taka shinkafa da wake sai muyi lissafi"
Ya sha saman kanshi tare da yunƙurawa ya fita bakin famfon tsakar gida yaje yayi alwala ya fita masallacin dake layin yayi sallar azahar, sannan ya dawo Sanda ya shiga gidan an kawo nepa saboda haka a falon ya zauna yaɗan tsakuri abincin ya sha ruwa ita kuma Aunty Aminta tana gefen shi tana Gyaran Turaren wutar data zuzzuba a kwalba da yake tana yin su na siyarwa.
Ture plate din abincin yayi gefe yana Jan ledojin data aje masa a gabanshi tsala tsalan atamfofi ne a babbar ledar ta biyun kuma Laces ne ɗayar kuma material ne da mayafai atamfofin zasu kai Turmi Biyar Laces kuma uku material Biyu mayafai Uku.
Cikin mamaki ya ɗago yana cewa.
"Yaya minau gaskiya kuɗina ba su kai asai waɗannan kayan ba shiyasa na biyo na kawo maki sauran cikon"
Murmushi tai tare da cewa.
"Ai kaga ma magana ta sauya na kira Hajjo da farida tin ranar da kazo nan mun tattauna shine suka ce kabar kuɗin ka kagan su a gefena na fito maka da shi du wannan kayan Hajjoh ce ta bada kuɗin aka siyo farida tace zata sai akwatina ni kuma zan ƙarasa sauran har kayan kwalliya wannan shine gudun mawar mu dakai auta"
Amaimakon ya yi farin ciki sai ya ɓata fuska yayi kicin kicin tare da cewa.
"Gaskiya ni baku kyauta min ba tayaya ko wacce tana fama da kanta a wannan rayuwar tare da ƴaƴanta sannan kuce zaku Min lefe salon ma a zageni"
Me Aunty Amina zatai in ba dariya ba harda ƙwalla.
"Kai Saadik matsala ta dakai kafiya wannan kaci sunan naka Dagiyar wato kai ba za'a maka komai ba abikinka mu muke hidima kake mana duk da ba'a biki da ɗan uwa amman ai kamanci kamata mu haihu kai mana kai mana abikin ƴaƴanmu Kai kaɗai Allah ya bamu Namiji acikinmu In bamu yi maka ba wa za muyi wa?"
Bai ce komai ba sai Miko mata kudin daya ke har lokacin dariya take kafin ta kwantar da murya sanin halin shi in har batai masa dubara ba wallahi ba zai amshi kayan ba sai dai su aje.
"Haba kawu saadik Innah fa tace bayan ka auri Adawiyya zaka auri Jiddah kaga akwai sauran Hidima akanka tinda wannan tamu ce mu mun maka ita kuma Jidda sai kai abin ka da kanka yanzu wannan kudin ka aje ka sai kayan abinci tinda Baba yace Hayar ma har ka fidda kuɗin Biyanta to wannan kasai kayan abinci dasu"
Ya mayar da ajiyar zuciya tare da furta.
"Allah ya saka da alheri"
Itama murmushi tai tare da cewa.
"Yauwa ko kai fa yanzu cikin wannan satin zamu kawo kayan Gidan ku in yaso ƴan uwa suka gama gani sai akai"
"Kinga Ya Minau nifa ko taro Innah baza tai ba karma ku faɗawa kowa dan babu wani abu da za'ai a bari in zan auri Jiddah sai ayi taron ƴan uwa"
Ita dai dariyar rikicin Saadik take har ya ƙare maganar shi ya Miƙe yana mata sallama zai tafi har waje ta raka shi da yake Gidan nata ba kowa acikin yaran nata ya zaro dubu Uku yace ta bawa yara ta sa hannu ta amsa tana godiya don tasan in bata ansa ba fushi zaiyi ya tafi.
Daga gidan ya minau shago ya wuce aiko ya sami masu jiran shi sabida gaba ɗaya bai buɗe shagon ba yau sakamakon Umar na hutun karatun jarrabawa Shiyasa ya dakatar da Usman yace Shima ya huta a gida sabida umar ya fisu Hankali In suka zauna za'a iya samin matsala.
Bayan buɗe shagon ya shiga sallamar Cincirindon matasan dake jiran shi wasu sun kawo rodi ne wasu ƙarfe wasu Robobi bai sami kan shi ba sai da akai la'asar ya kulle shagon ya tafi sallah bayan ya dawo ma sallamar mutane yake har akai magariba sannan ya kulle ya nufi gida.
Ya dakata a bakin wani shagon awo dake gab da layin su ya sai shinkafar tuwo da garin tuwo aka zuba masa a ƙatuwar leda ya ƙarasa gida.
Bai shiga ciki ba a ɗakin shi ya aje kayan daya sayo yayi alwala ya tafi masallaci da yake jikinsa babu datti domin idan zai awon ƙarafe yana amfani da safar hannu ne ta leda sannan kuma yawanci ma yana aje ƙananun kayan da yake sakewa in yana shago duk da yau yaje amakare kuma bai amfani da kayan da yake sawa ba hakan bai saka ya ɓata na jikinshi ba.
Daya dawo daga masallaci wanka yayi ya saka jallabiya Mai ruwan toka ya fesa turare mai sauƙin ƙamshi ya ɗauki ledar Shinkafar tuwon da gari ya ƙarasa Cikin gidan.
Muryar Aunty Hajjoh yaji tana cewa innah.
"To Innah ga autan naki nan hankalin ki sai ya kwanta"
Da sauri innah ta fito daga rumfarta tana cewa.
"Kaiko sadauki ina ka shiga aikena tara da abinci shagon ka baka nan"
Kamo hannunta yayi suka zauna a saman tabarmar rumfar tare da cewa.
"Ki kwantar da hankalin ki innah ba zan ɓata ba ina gidan Ya Minau muna lissafi bayan naje kasuwa na karɓi kuɗi can na wuce"
Innah ta sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi tare da furta.
"Alhamdulillahi ina ta kiran wayarka sai wannan baturiyar taita yarika kala kala"
Sayyidah mai zatai in ba dariya ba Khadija nayi ummi nayi Juyawar daya yi ne suka daidaita kansu.
Aunty Hajjo itama dariyar take tare da cewa.
"Wato shiyasa sayyidah tace Min Ummi don Allah kije dani gidan Innah naci dariyar soyayyarta da kawu saadik wai niko Hajiya Innarmu zaki bar ɗanki ya tare a wani gun wannan ƙauna haka"
Haɗe rai saadik yayi tare da tashi zai fita dama ya saba jin tsiyar Yaya Hajarah duk sanda tazo gidan sai yaji haushin tsiyar data ke mai ya fita ya bata gu Da sauri Innah ta riƙo hannun shi.
"Kinga Hajara ki fita daga idanuna zoki haɗa ƴarki ku bar min gida wallahi bamai ɓata min ran sadauki"
Ƙunshe sauran dariyarta ta yi tare da miƙewa ta basu guri domin tasan akan saadik zasu iya rabuwar faɗa da innah.
Tashi tayi bayan barin gun da su Aunty Hajjo sukai.
Ta shiga kitchen ta ɗauko masa abinci harda ruwan shayi a fulas
"Innah nikam a ƙoshe nake naci abinci gidan ya minau sai dai Ruwan shayin zan amfani da shi anjima"
Ta ɗan ɓata fuska.
"Kaiko kaci dambu ne na tsaki mai daɗi irin namu na mutan da"
Ya kalleta dama duk sanda taga ba zai ci abinci ba sai tai masa wannan dabarar yake ci.
Aiko janyo kwanon yayi ya sa cokali ya hau ci duk da ya ƙoshi amman haka yake cusawa a cikin sa don hankalinta ya kwanta ta ga dai ya ci ɗin.
Kaɗan ya rage yayi Hamdala sannan ya kira Ummi yace takai kwanon kitchen tare da Ledar Daya shigo da ita.
"Kinji innah su Ya minau sun min lefe"
Innah tai murmushi tare da cewa.
"Yanzu muke maganar da Hajjo faɗa take tayi wai akan mai yasa ba'a faɗa musu da wuri ba da sunyi shirin daya fi haka"
Ya lumshe ido wato ada yana jin takaicin tasowar shi, shi ɗaya acikin mata kuma shine ƙaramin su amman daga baya sai ya dinga ganin Cewar Matan suna da matiƙar jin ƙai da tausayi uwa uba kuma suna son shi sosai.
"Ni kam innah faɗa ma nahau yi don me zasu ɗorawa kan su nauyi"
Innah tai murmushin jin daɗi tare da cewa.
"Haba sadauki in su Hajjo ba su maka ba wai wa za su ma duk duniya ka ma daina maganar nan Ni dama burina Allah ya haɗa min kanku yau daɗin dana ji ko yanzu Allah ya ɗau raina babu abin da zan ƙara masa sai Godiya domin nasan zaka zame musu uba su kuma su zame maka iyaye"
Buɗa Aunty Hajjoh take daga cikin ɗakin Innah kafin ta fito tana cewa.
"Wai innah dole muyi ƙara'i a bikin ɗan auta, ranar kawai nake fata tazo nasha rawa son raina"
Innah ta hau salati.
"Haba Hajjo da ƴaƴanki har kina shirin karɓar jika kiyi rawa wannan son rawa taki naga ranar denawa"
Da sauri Saadik yace.
"Innah kima faɗa musu babu taro in taro za su yi su bari sai bikina da Jiddah don wannan auren dole ne"
"Kai da kata bafa zaka hanamu sakewa ba kaji da gulmarka kuma duk ranar dana ga kana kuka akan soyayyar adawiyya sai na maka tunin wannan maganar kuma abin da nake so dakai shine tin yanzu ka koyi adalci duk matan kane in ma kana son wata to ka barshi a ranka amman batun auren dole duk bai taso ba, Adawiyya ƙanwar ka ce daga baba sai kawu Amadu duk duniya bamu da kamar mahaifinta a cire maganar mahaifiyarta da ita kanta a kalli Zumuncin Allah duk wanda ya ɗauki ɗansa ya baka wallahi ya gama yi maka ƙarshen ƙauna"
Innah ta zubawa Hajarah ido tana kallon yadda take zabgawa Saadik faɗa shi kuma yay ƙasa da kanshi domin ba zai iya musu ba dama duk ƴaƴan nata Hajarah ce tsayayya bata ɗaukar raini sannan akwai tsage gaskiya shiyasa suke shakkarta dama gata ma sha Allah duk tafi su ya minau girma in ka dubeta sai kace ita ce ma babba acikin su.
Sosai Aunty Hajjoh tai masa faɗa mai haɗe da Nasiha sannan ta cewa ƴarta ta haɗa musu kaya zasu tafi gida shiya raka su titi har suka je babban titi tana ƙara Yi masa nasiha da koya masa dubarun zama da iyali.
Shiya biya mata na Mota sannan ya wuce shagon su Nura Saiti.
SO DA ALƘAWARI....! littafin kuɗi ne 500 Naira zuwa asusun bankin 0078174806 sterling bank, ko kuma,9022260850 Opay bank,Shaidar Biyan kuɗi zuwa 09022260850, Ƴan Private waɗan da ba sai nayi adding ɗinsu a grp ba ta Private kawai zan dinga tura musu 1000 Naira ne in sha Allah.
[12/16, 10:27] Autar Manya: *SO DA ALƘAWARI..!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
*12*
Sadiq Babu, Nura saiti, babawo duk suna cikin shagon Nuran suna Buga lido ga kofunan shayi nan irin ƙananun nan na buzaye a gefen su ihun su ya cika shagon, duk sallamar da Dagiya yake yi basu ji shiba tsaki yaja kaɗan ya nemi gefen katifar saiti ya zauna.
Babu ne ya kula da shigowar Saadik sabida haka ya dakata da Buga lidon hannun shi ya zabga ihu tare da cewa.
"Sai angon mata biyu na rabi da hauwa mai abin mamaki" Saadik ya haɗe fuska ya sha kunu ya na lalubar wayar shi da ke ringing, Nurah ya ƙunshe dariyar sa ganin rabin hararar akan shi take sauka.
"Haba Dagiya auren ka guda ya tashi amman ka kasa faɗa mana sai a bakin Nurah muke ji?"
Cewar Babawo daya juyo yana kallon Saadik, Shidai bai tan ka suba kuma bama shi da niyyar ya tanka sun sai ma hararar da yake sakarwa Nurah wato bin da yay masa rakiyar dubiyar Jidda shine ya zo yana tsaigunta wa su Babawo lamarin auren nashi daya jiyo, ƙwafa yayi tare da tashi yana ƙoƙarin fita daga shagon da sauri Babu ya tare mai hanya yana cewa.
"Mu zaka mayar marasa hankali mu kome muka yi sai mun faɗa maka amman auren ka guda ka kasa faɗa mana bada ban Saiti ya bika duba tafisu ba da bama zamu ji ba"
Saiti ya cafke da cewa.
"Ai kasan dana ji a wurin maman tafisu wajan Baba naje shiya faɗan komai na auren nashi, wallahi kai dai Dagiya ka daina haka zurfin cikin nan naka har ya fara isata, to me kake nufi da sai dai muji auren naka daga sama ko yaya, ka fa tina mu yanzu mun wuce Abokai wallahi mun zama ƴan uwa in ma kai a abokai ka ɗauke mu to mu a ɗan uwa muka ɗauke ka"
Ganin duk sun masa caa sai jikin shi yayi sanyi sanin kan shine ya san bai kyauta ba, ko yace ma baya kyauta wa su suna faɗa masa duk wata damuwar su hasalima shike kawo musu masalaha in wani abun ya taso musu amman shi da wiya suji lamarin shi haka tsarin shi yake kuma hakan halitta ce daga Allah wani bin ko innah baya faɗawa damuwar shi sai dai abin yayta cin ranshi.
Komawa da baya yayi ya zauna a saman kafitar Saiti ya dafe kan shi da hannu biyu, Ya jima a haka kafin ya ɗago idanun shi ya sauya kala ya koma ja, alamar damuwa ta bayyanar masa.
Gyaran murya yayi kamar kullum cikin ƙasa da murya kasancewar sa mutum marar son hayaniyya ko ɗaga murya.
"To babawo yanzu mai kuke son nace muku? so kuke na fito fili na bayyana muku cewar Baba auren dole zai mini ko yaya?"
Mai su Babawo za suyi in ba dariya ba Babu harda ƙwarewa ganin yanda Saadik ya taƙarƙare yana cewa auren dole.
Ganin zasu mai da shi sakarai yasa ya ƙara miƙewa a fusace ya bangaje saiti ya fice daga cikin shagon.
Saiti ya tsagaita dariyar tashi yana cewa.
"Kunga ku zo mu bishi dole ai zama akan auren nan, Domin Dagiya ɗan halak ne ba zamu bar shi da ɗawainiya shi kaɗai ba kuma don Allah kubar dariyar haka ai maganar hankali, Kun san halin shi kamar kuturu yake zuciya da fushi ba sabon abu bane wurin shi"
Ta shi sukai suka rufo shagon suka bi bayan Saadik da yake basu da nisa tuni suka shiga gidan su saadik ɗakin shi dake soro suka shiga baya ciki da alamun yana banɗaki Nura ya zauna a saman kujerar roba su babawo kuma suka zauna a saman carfet ya kusa minti goma a bayin kafin ya fito shige su yayi ya nufi hanyar ƙaramar wardrobe ɗin shi, ya ɗauki abin da zai ɗauka ya koma bayin Minti kaɗan ya fito cikin farin wandon polo da farar rigar polo marasa nauyi da alamun na baccin sa ne, ya ɗauki turare ya fesa sannan ya shinfiɗa darduma yayi sallar isha'i ganin yayi sallama yana kokarin mai da ta nafila Nura yayi gyaran murya.
"Kaga muma fa musulmai ne na ƙwarai tinda kayi sallar Isha'i ka bari muyi magana muma muje muyi tamu in mun fita sai kayi Nafilar"
Dan dai kawai ɗakin shi suka zo ne bai son suji ba daɗi shiyasa kawai ya juyo yana fuskantar su.
"Mu yanzu a matsayin mu na abokanka zamu ɗauki nauyin wasu abubuwan kama daga kayan abinci zuwa sauran hidimar tura motoci zuwa gidansu amarya"
Sai da ya ɗauki lokaci bai magana ba sannan yace.
"To nagode" a taƙaice.
"To ya batun mazauni fa?"
Cewar babu.
Ya shafa kanshi yana cewa.
"Nan gidan dake kallomu na kama kasan masu gidan zasu tashi shine ni zan shiga"
Babawo yace.
"Kai gaskiya yayi maka kaɗan kuts ni kaf arear nan ma akwai ƙaramin gida kamar wannan kuma har mata biyu zaka saka aciki"
A zafafe ya ce.
"To daidai ƙarfina kenan uban wa yace maka duk su biyun zan aura lokaci ɗaya ina zan kaisu Jiddah sai ta gama karatu kafin nan na fara ginina In sha Allah ko ɗaki biyu nayi saisu koma su duka mu zauna a muhallina"
Nurah yace.
"Eh to tinda mace ɗaya ce ai ya isa sai ai maganar gyare gyare zan saka Mizambilun gidanmu yaje yaga gidan tinda ya iya painti sai yaje yayi maka shafen ɗakuna dana tsakar gida"
Saadik yace.
"Wasu ɗakuna ɗaki ɗayane ciki da falo sai kicin da bayi amman bakaji kuɗin da suka sawa gidan ba haka dai zan biya tinda nina fi son kusa da innah gaskiya"
Nurah yace.
"Okay ba matsala sai batun lefe kuma?"
Ya ɗan haɗe rai.
"Nikam titsiye ni kuka zo yine to ban yi ba"
Babawo yayi dariya tare da cewa.
"Kaifa ka zama ɗan alallaɓa yanzu Angon Rabi in ma bakai lefe ba mu sai muyi karo karo"
Wani kallo ya watsama Babawon tare da cewa.
"Kasan dai ni ba rago bane babu abin da yake firgitani, Lefen yana gidan Yaya Minau kun san gidan sai kuje ku gani"
Saiti yace.
"Baka isa ba dole a kawo min kayan madam nai mata ɗinkuna masu fisgar hankali tasan ta auri abokin telan mata"
Ta shi yayi cak ya tada sallar shi sukam maganganun su suka cigaba dayi akan bikin kafin su miƙe su fita.
Shikam ya jima a sujjadar shi yana ƙara jaddada neman zaɓin Allah akan lamarin auren wanda dama wannan addu'ar yake ba dare ba rana in har yayi sallah sai ya miƙa koken shi wurin Allah akan lamarin auren nashi.
Bayan ya sallame ya na ɗe abin sallar ya kashe ƙwan ɗakin yayi kwanciyar shi.
Da asubahi suka haɗu da baba a masallaci wanda baban yake masa magana akan shirin auren bayanin yadda ake ciki yayi ma baba cikin ladabi, baba ya ƙara da cewa, mahaifin jiddah ma yay masa magana jiya akan wai sukai kuɗin aure in yaso in ta kammala karatun sai ayi bikin.
"Baba ka basu haƙuri kaga duk ƴan kuɗaɗen hannun nawa na haɗa zan kai kuɗin gidan can su min alfarma bayan biki sai na bada akai"
Baba ya murmusa tare da cewa.
"Hakane sadauki, amman tinda suka nemi akai to akai ɗin ni zan bada kuɗin akai musu kaga sanda zamu kai kuɗin Amadu yazo min da batun auren ka da rabi'ah to kar suga kamar ba zaka auri ƴarsu bane mutanan nan babu abin da zamu ce musu sai godiya da irin ƙaunar da suke nuna mana sabida haka Amadu yace jibi zai dawo kano in ya dawo zan bada Kuɗi suje su kai gidan su jiddan shida sauran ƴan uwan mu na ƙauye"
Saadik ya rissunar da kai ƙasa tare da cewa.
"A,a Baba Kana ta kanka ka ɗorawa kanka wahala ka bari bazai gagaraba in sha Allah, Burina akai lefen sannan na bawa masu gidan can kuɗin su sai hankalina ya kwanta"
Baba yace.
"Banda abin ka Sadauki In da ni mai hali ne ai da na ɗauke maka komai na hidimar aure, to ni babu mahaifiyarka babu sai kai kaɗai da Allah ya bawa ƙarfin zuciyar nema ga shi yanzu Nauyi zai ƙara ninkuwa akanka bayan namu Allah ya maka albarka kuma zan cire kuɗin auren akai Musu In sha Allahu"
Daɗa rissunawa yayi yana wa baba godiya sannan suka ƙarasa gida.
Ɗaki ya koma ya sake kaya dan ko wanka bai yi ba, a gurguje yaje suka gaisa da Innah ya fice shago tin sassafen don abin kari ma sai Usman ne yakai masa dole yabar Usman a shagon Shi kuma ya wuce Ƙofar ruwa.
Wajan ƙarfe Sha ɗayan safiya gaba ɗaya iyalan na Innah suka hallara agidan Aunty Amina da Ƴaƴanta jawahir wadda ba a jima da bikinta ba sai Hussaina wadda za'a ma biki kwanakin nan, Aunty hajjo da Fatima ƴarta wadda ke dauke da tsohon ciki sai Sayyidah, Sai faridah data zo tare da Sajidah da Sajjad ga kuma su Ummi nan don bama suje Makaranta ba ranar shiyasa gaba ɗaya gidan na Innah ya gama cika da Ƴaƴanta da Jikokinta ƙatuwar tukunya Khadija ta wanke aka ɗora wake da shinkafa a tsakar gida wadda za a ci da rana.
Babu komai da yake ta shi sai hayaniyar su, ta surutun su kuma duk akan bikin auta ne suke ta faman maganganu na yadda bikin zai tafi.
Shigowar Sayyid da Hassan ce ta sa surutun ya ɗan lafa, Sayyid ɗan Aunty Hajjo Hassan ɗan Aunty Amina, Suka shigo da akwatina niki niki da alamun daga kasuwa suke sai da suka shigo da akwatina saiti Biyar cif da ƙatuwar gana Hassan yay miƙa yana cewa
"Washh Allah Ummah ba ƙaramar wahala muka sha a kasuwa ba, da ƙyar Abba ya samo ɗaya atamfar nan fa"
Aunty amina ta fara janyo akwatinan tana cewa.
"Allah dai yay muku albarka dama nasan za a ci wahalar kafin a samo, da kuka amso ne kuka je gida kuka ɗauko akwatinan? to kun sallami mai ɗan sahun daya kawo ku?"
Sayyid yace.
"Eh mun sallame shi yama tafi Ummi nina wuce school"
Ya faɗa yana kallon Aunty Hajjo.
Innah da bakin ta ya ƙi rufuwa cewa take.
"A,a ku bari kuci abinci mana Allah ya maku albarka kuma ya ninka musu abin da kukai"
Matasan dai fita sukai sunawa Innah murmushi, tare da amsa addu'ar da tai musu suko su Ya Minau kayayyakin sukaita ɗagawa don an karo wasu kayan akan na da faridah ce mai shirya kayan ko wanne tana haɗe shi a inda ya dace.
Kafin Ya Minau ta cewa su Ummi suje maƙota su farfaɗa azo aga lefen kawun su saadik aiko Su Ummi fita sukai gida gida sukaita faɗa kafin kice kwabo gidan Innah ya cika da mutane ƴan kallon Lefe.
Sai dai mahaifiyar Jiddah furr taƙi zuwa ta kuma kafawa Jiddah takarar ko kallon saadik karta ƙara yi ranar Jiddah taci kuka ta godewa Allah, domin Wata irin ƙaunar Saadik ce ke ƙara ninka mata ruhinta.
Maƙota kowa yazo sai ya tambaya gidan su Jidda za'a kai sai Faridah ke musu bayanin Ai ƴar ƙanwar Baba zai aura Jiddah kuma sai ta kammala karatun ta wasu suyi fatan alheri wasu kuma su tafi suna ƙus ƙus ranar har dare ana shigowa kallon Lefen wanda kowa ya gani sai ya yaba shi kan sa Baba yayi mamakin rawar ganin da ƴaƴan nashi sukaiwa ƙanin nashi aiko sai saka Musu albarka yake.
Saadik bai shigo gida ba sai bayan Isha'i shima wayar innah ce ta saka ya tawo sabida a kwanakin nan cikin taskar Allah yana samun ciniki ne fiye da yadda yake yi ada shiyasa yake jimawa a shagon.
Tin daga bakin layi yaji mutane na masa Allah ya sanya alheri wani maƙocin su ne ya tare shi sanda zai shiga gida yana ce masa.
"Malam saadik ashe lokaci yayi to Allah ya sa alheri"
Dama da mamakin yadda ake masa Allah sanya alheri ya ƙaraso sai kuma ga wannan maƙocin nasu shima ya tare shi yana masan.
Ƙaƙalo murmushin dole yayi tare da cewa.
"Amin ya rabb! nagode"
Ya faɗa yana ƙoƙarin shiga gidansu.
"Amman Saadik kaji tsoron Allah naji ance ba Waccan yarinyar jiddah zaka aura ba, ƴar ƙanin mahaifinka zaka aura mai kuɗi shiyasa ma kuka haɗa lefen ƙarya, amman gaskiya bai ci kaiwa Jiddah haka ba kowa yasan yadda kake da yarinyar nan amman ka yaudare ta"
Da sauri ya ɗagawa maƙocin nasu hannu tare da faɗawa soron gidansu da sauri.........
SO DA ALƘAWARI....! littafin kuɗi ne 500 Naira zuwa asusun bankin 0078174806 sterling bank ko kuma, 9022260850 Opay bank,Shaidar Biyan kuɗi zuwa 09022260850, Ƴan Private waɗan da ba sai nayi adding ɗinsu a grp ba ta Private kawai zan dinga tura musu 1000 Naira ne in sha Allah.
[12/16, 10:27] Autar Manya: *SO DA ALƘAWARI..!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
*14*
Ya lumshe idanunsa yana fesar da Numfashi ƙasa ƙasa Sautin Kukan Ya Minau na ratsa dodon Kunnen shi, Kafin ya ɗago da idanun nashi ya dire kallon shi akan Innah wadda tai tagumi tare da zubawa Ya Minau Ido takaici da tarin damuwa ne bayyane a saman fuskarta.
Tsaki Aunty Nafi taja tana cewa.
"Haba Yaya gaskiya a sake tunani danni kam banga alfanun wannan aure ba, kowa ni ɗa namiji yana fatan samun macen ƙwarai wadda ta fito daga gidan martaba amman wannan kam mahaifiyar yarinyar nan ba ƴar mafuta bace"
Cikin damuwa Innah ta dubi Ya Minau tana cewa.
"To yaya zamuyi wannan ƴar, Babanku ya kafe akan ayi auren nan ni kaina ba so nake ba sabida Maryam ba ƙaunata take ba to abin ne yafi ƙarfina dole na tattara na zubawa sarautar Allah ido duk abin da Allah yayi akai daidai ne"
Faridah ma mita take Aunty Hajjo kam ta kasa magana sai faman Jijjiga ƙafa take duk irin wahalar da suka sha wajan haɗa lefen nan amman wannan cin zarafin ne zai biyo baya.
In kujerar daya ke kai tai motsi to Saadik yayi motsi acikin maganar su, sai dai zuciyar shi ƙunci ne tare da tarin damuwa haka ya cigaba da wanke takalmin shi ya kaɗe ruwan ciki ya jingine a jikin bango ya miƙe yabar Musu tsakar Gidan to shi mai zai ce, bayan duk Babane yaja musu da bai karɓi tayin ubanta ba da wannan tozarcin bai faru a gare suba.
Ɗaki yaje ya shirya cikin Jc jajaye wandon iya gwiwar shi sai farar safar ƙafa sai farin takalmin Ball ya fito bai ma shiga gidan ba ya wuce filin ball cikin son kau da damuwar daya bar ƴan uwan shi suka fara buga ƙwallo.
Da ƙyar innah ta rarrashi ya minau sabida dama itace babba amman tafi ƴan uwan sanyin zuciya da rauni har magariba suna gida suna jira shigowar Baba ganin bai shigo ba har bayan sallar yasa suka tattara suka wuce gidajen su duk