Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 9
Musulunci da yamma an gama tabbatar da duk abin da ake bukata na hujja gare shi, kotu ta yanke masa bulala dari gobe. Suna zaune suna hira da Malam Liman suna sauraren rediyo, anan ne yaji sanarwar batan da yayi. Sam bai damu ba domin yasan mahaifinsa ne ya saka ayi wannan cigiyar, don haka ya kudura a ransa ba zai koma gida ba har sai ya gama jinyar bulalar da aka yi masa sannan ne zai dawo gida kuma da zummar tonawa kansa asiri. "Allah Sarki, Allah Ya bayyanawa iyaycn yaron nan shi, ace saurayi mai wannan shekarun ya bata har yanzu ba a ganshi ba?" 168 Zuri'a Daya-l Sa'adatu Muhammad Waziri Kalaman Malam Liman su ne suka doki kunnen Hameed daga barin dogon tunanin da ya tafi. "Malam Aminu ban ji ka ce amin ba, ko baka ji sanarwar 6atan yaro saurayi mai irin shekarun ka ba?" Sunan da ya fada masa kenan ba don haka ba da yanzu asirin sa ya tonu a yau din nan, don cewa zai yi ya koma gida gurin iyayen sa don hankalin su ya kwanta. Cikin sauri ya ce, "Amin Baba, naji, to abin ne dai sai addu'a, kowa da irin nashi matsalar". Sun jima suna hira, daga bisani ya tafi ya barshi a gurin yana tunanin halin da zai shiga gobe, amma idan ya tuna cewa a gurin Allah ya yi (free) ba shi da wani tabo sai na Aziza sai ya samu yaji wani farin ciki ya kama shi, domin ya san shi din ma zata yafe masa idan ya je ya roke ta ya gabatar da cewa shi ne ya yi mata haka. Matukar ta yafe masa to ko kashe shi za ayi to ayi tun da ya tarkaka. 169 Zuri'a Daya-I _Sa'adatu Muhammad Waziri A ranar da ya cika kwana hudu a gidan a ranar ne aka yi masa bulala dari cif, haka aka yi masa a bainar jama'a ana kirgawa, tana cika aka saka kabbara tare da ce masa Allah Ya yafe masa. Duk wanda ke gurin sai da ya yaba da karfin zuciyar Hameed, domin ya nuna jarumta. Malam Liman sai da ya zubar masa da hawaye ba don komai ba sai don birge shi da ya yi, da tsayawa da kafarsa ganin yaji kunyar duniya d da ta lahira, da kuma dada yaba da ya yi gurin dagewa da sai an fitar da hakkin Allah akan sa. Tabbas a wannan zamanin da za a samu samari da suke da karfin imani da 'yan mata wanda za su bayyana laifin da suke yi don ayi musu hukunci da shari'ar Allah lallai da mun samu saukin wannan masifu da suke addabar mu cikin birane da kauyukа. Ya Allah Ka kawo mana Karshen wadannan rashin zaman lafiya da ya addabi 'yan uwa Musulmi a duk inda muke a fadin duniyar nan, Ka tona asirin dukkna azzalumai da suka hana mana zaman lafiya a kasar mu, ameen. 170 3 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Suna fitowa daga gurin da aka yi masa bulala a gurin ya fadi sumamme, hankalin Mal. Liman ya yi mugun tashi, domin ya yi matukar kaduwa ganin yadda yanayin sa ya koma, ko ina cikin jikinsa shatin bulala ne rudu-rudu. Ya jima can sai Allah Yasa ya farfado a haka cikin taimakon Allah suna shirin barin gurin nan ya sake yanke jiki ya fadi, jama'a da dama a gurin sun yi zaton ya mutu, canz sai ya soma numfashi. A na cikin wannan halin sai ga wani babban Alhaji ya zo da motar sa zai fita aka daga masa hannu akan ya zo ya taimaka musu. Yana zuwa gurin sai ya ga kamar ya gane fuskar sa, dubawar nan da zai yi kuwa sai ya ga ya gane fuskar sa, a kidime ya се. "Subhanallahi! Wannan ai Hameed ne, bayin Allah ku taimaka min na shigar da shi motar na kai shi asibiti, ai danmu ne yau kwanan sa hudu ba mu ganshi ba". A rude yake maganar yana ta faman cewa a taimaka masa, hade da cewa. "Hameed me ya faru da kai haka?" 171 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Mal. Liman ya ce, "Alhaji naji kanaccwa Hameed, wannan fa sunan sa Aminu". Bai jira ya saurari abin da yake cewa ba aka taimaka masa suka saka shi cikin motar, Mal. Liman ne ya shiga suka ja suka tafi abinsu. Arewa suka nufa cikin tashin hankali, a hanya ne Mal. Liman yake cewa. "Aminu ne fa sunan sa ba Hameed ba ranka ya dade". "Malam don Allah ka barni haka, ko ma dai meye sunan da ya fada maka wannan yaro na ne, kenan da sunana ya yi maka amfani? Ni ne Aminun shi kuma Hameed. To wai Malam meye ne ya faru da shi har ta kai shi ga zuwa kotu? Kuma naga duk jikin sa da jini, hatsari suka yi ne?" Duk a gaggauce yake masa wadannan tambayoyin. "Alhaji amma dai ba kai ne mahaifinsa ba ko?" "Eh ba ni na haife shi ba dan yayana ne da muke uba daya da shi, ni ne nake bin mahaifin sa a gurin uban mu". 1 172 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Yauwa ko da naji, muje ga zuwa asibitin mu yi kokarin ceto ransa, daga nan sai na sanar da kai halin da akc ciki". Yana rufe bakin sa sai gasu sun shiga cikin asibitin, a gaggauce aka fito da shi aka shiga ciki da shi, nan likitoci suka fara aiwatar da abin da ya kawo su. Tsananin rudani da tashin hankali ne suka bayyana a fuskar Alh. Aminu lokacin da ya gama sauraron bayanin da Mal. Liman yake yi masa na game da abin da ya faru ga Hamced. Tsabar takaici sai da hawaye suka zubo masa ba don komai ba sai don jin cewa ashe Hameed ne ya jefa su cikin wannan bakin cikin da ga a daya ZURI'Ar su suke ciki na tsawon kwanakin nan. Mikewa ya yi zumbur уa сс, "Пamced ba shi da wani amfani a gurin mu a yanzu, yaje shi da mahaifin sa mun yafe su cikin ZURI'A tun da abin nasu babu tsoron Allah a ciki. Wato dama yaya Jafar shi ne ya batar da dansa don kada kowa ya ganc me ya faru shi ne zai zo ya tayar mana da hankali, bamu fita daga wannan ba ya kara jefa mu cikin wani. 173 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Tunda ya ci amanarmu mu kuma za mu nuna masa cewa bai isa ba, domin sai mun datse duk wata igiyar DANGANTAKA da take tsakanin mu da shi, yajc su kara. Dan nasa ya mutu tunda abin na shi haka ne nima na tsame hannuna akan al'amarin sa". Yana gama fada ya juya zai tafi, da sauri Mal. Liman ya saka hannu bibbiyu ya riko shi, ya soma сewa. "Haba Alh. Aminu, bai kamata ka yanke wannan hukuncin ba lokaci guda, shi komai na duniya dan hakuri ne, duk abin da kayi hakuri akansa to cikin yardar Allah zai zamo tarihi. Ka tausayawa Hamed ka kuma duba muhimmancin zumuncin Allah, idan kai ma kayi haka kamar ka jagoranci cewa zumuncin ku ya Kare". Nan ya samu ya gaya masa duk abin da ya faru da Hameed da mahaifin sa, ya kuma tabbatar masa da cewa hakika Hamced ya yi laifi ya kuma yi matukar nadamar abin da ya aikata ba don mahaifinsa ya hana shi fadin cewa shi ne ya aikata wannan laifin ba da tuni ya bayyana muku kansa kun hukunta shi. 174 Zuri'a Daya-1 sa'adatu Muhammad Waziri Sai da ya gama fada masa komai jikinsa ya yi sanyi, nan take ya ji tausayin Hameed ya kama shi, ya daina ganin laifin sa sosai akan na mahaifin sa. Babu abin da Mal. Liman ya boyewa Alh. Aminu na game da labarin da Hamced ya fada masa game da abin da ya faru da shi tun daga ranar da abin ya faru har zuwa yau. = Kwana biyu Hameed ya yi a gadon asibiti bai san a wane hali yake ciki ba, Alh. Aminu ne yake zaune da Mal. Liman suna jiyyar sa domin babu wand aya fadawa cewa ya samu labarin Hameed. A rana ta uku ne ya dawo cikin hayyacin sa, nan ne likitoci suke fada musu cewa ya kamu da ciwon zuciya mai tsanani hade da ciwon (ulcer) domin tsananin damuwar da yake ciki da rashin cin abincin da yake yi. Lokacin da Hameed ya dawo cikin hayyacin sa da ya ga kawun sa a tare da shi ya shiga rudani da mamakin ganinsa, nan ya shiga kuka yana fada masa duk abin da ya faru da shi tas, babu abin da bai fada masa ba. 175 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Bai wani mamaki ba domin ya samu duk labarin gurin Mal. Liman, sai dai wani karin baynin da ya yi masa a game da mahaifin sa nan ya gaya masa ccwa don Allah Ya barshi ya mutu, bai son komawa ya kara ganin Zuri'ar su. Tausayin sa yaji sosai, ya ce ya daina kuka kuma komai zai wuce insha Allah tunda ya yi nadama, sai dai ya yi kokarin neman yafiyar abin gurin yarinyar da mahaifinta, idan sun yafe masa to ya yi (free) duniya da lahira tun da ya fitar da hakkin Allah, idan sun yafe masa shi kenan. Zaune suke a falon ya gama labarta masa halin da dansa Hameed yake ciki da kuma abin da ya faru suka foye musu. Zufa ce ta zubo masa, nan da nan hankalin sa ya yi matukar tashi, ya mike tsaye ya yi saurin dawowa gurinsa ya zauna kusa da shi, cikin kidimewa ya ce. "Aminu ka daure ka rufa mana asiri, matukar babu wanda ya sani don Allah ka rufe maganar nan a gurin nan, domin kada mu tozarta ni da iyalina a cikin Zuri'a". 176 Zuri'a Dayo-1 Sa'adatu Muhammad Waziri Ran Alh. Aminu ya yi mugun baci, ya cе. "Haba Yaya, wai kai me yasa ka fiyc son kanka ne? Kai komai kanka ka sani, baka son farin cikin kowa sai naka da na iyalinka. Ka tuna cewa uban yarinyar nan ya yi matukar yarda da kai da danka, amma ace kai da kanka kasan abin nan bayan ya faru amma ka ki ka je ka fada masa da kanka, ka ce kuma wani ba zai je ya fada masa. Yaron da kansa yana son ya fada masa amma ka hana shi don kada ka tozarta, amma kai danka ya tozarta tasu, to shin wannan a ganinka shi ne Zumunci ko halacci?" "Aminu wallahi nima ban yi farin ciki da faruwar hakan ba, har yanzu ina jin bakin cikin faruwar wannan al'amarin". "Ban yarda ba, idan har abin nan bai yi maka dadi ba to kamata ya yi ka hukunta Hameed a idanun duniya, ka nunawa Zuri'ar ka ccwa can cikin ka ya aikata ta'asa sai ka mika shi ayi masa dukkan hukuncin da ya kamata, sannan ka nuna kayi fushi da shi. Amma baka yi ba, don son nuna kaunar da sai shi ne ya yi abin da ya dacc. 177 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Don haka yau tun da komai ya zo kunne. na da kaina zan je na sanar da kowa na Zuri'a din nan yasan abin da danka ya yi mana". Cikin sauri ya rike shi ganin ya mike zai tafi, ya ce. "Aminu ka tsaya ka saurare ni ka kuma fahimce ni, wallahi ba a son raina haka ya faru ba. Ina so don girman Allah ka rufa min asiri kada kowa yasan mene ya faru, Aminu ka fadi duk abin da kake so a duniyar nan ko mene ne nayi maka alkawarin mallaka maka shi matukar za ka rufa min asiri". Juyowa ya yi yai maşa wani irin kallo na rashin fahimta. "Aminu ka daure ka rufa min asiri domin zumuncin da yake tsakanin mu, wallahi ko me kake so zan yi maka shi, ka fada das bakin ka". "Jafar bani da abin da zaka iya bani, ka barni na yi tafiya ta". "Aminu don Allah jira ni na fito". Yana fadin haka ya yi sauri ya shiga ya je ya fito da tarin wani (files) ya zo ya ajje su gaban sa, ya ce. 178 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri 1 "Aminu ka zauna ka duba (company) na ne da tarin manya-manyan filaye na ka zabi duk abin da kake so na baka shi duniya da lahira matukar zaka bar wannan sirrin tsakanin ni da kai, hatta shi Hameed din ba zan so ya san wannan sirrin ba, kai ko babban (company) na kake so mutukar zaka tufa min asiri to a shirye nake na baka shi yanzun nan zan saka hannu na mallaka maka shi duk domin kada ka tozarta min Hameed a idanun duniya". Zaro idanu ya yi yana kallon sa cikin mamaki, ya jinjina kalaman da yake masa magana. Tabbas yasan girman wannan Company din da suna da daukaka da ya yi a kasar nan, domin da wannan komfanin Zuri'ar nan take ji da shi, kuma nashi ne halak malak, babu kudinkowa, amma haka yake kokarin ganin ya sama kuwa nasa Investment a ciki shi ne yake masa maganar zai mallaka masa a matsayin toshiyar baki. Nan take yaji yana son gasgata kunnen sa, anya kuwa yaji abin da ya fada masa? ba?" "Aminu ko baka ji abin da na fada maka Cikin sauri ya ce, " Company?" 179 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Eh shi nake fada matukar ka amince zaka rufa min asiri to wallahi a shirye nake na mallaka maka shi a yanzu cikin sirri". Komawa ya yi ya zauna yana ajje numfashi, ganin yanayin sa a haka sai yaji ya fara samun nutsuwa don haka shima sai ya zauna. "Ba zan iya karbar wannan Company din ba, domin ni kaina idan nayi haka na shiga cikin tuhuma, don haka na yarda zan rufa maka asiri, sai dai ka bani dukkan kananan kamfanunuwan guda biyu na Lagos da na Kaduna, idan kayi min haka nima zan fi samun nutsuwadon babu wanda zai lura da haka, idan ka amince to nima na amince ka dauko mu yi yarjejeniya a yanzun nan". Farin ciki ne ya bayyana a fuskar Alh. Jafar, cikin hanzari ya се. "Wannan ba wani abin dimuwa bane, na amnce matukar maganar ba ta fito ba shi kenan, amma idan har ka kuskura magana ta fito to dole ne ka dawo min da abu na". 180 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Hankalin sa a tashe yakc kallon Hamced kwance kan gadon asibiti, tsananin tausayin yaron nasa da kaunar sa su ne suka rufe shi lokaci guda. Hameed yana kallon mahaifin sa ya kau da kai don baya son ganin sa, domin ya dauki laifin hana shi sukuni da kwanciyar hankali duk ya dora masa, domin da ya barshi ya fada abin da ya aikata da duk hakan bai taso ba. "Hameed ka cika kafiya da taurin kai, ka kuwa san irin tashin hankalin da na shiga da ban ganka ba, ashe kana cikin garin ka gama rudar damu? To shi kenan yanzu ai kja huce tun da kaje anyi maka bulalar ko?" Ya karasa fada cikin kasa da muryar sa. Runtse idanu yayi don bai son ganinsa, -, haka ya karaci bayanin sa bai ce da shi komai ba. "Hameed ba Daddy dinka ne yake maka magana ba ka rabu da shi?" "Kawu me zan ce da shi bayan bai son na samu nutsuwa cikin zuciya ta?" 181 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Alh. Aminu ya daka masa tsawa, ya ce, "Hameed kana da hankali kuwa? Kasan me kake fada kuwa? Mahaifinka ne fa?" Cikin zubar hawaye ya ce, "Kawu to me zan fada ban da haka? Matukar Daddy yana so na ci gaba da rayuwa cikin walwala da farin ciki to ya barni na je na wanke kaina gurin su Abba, na fada musu cewa ni ne na cuci Aziza, idan sun ji su yi min dukkan abin da idan suka yi min zai zamo sun fauki fansar abin da nayi musu. Ko kuma shi da kansa yaje ya fada musu cewa ni ne na aikata mata haka, tunda yanzu na dan fara samun nutsuwa cikin raina a gurin Allah na tsarkaka da laifin da nayi masa, don haka ya zamar min dole suma na samu abin da zai janyo nayi (free) a gurin su". "Hameed baka da hankali, kana tunanin akwai wani uba ko uwa da za su iya yafe maka wannan laifin da tashin hankalin da ka saka su? Idan kana tunanin za su yafe maka to kayi karyha, gwara ka ja bakinka ka yi shiru tunda Allah Shi Ya yafe maka". Cewar Alh. Jafar. 182 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Runtsc ido ya yi yana kokarin gyara kwanciyar sa hade da datsc baki don zafin da yakc ji a jikin sa. Da sauri Alh. Jafar dya zo zai rike shi, ya yi sauri ya daga hannu alamar kada ya taba shi. Saroro suka yi suna kallon sa don abin ya yi matukar bashi mamaki. Hameed ya ce, "Daddy duk abin da kake magana akai da gangan kake yin sa, ka sani Allah Bai yafe hakkin wanda aka zalunta, kawai son zuciya da son da kake min duk su ne suka rufe maka ido, kana kallon gaskiya kake kaucewa. Dadddy, idan ba ka taimaka min gurin Allah na tsira ba to me zaka yi min a duniyar nan?" Ya fada yana mai kafe idanunsa akan shi. Jikin su ya yi sanyi, aka rasa mai iya cewa komai cikin su. "Kawu kai idan kana son na samu farin ciki tun daz na fada maka komai kaje ka sanar da su Abba su sani tun da shi Daddy ba zai iya ba". 183 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Hamced naji, ka kwantar da hakalin ka insha Allahu komai zai zo cikin sauki, muna son abi komai a hankali don mu samu zumuncin mu kada ya zo ya samu tangarda, abi abin cikin kwanciyar rai da yardar Allah za mu dai-dai ta yadda za'a fahimci juna". "Shi kenan Kawu, ina jiran lokacin, amma fa ba de dadewa ba. Ina son kafin a sallame ni ku sanar da su don maiukar baku yi min haka bą to ni da kaina zan je na fada musu kamar yadda na kawo kaina kotun Musulunci babu wanda ya sani to haka can ma zani ba tare da kun sani ba". Daga hannu ya yi ya dauke Hameed da mari cikin kunar rai, sam ya manta a cikin jinya yake. Cikin kaushin murya ya ce. "Ranar kuwa da na tsine maka, na fitar da kai daga jerin ahalina na har abada tun da baka son rufin asirinmu, bayan wannan abin duk din kada ka tozarta nake yinsa". "Haba Yaya, me. ya yi zafi zhaka? Ko ka manta a kwance yake bashi da lafiya ne?" Huci yake yi kamar damisa, ya cе. 184 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Aminu ni yaron nan zai kawo wa sakarcin banza don yana yin abu ina bin bayan sa? Zo mu tafi, Allah Ya bashi sa'a yajc ya yi duk abin da zai yi, ni kuma zai ga wane mataki zan dauka akan sa". Yana gama fadin haka ya sa kai ya fice zuciyar sa na yi masa zafi, yana mamakin wai Hameed dinsa ne ya zama haka. Alh. Aminu tsaye gurin sa yana bashi baki akan ya daina yi ma mahaifin sa taurin kai, ya bi abin a hankali shi da kansa zai san abin da zai yi. Kuka Hameed ya fara yi, ya ce, "Kawu ni kaina ba a son raina na fadawa Daddy zhaka ba, nayi masa hakan ne don ya tsane ni ya barni nayi abin da ya dace. Hakika nasan saboda son da yake min yake hana ni na je na fada, to amma ya za ayi na ci gaba da rayuwa da kunci a rayuwata da hakkin da ba a yafe min ba? Don haka Kawu dole ne na fada musu idan ku ba za ku iya ba". 185 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Hamced ka bar maganar nan tun da mahaifin ka baya so, ka bari cikin ruwan sanyi zan yi masa dole da kansa zamu je gurin su mu fada musu". Farin ciki ya kama shi, ya ce, "Kawu na gode sosai, kuma don Allah ka bawa Daddy hakuri, na san ya yi fishi da abin da na fada masa". "Kada ka damu, zan ganar da shi kuma insha Allah komai zai zo cikin sauki". * * * A 'yan kwanakin nan kullum cikin tashin hankali muke a cikin asibiti, domin Aziza kullum cikin firgita take da yawan yin kara sai dai kuma yanzu sam bata son ganin namiji a gabanta ko ma wane, domin ta dinga shiga razana dole ya zamo mu mata da likitoci mata su ne muke kula da ita. Haka abin ya ci gaba da tsorata mu har muke tunanin cewa ko ta samu tabin hankali ne, bayanan likitocin suka yi mana shi ne ya soma kwantar mana da hankali na cewa yin 186 1 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri hakan na nuni da cewa tunanin ta ne yakc kokarin dawowa, kuma cikin yardar Allah za ayi nasara. Ban da addu'a babu abin da muke yi kullum, sannan haka muke haduwa akan Allah Ya bayyana Hamced da batan da yayi. Zaune muke muna hira domin samun labari mai dadi da muke yi gurin likitoci na cewa kada mu daga hankalin mu na rashin tashin Aziza daga bacci na tsawon kwana uku, tabbas suna tunanin nasara ce domin hakan yana nuna cewa kwanyarta na diban hutu ne, kuma da alamu idan Allah Ya farkar da ita ta dawo cikin hankalin ta domin sun taba samun hakan ya faru a cikin wannan asibitin. Murna muka shiga yi don sai muke ji a ranmu kamar ma taji sauki. Kwanan Hameed goma sha uku da bata har yanzu bamu samu labarin komai game da batansa ba, haka dai muka ci gaba da addu'a. Kwance nake kan katifar dake kusa da gadon da Aziza take kwance, lokacin ni kadai 187 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri ce a gurinta nima na dan kishingida bacci ya kwashe ni. Ji nayi ana kiran sunana hade da bubbuga ni, sai nake jin kamar a cikin mafarki. Ina bude idanuna kawai sai naga Aziza zaune kusa dani, da sauri na murtsike idanuna ina kallon ta cikin kaduwa domin ban san dame ta tashi ba, ta dawo cikin hayyacin ta ko har yanzu tana nan yadda take? Rike hannuna tayi ta ce, "Granny ni ce kuwa? Shin mafarki nake yi ko gaske ne abin da ya faru dani? Shin me ya faru dani na ganni a asibiti?" Rudewa nayi, murna- murna kuka-kuka, na rike hannunta na ce. "Aziza kin gane ni, ni ce ko?" Hawaye ne ya ciko idanunta, ta ce, "Granny abin da ya faru dani ba mafarki nayi ba gaske ne ko? (Please) Granny ki fada min don na gasgata abin da nake ji a raina". "Shin Granny da gaske Yaya Hameed shi ne ya yi sanadiyyar zuwa na asibitin nan ko dai mafarkin nake yi?" 188 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammod Waziri Ji rayi gabana ya yi matukar faduwa, hankali na ya tashi, na се. "Aziza me kike cewa dani ne? Fada min me kike son fada ko me kika gani cikin mafarkin ki?" Hawaye ne suka shiga zubowa a idanunta, ta ce. "(Please) Granny na roke ki da ki fara fada min me ya faru dani don Allah, domin na fara gasgata wani abu cikin raina. (Please) da gaske ba mafarki nake yi ba yaya Hameed shi ne ya cuce ni ya bata min rayuwata har na zo nan ko kuma mafarki nayi?" Dafe kirji nayi na shiga salati, hawaye na zubowa cikin idanuna na cе. "Hakika wani abu ya faru da ke Aziza, sai dai cikin mu babu wanda yasan wane ya yi miki wani abu". Kuka ta saka mai tsuma rai, nan da nan tayi sauri ta rungume ni ta shiga kuka tana cewa. 189 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Granny na shiga uku na lalace, yaya Hameed ya cuce ni, shi ne ya hakke min. Wayyo Allah Granny, ya cuce ni". Kara rudewa nayi na kara kankame ta nima ina kuka ina sakin salati, haka ta shiga kuka tana bani labarin duk abin da ya faru da ita. Tun da ta fara bani labari nake zubar da hawaye domin tsabar kaduwa da tausayin abin da ya faru da ita, daga ni har ita kuka muke tayi, domin na rasa abin da zan iya cewa da ita. Haka Abban ku da Ammin ku suka shigo suka iske mu a cikin wannan halin. Gaban su ne ya fadi da suka hangi Aziza kwance kan gwiwata, da sauri suka karaso gurin, ya се. "Umma me ya faru da Ammi na?" Jin muryar mahaifin ta tayi sauri ta mike tana ganinsa da sauri ta zo ta rungume shi tana kuka tana cewa. "Abba Ya Hameed ya cuce niya bata min rayuwa ta". 190 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri Bambarekwai yaji kalaman nata, domin sam bai fahimci abin da yake faruwa da ita ba. Nan da nan ya ji shi wani iri tarc da jin wani faduwar gaba ya zo masa. Sauri ya yi ya rike hannayen ta ya raba ta da jikinsa, ya dube ta sosai ya ce. "Ammi na me kike cewa dani ne?" Kuka ta kara sawa ta sake rungume shi, kallon sa ya mayar gare ni cikin rudani nima kukan ya gani ima yi. A rude ya ce, "Umma wai me ke faruwa ne? Shin Ammi na ta warke ne? Wai me yake faruwa ne? Ni fa na rude naji tana kiran Hameed, me Hameed din ya zo ya yi? Ko an ganshi ne?" "Abba gani, dama ba bata nayi ba". Gaba dayan su suka juyo suka kalli bakin kofar shigowa inda suka jiyo muryar sa. Hameed ne tsaye bakin kofar yana mai kokarin shigowa. "Kada ka sake ka karaso nan gurin Ya Hameed, na tsane ka, ba zan taba yafe maka 191 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri ba, macuci, azzalumi, mara tausayi. Wallahi sai Allah Ya saka min abin da kayi min". Tana fadin haka ta fashe da kuka tayi sauri ta hangi wani kwalbar lemo ta dauka da sauri ta je ta doka masa a goshin sa, nan take jni ya wanke fusakar sa. Kowa na gurin kasa motsi ya yhi, ana tsaye ana kallon ikon Allah. Nan da nan Mustaphra ya kara rudewa domin har yanzu bai fuskanci inda suka dosa ba. Hameed yana tsaye yana mamakin furucin Aziza nan take ya gane cewa tunaninta ya dawo, murmushin farin ciki ya yi mai tare da takaici. "Ammi meye haka kuma? Me yayan naki ya yi miki haka har kika ji masa wannan rauni haka?" Ya fada cikin tsawa. Cikin kuka ta ce, "Abba bai kamata kayi mini tsawa ba don baka gane abin da Ya Hameed ya yi min ba". Tana gama fadin haka sai ta fashe da kuka, Aisha tana kuka. 192 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Abba ka bar Aziza tayi min duk abinda ranta yake so matukar idan tayi hakan zai sa ta huce ta yafe min abin da nayi mata. Abba ba ita ya kamata ka yiwa tsawa ba ni ya kamata ka yiwa tsawa, kamar yadda ta kira ni macuc, azzalumi hakan nake, kuma na yarda na amsa sunan da ta bani, domin babu irin roko da kukan da bata yi ba akan kada na cutar da ita amma nayi burus da ita sai da na hakke mata. Abba ku yafe min, ni ne na cutar da rayuwar Aziza, na zbata mata rayuwar ta, don haka ku yi min duk abin da za ku dauk fansa akan abin da nayi muku". Zaman

Chapter 8 of 9