Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 9
ya ce, "Granny me ta ce? Fada min naji ko ta fadi wane ya yi mata hakan". 94 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri. "Kwantar da hankalin ka Abdulhameed, bata iya fadin kowa ne sai dai ta kira suna na da Abban ku akan wai mu taimake ta". "Daga haka bata kara ccwa komai ba, ko ta kara ce muku wani abu?" "Gaskiya babu abinda naji ance ta ce tunda ni bana gurin". "Toh me likitan ya ce game da dawowar tunanin ta? Shin ya fada zai dawo ko ya tafi gaba daya?" Alh. Jafar ya fada yana kallo na. Maryam ta ce, "Yaya bai dai ce komai ba akan haka, mu dai fatan mu dai Allah Yasa ta warke ras, ba ma fatan ta warke ta kuma tashi da mantuwar tunanin, don yin haka ba karamin nakasa ta samu ba, domin da ita da nakashasshiya duk daya ne ko ma yafi". Ya ja ajiyar zuciya, ya ce, "Gaskiya ne". Na yi duba ga goshin Hameed da yake daure da bandeji, na се. "Abdulhameed mene ya faru da kai a goshin ka haka?" Dora hannun sa ya yi akan goshin ya shiga inda-inda, ya mai da kallon sa ga mahaifin sa, zuwa can ya yi karfin hali ya cе. 95 e Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri warke ko da tunaninta bai dawo ba ni zan zauna da ita, ban damu da su wane suka yi mata haka ba, zan so na rayu da 'yar uwata a haka, ni dai ina sonta, zan kuma dauki dawainiyarta a haka". Duk jikin mu ya yi sanyi ni da Maryam, take naji hawaye sun zo min, na ce. "Abdulhameed kai yaro ne, a matsayin shekarun ka ha karatun ka ai ya yi wuri ace kana da aure, kuma ga ta da lalura, shin ya zaka yi da karatun ka?" "Granny idan za a yarda na auri Aziza a yanzu a cikin wannan halin zan iya hakura da komai har karatun na tsaya na lura da rayuwar ta saboda nasan na girma zan kuma iya kula da ita don haka yanzu na fadawa Daddy haka ne shi yasa muka zo nan tare domin ke kadai ce za ki yarda da haka a aura min ita". "Umma wannan haka yake, gaskiya ya fada, ki daurc ki yarda da hakan". "Jafar babu damuwa tun da ZURI'A DAYA muke, babu wani abu da zai gagara a ciki, amma ku dan yi hakuri ka ci gaba da fahimtar Abdulhameed, insha Allahu shi ne zai 97 Zuri'a Daya-! Sa'adatu Muhammad Waziri auri Aziza bayan ta ji sauki, amma dai mu jira mu ga yadda hukuncin da Ubangiji zai zartar". "Shi kenan, Allah Ya bata lafiya, bari mu karasa gurin Mustapha din". Haka suka mikc suka shiga cikin gurin da aka kwantar da Aziza, nan suka hangeta kwance iyayenta sun zagayc ta sai kuka suke yi, gata nan gaban su kwance babu awani alamun tana motsi a tare da ita. Suka yi sallama suka shiga, da yake lokacin ana barin na jiki su shiga don haka suka shiga tare gaba dayan su. Tsananin tausayi da dana sani su ne bayyane a fuskar Hameed, bayan sun gaisa ne iyaye duk suka fita suka bar Hameed a gurin, dukawa ya yi ya riko hanunta, nan take hawaye suka wanke masa idanu, cikin kuka ya fara cewa. "Aziza na ki yafe min abin da nayi miki, ban san ni azzalumi ne ba sai bayan na hakke miki, Aziza na ban taba tunanin zan jefa rayuwar ki cikin wannan halin ba sharrin zuciya da shaidan su ne suka kai ni ga haka. Aziza me yasa na kasa tausaya miki ban cutar da ke ba bayan irin roko da hakurin da ki 98 Zuri'a Daya-1. Sa'adatu Muhammad Waziri ka ba ni, amma tsabar rashin tausayina na manta da cewa ke Aziza na cc? Hakika na san ba zaki taba yafe min ba har tsawon farshen rayuwar mu, na tsani kaina, na tsani rayuwata gaba daya tun bayan faruwar al'amarin nan, Aziza ina tsoro kada ace ni ne da hannuna zan yi sanadin mutuwar ki. Wayyo Allah! Ya Allah Ka yafe min, Ka bawa Aziza na lafiya ta warke, ta yanke min duk hukuncin da take so, domin na zama azzalumi akan ta. (Why) Daddy? Me yasa baka hukunta ni ba da ku ka gane kai da Momi abin da na aikatawa 'yar uwata, kanwata? Me yasa ba kwa so duniya ta gane cewa ni ne na cutar da Aziza na? Daddy me yasa ka nuna son kai bayan kasan ban boye maka cewa ni ne na cutar da Aziza ba? Ya Allah Ka kawo hanyar da asirina zai tonu a gane ni ne, domin naji a yanzu gaba daya na tsani rayuwata gaba daya". Nan ya shiga sharfar hawayen sa, ya kara damke hannun Aziza ya ce. "Aziza na ina so Allah Ya baki lafiya ki tona min asiri, kuma ba zan karyata ki ba, ba zan 99 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri musa miki ba, domin nasan na cucc ki, na cuci kaina, na kuma cuci ZURI'Ar mu. Na zamo mugu, mara imani. Aziza bana so ki yafc min har sai an hukunta ni dai dai da abin da na aikata miki, ko da kuwa kashe ni shi ne mafita gare ni, idan haka ya faru to sai ki yafe min. Yau na zo gare ki don ki yafe min, ba zan taba barin asibitin nan ba har sai Allah Ya baki lafiya kin sa an hukunta ni da hannun ki sannan zan samu nutsuwa a cikin rai na, amma nasan ni da farin ciki har karshen rayuwata, domin tun ranar da abin nan ya faru na rasa farin ciki na har abada. Ya Allah! Ya Allah!! Ya Allah Ka bawa Aziza na laifya, ta dawo kamar yadda take rayuwa". "Ameen Abdul, bar kukan haka kayi hakuri da sanin Allah, zata samu sauki". Zumbur ya yi ya yi sauri ya dago kansa da ya kifa a jikin gadon yana kuka, ni ya gani da sauri ya cе, "Granny yaushe ki ka shigo ban ji zuwan ki ba?" 100 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri Na ce, "Shigowa ta kcnan naji kana addu'ar Allah Ya bawa Azizan ka lafiya". Da sauri ya zo ya rike kafafuna yana kuka yana cewa. "Granny ya zan yi da rayuwata? Ya zan yi da raina? Granny ba zan iya jure ganin Aziza na cikin wannan halin bame yasa haka ya faru da rayuwar Aziza? Me yasa na...". "Kai Hameed haukan me kake yi haka zaka tsaya kana kuka? Maimakon kayi mata addu'a shi ne zaka sa ta gaba kana kuka kamar kukan ka ne zai bata lafiya?" Shiru ya yi bai dago kansa ba domin ya gano muryar mahaifinsa ne ta katse shi da shirin tonawa kansa asiri da yayi niyya. Nan ya karaso gurinsa ya kama shi ya dago shi, ya ce. "Haba Hameed, ka daina irinowannan surutan kamar karamin yaro, ka ci gaba da yi mata addu'a, hakan yasa bana son barin ka zuwa nan gurin domin idan ka ganta kara ta da hankalin ka kake yi, don haka ka zo mu koma gida kai ma ka huta, kada ciwon kai ya kama ka". 101 Zuri'a Daya-I _Sa'adatu Muhammad Waziri "Daddy babu inda zan iya komawa tunda Allah Yasa ka barni yau na zo to na zo kenan har sai Aziza na taji sauki ta yanke min hukunci da hannunta kan abin da nayi mata". Gaba daya hankalin mu ya tashi jin irin furucin da Hameed yayi, da sauri muka hada baki da Mustapha muka ce. "Hamced, me ka yiwa Azizan?" Juyowa ya yi gare ni ya fara kuka, ya ce. "Granny na yiwa, Aziza laifin da ba zata yafe min ba, domin na bari wani ya zo ya cutar da ita banzo na taimake ta ba, don haka nasan ba zata taba yafe min ba. Nasan a lokacin da abin zai faru ta kira suna na don na cece ta amma ban zo ba, hakan yasa na ce nayi mata laifin da ba zata taba yafe min ba". Gaba dayan mu sai a lokacin ne muka yi ajiyar zuciya, domin mun gano nufin sa. Mustapha ya karaso gurin sa ya riko hannayen sa biyu idanunsa sun ciko da hawaye, ya ce. "Hameed ba kai kadai ne Ammi na ba zata yafewa ba har dani, tunda ban zo nima na cece ta ba. 102 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri Hameed ka saki ranka ka daina kuka, kaje kana addu'a akan Allah Ya bawa Azizan ka sauki, Ya kuma tona asirin wanda suka yi mata haka. Ka wuce ku je gida Daddyn ka ya yi min bayanin komai game da burin ka don haka ban yi maka alkawari ba, mu jira har sai ta ji sauki na bata dukkan farin ciki a rayuwarta, na kawar mata da dukkan wani kunci da damuwar da ta shiga. Sai naga farin ciki a fuskar ta sannan zan yarda nayi mata maganar auren ka, amma ban da yanzu. Hameed na yarda da kai, na yarda da kaunar da kake yiwa 'yar uwarka, kuma ina da yakinin zaka iya bata dukkan farin cikin da nake hangowa zata samu a rayuwar ta, domin ba ka gujeta ba bayan wannan iftila'in da ya faru gare ta. Don haka na gode, na gode, ka wuce kuje gida domin ni kaina ba zan jure ganinka cikin tashin hankali ba". "Abba kayi hakuri, nasan ban kyautawa Aziza na ba da na bari haka ya faru da ita". 103 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Na ce Hameed kada ka karya mana zuciya, ka wuce ka tafi abin ka, inshaa Allah zata ji sauki". Daga nan bai sake cewa komai ba ya sa kai ya fice yana share hawayen da suke zubo masa, jikin Alh. Jafar a sanyayes ya biyo bayan sa shima suka fice. Yadda al'amarin ya faru tun baya, a lokacin da Hameed ya gama biyan bukatar sa da Aziza bayan irin rashin tausayin da ya nuna mata, da rashin imani, tun tana neman dauki har ta yi shiru domin karfinta da kuzarin ta duk sun kare, tuni ta suma ta fita cikin hayyacin ta, amma duk da haka bai sa ya kai ga tausaya mata ba. Bayan ya dawo cikin hayyacin sa ne ya shiga rudani da fargaba domin ganin irin jini da yake fita a jikin ta, nan ya rude ya shiga jijjiga ta amma ina! Babu wani sauran numfashi a jikinta, nan ya dimauce ya ci gaba da jijjigata tare da kiran sunanta, amma ina! babu wani motsi, hakan ya saka ma ransa cewa ta mutu. Da gudu ya mike ya zo ya fita daga gidan cikin rudani, amma sai da ya yi taka tsantsan don 104 1 4 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri haka zai jefa kansa cikin wannan tashin hankalin da bai yarda zuciyar sa ta ingiza shi ya gwada mata wannan rashin imanin ba. Hannu yasa akan sa yana cewa. "Wayyo Allah na! Wayyo Aziza na, me yasa na yardar ma zuciya ta na cuce ki, na manta da ke da kuma kukan da naga kina yi kina rokona? Idan kika mutu ban san ya zan yi da rayuwa na ba, wallahi nayi nadama, naji na tsani kaina, na tsani rayuwar gaba daya, Da na sani shi ne abinda nayi ne a yanzu". Tabbs hawaye rahama ne, sai yanzu ne Hameed yaji dan wani sanyi cikin ransa dalilin zubar hawayen nasa, haka ya zauna yana ta yin kukan sa tare da aikin da na sani da ya zamo keya. Haka ya wanzu cikin wannan ranar ya kasa assasa komai, don yana zaune cikin dakin yana ta aikin zubar da hawaye. Yana jin lokacin da iyayen sa suka dawo cikin tashin hankali suna tattauna wulakanci da keta haddin da aka yi ma Aziza, ga rashin tausayin da aka nuna mata. Hankalin sa ya kara tashi, domin bai ji sunce tana raye ko a mace ba. Haka suka zo suna 106 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri buga dakin na sa, tunanin su ko yana ciki ya barci, domin sun san halinsa, haka suka shiga bugawa amma shiru babu shi babu alamarsa. Har cikin dare suka zo suna buga dakin yana jinsu amma ya ki motsawa ko nan da can, yana guri guda ya takure da an buga sai ya takure ya rungume jiknsa, ban da aikin zubar hawaye babu abin da yake yi na tarin nadamar abin da ya aikata. Su kuma hankalin su ya tashi, suka shiga tunanin ina ya nufa a wannan rana? Domin bai taba yin haka ba a rayuwar sa, haka suka hana kansu barci suka zo bakin dakinsa suka tsaya suna jiran ganin ta yadda zai bullo. Suna cikin haka sai suka ga an kashe wutar dakin, da sauri suka zo suka shiga kiransa da bubbuga kofar akan ya zo ya bude, amma ina! Ya yi shiru ya ki motsawa daga inda yakc, nan mahaifinsa yaje ya zaga ta (window) ya hango shi can matsin gadon sa ya takure yana kuka kamar mai jin sanyi. Nan ya shiga kiransa amma takar ba da shi yake ba, haka ya hakura ya dawo bakin kofar ya shiga buga masa kofar, amma yayi fumfurus da shi. 107 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Ransa ya yi matukar 6aci, ya shiga yi masa fada tare da zaginsa amma ina! Haka nan ya hakura mahaifiyar sa itama ta soma nata amma babu yadda suka yi, dole suka rabu da shi. Sun yi-sun yi akan ya fada musu me ya faru da shi yasa ya kulle dakinsa? Amma ya ki, can da yaji sun daina motsi a gurin sai yaje ya bude kofar ya nufo falo, nan ya iske su suna zaune sun yi jigum. Sun ganshi amma ko mikewa ba suyi ba, suka zuba masa ido, haka ya karaso falon suka ga goshinsa da jini jaga-jaga, da sauri Alh. Jafar ya mike zai nufe shi cikin tashin hankali. "Hameed me ya faru da kai haka?" Ya fada cikin rudewa. Cikin kunar rai Haj. Asiya ta ce, "Daddy kada ka kuskura ka karasa gurin yaron nan, domin gashi a bayyanc, zarginmu ya zama gaske". Cikin tsawa da 6acin rai ya juyo ya kalleta, ya се. "Asiya kin san irin mugun furucin da kike yiwa dan da kika haifa a cikin kuwa? Don kawai 108 Zuri'a Daya-1 Sc'adatu Muhammad Waziri zuciyar ki tana zargin wani abu sai kawai ki zartar da hukunci kai tsaye?" "Daddy idan har kuna zargina da wani abu to haka ne, ni ne na aikata, ni ne na jcfa Aziza cikin halin da take ciki yanzu". Tasss! Ya dauke shi da wani wawan mari, sai da ya ga (stars) suna masa yawo a cikin idanunsa, ya yi sauri ya dafe kuncin sa, ya yi taga-taga zai fadi. "Kana da hankałi kuwa? Kasan abin da kake fada min da bakin ka? Yaushe ka fara hauka nc?" "Daddy wallahi sharrin zuciya da shaidan su nc suka debe ni na aikatawa Aziza haka, Daddy ku yafc min, wallahi nayi nadama fiye da tunanin ku". "Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un! Hamced zargina ya zama dai-dai kenan? Ya Allah Ka dauki riana da ganin wannan rana mai tarin takaici, yanzu dama kaine ka aikata mata haka? Amma dai ka cuce mu, ka janyo mana gori da surutu cikin zuri'a, ka wulakanta mu, ka wulakanta kanka. Ni Asiya yau naga ta kaina". 109 Zuri'a Daya-I sa'adatu Muhammad Waziri Cikin kuka ya cc, "Mommy kiyi hakuri, wallahi nayi nadamar abinda na aikata a rayuwata". Nan ya taho zai rikcta ta kauce itama cikin kuka, ta cс. "Wallahi idan ka taba ni zan tsine maka, domin da ganinka gabana gwara gawar ka, domin ka janyo mana bakin jini da gaba a cikin lardinmu". Cikin tsawa Alh. Jafar ya ce, "Asiya kina hauka ne? Kin san wane furuci kike yiwa dana? Kada ki kuskura ki furta masa tsinuwa domin kina tsine masa nima zan datse igiyar auren mu ni da ke ta har abada". "Jafar me kake son fada min ne?" Ta ambaci sunan sa kai tsayc cikin bacin rai, sunan da ta dade bata ambata masa ba tun lokacin da Allah Ya basu yara. Cikin kunar rai ya ce, "(Okay) baki ji abin da na fada miki ba kenan sai na maimaita?" Nan take ya sake maimaita mata abinda ya fada da farko. Cikin zubar hawayc ta ce, "Idan har ni ce na tsuguna na haifi Hameed to ba zan taba yafe 110 Zuri'a Daya-I Se'adatu Muhammad Waziri masa abinda ya yiwa Aziza ba har sai yaje ya bayyanawa duniya cewa shi ne ya yi mata wannan rashin tausayin, amma idan ba haka ba to na yafewa duniya shi har da kaima kanka". Da sauri Hameed ya zo ya rungume ta yana kuka yana ccwa. "(Pleasc) Momce ka da kiyi fushi dani, idan har za ki yafe min to zan je na fadawa kowa cewa ni ne na cutar da Aziza ba kowa ba". "Karya ku ke yi ke da shi, babu wanda ya isa ya tona min asiri cikin zuri'a, na yarda cewa Hamecd shi ne ya aikata ma Aziza wannan danyen aikin, naji ni da kaina zan hukunta shi ba tare da kowa ya sani ba. Amma ya je ya tunkari Zuri'ar mu da wannan labarin ai tamkar kun tabа min wuka a ciki ne. A barni da kaina zan hukunta abuna". "Yin hakan ba adalci bane Jafar, kuma ba addini bane, tsabar son kanka da zuciyar ka shi ne zai sa ka fadi haka. Bari na fada maka, idan kana tunanin wannan shi nc soyayya ga abin da ka haifa to kayi kuskure, domin ka jefa danka cikin halaka, gwara kawai ka barshi a hukunta shi kamar yadda shari'a ta tanada, amma yin 111 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri hakan babu abin da zai haifar maka sai larin bakin ciki da nadama". "Asiya ban taba tunanin ba kya son danki ba sai yau, ya aikata laifi bai 6oyc mana ba shi nc mu kuma za mu tonawa kanmu asiri duniya da Zuri'a su zage mu, to ni ba zan yi haka ba, na yarda yayi laifi a barni na hukunta shi da kaina". "Sam wannan ba addini ba ne Jafar, sannan kuma ba so bane. Me za ayi da yaron da zai gwada wannan rashin imanin? Zan iya yafe auren ka matukar ba ka bari an hukunta Hameed ba, don na rasa wane irin so kake ma 'ya'yan da har idon ka ya rufe baka son ganin laifin su ko da kuwa wanc irin laifi suka yi? Duk cikin Zuri'ar nan yaran gidan nan sun fita daban wurin tarbiyyar su, wanda kuwa hakan duk ya samo asali ne daga irin son da kake musu. Dalilin da yasa kenan ta kai ga Hameed ya aikata wannan rashin imanin". Cikin tsawa ya cc, "Asiya ki rufc min baki na ce, Hameed dana ne, ina son shi fiye da dukkan yaran da na haifa, don haka banga abin da zai yi na juya masa baya ba a fadin duniyar nan, matukar nima zan iya hukunta shi da hannu 112 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri na. Ki zuba idanu ki gani, ni da kaina zan yi masa abin da baki yi tunani ba". Cikin kuka Hamced ya karaso ya rike Kafar mahaifinsa yana ccwa. "Daddy ka barni a hukunta ni kamar yadda addini ya tanadar, domin yin hakan shi ne zai sa na samu nutsuwa cikin zuciyata da kuma samun gafarar Allah. Daddy nayi nadamar abinda na yiwa Aziza na, ban taba tunanin dai-dai da rana daya zan cutar da ita ba, sai gashi zuciya ta sa ni na yi aikin da na sani. (Please) Daddy ka barni ayi min abin da Momce ta ce, domin bana son tayi fushi da ni, don ina son ganinta cikin farin ciki". "Baka isa ba Hamced! Ba za ku kunyata ni cikin Zuri'a ta ba da kuma idon duniya, saboda zan zamo ba komai ba a cikin su, girmana da mutuncina da daraja ta za su zube a wajen su, ni kuwa da na rasa mutunci da daraja ta cikin ZURI'A ta da idon duniya gwara na rasa shi a idon matar da nakc aurc da kai dana na kaina. Na yarda ban goyi bayan abin da ka aikata ba, naji ciwo sosai har cikin zuciyata. Tunda 113 Zuri'a Daya-! Sa'adatu Muhammad Waziri babu wanda yasan kainc ka aikata to ni dai da hannuna ko baki na ba zan iya daukar wuka na dabawa kaina ba, ma'ana na fadawa duniya ccwa kai nc, don haka tun wuri mu rufe zancen a nan. Matukar kaje ka tonawa kanka asiri ni ma zan tsinc maka, zan kuma yanke duk wani alaka a tsakanin mu ni da kai na har abada, don haka ka tsaya kayi tunani. Ke kuma na fasa sakin, kije ki fada, ina da hanyoyi da dama da zan bi don ganin na hukunta ki da su, kema kiyi tunani tona asirin ko rufa shi, cikin biyu dole ki yi daya. Kai kuma wuce muje ka ga likita don ya duba maka wannan goshin naka". Bai tsaya ya jira amsar su ba ya ja hannun sa suka fice, kai tsaye mota suka je suka shiga sai asibiti. Tun da suka tafi Hameed yake kuka bai sarara ba, haka mahaifin sa ya shiga tausar sa da ba shi baki akan ya diana daga hankalin sa, babuabin da faru da shi sai alheri. Bayan fitar su Haj. Asiya ta zube a kasa tana kuka mai isar ta, tana tunanin irin rashin 114 Zuri'a Dayo-1 Sa'adatu Muhammad Waziri adalcin mai gidanta, tsabar rashin imani da tsoron Allah ga irin abin da yake furta mata. Tabbas tasan irin mugun halin sa da kafiya da rashin kwantar da kai a cikin abin da yasa gaba, bashi da mai sa shi haka ba shi da mai hana shi. Tabbas tasan rabuwar kan ZURI'Ar su ya zo, domin babu wani da za a viwa haka cikin Zuri'ar ya dauka, domin hakurin sa da son zumuncin sa, donmn wannan keta haddin ya yi yawa. Sannan shin Jafar baya tunanin ccwa wannan abin da yake wa yaransa shi ne gata ko so? Sai kana daurewa yaranka gindi kana fifita son su akan sauran yaran duniya? Tabbas ka yi kuskure, dole idan baka daina ba wata rana da kanka zaka dora hannu kayi kuka. Shin ma wai ina tunaninsa da kwakwalwar sa suka nufa? Idan ni ko Hameed wani bai fada ba ita idan Allah Ya tashi kafadar ta zai rufe mata bakin ta ne akan kada ta fada? To wannan nc bai isa ba". 115 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Nan ta daga hannu sama tana addu'a akan Allah Ya bata lafiya don gaskiya tayi halinta. Da wannan tunani ko nace addu'ar tayi dakinta, tajc ta ja ta rufc zuciyar ta da kuncin abin da ya faru. Sai da safc ta ganshi anyi masa (drcss) a gurin da yaji ciwon, suna haduwa ta daure fuska ya yi naciz akan ta saurare shi ta ki, dole ya koma dakinsa ya kulle yana kuka. Haka yaji gaba daya duniyar tayi masa ba dadi, ya kara jin tsanar kansa da rayuwar ma gaba daya. laka dai ya zamo abin tsangwama a gurin mahaifiyar sa, dole yasa ya koma rayuwar sa shi kadai a cikin daki. Tun sanda mahaifin sa ya zo masa da labarin abin da likita ya fada musu na cewa ba lallai bane ta iya tuna abin da ya faru da ita ba, domin ta samu ta yi wata irin razana mai tsanani wanda hakan ya janyo mata fadawa cikin mawuyacin hali. Da farko ya yi murna har yake fatan Allah Yasa kada ta dawo cikin hayyacin ta domin kada ta tuna abin da ya faru a baya da ita, ta hakan ne 116 3 ZvriaDayarlarumuile adotu Muhammad Waziri zai iye bin duk hanyar da zai janyo ya wanke laifin d aya yi mata, amma fa a tunaninsa. nibsb Amma tun sanda ya je ya ganta ya rasa ma kansa nutsuwahaka kullum zai kefe kansa a daki ya shiga yin kuka idan bai samu nutsuwa ba sai ya dauki Alkur'ani yana karantawa sai yajinya nemi damuwar sa ya rasa.sgide sy unide iv ay ise Sam Momin sa ta iki sauraron sa, küllum haka zai sa ta gaba yana kuka haka ita ma za tai tayi, ita babban takaicin ta yadda Alh. Jafar ya yi mata katanga da zuwa asibiti domin yana ganin kamar idan ta je zata iya cewa Hameed nelya aikata mata wannan al'amarinsı asnnaw A asask nimob sbig owsb sue nilslasd nidest Bb Hameed nedavakansa byamtakura ma mahaifin nasa akan ala dole sai ya je asibitin ya sake ganin halin da Aziza takedciki, domin shi ma ya hana shi ganin yadda yake ce masa shi a bar shi ya bayyana cewa shi ne ya aikata mata haka ko ya samu ya samu nutsuwa, amma ya ce masa bai yarda ba. inuw ab sysb snBWK CL SY Ganin kafiyar da iya nuna na son ganinta ya salya ce ya amince suje, amma ba zai barshi sbud sy sb σε πολοτ αί anay nileb enilsd s syse 117 Zuri'a Daya-I sa'adatu Muhammad Wazji shi kadai ba don gudun kada ya kwanto masa kura. Har cikin ran Alh. Jafar baya jin dadin abin da ya faru da Aziza, ya so kwarai da farko ya dauki mataki mai arfi a ranar da abin ya faru, amma daga baya da ya gane abin a gindinsa yake sai ya yi shiru ya shiga taka tsantsan da al'amarin don kada abu ya fito aji kunya. Dole ya sa yake faranta ran Haj. Asiya don kada tayi fushi ta tona asirin dansu, amma duk abin da zai yi mata a banza domin kawai kallon sa take yi. A wannan ranar ce suka je da Hameed din da tashin hankalin suka dawo gida, domin kadan ya rage Hameed ya tonawa kansa asiri. A cikin mota ya shiga yi masa masifa da inda ya shiga ba ta nan yake fita ba, shi kuwa Hameed shiru yayi yana dubansa, bai ce da shi komai ba. Da suka dawo gida haka ya shiga dakinsa ya rufe kwana daya da wuni ya yi bai bude ba, hankalin Alh. Jafar ya yi matukar tashi. Washegari ko wurin aiki bai je ba, ya tsaya a bakins dakin yana ta rokon są da ya bude 118 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri don da farko zaginsa yake ta yi ganin ya ki dole ya dawo yana rarrashin sa da bashi baki akan zai masa duk abinda yake so idan ya budc kofar. Haka yayi ya gaji ya koma ya dawo, haka ya yi tsawon ranar shi ba abinda yaje ya fadawa wani cikin 'yan uwansa ba abin da yake gudu ya zo ya faru, domin dole ne sai sun so jin dalilin sa na yin hakan, shi kuma ba zai iya fadawa kowa ba. Haj. Asiya ana kallon su babu abin da ta ce da su sai tsananin mamakin irin kaunar da yake nunawa Hameed kamar ransa, wanda hakan ne ya janyo ya fada cikin wannan halakar. Don tabbas ta san Alh. Jafar yana matukar son Hameed fiye da komai a cikin rayuwar sa, ta san zai iya aikata komai akan sa, don ya ga ya bashi farin ciki. Sai dai kuma a yanzu yanda ake da wuya ya bawa Hameed farin cikin da yake so, domin farin cikin sa a yanzu shi ne ya bar shi ya fada cewa shi ne ya yiwa Aziza wannan aika-aikar. Amma ina! ba zai taba barin haka ya fsaru ba. Sai misalin sallar isha taje

Chapter 5 of 9