sameta akan lallai tazo gida Jikin mahaifiyarsu Iyah ya rikice haka ta ɗauki jakarta a gigice ta fice Ɗakin Abbah Yana bacci dan haka ta wuce parking space Ta kira driver suka wuce Gida.
A hanya taga wayar Lubna wadda tace mata ta fito, ta bata amsa da tana hanyar hotoro Iyah ce babu lafiya badan Lubna ta yarda da maganar ba tayi mata Allah sawaƙe ta kashe wayar.
Cikin Kiɗima Momi ta shiga gidansu wanda ta gyarawa mahaifiyarta ta zuba mata komai na alatun rayuwa domin Morewa da jin daɗin Rayuwar Duniya a falon Iyah Likita na zaune a gabanta inda take kwance a saman katifa Yana Ɗaura mata ruwa Abbas ƙaninta da Mariya Ƙanwarta mai aure itama data ƙaraso Gidan, Suke zaune a gefen Iyah Momi ta ƙarasa cikin fargaba ta zauna a kusa da iyah tana ta jera mata sannu.
Bayan Likita ya saka mata ruwan ya dube su cikin son kwantar Musu da hankali yace musu ɗan zazzaɓi ne ke damunta dama jikin girma ya gaji haka sallama yayi musu tunda Mariya ƙanwarta Nurse ce in ruwan ya ƙare zata cire wa Iyar.
Seda ruwan ya ƙare Mariya ta cire mata sannan Iyah ta buɗe ido tana kallon Momi.
"Maryama waya taso ki?"
Momi ta kama Hannun Iyah kana tace.
"Abbas ne ya kirani dama na shirya zani anguwa dana ji wayar shi shine kawai na tawo nan"
Iyah bata kuma cewa komai ba ta juya ta koma baccinta Mariya ganin Jikin da sauƙi tai musu sallama ta tafi gidanta dama Ƴaƴan Iya daga Momi ne se Abbas se mariya su uku ne, Mariya nada ƴaƴa uku Abbas bai aure ba Momi ce Babba Nada Ƴa ɗaya Adaah, da yake ba wani shiri suka fiya yi da Mariya da Momi ba sakamakon ita momi Ƴar ƙarya ce bata fiye jan Mariya ajiki ba sabida ta raina ajinta Mijin mariya malamin makaranta ne Ita kuma Nurse se Mariya ma ta shekara bata je wajan Momi ba duk da cikinsu guda dan Momi tafi bawa Ƙawaye mahimmanci fiye da ƴan uwanta dan ma Inda Allah ya tarfota tana jin tsoron Iyah mahaifiyarta kamar me da wannan aka ɗan sami sauƙin ta.
Dan ko abu taiwa Iyah se Iyah taƙi amsa tace seta ba Mariya, Shi dama Abbas Ba anan yake aiki ba bai fiye zaman kano ba se ya ɗanzo week end.
Bayan fitar Mariya Abbas ma yace mata bari yaje ya dawo falon daga iyah sai Momi.
Iyah ta yunƙura domin tashi Momi ta taimaka mata, Bayan ta tashi ta haɗo mata tea mai kauri ta kawo mata.
Bayan tasha Ta dubi Momi tace mata.
"Maryama kamar naganki acikin damuwa meke damunki?"
Momi tai ƙasa da kanta tana wasa da yatsun hannunta.
"Babu komai Iya kawai bacci ne akaina"
Iyah tai mata wani kallo kafin tace.
"Jiya ai Amadu yazo nan ashe Rabi tayi miji shine nace kin sake dangi ne dani baki gayan ba?"
Jikin Momi yayi sanyi nan da nan, domin batai zaton Abbah yazo wajan mahaifiyarta ba, lallai duk inda tai zaton lamarin yaso ya wuce zaton ta.
A hankali tace.
"Iyah Bata son shi wallahi Auren dole yake son yayi mata"
Iyah ta watsa mata kallon banza kana tace.
"Sabida shi wanda zata aura ɗin talaka ne?"
Da sauri momi ta zaro ido iyah ta kuma cewa.
"Eh mana ai nasan baki son talaka maryam domin ke rayuwarki da faɗi, bayan mu ɗin ba kowa bane amman kin haɗu da Ƴan duniya sun sauya Miki rayuwa"
Momi ta fashe da kuka mai sauti tana cewa.
"Iyah kema zargin da kike mini kenan fisabilillahi Iyah Alhaji yayi daidai zai ɗauki ƴarsa mai ilimi ya bawa sakaran talaka marar galihu nidai an cuceni"
Iya ta ɗauki Kofin shayi ta jefowa momi wadda tai saurin gocewa tana kuka cikin zafin rai tace.
"Ashe Duk abin da ake faɗa ba ƙarya bane, Maryam ina shi wanda Uban Rabin ya zaɓa mata Musulmi ne, Ina jiye Miki duniya maryam bam miki baki ba amman wallahi ki guji duniya da uban yaron nan da Uban Rabi uwarsu ɗaya uban su ɗaya meye naki aciki da talaka da mai kuɗi duk Allah ne yayi su Ina baki shawara ki ɗauke kanki daga batun auren nan babu ruwanki"
Da kuka Momi tace.
"Iyah ita ma fa bata so wallahi"
Iyah ta zaburo kana tace.
"Ai dole taƙi tunda kin zugeta Rabi dai batai sa'ar uwa ba shiyasa duk baƙin halinki ta kwafe yarinyar da ko cikin mutane bata son shiga Kin rabata da dangin mahaifinta Kin cusa mata aƙidar raini da girman kai da izzah tun wuri ki sauya hali maryam nidai Allah ya sani baki gado halina ba wallahi acan duniya kika samo halin ki"
Bakin momi ya mutu don a duniya Mahaifiyarta ita kaɗai ke taka mata burki sabida duk rashin mutuncin da take shukawa labarin na zuwar wa Iyah shiyasa iyah takanas tasa aka kira mata Baban Chiranchi ta Nuna goyon bayanta ga auren da zasu haɗa Ko hakan yasa Maryam ta saduda kawai dan dangin Mijinka talakawa ne seka ƙyamace su ko taron su bata zuwa a cewarta tafi ƙarfin ajin su ba kuma komai bane yaja mata hakan face Yawan ƙawaye waɗanda suke hure mata kunne.
Tass iyah tayi mata sannan ta zabga mata Allah ya isa idan har tabi malamai ta rusa auren, Ranar Momi da kuka ta baro gidan Iyah da ta dawo kuma ta tarar da tijarar Abbah dan da cewa yayi seta koma inda ta fito seda tai wa Abbas ƙaninta waya ya kira Abban yace shiya kirata Iyah ce babu lafiya, Sannan ta bawa Abban haƙuri ta shige ɗaki.
Ita kuwa dama Adaah data tashi daga bacci shirin school tayi bayan ta kammala ta leƙa room ɗin momi a rufe tai zaton tana wajan Abba sabida haka setai ficewarta a motar ta fara mai kyau kai tsaye Bayero University ta shiga sabida anan take karatu tana matakin lavel 2 ne yanzu haka exams suke yi wadda in suka kammala zasu tafi hutu.
Bayan sun fito daga exams suka haɗu da Habeeb wanda yake zaune saman motarta yana jiranta koda ta iso daga nesa da shi ta tsaya tana harɗe hannayenta a saman ƙirjinta yanayin kallon ƙurullar da yake aika mata shiya bawa gangar Jikinta damar Mutuwa.
Saukowa yayi daga motar yana wasa da keyn hannun sa ya ƙaraso gabanta.
Iska ya hura mata a saman fuskarta idanunta Lumshe taɗan saki ajiyar zuciya.
A hankali yace.
"Muje"
Ba musu tayi gaba yana binta a baya motarta ta shiga ta zauna shima ya buɗe emty seat ya zauna yana facing ɗinta.
A hankali yake gaya mata daɗaɗan kalamai waɗanda ya kashe mata Jiki dasu shima akaran kansa yasan a yau ta bashi damar da bai taɓa samu ba domin ta saurare shi.
"Zaki aure ni Baby karki damu da ina karatu, wallahi ina zuwa kasuwa Ina da halin da zan riƙe ki"
Ya faɗa Cikin kashe Murya.
Zuciyarta ce tai rauni, tabbas Inda da dama gwara ta auri Habeeb akan ta auri wancan garan da Abbah yake son Liƙa mata.
Cikin Nutsuwa tace.
"Zanyi tunani akan maganarka Habeeb ka ɗan bani lokaci"
Daɗi yaji har cikin zuciyarsa.
Da kansa yaja Motar tata seda ya kaita har ƙofar Gidansu sannan ya fita ya bata Key ɗin yana ɗaga mata hannu.
Lumshe idanunta tayi tana Jin wani irin yanayi mai kama da amsuwar tayin soyayyar Habeeb acikin zuciyarta.
Gidan nasu yayi shuru, alamun ya nuna kamar babu kowa room ɗinta ta shiga tayi wanka ta saka doguwar riga marar nauyi ajikinta sannan ta nufi Room ɗin Momi
************
A gajiye liss ya shiga Gida Lokacin ana Kiran sallar Magarib seda ya wanke jikinsa damma yana amfani da safar hannu wajan awon ƙarafan amman duk da haka seya yi wanka in ya dawo Gida.
Yayi shiri cikin Farar shirt da Baƙin jeans, Ya fesa turare mai sauƙin kuɗi.
Masallaci yaje yayi sallah tare da Baba suka jero zuwa gida yana ƙoƙarin shiga ɗaki Baba ya kira shi.
"Sadauki,Muje muci tuwon dare tare mana"
Ya shafa kanshi kana yabi bayan Baba.
A rumfar Baba suka zauna tare suka ci tuwon da Mahaifin sa bayan sun kammala ya ɗauke kwanikan yakai Kicin.
Daga nan fita yayi dan yasan Ba komai bane yasa Baba Yi masa hakan face yana son yaji yadda sukai da waccan yarinyar shi kuma bai san me ze cewa Baban Ba.
Karo suka ci da juna goshin su ya gwaru waje ɗaya, dafe goshin nasa yayi........09022260850
[12/16, 10:27] Autar Manya: *SO DA ALƘAWARI..!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
*004*
Zama tayi a gefen gadon Momi tana jiran ta sabida ta jiyo alamun saukar ruwa wanda ya bata tabbacin wanka momi take yi.
Babu jimawa Momi ta fito daga cikin toilet Jikinta rufe da Ƙaton Hijabi ganin haka yasa Adaah fita falo domin ta bawa Momi damar shiryawa kusan awa Guda da fitar tata Momi ta biyo bayanta.
A kusa da ita ta zauna tana jan tsaki.
"Shalele Mahaifin ki yayi min shigar sauri a lamarin auren ki sai dai ni kuma zan nuna masa Nina haifeki wallahi Koda kin Auri yaron nan ba zaki Zauna lafiya a gidan ba har sai Kin kaso wannan ƙaddararren aure na kwaɗayi sabida anga ke ɗaya ya haifa shine za'a ƙaƙaba maki auren dangi"
Taɓe baki Adaah tayi tana Jin zafin furucin kalmar auren nata da Momi ta faɗi kafin tace.
"Yanzu Momy ke kina tunanin zanyi rayuwa da shi? Haba Momy kimin Fatan alheri mana dan wallahi dana aure shi gwara na auri Habib duk da Habib ɗin ba wani shigemin rai na yayi ba"
Da tarin takaici Momi tace mata.
"Inda dama mahaifinki ya bayar akan ki fidda Miji ni kaina dana haɗaki da Yaron Hajiya Lubna
Maheer amman kina kallo fa umarni ya bamu bawai dama ba wannan makircin Na rasa daga ina ya fito hatta Mahaifiyata anje an faɗa mata ƙarya da gaskiya"
Zaro ido Adaah tayi haɗi da saurin cewa.
"Iyah aka faɗama maganar auren nawa? Wayyo! Shikenan yanzu zata ce in baki bari ba Bata yafe ba Haba Abbah yaya zeyi min haka ya rasa da wa zai haɗani sai Ƙasƙantaccen Mutum ɗan talakawa"
Kuka Adaah take mai cike da tsananin ƙiyayyar Auren da za'ayi mata Tin Momy na rarrashinta Har abin ya faskara sai ta zuba mata ido tana kallonta domin duk yanda take zato Adaah ta fita Ƙiyayyar Auren har akai sallar Magarib tana zaune batare data Miƙe Domin gabatar da sallah ba tana ta kuka a wurin Gajiya Momi tayi ta Tashi ta nufi Bedroom Domin gabatar da sallah.
Ana idar da sallah Abbah ya shigo Jin Shashsheƙar Kukanta yasa shi ƙarasowa wajanta ya fasa hawa saman dayay niyya Gyaran Murya yayi tare da Zama a kusa da ita Wanda Itan kuma tai saurin Zamewa ta zauna a ƙasa tana Goge hawayenta.
Da sassauci acikin Muryar Abbah ya dube ta.
"Rabi'atuna kukan mai kike Ɗiyar Abbanta kome Kike so ki faɗa min Kinji bana son damuwarki"
Jin wannan kalmar daya ambata sai taji zuciyarta tayi sanyi ta ƙara Goge sauran hawayenta tare da cewa.
"Abba dan Allah karka aura Min shi wallahi har cikin raina bana son shi"
Tsira mata ido Abba yayi tare da kamewa sosai ya kalleta na wani Lokaci sannan yace.
"Ko kina da dalilin Ƙin Yi mini Biyayya wadda bata saɓawa Allah ba? Ni Mahaifin ki na zaɓa maki Mijin Aure Kice zaɓina bai maki ba Ko kina da zaɓin ki? sannan Ki bani dalilin Ƙin wannan aure da Kike?"
Daburcewa tayi seda ta aro jarumta wurin furta kalmar.
"Abbah ka duba Gidannan ka duba tsarin shi sannan ka duba tarin dukiyar dake gareka sannan ka duba yanda na taso Sannan Abbah kace zan auri wanda Da ƙyar In yayi karatun Boko ma daga ganin shi yafi kama da ƴan jagaliyar anguwa Abbah na roƙeka karka aurawa Ƴarka tilo ɗaya tal wanda ba tsaranta ba kuma ba ajinta ba"
Ɗaga mata hannu yayi tare da dafe saitin zuciyar sa.
"Innalillahi wa'innah Ilaihirraju'un"
Ya furta a fili yaushe Rabi'ah ta ɓaci haka yaushe ne ta zama mai raini da ƙasƙanci ga mutane tabbas ba laifin kowa bane face na Mahaifiyarta shiba zama yake a gari ba yawanci In yazo baya daɗewa yake tafiya dalilin daya sa harya ƙauracewa zuwa gidan Yayan nasa kenan sedai ya aika masa da kayan abinci da kuɗi wanda takanas Shi Kuma Baban Chiranci ya aiko masa da cewar Ya daina amsa shiba wannan yake soba Zumunci yake so Yanayin kasuwanci yau ya fita ƙasa kaza gobe ya fita ƙasa Kaza shine silar tarwatsewar Komai, Gudun kar Ƴarsa ta Koyi Wata Tarbiyar yasa ya hanata Karatu a ƙasar waje ashe Gudun Gara yayi domin ya mance yawanci Ƴaƴa suna samun tarbiya ne daga wajan Iyayensu mata.
A fusace ya shiga Kiranta.
"Maryam! Maryam!!Maryam!!!
Da tsananin zafi ita kuma da tsananin sauri ta ƙaraso Falon.
"Alhaji sallah na idar ina addu'a kana kirana da ƙyar na shafa wallahi ka ɗagamin hankali"
"Dole na ɗaga miki hankali Maryama Kin kyauta da tarin tarbiyar da Kika bawa Ƴarki Amman Ina so a daren nan Ki shaida mata waye Abubakar a wajena waye mahaifinsa wacce Irin Rawa mahaifinshi ya taka a rayuwata Kuma ki sanar mata In Mutuwa tayi zan kaita Gidan Mijinta daga nan a suturtata akaita makwancinta Amman Auren ta da Abubakar Babu fashi In har Nine mahaifinta"
Fuww Ya tashi yabar wajan Tagumi Momi ta zabga wato duk yadda take zaton lamarin so yake ya fi ƙarfinta, Mijinta mai son ta da ƙaunarta Ko magana zai mata baya mata ita cikin faɗa sai a hankali sabida Gudun Ɓacin Ranta kasancewarta mai kirsa yanda take wa Alhaji ba zaka ce Wannan matsala zata zo ta shiga tsakanin suba duk yadda takai da kirsarta a Lamarin Auren nan ta kasa dannewa jita ke ba zata iya Gani talaka yazo ya aurar mata ƴaba kuma Ama rasa daga ina zai fito sai daga gidan maƙiyanta dan Momi a duniya bata Ƙaunar Baba da Innah domin sai da takai ga har Gida taje ta Yiwa Innah gargaɗi akan mijinta ada sanda Yake Musu Hidima sosai kafin ta janye shi da Kinibibinta.
Duk da sanyin falon Momi zufa take Adaah kuma na kuka wayarta dake Gefen Kujera ta janyo ta shiga Kiran Ƙawarta Lubnah.
Hajiya Lubna dake zaune Tare da Ɗanta Maheer suna tattaunawa taga wayar Ƙawarta Murmushi tayi tare da cewa.
'Kaga ƴar halak kamar tasan zancenta Muke"
Da sauri Maheer yace.
"Mama ki ɗaga mana Kiji"
Gyara zama tayi tare da ɗaukar wayar daga ɓarin Momi a gigice ta shiga zayyanewa Hajiya Lubnah Halin data ke ciki.
Tsaki Hajiya Lubnah tayi.
"Ga Hanya mafi sauƙi na faɗa Miki kizo mu fita da tuni wata maganar ake Keni In ba zaki bi malamai akan wannan matsalar ba dan Allah karki sake Kirana"
Tana Ƙoƙarin kashe wayar Momi tace.
"Zani wallahi dole ma naje inya so saina nemi gafarar Iyah In komai ya daidaita Amman ba zan ga wannan abun na bari ba wato in suka aura masa Ita shikenan Komai Namu ya koma Gindinsu Daga ƙarshema su gaje Dukiyarmu tinda Ƴar tawa dana Ke tutiya da ita ta koma cikinsu wallahi Hafsatu ba zata ci galaba akaina ba"
Dariya Hajiya Lubnah ta saki gami da cewa.
"To ai tuni nake faɗa maki karki ga kin sami daula dole sai kin Miƙe tsaye to gashi nan dai Kirsar da kike cewa kina da Ita bata hana Mijinki Botsare miki ba"
Momy ta ɓata rai.
"Keni kada ki faɗa min magana mafita kawai nake Nema Amman Ni nasan Kirsata tai Min maganin waɗancan tsinannun"
Taɓe baki Lubnah tayi tare da cewa.
"Yanzu dai turo min wani abun Da zan turawa malam ya fara Bincika mana Halin da ake ciki"
Da sauri Momy tace.
"Baki da matsala bari na sako Miki Kuɗin nan ƙawata Aminiyata ta duk duniya dan wallahi Kinfi min ƴan uwana don basa damuwa dani kamar Ke"
Lubnah tai dariya tare da cewa.
"Karki damu Komai nai miki kaina nayi wa Kin manta taren fa bata yanzu bace, Nima Kin min Komai a rayuwata duk da Mijinki yafi nawa arziƙi Amman baki taɓa yada ni ba Komai naki sai kin saka dani Allah dai yabar mu tare"
Bayan sun kashe wayar Momi ta rarrashi Adaah Ta nufi ɗaki domin sallah, Ita kuma Momi ta zauna tana turawa Hajiya Lubnah kuɗin data Buƙata Bayan Awa Biyu Hajiya Lubnah ta Kira Momi tare da ce mata Lamari fa ya wuce nan dole seta zo sunje tare dan bayani a waya ba zai yuwu ba.
Tashin hankalin ƙaryar da zatai wa Abbah ta shiga domin tasan Ba zai barta Ta fita cikin sauƙi ba Koda kuwa da Jikin Iyah tayi ƙarya A haka ta kwana tana Juyi tare da saƙe saƙen yanda zatai Cikin Ikon Allah ma washe gari da asubah Abbah ya zo mata sallama akan zashi lagos sati ɗaya zai yi wato rashin Jituwar da basa yine bai faɗa mata ba, Itama babu wata walwala tai masa fatan dawowa Lafiya ta Juya ta cigaba da uzirin gabanta.
Sai da taji fitar shi sannan ta kira Hajiya Lubnah Akan fitar tasu da magagin Bacci Lubnah ta miƙe se Lokacin ma tasan Asubah tayi Ta shiga Toilet dan ta kintsa domin a cewarta fitar wuri zasu yi.
Itama Momi Kintsawa ta shiga yi tasan Adaah inta farka taga bata nan ba damuwa zatai ba dan haka data kammala shirin sai ta zauna tana Jiran isowar Aminiyar tata.
Abbah Har ya nufi Airport Sai ya cewa driver ya koma da baya suje Chiranchi tinda akwai sauran Lokaci kafin tashin Jirginsu Suna tafe yana duba hanya don ya kwana Biyu bai zo wajan Ɗan uwan nashi ba sanda Motar su ta shiga Layin Baba yana Addu'ar fita daga gida sabida sammako zaiyi Abbatuwa wajan sarin nama domin Idan kana son Nama mai Arha sai kayi Asubanci.
Da sauri Abbah ya Ɓalle Murfin Motar ya fita ya ƙarasa gaban Baba ya tsugunna har ƙasa tare da cewa.
"Yaya barka da Asuba"
Baba ya miƙawa Abba Hannu cikin so da ƙauna irin ta Jini Abba ya kama Hannun Baba ya miƙe suka shiga Cikin Gidan.
Da Saadik suka ci karo wanda yake zaune a bakin Rijiya yana Brush cikin sakin fuska Abba yace.
"Malam Abubakar ashe yau zamu haɗu barka da asubah"
Sai da ya wanke baki sannan ya shiga gaida Abba wanda yaketa Kallon Saadik cike da son Ƙulla Alaƙar Aure tsakanin shi da Ƴarsa shiko Saadik ɗaki ya wuce ba wata cikakkiyar walwala a tare dashi domin shi Mutum ne mai gudun ƙasƙanci.
Abba yabi bayan ɗan uwanshi yana waigen Saadik aranshi yana Jin amintar bashi Ƴarshi domin Irin Yaron da wiya mace ta raina shi, Har Saadik ya shige Abba na waigen shi Tare da Jin rashin daɗin yanda baya sakewa dashi daga gaisuwa shikenan kwanakin baya babu yanda bai da shi ba akan ya dinga zuwa kasuwa wajan shi Amman fafur Yaƙi Yace shi Gwangwan ɗin shi ta fiye mishi zuwa kasuwa.
Innah dake fitowa daga Kitchen hannunta Riƙe da Ludayin Miya wanda take Juya Miyar da zatai Ɗumaman tuwon Ƴammakaranta ta saki fuska sosai tana amsa gaisuwar Abbah
"Dama Amadu kana duniya yaushe rabon duniya da ayyaraye rabon dana ganka har na mance fa"
Abbah ya sosa kai Zai bata amsa Baba ya ɗaga Murya yana cewa.
"Amadu Rabu da Hafsa yau wasan ƙanin Miji take maka zo mu gaisa Ina sauri"
Jiki a sanyaye Abbah ya shiga Rumfar da Baba ke zaune a nutse suka gaisa dan tsananin Kunya Abbah yama kasa ɗagowa ya kalli Baba shiko Baba sai jan Abba yake da Hira koda wasa bai masa maganar komai ba.
Tuwon dawa miyar kuka sai tashin ƙamshi daddawa yake Innah ta shigo masu da shi tare da Koko mai zafi.
"Wato Amadu yasa dole sena karya zan tafi kasuwa, Kin san Hafsatu fa da tuni nakai Titi Amadu wanke hannu a silba Muci tuwo".
Abbah ya ɗauki ruwa ya na wanke hannun shi tare da cewa.
"Wato na jima banci tuwon Innah ba kuma ina marmarin tuwon innah kasan Yaya yawanci matan yanzu ba ko wacce bace ta iya tuwon dawa kamar na Innah"
Aiko mai innah zatai In ba dariya ba ta fice tana cewa.
"Kai Amadu kodai zolaya ta kake yi nikam ba zan tsaya jin daɗin bakin kaba nayi nan"
Daga shi har Abba dariya suke Suka saka hannu tare da Bismillah suka fara cin tuwon Abbah ya zage yaci sosai yasha Kokon Shi kam Baba bai ma ci da yawa ba Ya tashi ya wanko Hannu Abbah ne yakai kwanukan bakin Rijiya ya wanko hannu shima ya dawo.
Bayan sun zauna Abbah yace.
"Dama Yayah batun auren yaran nanne Ina ganin idan na dawo daga wannan tafiyar sai a ɗaura musu Auren, Batun Hidimar Aure dama nace maka bana buƙatar Komai sai sadaki Zan basu gida sannan don Allah maganar Kasuwa har yanzu Ina Barar yazo wajena Ya nemi abincin shi na bawa wasu ma waje bare kuma nawa"
Baba ya nisa kana yace.
"Haƙiƙa Amadu a baya nayi Fushi dakai sabida yadda ka ƙaurace mini ka daina zuwa inda nake, Amman yanzu na huce sabida haka Bari na kira Sadauki! inya Aminta da tayin naka sai ayi komai a nutse dama bai fara Ginin Gidanshi ba kasan yadda lamarin yake yadai sayi fili anan bayan Gidannan"
Baba ya fita yasa Ummi tayi Kiran Saadik wadda tai shirin makaranta Cikin Blue Ɗin Uniform ɗinta.
"Ke Ummi in kika fita ki kira min kawun ku a ɗakin soro"
Ummi ta amsa wa Baba tana nufar soron sai dai ta ga Khadija a raɓe tana share hawaye Ummi tai saurin cewa.
"Ke kuma keda wa kike faman share hawaye?"
Cikin ƙasa da Murya Khadija tace.
"Kibi a hankali kayan kari Innah ta bani na kaiwa kawu Saadik wallahi bakiji ranƙwashin daya Min ba wai banyi sallama ba kuma nayi fa"
Dariya Ummi tayi tana cewa.
"Ba lallai Kinyi ba kuma kinsan halin Kawu su Ya Umar ma shakkarshi suke bare mu"
Ummi ta wuce A bakin Ƙofa tayi sallama sai da yaja aji kafin yace.
"Waye ne?"
Ummi tace.
"Kawu dama baba ne"
Bata ƙarasa ba jin yayi shuru sai can yace.
"Ni kike faɗawa ko ƴan Ƙofar Gida?"
Fahimtar mai yake Nufi yasa taja Labulan ɗakin nashi Ƙamshi da wani Irin sanyi ne suka bugeta daga Nesa dashi ta durƙusa duk Girmansa ya cika ɗakin.
Murya a hankali tace "Dama Baba ne yace kazo"
Ta faɗa tana Raba ido sabida yadda yayi mata masifar kwarjini.
Batare daya kalleta ba yace.
"Kice gani nan"
Ya faɗa yana ƙoƙarin miƙewa daga bakin katifar.
Da.
"To" Ummi ta amsa tana miƙewa ta fita daga ɗakin taje ta sanar da Baba Saƙon sannan suka tafi makaranta Lokacin ƙarfe bakwai da rabin safiya tayi.
09022260850
[12/16, 10:27] Autar Manya: *SO DA ALƘAWARI..!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
*003*
Ita kuma tayi saurin taɓe baki tayi raurau da manyan idanunta waɗanda suka ciko da hawaye ta ƙura masa idanun nata duka tana kallon shi.
Murmushi yake yi har Lokacin hannunsa yana dafe da goshinsa.
"Ni da kika bugawa wannan ƙaton Goshin naki banyi hawaye ba sai ke?"
Hannu tasa ta kare fuskarta tana Murmushi ga hawaye kuma na ƙara zubowa.
Ya ƙara matsowa gabanta ya fita tsayi nesa ba kusa ba hakan ya sa ta ƙara komawa ƴar ƙarama a gabansa.
"To ni yaufa naga takaina Kinga dan Allah zoki rama Duk da nima dai naji zafi"
Dariya ta saki tana cewa.
"Kai kawu Saadik tsokanar kafa nake yi wai ina zaka je Sai ƙamshin turare kakeyi?"
Ta faɗa cikin sigar tsokana
Ya tsuke fuska kaɗan.
"Dama bana saka turare sai zan fita Hawwa'u?"
Saurin dafe baki tayi tana wara ido.
"Wasa nake maka fa"
Ya ɗan kalleta.
"Wai bana ce na soke kawun nan ba su in sun cemin kawu kema sai kice min kawu maza sai wata tazo tana cemin my love ke kina faɗin wani kawu"
Ƙafafu ta hau dirawa ta fara Kukan ƙarya Raɓeta yayi zai shiga ɗakin shi dake soro da sauri ta bishi
Ya tsaya a bakin ƙofar ya kare hanyar da zata shiga ɗakin ya tsareta da ido.
"Abinchi na kawo maka na miƙo maka?"
Ta faɗa tana Waigawa bayanta tare da ɗaukar Kular data zubo masa Abinchin.
Cikin tsananin so da tausayi ya dubeta.
"Bana hanaki kawo abincin nan ba yanzun nan muka kammala cin tuwon innah nida Baba"
Turo baki tayi kaɗan.
"Nima Gas ɗinmu ne ya ƙare seda ummah tayi wa Yayah Fa'izu waya ya kawo mana shiyasa ban kawo maka abincin da wuri ba"
Yadda take maganar Jiki a sanyaye ta ɗan bashi tausayi shikam ya rasa wani irin so yarinyar take mishi wanda yake ganin son da take mishi kamar yafi nashi duk da shima yana sonta.
Ya zira hannunshi ɗaya ajikin aljihun wandon shi.
"To ni yanzu yaya zanyi da wannan abincin tinda nidai cikina ya ƙoshi"
Yanda yayi maganar ta bata haushi sai kawai ta juya