ta yiwa
Hameed magan akan ya bude dakin, da yaji
119
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
muryar ta ne da sauri ya bude don ya ji dadi, don
ko ba komai zai samu wata nutsuwar domin
rashin wata nutsuwar har da rashin kulawar da
yake samu gurinta, hakan ma ya sake sa shi cikin
wani azabar.
Lokacin da ya bude ta ganshi sai da itama
hankalin ta ya tashi, abinka da tsakanin da da
mahaifi. Cani tayi ya yi mugun fadawa cikin
kwana daya da wuni daya babu ci babu sha, nan
take taji kwalla ta ciko idanunta, tayi sauri ta kau
da kai don kad aya ga ta tausaya masa.
Da sauri ta juya zaya bar gurin, ya yi
saurin riko hannunta, duk da ba shi da kwarin
jiki sosai amma ya yi kokari ya yi mata wani
rikon tsauri.
Cikin kuka ya ce, "Mom me yasa ba kya
tausaya min? Ki taimaka min na fita cikin
kuncin da nake ciki duk da kuwa nasan ba zan
taba samun wani farin ciki da sukun ba tun da na
riga na yiwa rayuwar Aziza na illa, na san haka
zan kare rayuwa ta.
Mom da kina bani kulawa duk da na san
ban cancanta a bani ita ba amma Momi idan kika
duba nayi nadama, kuma a shirye nake da а
120
Zuri'a Daya-I sa'adatu Muhammad Waziri
zartar min da kowanc irin hukunci ko da na kisa
ne domin bai kamata a barni haka ba.
Momcc sai yanzu na gane cewa ke kadai
ki ke kaunata ba Daddy ba, domin ke cc ki ke so
a hukunta ni shi baya so.
Ganin halin da Aziza takc ciki a (hospital)
yasa na kara tsanar kaina da fitar da ran idan ta
mutu a haka ba zan taba samun rahamar Allah
ba, domin ban ce ta yafe min ba. Don haka na
yanke shawarar ko da Daddy zai kashe ni sai na
tona asirin kaina don na samu nutsuwa.
Don haka Momee ki yafe min, ki kuma ci
gaba da nemar min gafara gurin allah, wallahi na
tuba, kuma nayi nadama, ba zan sake ba".
Hawaye ne sosai suka gangaro a fuskarta,
ta sa hannu ta goge da dayan hannun, ta juyo ta
kalli Hamced ta kara tausaya masa, ta cc.
"Hamecd, mc yas aka yiwa 'yar uwarka
haka?"
Shima cikin kuka ya ce, "Momcc wallahi
sharrin zuciya ne da shaidan, amma don Allah ki
yafc min ko don wannan hawayen da na sa ki,
(pleasc) mom na san ina cikin fushin Ubangiji".
121
Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri
"Hameed, kana da wannan tunanin da
kuma tsoron Ubangijin ka amma har kaje ka yi
wannan mugun aikin? Hameed ba zan yi maka
baki ba ko wani mugun kalami, jin furucin ka
yau yasa na yafe maka amma dai dole ka
bayyanawa iyayen ka ko me zai faru ya faru.
Idan ka ci gaba da Istigfari da kaskantar
da kai Allah Zai iya yafe maka naka laifin kai da
shi, domin Yana son ganin bawan sa mai nuna
nadama da neman tuba na gaskiya. Amma ba Zai
iya yafe maka hakkin Aziza ba, wannan sai kai
da ita".
Ji ya yi wani sanyi da farin ciki sun tsirga
masa, ya yi sauri ya rungume mahaifiyar sa yana
kuka yana cewa ya gide, kuma ta saka ido zai yi
mata abin da rake so.
A wannan halin Alh. Jafar ya shigo cikin
gidan, yana ganin Hameed wani farin ciki mara
misaltuwa ya ratsa masa zuciya, ya ji kamar an
masa albishir da gidan aljannah. Da sauri ya zo
ya rungume shi, ya ce.
"Haba, me yasa ka cika taurin kai ne? Na
ce ka cire damuwa insha Allah komai zai zo
cikin sauki, mu ci gaba da yin addu'a Allah Ya
122
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
bawa Aziza sauki. Sai dai ba zamu so ta tuno bin
da ya faru a baya ba, don gudun tonuwar asitin
mu.
Hamced, kada kaji ina fadar haka kana
ganin kamar ina farin ciki da abin da ya faru da
Azizan ka, ko kadan wallahi duk loakcin da na
zauna na tuno da halin da take ciki sai na ji ba
dadi, amma idan na tuno kai ne ka aikata hakan
sai gwiwoyi na suyi sanyi, domin babu abin da
zan iya yi a ka".
Hada idanu suka yi da mahaifiyar sa, ya
ga bacin rai sosai a tare da ita, har ya yi niyyar
yin magana ta sa hannu ta dakatar da shi ta cе.
"Ban yarda da cewa kana tausayin 'yar dan
uwnaka baidan har da gaske tausayin kake yi me
yasa ba zaka tona asirin wanda ya yi laifin ba?
Don kawai son zuciya irin taka da rashin son
zumuncin Allah, kasan abin yana karkashin ka
amma ka ki ka bayyana.
Ni dai zan debar muku lokaci daga kai har
shi, matukar ba ku bayyana ba to ni zan bayyana
ko kuma shi Allah da Kansa Ya bata lafiya ta
fada da kanta tunda komai a Hannun sa yakc Zai
iya yin komai cikin kankanin lokaci".
123
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
Cikin zafin rai ya ce, "Asiya na fuakanta
yanzu duk abin da ya zo bakin ki kina rufc ido ki
fada min ko? To kijc ki fadawa duk wanda za ki
fadawa.
Ciwo na Allah ne, idan Allah Bai ga
damar dawo mata da tunaninta ba babu mai
iyawa, domin da asitin Hameed ya tonu na
gwammace Aziza taji sauki ba tare da tunaninta
ya dawo ba, domin idan Allah Ya bata lafiya a
shirye nake ni da Hameed mu shiga cikin
rayuwar ta mu kawo mata dukkan farin ciki а
rayuwar ta, domin shi ne zai aure ta don ya
wanke dukkan laifin da ya yi mata".
Cikin mamaki ta ce, "Jafar kai ne da kanka
kake irin wannan maganar kamar ta yara don
kawai son danka ya rufe maka idanu? To lallai
ka ke yi da gaske, domin wata rana kana tare da
daukar jin kunya".
Tana gama fadin haka ta juya ta bar su a
gurin.
Bayan ya bita da kallo ta wuce, sannan ya
dawo da hankalin sa kan Hamced, ya dube shi
sosai ya ga yadda ya koma cikin kwana daya da
wuni daya, domin dazun bai gama lura da
124
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
yanayin sa ba, ganinsa ya bude yasa murna ta
mantar da shi.
"Hameed, kaga kuwa yadda ka koma cikin
kwana daya kawai? Haba my boy, me yasa ka
cika kafiya da taurin kai? Me yasa ba ka tausaya
min ne? Kaga halin da nake ciki tunda abin nan
ya faru har yanzu nima bana cikin walwala
domin na san kaima ba ka ciki.
Hamced ka saki ranka don Allah ka dawo
cikin walwalar ka kamar yadda kake can da".
Murmushi Hameed ya yi na takaici wanda
daga ka gani ka san ba cikin dadi aka yi shi ba,
anyi ne kawai, ya ce.
"Daddy walwala ta fa ka ce? Daddy tuni
na manta wannan cikin rayuwa ta, Daddy na san
tunda na taso kake bani farin ciki dai-dai da rana
daya ba ka taba bari na rasa wani farin ciki ba
indai daga garc ka ne, to (why) yanzu ka hana ni
samun sa a yanzu bayan yanzu ne nake bukatar
sa?
Daddy tsawon kwana ki kana hana ni duk abin
da nake so, ina ta bin umarnin ka don kada na
6ata maka wanda kai da kanka ka hana ni zuwa
asibiti gurin Aziza duk da kuwa zan iya zuwa a
125
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
sacc baka sani ba, amma duk nayi don kai ma na
baka irin farin cikin da ka jima kana bani".
"Hameed ban taba hana ka wani farin ciki
ba har yanzu, ka fada min wanne farin ciki na
hana ka samu a yanzu?"
Ajiyar zuciya Hameed ya yiya ce.
"Daddy farin ciki daya nake so na ga na
samu, idan kayi min haka to Daddy zan san cewa
kai mai son farin ciki na ne.
Ba komai nake so ba illa ka barni naje a
hukunta ni, ma'ana zan jc kotun Musulunci a yi
bulala domin a fitar da hakkin Allah a kaina,
daga nan sai na je gurin su Abba na fada musu
cewa ni ne na aikatawa Aziza wannan danyen
aikin".
Cikin huci da masifa ya сe, "Hameed baka
da hankali ne? Kana son tube min rigar mutunci
na a cikin 'yan uwana bayan duk irin zafin da
nakc yi akan wannan faruwar al'amarin daga
baya su ji cewa daga gindina abin yake me kake
tunanin za su dauke ni? To kuwa indai wannan
shi ne farin cikin naka to sai dai ka ce tunda nakс
ban taba baka shi ba.
126
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
Abu daya zan yardar maka, shi nc kajc
duk inda za a fitar maka da hakkin Allah, ma'ana
ayi maka bulala. Na yarda da wannan don kada
ka yi tunanin bana tsoron gamuwa da Allah,
amma ni dai ba zan yarda 'yan uwana su san
cewa kai ne ka aikata wannan rashin imanin ba".
"Shi kenan Daddy, zan yi abin da ka cc
zan je a yi min bulalar".
Runtse idanu Alh. Jafar ya yi, ya cc,
"Hamced ban son kaje a taba lafiyar ka, kaje
kayi ta Istigfari Allah Zai yafc maka".
"Daddy nutsuwa nake son na samu ta
fasrko, matukar aka yi min bulalar nan zan fiye
zaton samun rahama tunda Allah ne Ya fada da
Kansa. Na sani idan na dukufa da ilstigfari Allah
Ya dubi zuciya ta zai iya yafe min, amma tunda
ga yadda Ya ce mu bi dole ne mu bi hakan.
Daddy a yadda nake ji matukar aka ce
kashe ni za ayi idan na yi haka zan kubuta gurin
Allah har da cewa Aziza ta yafe min, to zan
yarda a kashe ni".
"Hameed ka yi min shiru, bana son jin
zancen mutuwa! Ba haka Allah Ya ce ba, ga
saurayi da bai taba aurc ba bulala dari, idan mai
127
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
aurc ne kuma a jefe shi har sai ya mutu. Haka
itama macc idan bata da aure bulala dari, idan
mai aure ce a jefe ta, sai dai idan tana da ciki shi
nc za a bari ta haihu ta gama shayarwa daga nan
sai a jefe ta. Don haka kai ba kisa za a yi maka
ba, bulala се.
Tunda kana so kaje ni ba zan iya kai ka
ba, amma bana so ka yi a garin nan domin ba zan
jure ganin ka cikin jinya ba".
Cikin farin ciki mai hade da kuka ya ce,
"Daddy na gode, zan yi duk abin da ka ce, sai dai
ina neman wata alfarma a gurinka, kafin wannan
ina so muje da kai a matsayin ka na mahaifi na
domin mu yi koyi da Sahabin Manzon Allah
(S.A.W), Umar (R.A) da hannunsa ya kai dansa
aka hukunta shi, don haka nima zan yi farin ciki
a ce mahaifina ne da kansa ya kai ni aka fitar da
hakkin Allah akai na".
Hawaye ne suka zubo a idanun Alh. Jafar
domin tausayin dansa da yaji ya kama shi, tabbas
ya yarda cewa sharrin shaidan ne da rudin
zuciya suka debe shi ya afka wannan ta'asar,
gashi da kansa yake neman ayi masa hukuncin
da Allah Ya tanadar wa mai irin laifin sa.
128
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
Saka hannu ya yi ya goge hawayen, ya сe.
"Hameed naji zan kai ka da hannu na, to
amma ka dan bani lokaci kadan ina wani shiryeshirye ne".
Murmushi ya yi ya zo ya rungume
mahaifin sa yana masa godiya da ya amshi
bukatar sa.
Alh. Jafar ne da kansa ya je ya hado masa
kayan abinci, ya saka shi a gaba yana bashi a
baki kamar wani karamin yaro, haka ya soma ci
sosai domin rabon sa da cin abinci har ya manta,
sai dai ruwa kawai yake ta'ammali da shi.
Haj. Asiya tana can daga nesa tana hangen
irin so da kaunar da Alh. Jafar yake nunawa
dansa kamar shi kadai Allah Ya mallaka masa a
duniya. Ta yi kwafa ta bar gurin, domin tana
labe duk taji abin da suka yi magana akai, ta
yiwa Allah godiya tare da cewa Allah Yasa ya
aikata abin da ya ce zai yi.
* * *
Watannin Aziza biyu a kwnace da sati
biyu, sai dai muce sauki yana gurin Allah, domin
dai har kawo wannan lokacin tana cikin doguwar
129
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Wazii
suma (Coma), abin da likita dai ya fada mana shi
nc tana rayc dai har yanzu, kuma cikin kowane
lokaci zata iya farkawa. Mu dai kawai muna
jinsa ne kawai, tabbas ba don na'urorin da muke
gani suna amfani a jikinta ba da sai muce ta jima
da mutuwa bai son gaya mana ne.
Abban ki duk ya kare ya kasa yin komai,
jinya ta mata ce amma da shi ake yi, ya daina
zuwa wurin aiki sam, ya yi baki duk ya rame
domin yadda yake nunawa idan Aziza ta cuka
wtaa uku bata dawo cikin hayyacin ta ba zai
shirya fita da ita kasar waje, haka likitocin suka
shiga bashi hakuri akan ya dan kara hakuri.
A lokacin babu wadda muke tausayawa
kamar ki, kullum sai kin yi kuka ke dai Aunty ki
Aziza za ki wajen ta, a lokacin da ki ka ganta
kwance cikin na'urori duk sai kika tsorata kike ta
yin kuka wai ke a tashe ta ku tafi gida. Lokacin
babu wanda bai zubar miki da hawaye ba don
tausayin ki, haka dai muka ci gaba da rayuwa
cikin jiran tsammani.
Da yake Allah maji rokon bawansa ne,
Gagara misali, wata rana na shiga bandaki
Ammin ku ta futa waje don yin rakiyar 'yan
130
Zuri'a Daya-1 sa'adatu Muhammad Waziri
dubiya da suka zo, Abban ku yana can masallaci
kamar yadda ya saba yana karatun Alkur'ani.
Ina fitowa sai kawai na iske Aziza zaune
kan gadon esibiti ita kadai garau da ita sai dubedube take, cikin murna da doki na ce.
"Aziza na!".
Na fada cikin karaji da doki, sannan na
daga hannu sama na fara yiwa Allah godiya.
Abin mamaki Aziza bata juyo ba bare ta
lura da abin d anake yi, ita dai hankalin ta gaba
daya yana kan robar igiyoyin da suke jone
jikinta su tabi da kallo tana mamakin yadda aka
makala mata su.
Da sauri na zo gabanta na rike hannaycn
ta, hawaye na zubo min na ce.
"Aziza ba ki ganni bane? Granny dinki ce
fa?"
Wani irin kallo na rashin' fahimta ta bini
da shi kamar tana so ta yi tunani, sai ta kasa, nan
dai Allah Ya taimaka ta cc.
"Wace ke?"
Murmushi nayi mai hade da kkuka, na
sake damke hannuwan tana ce.
131
Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri
"Aziza Granny ce fa? Ko baki ganc ni
bane?"
Dai-dai lokacin Aisha ta shigo dakin tana
hango Aziza zaunc da sauri ta karaso gurin cikin
murna, ta ce.
"Umma ba dai Ammi na ta farfado ba?"
Ta fada cikin karaji.
Itama binta tayi da kallo irn na rashin
fahimta, bata ce da ita komai ba, haka ta kura
mata ido ta kasa cewa da ita komai. Ta rike
hannunta tana murna, ta ce.
"Ammi na baki gane ni bane? Ni ce fa".
Shiru tayi har yanzu ta tsaya tana kallon
mu daya bayan daya kamar tana so ta tuno wani
abu, sai ta kasa.
Aisha ta soma rudewa da ta shiga tambaya
ta cikin kuka.
"Umma, ko dai Ammi na ta dawo kurma
ne?"
Girgiza kai nayi, na ce, "A'ah, tana
magana don tayi min magana kenan sai kika
shigo".
Nan ta dubi Aisha ta ce, "Kema wace?"
132
Zuri'a Daya-l Sa'adatu Muhammad Waziri
Ta nuna ni, ta cc, "Ke kince min Granny,
ni Aziza, ita kuma ta ce miki Umma, ni kuma
Ammi, to ita kuma wace? Ni kuma wanne ne
suna na, Aziza ko Ammi? Ni fa ban san wace ni
ba, ku kuma su wane?"
Nan da nan tashin hankali mara misaltuwa
ya bayyana a tare damu, muka shiga cikin rudani
da fargaba, kan kace komai Aisha ta juya ta fice
da gudu cikin kuka.
Nima hawaye ne ya shiga zubo min, nan
take naji tausayin Aziza ya kama ni domin
tunaninta na baya ya gushe kamar yadda likita ya
fada a baya cewa idan ba a yi nasara ba
tunaninta zai iya gushewa na wasu lokaci, idan
kuma Allah Ya nufa zata iya dawowa cikin
hankalin ta ba tare da gushewar tunanin ta ba.
Kalaman likitan ne suka dawo min cikin
kwanya ta, nan take hawaye suka shiga zubo min
a fuska ta, sai kawai na ga Aziza ta sa hannu tana
goge min hawayen, ta ce,
"Mene ya sa ki kuka? Wai ku din su wane
ne? Na tambaye ku ba ku bani amsa ba".
Na bude baki da niyyar bata amsa kenan
sai ga Abban ku nan da gudu tare da wasu
133
Zuri'a Daya-Sa'ádatu Muhammad Waziri.
likitoci guda ukuisun 'shigo dakin, yana zuwa ya
yi saüri ya riko Aziza ya rungume ta yana kuka
yana yiwa Allabi gödiyada Yasa ta farfado. Nan
ya shiga cewand sl iM thmA ok алiу л Бан
"Ammi na Allah agodea damYarbaki
kadiyallai sism illsd sidesi man ab aski
insbuntana rungune darita bayanaryavgama
mürna yaşakestáziya raba tanda jikin şaya shiga
dubanta yana cewa. eluri midio ubra ab
smmisna kin yi shirubakicce dani komai
bayko nimasbaski gancni.ba?"oiveaust sn elsi
sy stilinbastayis da kalloutances Al ina kakeskai
kdmasaMcyegsunandkaNa jiwka ce minsAmmi
nabsurero hakal sworders syi iss stainamut
nidio Muwnshis yayis maîuhade dåslkukamуа
shigagirgizarkaityana cewa.nb ost sd et nilsdasd
nizlio disi newAbbablil namsis
nim odiAhb yswed okst asn st eyaswk
ans! uddaal taki aniurnatakamashia da yajin ta
ambaci sunan sa, cikin dokisyarceswsd nim сgog
onsw Kigalánk2ul id s2 εγ οποM"
Girlidaszmasa kai tayiy/sarinan daree,Aah
nishan sanka bad BYin sh ided obud s
uesw eb sust buy bol nadd A By isa
138 134
Σ
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
Tashin hankali ne ya sake bayvana a tarc
da shi ganin yadda ya gigice yasa likitocin suka
ce damu muyi hakuri mu basu guri za su yi aikin
su. Dole amu musa musu ba haka muka fito
jikinmu babu kwari, muka tsaya jiran ikon Allah,
domin duk mun shiga cikin rudani.
Sun dauki tsawon lokaci kafin su fito daga
baya, can sai gasu nan sun fito. Muna ganinsu
muka yi saurin mikewa daga inda muke zaune,
muka yo gurin su a sukwane.
Abban ku ne ya ce, "Doctor lafiya dai? Ya
ake ciki ne?"
"Ku kwantar da hankalin ku, babu
damuwa, mun yi mata allura ta koma barci. Su
za su iya shiga kai kuma muje zuwa (office) za
muyi maka karin bayani".
Suka tafi mu kuma muka shiga ciki, cikin
wani irin yanayi mara misaltuwa.
Mun dan jima kadan muna jiran dawowar
sa muji ya akc ciki? Sai gashi nan ya shigo cikin
sanyin jii, muna ganin shi sai muma muka kara
shiga cikin damuwa, domin bamu san da me ya
zo mana ba.
135
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
Guri ya zo ya samu ya zauna hawaye cike.
a idanun sa, kowannen mu ya shiga jero masa
tambayoyi.
Cikin karfin hali ya ce, "Aziza tana cikin
tashin hankali domin likitoci sun ce ta manta
dukkan tunanin ta na baya, ba zata taba iya tuno
abin da ya faru da ita a baya ba, komai na cikin
kwakwalwar ta ya shude, ba zai dawo ba sai
lokacin da Allah Ya tsara hakan, don su kansu
sun ce basu da tabbacin tunaninta zai dawo ko ba
zai dawo ba, saboda muguwar firgitar da tayi a
lokacin da abin yake faruwa, hakan yasa abin ya
taba wurin ajiyar tunanin ta.
Don haka sai dai mu ci gaba da addu'a da
zubawa Sarautar Allah ido, sun ce abin da muka
koyar da ita ko muka ganar da ita shi yanzu da
shi zata dauka".
Gaba dayan mu sai muka sa kuka da yin
Salati, muka bi Aziza da kallo akan gadon da
take kwance tsabar tausayin ta da muke ji,
yarinya karama ta gamu da babbar kaddara
rayuwar ta.
a
136
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
Zuba mana idanu ya yi muna ta kuka
domin kasa ccwa damu komai yayi, domin
shima ya yi nasa kukan har ya gaji.
Muna cikin haka sai ga Mukhtar nan ya zo
shi da Mama, shi ne ya samu ya hakurtar damu
ya nuna mana babu yadda za muyi sai dai mu
rungumi kaddara, haka Allah Ya shiryawa
rayuwarta da mu kanmu baki daya.
Sai yammaci sosai sannan ta farka, tana
bude ido babu wanda ta kira sai Abban ku.
"Abba!".
Abin da ta fada kenan duk muka juya da
muka ji muryarta, domin a tunanin mu ta gane
mu, ta dawo cikin tunaninta. Haka kowa ya fara
murna, lokaci daya muka hada baki muka ce.
"Ammi kin tashi ne?"
ba.
Har da Mukhtar, domin yana nan bai tafi
Sai hanlkalin ta ya yi kansa, domin kafin
ta kwanta dazu bata ganshi ba, kallon sa ta shiga
yi sannan ta ce.
"Kaima din Abba na ne?"
137
Zuri'a Daya-l Sa'adatu Muhammad Wazíri
Gaba daya sai suka yi saroro suna kallon
ta, haka itama ta kura masa ido tana son jin
karin bayani daga gare shi.
Ganin yadda take mana kallon tuhuma sai
Mukhtar ya yi sauri ya cе.
"Eh, ammi ni (Uncle) ne, Uncle Mukhtar
suna na, wannan Abba, ga Ammin ki sannan
kuma ga Granny dinki".
Murmushi tayi ta ce, "Uncle dinku ku
nawa ne?"
"Eh mana". Ya fada yana murmushi".
"To na gode".
Ta fada ba tare da tayi masa murmushi ba.
Hannu ya mika mata kamar yadda suka
saba a da can idan ya yi mata abu tayi masa
godiya sai ya miko mata hannu su tafa, shiru ya
gani bata miko masa ba, sai jikinsa ya yi sanyi,
tausayin ta ya kama shi, nan ya kara tabbatarwa
cewa bata ita tuna komai.
Haka ya mayar da hannunsa domin ya lura
ba zata iya gane me yake nufi ba.
Nan da nan labari ya bazu cikin ZURI'A
cewa Aziza taji sauki, duk wanda yaji sai ka
ganshi ya zo amma idan ya zo ya ga bata gane
138
1
Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri
shi ba sai su ji ba dadi, haka za su koma tausaya mata, wasu kuwa saj dai su yi ta kuka.
Haka ta tsaya tana ganin kowa sabo domin
duk ba wand ata gane, dole tayi hakuri ta daina tambayar su wane su domin ance mata duk 'yan
uwańta ne.
Alh. Jafar tunda ya ji ance Aziza ta
farfado hanalin sa da na Hameed ya yi mugun
tashi, domin jira suke su ji anyi sallama ance su
fito ana tuhumar Hameed abinda ya aikata, don
haka bai samu ya je asibitin ba domin yana cikin
zulumi.
Amma kuwa Haj. Asiya cikin tawaga ta bi
'yan uwanta suka je dubiya, ta sani sarai bata
ganc kowa amma ta ki gaya musu domin bata
son ganin kwanciyar hankalin su, ba don komai
ba sai don yadda ya mantar da Hameed da
kudurin sa tun yana nacin har ya daina domin
kullum sai yana bashi UZURIn karya dole ya
barshi bai je anyi masa bulalar bayau tsawon
wata uku kenan cif.
139
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
Bayan kwana uku da faruwar haka Alh.
Jafar ya shigo gida da murna ya kira Haj. Asiya
da Hameed yake fada musu ya samu labarin
cewa Aziza bata iya tuna abin da ya faru da ita a
baya, haka ya daga hannu ya yiwa Allah godiya
a gabansu.
Suka bishi da kallo kamar ta6a66e, ganin
irin kallon da suke masa sai yaji wani iri, kai
tsaye ya cсе.
"Ba za ku hana ni murna ba domin addu'a
nayi akan rufuwar asirin mu kuma allah Ya
karba don haka dole ne nayi murna, don haka ku
shiga ku shirya muje mu duba jikin nata yanzu".
Babu wanda ya yi masa musu, haka suka
bar yaran a gida suka taho abin su.
A can asibiti tunda Aziza ta ci abinci a
ranar ya shiga tayar mata da zuciya, amai take
babu misaltuwa. Hankalin su ya tashi, suna
tunanin ko wani abu ta ci ya tayar mata da
zuciya.
Ni kuwa tuni na rude hade da fargaba
Allah Yasa ba abinda nake zato bane, haka na ja
baki na nayi shiru.
140
Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri
Zaune muke muna jiran dawowar Abban
ku likita ya kira shi, hira muke tayi ita kuma
Aziza ta sha magani bacci ya dauke ta. Bamu yi
aune ba sai muka ga Mustapha ya shigo a rude
yana kuka, gaba daya mikewa muka yi muna
jiran me zai ce damu?
Mukhtar ne ya fara tambayar sa da cewa,
"Yaya me kuma ya faru naga kana kuka?"
Cikin uka ya mika masa 'yar takardar da
take hannun sa, ya ce.
"Mukhtar wata masifar ce ta kara samun
mu gaba dawa, duba takardar nan ka gani, likita
ne ya ce min Ammi na dauke da ciki wata uku
cif".
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!".
Abin da gaba dayan mu yake fitowa daga
cikin bakunan mu, mikewa nayi amma ban san
lokacin da na koma na zauna ba. Gaba dayan mu
babu wanda yakara čewa komai, sai tausayin
kanmu da na Aziza da ya kama mu.
Haka na mayar da kallo na gareta tana ta
baccin ta cikin kwanciyar hankali, hawaye suka
zubo daga idanu na.
141
Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri
Mustapha ya soma kuka kamar Karamin
yaro yana cewa.
"Ya Allah Ka tona asirin wanda ya janyo
mana wannan tashin hakalin, Allah kada Ka
barshi cikin nutsuwa da farin ciki".
"Ameen Ya Allah, Allah Ka saka mana".
Cewar Mukhtar, haka duk muka yi jigum
babu wani mai iya cewa komai tsabar jin radadin
abin da kunnuwan mu suka jiyar mana.
Sallamar Alh. Jafar da iyalansa ita ce ta
janyo hankalin mu zuwa gare su, ganin mu duk a
tsaye cikin yanayin tashin hankali su ma sai suka
razana, da sauri ya karaso cikin gurin ya yi
saurin rike hannun Mustapha ya ce.
"Mustapha, me ya faru? Ba dai rasuwa
Azizan tayi ba?"
Cikin kuka ya rungume dan uwansa ya ce.
"Yaya Jafar ba mutuwa tayi ba, amma a
yanzu zan so ace. Aziza ta rasu domin ta ramu
nutsuwa akan wadannan masifu da suke ta
faruwa da ita, daga wannan sai wannan. Wai
likita ne yanzu yake fada min wai tana dauke da
juna biyu na tsawon wata uku".
142
Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri
Mutuwar tsaye Alh. Jafar ya yi, nan da
nan yashiga cewa.
sa.
"Ya Hayyu Ta Kayyumu!".
Abinda ya yi ta maimaitawa kenan a bakin
Hameed da yake gefe dora hannu bjyu
yayi akai yana salati hade da kuka, haka itama
Haj. Asiya.
Ya koma gefe yana ta buga hannunsa a
jikin garu, nar da t Mukhtar ya yi sauri ya rike shi ya се.
"Hameed baka da hankali? So kake ka ji
ma kanka rauni ne?"
"Uncle ka barni, bani da wani amfani a
rayuwata tunda har...".
"Hameed ba zaka yi shiru da bakinka ba
sai kana mana surutan banza!".
Alh. Jafar ya katse shi cikin hanzari, da
sauri ya zo ya rike masa hannu ya се.
"Hameed, idan ba zaka tsaya ka kwnatar
da hankalin ka ba zan hana ka zuwa nan gurin,
baka ganin mu ma kullum hakuri muke yi?
Yadda kake jin abin nan mu ma haka muke ji".
143
Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri
Abba ya karaso gurin shima ya ce,
"Hameed mu dauki kaddara, haka Allah Ya
rubutawa 'yar uwarka tun fil'azal, babu wanda ya
isa ya goge ko ya hana faruwar hakan".
Kuka sosai Hameed ya saka ya sulale kada
yana