa anjima zasu kawo lefen Adah ni kaina ma ya kulle"
Da sauri Lubna tace.
"Kamar yaya dama baki zuba masa magani a ruwan ya sha ba har ya sami zarafin maganar auren?"
Momi ta juya tana kallon hanyar da Abbah yabi taga ya ƙullewa ganinta sai tace.
"Yau fa ya dawo gari yanzun nan ya sauka yake wannan bayani wallahi bai ma bani fuskar na bashi ruwan ba bare akai ga na saka ke nifa gani nake suma aiki suke akan Alhaji duk yabi ya birkice min kamar ba shi ba"
Ƙaramin tsaki Lubna taja ido rufe da son biyan buƙatar kanta tace.
"Duk yadda za'ai karki yarda da wannan aure nima zanyi ƙoƙari na ta nan, Nifa ko ba Mahir ba wallahi nafi son Adaah ta auri Miji na kece sa'a irin yadda ƴaƴan ƙawayen mu suke aura haba ƙiri ƙiri za'a tauyeki ƴa ɗaya da Allah ya baki za'a cutar da ke a bata Ɗan jagaliya talaka faƙiri marar ilimi wanda ba lallai yasan darajar mace ba Niba burina Adaah ta auri ɗana ba Burina ta sami Mijin nuna sa'a mijin da zamu nunawa duniya cewa ƴarmu ta auri Namiji, wallahi inda ina da ƴa mace Budurwa Maryam kota halin ƙaƙa sai na shiga na fita na nemo mata wani ƙusa a ƙasar nan Ina zan yarda ƴata ta auri talaka"
Kalaman Lubna suka ƙara Raunana momi suka kuma ƙara bata ƙarfin gwiwar Tsanar auren da za'ai wa Adaah a raunane tace.
"Lubnah wallahi bada ban kar nai ƙarya ba sai nace kinfi kowa sona da damuwa dani, Tinda lamarin nan ya kunno ke kaɗai kike bani ƙarfin gwiwa duk da malam yace Adaah ta auri mahir amman ke ba burin ki ma ta aure shin ba ke burin ki ta tsallake ta sami miji na kere sa'a ya zanyi yanzu yau fa zasu kawo lefe?"
Ta faɗa tana kuka!
Lubnah ta cije baki ita kaɗai tasan meke ƙasan zuciyarta sai kuma Allah kafin tace.
"Karki musun zuwan su wannan ma wata dama ce da zaki ci musu mutunci karma ki gayyaci kowa daga dangin ki ke kaɗai zaki zauna su zo ki ci zarafin su tass kwaɗayayyun banza kinga daga nan suma in suka ji haushi zasu koma da ɓacin ranki nan ma wata damar ce da zaki wargaza auren"
Da sauri momi tace.
"Haka ne lubna dama wa zan faɗawa a dangina Allah na tuba Ai wallahi dama ni burina in Adaah ta sami miji ku zaku yi komai cikin girma ba tare da kun bani kunya ba"
Sai da suka gama tattauna komai sannan sukai sallama momi ba abin da take sai girgiza ƙafafu Adaah ta ja jiki ta ƙaraso wurin Momi.
Murya cikin rauni tace.
"Allah momi ina son ya Mahir ɗin Momy lubna yanzu bani jin zan iya rayuwa da wani idan ba shi ba momi kada ki bari Abba yayi mini auren dole"
Momi ta janyo Adaah jikinta tana rarrashinta
Har ta samu ta saki ranta.
Cikin shiri Abbah ya sakko sabida zai fita kasuwa zasu gana da wani mutum dake jiran shi duk da yana buƙatar hutu amman hakan ba zai samu ba.
Har lokacin bai da sukuni a fuskar shi ya ce.
"Maryam sai ki sanar da Ƴan uwanki nan da lokaci kaɗan zasu kawo kayan lefen akwai Lemuka da ruwa dana sa akawo sai ki sa masu aiki suyi musu Girki ki ɗauki kuɗi a ɗakina ki sallame su duk da ƴan gida ne amman yaba kyauta tukwici"
Idan kujerar data ke kai ta tanka to ta tanka wa Abbah har ya ƙare ya fita itama Adaah da ƙyar tai masa Adawo lafiya aiko yana fita tai ɗaki aguje tana kuka.
Momi da takaici ya hanata motsi a nan ta cigaba da zama koda mai kawo ruwa da lemuka ya turo mai gadi cewar ya ƙaraso cewa tai ace ya mayar dasu basa buƙata haka ya juya har akai azahar tana zaune sai da ta gaji dan kanta sannan ta miƙe ta shiga ɗaki tayi sallah ta ƙara dawowa parlourn jira kawai take masu kawo lefen su zo.
Ƙarfe ukun yammaci daidai Maimuna tai wa su Ya minau Iso babban parlourn gidan ƙanin mahaifin nasu wanda in za a kashe su ba zasu iya cewa ga yanayin gidan kawun nasu ba sabida ba zuwa suke yi ba.
Ya minau ce, sai Aunty hajjo, da Faridah da Aunty Nafi ƙanwar Innah sabida innah tace karsu faɗawa kowa daga cikin danginta domin basu san kalar tarar da zasu samu ba gudun abin kunya, gwara Aunty nafi ƙanwar Innah ce cikinsu ɗaya bazzawara ce take zaman gida.
Su Ya minau suka nemi guri suka zauna Umar ne ya dinga shigo da akwati nan ya jere su reras a parlourn.
Momi tana kallon su batare data amsa sallamar su bare akai ga batun ta amsa gaisuwar da suke mata ba.
Aunty nafi ta ce.
"Ina mutan gidan ne muna ta sallama kamar babu kowa"
Tsaki mai ƙarfi Momi ta saka tare da ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya tana ƙaro Ƙarfin Tv.
Aunty Hajjo ce tace.
"Innah Maryam barka da rana ga abin arziƙi mun kawo kuma mun zo kamar baku shirya zuwan namu ba naga babu ƴan ɗaga kaya koda yake abune duk gida ina amaryar tamu?"
A fusace