tare da cewa.
"Haba ƴar aljannah, ban sanki da fushi ba haba Hauwa'na mai jiddana"
Yadda yayi maganar ba ƙaramar dariya ya bata ba, Seta sa hannu ta rufe baki tana dariya ƙasa ƙasa, ya wani gyara tsaiwa ya ɗan tsira mata ido kaɗan sannan ya kauda idon nashi.
"Yanzu dai ki wuce muje cikin gida Innah tace bakya zuwa kwana biyu sabida kin zama surukarta tace ko kin ganta guduwa kike yi"
Zaro ido tayi kaɗan cikin sanyin halinta tace.
"Wallahi ina zuwa kawai kwana biyun nan ne, Bana zama kaima ai kasani sauka ta sakoni gaba sai munyi zan sami sukunin zama"
Yadda tai maganar ya kwaikwaiya sai ta kawo masa dukan wasa tana shura ƙafafunta da gudu yayi soron gidansu ta bi bayan shi da wayo ya jata har Rumfar Innah wadda duk suna zazzaune an kunna Fitila mai farin ƙwai sabida babu nepa.
Su kansu su Ummi zuba masa ido sukai ganin yadda ya faɗo Rumfar yana dariya wadda tai mugun yi masa kyau don shi ba ma'abocin yin ta bane.
Inna ce tace.
"Lafiyar ka kaikam ka faɗo min ɗaki kana faman dariya"
Muryar shi ce ta katse maganar Innah inda yake wa Jiddah magana yana waigowa wajan innah.
"Ki shigo mana kin wani raɓe to wai gidan baƙon kine?"
Sai lokacin Innah ta fahimci silar dariyar tashi wato tare da Jiddah suke.
Sai ta kada baki cike da Murnar Ganin Jiddan tace mata.
"Maza shigo Hauwa'u ni na rasa kwana biyu kunyar da kike ji tawa Ko a waje bana ganin ki ko wajan ƙawar taki bakya shigowa duk sabida Sadauki?"
Duk su Ummi dariya suka saka Banda Saadik daya ɗaure fuska aiko ba shiri su Ummi suka kama kansu kowacce ta yi ɗaki sim sim gudun Karsu jawa kansu masga.
Da sanyin ta tashigo ciki ta raɓe a gefe shiko ba kunya ya matsa wajanta Jug ɗin dake hannunta ya karɓa.
Yana ƙwalawa Khadija kira da sauri tazo gaban shi.
"Kawu gani?"
Umarni ya bata akan taje Kitchen ta ɗauko masa Kofi ƙarami ba jimawa ta kawo masa ya fara tsiyaya Kunun ayar aciki ya ɗagawa ya kurɓa ya wani Lumshe ido yana Murmushi.
Jiddah ta ɗan saci kallon shi tare da cewa.
"Nifa ba kai na zowa da shi ba"
Sannan ta kalli Innah tace.
"Innah kinga ya shamin abuna ko?"
Me Innah zatai In ba dariya ba kafin ta Miƙe tana cewa.
"Nikam babu ruwana da sha'anin ku kunfi Kusa ba ina jinki watarana Kina kawo masa ɗan Girke Girken kuba Ni wallahi gwarama anyi auren nan mun huta"
Ƙunshe fuska Jiddah tayi tana Murmushi shiko Saadik kallon Innah yayi yana cewa.
"Innah ko nayi aure ina tare dake babu mai rabani dake"
Innah data kai bakin Ƙofar fita tace.
"Kaji dashi dai ni ba za a min daɗin baki ba"
Innah tana fita ya matsa gabanta ya Miƙa mata Kofin Hannunshi.
"Kema ki shiga kiji gaskiya yayi daɗi nayi dacen mata komai fa Kin iya"
Juya fuska tayi tana ce masa.
"Dan Allah ka matsa baya kar Innah ta shigo"
Da taga yaƙi matsawar sai ta Miƙe tsaye ta fice daga ɗakin, Binta yayi da kallon So da ƙauna Tsananin kunyarta tana ƙara Jefa zuciyar shi a tafkin sonta da ƙaunarta.
Da sauri yabi bayanta kafin ya fita harta kai waje dama yasan ba zata tsaya ba.
Yaji daɗin Kunun Ayar sabida haka da shi ya wuce Ɗakin shi.
Yana shirin zama.
Nurah saiti da Abubakar Babu suka kutso cikin ɗakin nashi Saiti da Babu abokan shi ne tin na ƙuruciya da ihu suka faɗo ɗakin nashi suna rige rigen zama a saman katifa.
Aje Jug ɗin yayi tare da shiga Cikin banɗaki kafin ya fito har sun shanye Kunun ayar yayi tsaki tare da cewa.
"Ku dalla meye haka? daga ganin abun mutum kawai ku ɗauka Ku sha babu izini?"
Babu ne ya yi dariya tare da cewa.
"Dallah ware mu kaje wajan Hajiya Innah ka samo mana abinci yau ba kanta"
A fusace yace
"Ni ba maganar abinci nake muku ba ina ruwana da yunwarku ko gidan baƙon kune Kunun ayar da Kuka shamin zaku biyani"
Nura saiti me zeyi inba dariya ba.
"Haba Dagiya don Tafisu tayo maka kunu mun sha shine kake wannan masifar, Ko shima kunun nata Kishin sa kake tinda naga ƙiri Ƙiri ka hana Tafisu saka mayafi sai Hijabi"
Babu ne ya tare Numfashin saiti da cewa.
"In ma bita zaizai aka zubo maka to sai mu bita tare"
Juya musu baya yayi tare da kwanciya a can ƙarshen katifa bai Kuma yi musu magana ba.
Babu ya miƙe jim kaɗan ya kawo musu tuwon daya je Innah ta zubo musu suka ci suka Ƙoshi suka bar masa kwanukan a wajan sukai tafiyar su dama inda sabo sun riga sun saba da Halin shi abin masifa da ƙunci baya masa wahala.
Uban ƴan tsaftan suna fita ya share ɗakin ya kira salmanu ya fitar da kwanukan harda sawa a samo mai garwashi ya zuba turaren wuta nan da nan ɗakin ya cika da Ƙamshi.
Da yake babbar yaya Aunty Aminah Irin sana'arta kenan turaren wuta take tana aikawa gari gari. to shi kuma mayen ƙamshi ne duk sanda tayi sabo ta aikowa da Innah seta ware nashi daban tace a bawa Auta.
Cire kayan Jikin sa yayi ya ɗaura ƙaramin Tawul ya shiga wanka mayen wanka ne innah har faɗa take masa akan ya rage yawan watsawa Jikinsa ruwa, to da yake shi Mutum ne mai Jin zafi Bini bini ya yi wanka hakan yasa baya rabuwa da Mura wadda inta tayar masa kamar zai Mutu domin tana Matiƙar bashi wahala.
Seda ya kintsa komai sannan ya kwanta.
Yadda Momi ta sami Adaah Hankalinta yayi Mugun tashi kwance ta tarar da ita sai Nishi take sabida tana da matsalar Ciwon Ƙirji Muddin tai kuka Ko ranta ya ɓaci yanzu Ƙirjin nata zai sarƙe numfashinta yayi ta kaiwa da kawowa kamar mai Asma, yawan ciwon Ƙirjinta yasa Ba kasafai take sa kaya masu matse Jiki ba musamman riga domin in har zata sa rigar data Matseta yanzu zaki ganta tana Haƙi tana nishi.
Da sauri momi ta janyota Jikinta.
"Haba Shalelena meze sa ki ɗagawa kanki hankali kita Kuka so kike bayan matsalar Ciwon ki wata damuwar ta Kunno kai In maganar aure ce an gama rusa ta Nan da kwanaki kaɗan zakiji labari mai daɗi ai alƙawari nai miki wannan aure bamai tabbata bane"
Kwanciya tayi akan cinyar Momy hawaye na zuba kamar famfo a idanunta muryarta a dashe tace.
"Baki ga maganganun daya gaya min ɗazu daya zo ba, Mai yasa Abbah na zai kaini Gidan halaka yadda nake hango idanunshi Momy baya da imani Momy don Allah karki bar wannan auren ya tabbata"
Girgiza ƙafa Momy take Iya ɓacin rai Ranta ya ɓaci matiƙa Musamman yadda Adaah ke bata labarin har cikin falon su ya shigo ya gargasa mata magana son ranshi ya tafi.
Wata irin tsuma jikin Momi yake Ture Adaah tayi daga Jikinta tabar Ɗakin domin ba zata Iya zama ta cigaba da sauraron wannan Ɓacin ran ba.
Ranar sai ɓacci ɓarawo Amman Momi kwana tayi tana saƙa yadda zata kasance In burin su ya cika na Rusa batun auren Adaan
Washe gari wajan taran safiya Abbas ƙanin Momi ya kirata a waya bayan sun gaisa yace.
"Yaya maryam dama Iyah ce tace na kiraki gata zakuyi magana"
Jikin Momy a sanyaye ta fara gaishe da mahaifiyarta.
Cikin dattijantaka Iyah tace.
"Maryam ya shirye shiryen aurem Rabin?"
Momi ciki ciki ta amsa da Sai Godiya Innah bata jira cewar Momi ba ta cigaba da yi mata magana kamar haka
"Amadu yace daya dawo za'a ɗaura aure, sabida haka nake son Ki turo Min Rabi tunda Ni ban isa an kawota wajena a matsayina na kakarta ba, To nina na roƙa Ki kawon Ita ta Koyi wasu abubuwan Kona kwanaki Ne kafin tariyarta Kin san Dole sai Ƴarki ta sake halinta ta Koyi tarbiyar Gidan Miji sannan zamanta zai yi daidai"
Ajiyar zuciya mai ƙarfi Momi ta sauke kafin tace.
"Iyah don Allah Kiyi haƙuri wallahi Nasan Adaah ba zata zo gidan kiba, kinga da nan da wajanki akwai bambanci sannan maganar Aure kuma Iyah babu Ita in sha Allahu Adaah ba zata Auri Wannan Baƙin Mugun ba"
Momy ta ƙarasa maganar tana Haɗe ranta, sabida tasan koda wasa Adaah ba zata zauna wajan Iyah ba duk da ta ƙere Gidan Iyah amman ba wani babba bane tasan ƴar tata akwai Tsurfa kwata kwata bata ma saba da Zuwa gidan Iyah ɗin ba tafi zuwa gidan Ƙawayen ta masu cewa tazo ta kwana haka zata haɗa kayanta taje can Shiyasa sai daga baya ta ganar da Adan cewar bafa ƴan uwanta bane waɗancan Ƙawayene.
To yanzu ma kwata kwata bata zuwa ko ina tinda ta ƙara Girma Daga makaranta sai Gida Ko sunce taje bata zuwa.
Ba tare da mamaki ba Iyah tace
"Nasan zaki faɗi fin haka Maryam tinda Allah ya ara miki dama har Kike ganin dan Ƴarki tazo wajena Ƙasƙanci ne, Nima ina ga bada ban albarkacin haihuwa ba da tuni Kin sakeni Kin ɗauki Duniya da ƴan duniya Kin maidasu dangi Ai shikenan Maryama duk yadda kika gani Kiyi duniya ce"
Iyah ta kashe wayar Jikin Momi na rawa take sake Kira amman ba'a ɗaga ba Inda dane da hankalinta baze kwanta ba har sai tabi Iyah gida ta bata haƙuri amman yanzu da yake hankalinta baya Tare da ita yana can wajan son cikar Burinta bata sake Bi takan Iyah ba ta shiga Kiran Lubnah.
Bayan Lubna ta ɗauka tattaunawa sukai akan zuwan Mahir wajan Adaah.Wanda suka bari akan yau zai shigo da Yammah tana gama wayar Kiran ƙawarta Hajiya Sa'a ya kuma shigowa akan yau ake kawo Lefen ƴar ta, wadda zata auri ɗan sarkin Yola.
Momi dabur cewa ta kuma yi a daddafe sukai sallama da wannan ƙawar tata ta shiga sintiri kai ai bama zata bari Adaah ta auri wannan yaro ba ina sam ai hakan babban Ci bayane a agare ta.
Cikin shirin Makaranta Adaah ta fito doguwar Rigar Material mai mayafi ce ajikinta har Lokacin Fuskarta bata saɓe daga Kumburin kuka ba ta ƙaraso ɗakin Momy domin tai mata sallama Momy ta zubawa Ƴar tata ido kafin tace.
"Kai Allah ya isa! wallahi duk wanda yayi silar Jefaki a damuwa Allah ya saka miki Jibi Yadda kika Koma don Allah Kije ki saka kwalli ki gyara anjima Maheer zaizo wajanki Ɗan Babarki Lubnah in kuka daidaita Kawai auren ki zeyi mu huta da wancan auren tsiyar"
Dafe gefen kanta tayi,tana rintsa ido tana so taiwa Momi magana amman ta kasa saboda yadda kan nata Ke faman sarawa
Se zama tai a bakin gado da tausayi momi tace mata In bata Jin daɗi ta haƙura da zuwa makarantar.
Kwanciya tayi a gefen gado tai lamo tana Tuna waye ma Mahir Ita yaushe rabonta da shi
Waya tayi wa ƙawarta Husnah akan yau ba zata iya shiga School ba bata jin daɗi Husnah tai mata ya jiki sukai sallama a ɗakin Momy taita Birgima har bacci yayi awon gaba da ita dama rashin baccine yasa mata ciwon kan.
Bayan sallar la'asar tayi wanka tayi sallah tana zaune Mahir ɗin ya faɗo falon yana faman Kiran Momi kallo ɗaya Adaah tai masa ta shaida shi kauda kanta tayi ko kaɗan bai mata ba, bama kalar Namijin data ke so bane.
Ita ko Momi Sai Murna take suruki yazo se sawa take ana kawo masa kayan Motsa baki shiko ya wani kafe Adaah da kallo tsaki taja ta bar Mishi falon kuma duk yadda Momi ta Bita ta rarrasheta akan tazo su gaisa da mahir taƙi daga ƙarshe ma seta sa kuka tana cewa.
"Yaya zanyi ne Abbah ya kawon ɗan jagaliya ke kin kawon mai kama da fefe tsakani da Allah wazan zaɓa wallahi Momy bai Yi min ba Koni fa na fisa tsayi Ga shegen rawar kan tsiya gaskiya Momy ki sake shawara Nidai abar min Habib yafi min su dukan su"
Ran Momi ya ɓaci tana gudun kar tirjiyar Adaah ya basu matsala da ƙawarta fita tayi ta bawa Mahir haƙuri akan Cewa Adan bata da lafiya ne ta kwanta.
Da rawar Jiki yace amata sannu zai dawo domin shi kam yaga waje dan baya jin zai iya haƙura da Neman aurenta koda in ya auren ta zata kashe kanta ne sabida wannan Dukiya daya hanga a gidan yasan in ya auri Adaah Kakarshi ta yanke saƙa ai shi du yadda Mamanshi ke kwaɗaita masa abin Bai tabbatar ba seda yazo dan shi bai taɓa shiga Cikin Gidan ba sai yau ko kawo mamarsu yayi to daga waje yake Juyawa.
Tare suka jero da Baba shi ya dawo daga shago baba kuma ya dawo daga kasuwa, Hannun Saadik riƙe da manyan ledojin daya yo musu siyayyar gida.
Har tsakar gida suka ƙarasa Innah tana daka daddawa Saadik ya mata sannu da aiki ya aje Ledojin yana ƙoƙarin ya juya Baba ya kira shi.
Ya dawo gaban baba ya tsugunna Baba yace.
"Sadauki nikam banji kana yin shirin bikin kaba, kaga jiya Amadu ya min waya yana ƙara tabbatar Min da ɗaurin auren ku bayan ya dawo"
Cije yatsa yayi sam ya manta da maganar gaba ɗaya Tunanin shi bama ya kan batun
"Baba akwai wasu kuɗaɗe dana aje akan fara ginina In sha Allah zan kaiwa Aunty Amina a fara haɗa lefe sannan batun wajan zama wannan Gidan da yake kallon mu naga masu gidan sun tashi zan wa mai gidan magana in babu wanda ya kama ni Ina so"
Baba ya faɗaɗa far'a tare da cewa.
"To Allah yayi jagora Ubangiji ya sawa abin albarka yanzu naji batu"
Innah kam dakanta ta cigaba dayi dan ba zata tabbatar da Murna ko takaicin auren ɗan nata ba tana dai yin addu'ar zaɓin alheri kawai.
Tashi yayi tare da nufar ɗakin shi.
Har ji yayi kansa na juyawa sabida Tada maganar da Baba yayi.
Ya zira Key a jikin Ƙofa Yaji alamun Kuka a bayan shi da sauri ya juya sukai idanu Huɗu da Jiddah Kwanon abinci ne ta kawo masa tazo Baya ɗaki zata Miƙawa Innah ta aje masa ta kuma gaida Innar wadda tace bata shigo wa kwana biyu tana shirin shiga Gidan taji maganar Baba wadda yake wa Saadik kuma tasan ba akan ta bane to wacece wannan wadda zata aure shi in ba ita ba inko itan ce ai ba shirin yanzu bane tinda taji Baffa yace seta gama makaranta.
Tana ƙara kallon shi sai taji zuciyarta ta karye wani Irin ƙaƙƙarfan kuka na ƙara tawo mata.......
SO DA ALƘAWARI....! littafin kuɗi ne 500 Naira zuwa asusun bankin 0078174806 sterling bank ko kuma, 9022260850 Opay bank,Shaidar Biyan kuɗi zuwa 09022260850, Ƴan Private waɗan da ba sai nayi adding ɗinsu a grp ba ta Private kawai zan dinga tura musu 1000 Naira ne in sha Allah.
[12/16, 10:27] Autar Manya: *SO DA ALƘAWARI..!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
*009*
Yana sa ƙafafun sa a ɗakin sukai idanu huɗu da ita kallon juna suka shiga yi kafin da sauri ta janye idanunta daga cikin nashi tana mai juya kanta gefe bata sake kallon shiba.
Saiti da Fa'izu suka sami gurin zama suna gaida ummah saɓanin Shi daya ƙarasa gaban gadon yana zubawa inda ta juya idanu.
Tsananin kunyar Umma tasa ya nemi gefe ya jingina kafin yaɗan rissuna ya shiga gaisheta.
Ba yabo ba fallasa umman take amsawa fuskarta ɗauke da damuwa.
Maganar fa'izu ce ta katse shurun ɗakin sabida tinda suka gaisa babu wanda ya kuma yin wata magana.
"Ummah wai me ya sameta har kuka zo asibiti?"
Shuru ummah tayi kafin ta furta.
"Shirme ne kawai irin na Jidda da yarinya yo Allah na tuba namiji goma uba goma ne ni wallahi tin kafin ayi auren nan lamarin nan ya fitar min da ga rai"
Saadik ya rintse ido ya shiga furzar da iska mai zafi, yaji ɗacin maganganun ummah domin tana Babba bai dace tana faɗin irin haka ba, in rai ya ɓaci zuciya ake dannewa bare ma shi bai ga wani abun zafi daya ma ƴarta ba.
"Umma wani abunne ya faru da Jiddan ni duk kin sakani a duhu na kasa fahimtar abin da kike nufi wallahi"
Ƙaramin tsaki taja.
"Wai dan mahaifan Abbakar sunce zasu aura masa ƴar uwarsa shikenan ta faɗi a soron gidansu ta suma yana kallon ƴar tawa ya tsallake ya tafi ya barta a haka ba da ban Allah yasa mutan gidan sun ganta ba da ko mutuwa zatai babu wanda ya sani ni wallahi Jiddah batai zuciyata ba sam danni inda nice da yanzu wata maganar ake ta daban banda abin ta menene na ɗaga hankali akan namiji"
Murmushi fa'izu yayi gaba ɗaya kunyar abin da mahaifiyar shi tayi yanzu ta gama kamashi inya fahimta ummah tana cikin zafin kishin ƴarta ne shiyasa take faɗin duk maganar data zo bakinta.
"Ummah bai kamata ki dinga faɗin irin haka ba shi aure nufin Allah ne karku bar shaiɗan ya raba alkairi don Allah ku dinga sauƙaƙa zuciyarku"
Ɗaga masa hannu tayi da sauri Saadik ya fita daga ɗakin yana jin ba zai iya jure cin fuskar da mahaifiyar Jiddah ke masa ba kuma baya jin zai iya tanka abin da take faɗa sabida yana ganin girmanta.
Nura da kansa ya kulle da lamarin shiya iya musu sallama ya baro ɗakin a titi ya hango Saadik yana tafiya sabida saurin da yake har yayi wa Nura nisan da bai tunani ba sai da Nura ya ƙarasa da gudu sannan ya cimmasa.
Tafe suke babu wani wanda yace wa ɗan uwan shi wani abun, sanin halin Saadik da Nura yayi in yana cikin damuwa baya magana har sai ya huce damuwar ta tafi sannan yake samun damar yin maganar.
Da ƙafa suka ƙarasa gida a ɗakin Saadik suka yada zango Nura ya zauna a gefen katifa shi kuma Saadik ya shiga banɗaki ya jima aciki sannan ya fito ya ɗauki Jallabiya ya koma banɗakin ya saka sannan ya dawo ya zauna.
"Wai Dagiya meya ke faruwa ne?, gaba ɗaya kaina ya kulle kaifa kana da matsala wato mu semu faɗa maka duk abin da yake damun mu amman kai zurfin cikin tsiya baka bari a tattauna damuwarka"
Yaja ajiyar zuciya mai ƙarfi saman hancinsa kamar kullum yayi jajir sabida ɓacin rai da damuwa idanunsa ya kaɗa yayi ja ya kalli Saiti tare da cewa.
"Aure baba zai mini, auren dole shine ita kuma take wannan shirmen har take kwanciya a asibiti"
Da mamaki saiti yace.
"Aure kuma kai ban fahimta ba aure da wa kuma?"
Ya lumshe ido kafin ya buɗe a wahalce yace.
"Wata yarinya ce ƴar ƙaninshi da sukai alƙawari zasu haɗa auren mu, to abin nima kaina da ka ya zo mini"
Saiti me zeyi in ba dariya ba harda kifawa ganin Yadda Saadik ya haɗe ranshi yana cewa auren dole baba zai mashi.
"To kai kam kaji daɗin ka ina ma nine aure a wannan ƙadamin ai sai ka shirya, Allah ya tabbatar da alheri inna fahimta Maman Tafisu taya ƴarta kishi take yi har taso tai abin kunya a gabanmu"
Jingina kanshi yayi da jikin bango ya rintse ido maganganun Ummah sun ƙona masa ranshi, inya fahimta Jiddah ce ta haɗa masa ƙarya da gaskiya a wurinta shine ita kuma ta hau ta zauna ta goyi bayan ƴarta in ko haka rayuwarsu zata tafi akwai matsala babba tabbas!
Nura ya tashi yana masa sallama tare da ce masa gobe zasu haɗu dasu Babu a tattauna akan bikin shidai bai cewa Saiti komi ba har ya bar masa ɗakin.
Dama ya ɗaura alwala a banɗaki sabida haka sallar isha'i yayi har ya cire jallabiyar jikinsa zai kwanta ya tina bai leƙa wajan innah ba yasan ko yayi bacci sai ta tashe shi yaci abincin dare, sabida haka rigar ya maida a jikinsa ya saka takalmi ya fita cikin gidan.
Da umar suka ci karo zai shiga cikin gidan shima, umar yaja baya yana bawa Saadik wuri don ya wuce, sai da ya shiga sannan umar yabi bayan shi yana cewa.
"Dama Kawu Saadik neman ka nake naje ɗakin ka na ganshi a kulle lissafin kuɗin ƙarfan motar nan ne"
A hankali yace.
"Umar kaje ka huta mu barwa safiya mana sai kace zaka gudu"
Dariya umar yayi yana cewa.
"Gobe ina da Exams a school zan fita da wuri sabida karatu"
Ya ɗan juyo yace.
"Ban gane sabida karatu ba, da me kake yi da baka yi karatun jarrabawar ba?"
Umar ya shafa kai tare da cewa.
"Kasan yanayin shagon yanzu anfi ciniki sabida masu cire rodin aikin titi, shiyasa bana son na motsa ko ina, kasan su Usman ba kamar niba in aka ga sune a shagon raina musu hankali ake su tsula kuɗi suyi tsada"
Saadik yaɗan ja ƙaramin tsaki.
"Wannan ba dalili bane, kada ka kuma sake jarrabawa tazo bakai karatu ba, ka miƙo makullin shagon ni sai na zauna kai kuma ka dinga zama a gida kana karatun ka har ku gama jarrabawar Allah ya bada nasara, in da wani abun da zasu siya kuma ka sanar dani koka ɗauka kawai"
Umar ya rissuna cikin ladabi yana masa godiya su kam tsakanin su da kawun nasu sai dai addu'a amman abin da yake musu a rayuwa na kyautatawa yafi gaban baki ya furta.
Shiga ɗakin Innah yayi shi kuma Umar ya shiga nasu ɗakin da yake kusa dana Baba.
Da sallama a bakin sa ya zauna a gefen gadon innah kafin ya jingina kansa ajikin gadon ya zuba mata ido tana lazumi ne carbi mai dubu a gabanta.
Har ya soma bacci sama sama yaji muryarta tana tashin sa.
"Sadauki! sadauki!! bawan Allah wato har yayi bacci"
Ya Mitsika idanun shi waɗanda suka ƙanƙance sabida bacci yana kallonta.
"Innah wai sai yanzu kika kammala kenan na dawo ne shine nace bara na zo muyi sallama sai da safe kuma"
Ya faɗa yana miƙewa yana saka hannu a baki yana hamma.
"A,a sadauki ka daure kaci tuwo mana kada ka kwana da yunwa"
Ya wani zaro ido ya saki ƙaramar dariya.
"Haba Innah so kike dole dai na zama ɗan gargajiya, tuwon darannan kumbura min cikina yake amman ke dole sai naci"
Dariyar itama ta saki.
"Dama kai tin kana yaro baka son cin abinci sosai to yanzu bara na dafa maka ruwan shayi kasha sai ka kwanta, Yaya jikin Jiddan?"
Ya lumshe ido ya buɗe tare da cewa.
"Da sauki tana ma gaishe ki"
Ya ɓoye mata zuwa asibitin da kuma maganganun ummah sabida su iyaye ba komi ake son faɗa musu na ɓacin rai ba.
"Innah kibar shayin nan zan fita na sayi kankana da lemo na sha na kwanta"
Ta zuba masa ido cikin so da kauna tace.
"To kadai kafe amman mai kankana zata maka maza jeka ka siyo ɗin kada dare yayi"
Ya fita yana dariya ƙasa ƙasa tin yana yaro innah ta saba masa da zaman gida in baya gida yana wajan neman kuɗi ko makaranta, bata son yawo ko kaɗan kuma bata son yawan abokai ko su Nurah ma don abokan shine tin na ƙuruciya shiyasa ta barsu tare amman innah macece mai saka ido sosai akan lamarin ƴaƴanta ta gwammace in yana gida ya zauna suyi hira ko girki tare, to hakama ƴan jikokin nan nata Motsi kaɗan tace a duba mata wane takan ce Allah shike da rayuwa dai amman kaima ka kula sosai ka kuma haɗa da yin addu'a.
Sai da ya je ya siyo kankanar ɗauri uku aka masa ya kai tasa ɗaki ya miƙawa Innah leda biyun aiko tana tsakar gida da fitila a hannunta.
"Yawwa dama kai nake jira ka shigo to sai da safe"
Ta karɓa ta juya ɗakinta.
Shima nashi ɗakin ya ƙarasa yayi duk abin da zai ya sha kankanar ya yi brush haɗi da ɗaura alwala sannan ya kwanta nan da nan bacci mai daɗi ya ɗebe shi.
***
Sai da Momi taga fitar Mahir sannan taja ajiyar zuciya ta shiga sintiri a falo kanta ya ɗau zafi gaba ɗaya lamarin Adaah nason bata matsala tana ganin kawo Mahir shine mafi sauƙi da kuma mafita a garesu amman Adaah zata ce beyi mata ba.
Da sauri ta koma cikin ɗakin Adaah wadda take zaune ta zabga tagumi Motsin Momi yasa ta ɗago ta zubawa momi idanu har momi ta ƙaraso bakin gadon ta zauna jiki a sanyaye.
Ta dubi Adaah kafin tace mata.
"Ki nutsu zamuyi magana"
Cikin sanyin jiki tace.
"Ina sauraron ki Momy"
Momi ta gyara zama tare da tattara hankalinta ga Adaah kafin tace.
"Ni ban gane miki ba fa Adawiyyah jiya kinsan wahalar dana sha kuma duk akanki, tafiya mukai tamkar zamu bar garin muka je wajan wani shahararren malami shiya ce mana dole auren ki da Mahir shine mafita sauran bayanan kanki bazai ɗauka ba, amman dai don Allah kada ki watsa min ƙasa a ido duk