Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 9
suke mata. A ranar sai da muka rabota da su domin babu wacce na ragawa a cikin su, dama kuma suna jin shakkata domin tun da na dawo gidan kishin ya koma kaina har Allah Ya kawo lokacin haihuwar ta, ta haifi da namiji mai kama da ubansa fitik, don duk cikin 'ya'yan sa babu wanda yake da tsananin kama da shi irinsa. 23 Zuri'a DayaI Sa'adatu Muhammad Waziri Murna a ranar tamkar akansa ya farа samun haihuwa, wanda hakan ya dasa tsana da Kiyayya akan wannan haihuwar. Ko kadan Alh. Nasir baya iya 6oye murnar sa ta haihuwar yaron, ranar suna aka saka masa suna Mustapha. Shekarar Mustapha biyu a duniya a lokacin ne Baffan mu ya matsa min akan dole sai na baro nan na dawo gida, ya gaji da masu yi masa maganar aure na. Wannan karon haka muka hakura na dawo gida cike da kewar 'yar uwata da dana Mustapha. Maganar bikina ta kankama, har an fara shirin biki wanda zan aura ya ce ya fasa, ni dai nasan ba laifi nayi masa ba dole aka nemi sanin dalili aka rasa, haka aka hakura dole. Da Baffana ya zaci ni ne na ki shi, wasa gaske har mutum uku suna sake fitowa rimi-rimi sai magana ta rushe. Baffa ya shiga damuwa, Alh. Nasir da kansa ya zo ya roki Baffa ya barni na koma can ko mijina a can yake da kyar ya yarda don dai babu yadda zai yi nc. Lokacin da na dawo nan na iske 'yar uwata Innawuro na fauke da ciki na biyu wanda sam 24 Zuri'a Daya-I _Sa'adatu Muhammad Waziri bata wahala kamar wancan ba, haka murna ta kama ni domin dama ni da za a barni tare da 'yar uwata mu rayu guri guda da haka ya fi min dadi. Wannan haka yake itama a gurinta, domin idan ina tare da ita ta fi jin dadin gidan da kuma samun sukunin tsangwamar da take samu gurin abokan zamanta, domin har yanzu sun ki su barta ta sake a cikin gidan su, kuma suna bakin cikin zamana a gidan, domin babu abin da nake bari Innawuro tayi da kanta, komai ni ce nake mata na hidimar gida da na yaro wanda ya danganci na mijinta ita ke yi da kanta, su kuma hakan na kona musu rai. Daf da cikinta ya kusa isa haihuwa lokacin abokin Alh. Nasir ya fito za'a yi mana aure, an gama shirin komai za ai biki ranar da Innawuro ta haihu ta haifi diya mace, a ranar muka samu labarin Allah Ya yiwa Alh. Kabiru rasuwa, hankali na ya tashi har na fara tunanin ko ba zan taba yin aure ba daga wannan sai wannan. Ranar suna aka sanyawa jaririya suna Maryarı, lokacin 'ya mai kama da uwarta fitik kamar an tsaga kara, haka muka wanzu cikin murna da kuma jimamin rashin da muka yi na 25 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Alh. Kabiru, babu wanda bai tausaya min ba amma ni samun Maryam shi ne ya kara dauke min damuwar, tun daga lokacin na fara fitar da rai na akan aure. Mustapha na da shekara hudu Maryam na da shekara daya a duniya Innawuro ta samu cik wanda tun daga samun sa take cikin matsala, ga kuma laulayi na kin karawa, domin kullum tana cikin larura, dole yasa aka cire Maryam daga shan Mama ganin itama ta fara yin rashin lafiya. Kullum muka zauna ni da ita ta dinga yi min magana akan cikin nan, da kuma cewa. "Rehana anya kuwa wannan cikin zai barni na rayu da ku? Domin tunda nake ban taba daukar ciki mai wuya haka ba. Idan har na mutu ki daure ki kular min da Maryam da Mustapha, ki rike su tamkar yadda za ki rike yaran da kika haifa a cikin ki, bana so ki bar su hannun su Saude, domin ba za su rike su tsakani da Allah ba. Domin na fuskanci tsanar da suke min ita ce ta koma kansu idan har na haifi wannan cikin shima ki hada ki rike, domin ji na nake kamar rayuwata ta zo karshe. 26 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Hankalina ya yi mugun tashi domin kalamanta sun taba zuciyata, nan take na nuna mata kada ta ji komai yadda ta haifi sauran haka ma wannan zata haihu lafiya, ciwo ne kawai yasa take wannan sambatun. Kullum muka zauna sai tayi min wannan zancen, nan take na ce ni dai ta daina. Da ciwo ya yi yawa dole muka tattara muka koma Rano, watanmu kusan uku a can ta warware sarai. Sai a lokacin hankalin kowa ya dawo jikinsa, amma kullum muka cauna sai ta ce min. "Raihanatu, don Allah ki kula da yaranki sosai, ga amanar su nan duniya da lahira". Haka zan nuna mata ta daina min irin wannan zancen, ganin bana so yasa ta daina yi min. Tun komawar mu Rano sau biyu ne zan cе ga kafar su Saude a gidanmu, domin ni a gurina da zuwan su da rashin zuwan su duk daya. Ranar da suka yi zuwa na uku ne a nan ne Innawuro ta nemi su yafe ma juna, su kansu sai a lokacin suka ji nadamar abinda suke mata. 27 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Cikinta wata takwas bai isa haihuwa ba rana daya wani ciwo ya tasar mata, kwananta biyu a asibiti ta ce ga garinku nan. Tsananin rudani da rikicewa babu wanda ban shiga ba, domin ban taba dandana jin zafin mutuwa irin wannan ba. Babu yadda za mu yi dole mu dauki hakuri da kaddara. Alh. Nasir ya yi matukar jin mutuwar nan, amma duk da haka sai ya nuna yafi tausaya min da yaran da aka bari. Haka kowa ya zo gaisuwa sai ya tausaya min, Mustapha da Maryam kuwa suna nanike dani, babu wanda suke yarda da shi sai ni. Da na kalli yaran sai naji kuka ya zo min. Ana gobe sadakar arba'in muna zaune da su Baffa da Innar su suka zo min da wani labari da ya ruda ni rudu na gaske kuwa, na cewa wai gobe a gurin addu'a za a daura aure na da Alh. Nasir a yi madadi da ni. Kuka na saka musu na ce ban yarda ba na auri mijin 'yar uwata, aka yi aka yi dani na tsaya da kukan na ki. Nan wasu daga cikin iyayen mu maza da mata suka shiga saka baki tare fa fada min cewa Alh. Nasir nemi hakan da kansa. 28 Zuri'a Daya-l Sa'adatu Muhammad Waziri Ya cc, "A rokar masa gurinki, ba don komai ba sai don saboda yara sun riga da sun gama sabawa da ke, babu wanda suke sani bayan ke". Shiru nayi ina kuka, mahaifiyar sa ta karbata ce, "Raihanatu ko ba don komai ba don yaranki ki daure ki maye gurbin 'yar uwarki, domin kin fi kowa sanin zaman da za su yi a gidan ubansu idan ba kya kusa da su. Sannan kuma da ana mutuwa a dawo idan ki ka yiwa 'yar uwarki haka ta dawo ta gani zata yi murna da farin cikin kin kula da yaran ta, na tabbata ta baki amanar yaranta a hannun ki". Nan nayi shiru na dinga tunanin irin maganganun da muke yi da ita akan yara, tun kafin ta kwanta rashin laifyar nan. Na ci kukana na koshi, babu yadda na iya dole na amsa musu na yarda. Nan farin ciki ya cika su, suka shiga saka min albarka da nuna min cewa dama haka Allah Ya rubuta, shi yasa tun farko Allah bai kaddara yin aurena ba, domin a lokacin shekaru na sun 29 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri dan soma dagawa sabanin yadda akewa kowacce budurwar are a kauyen mu. Da daddare Alh. Nasir ya zo ya yi min godiya da taimakon da nayi masa, kuma insha Allahu ba zai taba barinta cikin damuwa ba, zai mata duk abinda take so ita da yaransa. Kuka na saka mishi domin ban san da wacce kalma zan ce da shi ba, ganina cikin damuwa ya bani hakuri ya ce na tashi na koma cikin gida. Kafin na koma ciki aka kawo min yara suna kuka, a wannan lokacin naji dole ne ma na saki riana na auri Alh. Nasir domin yaran su tashi gaban mahaifinsu, don mu samu damar basu tarbiyya ni da shi. Ganin yadda suka yi shiru a jikina sai ya samu damar cewa. "Raihanatu ko ba don ni ba don yaran nan da suke ganinki kamar wacce.ta haife su ki yarda ki maye gurbin 'yar uwarki matukar ba kya so su san maraici". "Babu komai na amince, ita kkuma Allah Ya jikanta da rahama". 30 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Murna ya nuna sosai, ya yi min godiya, haka muka rabu na shiga ciki da yara. Maryam na rungume a kafada ta shi kuma Mustapha na rikc masa hannu muka shige muka bar shi zaunc a gurin. Washe gari haka aka hada daurin aurenmu da addu'ar arba'in din Innawuro, mutane da dama sun nuna farin cikin yin haka, addu'a aka yi sosai a gurin. Tunda ana cikin alhini ba wani shagalin biki don haka aka tsayar sati mai zuwa zan tare dakin 'yar uwaia nade da yara na biyu.M a Sam Alh. Kabir bai sanarwa da matansa maganar auren mu ba, don bai barsu sun zo Ranon ba, haka ya ce su zauna a Kanon su yi duk abinda ya dace, sai washegari ya zo musu da abarin daurin auren, haka suka ji abin sama. Take hankalin su ya yi mummunan tashi, suka shiga ce mas aya ci amanar su ya yi aurc ba tare da sanin su ba. Ganin da yayi za su bata masa okaci ya tafi ya barsu a gurin. Haka dai na zo na tare a dakin 'yar uwata, gori da takaici da habaici babu abin da ban uskanta gurin A'i da Saude ba, duk bakina amma na kasa yi musu komai, da zama ya fara 31 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri zama na gaji da abin da suke yi min na fara tanka musu. Ke na takaita miki daga ni har yaran sai da zaman gidan yaso ma gagarar mu, da kyar ya tsaya akan gidansa abubuwa suka dan soma sauki, da suka ga an soma girma sai suka saduda. Haihuwa ta uku, da fari na haifi Aziza, sai Mukhtar wanda ya ci sunan Baffanmu da Allah Ya yiwa rasuwa, sai dan auta na Usman. Kafin su girma Allah Ya dauki Aziza da Usman, Ya bar min Mustapha da Maryam da Mukhtar. Ita kuma Haj. A'i tana da yara biyar masu rai, su ne Bara'atu, Jafar, Lukman, Habib sai Shchu da aka sa ma sunan Usman nawa. Ita kuma ta binnc uku duk mata. Sai Haj. Saude tana da hudu, Aminu, Hamza, Aminatu da Hajara. Kinji yaran nan guda goma sha biyu da na lissafa miki su ne suka hadu suka gina junan su, suka zamo ZURI'A DAYA, ta cikin ZURI'Ar su ne aka samę ku, kuma cikin su har yanzu suna nan babu wanda ya rasu, sai ba a guri daya suke yanzu ba, za kiji dalilin da yasa duk suka watsu cikin duniya". 32 Zvri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri "Raihanatu na faro miki labarin nc tur daga tushen ku, don ki ganc komai dalla-dalla, shi yasa na yi miki haka saboda kada zuwa gaba ki cc ba ki gane kowa ba tunda na ware miki daki-daki kin gani". Haana tayi murmushi cikin alhini ta ce. "Granny na tausaya miki wallahi, kuma kin yi kokari sosai. To shin ina su Haj. Saude da Haj. A'i? Suma suna raye ko sun rasu?" Tayi murmushi ta ce, "Raihanatu kenan, ai baki ji komai ba, ki biyo ni a sannu domin yanzu ne zan fara baki labarin komai har zuwa yau din nan da muke ciki, domin duk abubuwan da kika ji a baya somin tabi ne, ke dai ki saurare ni". Ta gyara zama ta cc, "Tam". "Kamar yadda na fara fada miki zaman kishi muka yi sosai da kishiyoyi na har sai da yara suka girma aka dasa musu 'yan ubanci, wannan baya son wannan dan dakin, amma nawa ne kawai ake yiwa haka. Da kansa Alh. Nasir ya ganc haka, ya tara kan yaransa gaba daya da matansa ya ce matukar ba a kawar masa da wannan muguwar al'adar ba to gaba daya zai kori matan ya sakc wasu. 33 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri Sanin zafin sa da suka yi da kuma ganin tarin dukiyar da yake da shi a yanzu, domin akan arzikin sa na da sai mucc ya ninka zaman sa a wannan lokacin, don yanzu komai nashi ne na kansa ba tare yake da na kowa ba. Domin ba gidansa kadai ba, 'yan uwansa na jini babu wanda bai dagawa kafa ba ya gina kansa, kusan duk kannen sa sai da ya dawo da su cikin garin Kano suma suka kafa kansu. Don haka ya tsaya sosai akan iyalinsa, sai da ya kawar da wannan bambancc-bambancen ya gina kauna da soyayya tsakanin yaransa. Hakan ba karamin dadi naji ba, domin burina kenan naga mun samu hadin kan yaranmu. Babu laifi nima mun dan samu dai daituwa da abokan zamana. Arzikin Alh. Nasir kullum daduwa yake yi, domin ya rungumi zumuncin Allah, duk wanda ya raße shi shima sai ya yi arziki, domin bashi da bakin ciki matukar zaka yi gaskiya to zai daga maka kai ma ka tsaya da kafar ka. Da yaransa da na 'yan uwan ya tsaya akan su, duk abin da zai wa dansa shi zai yiwa dan dan uwansa don haka duk 'wanda ya gama 34 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri karatunsa wajc yakc tura shi ya karo karatu tun duniya na kwance. Haka ya shiga gina manya-manyan (company) a garuruwan Arewa yana diban jama'a yana sawa ciki, duk burinsa adan yaransa sun girma bai da burin barinsu aikin gwamnati, yana so su hadu a gùri guda don su zama wani abin kwatance a duniya. Bara'atu ita ce diyar da muka fara aurarwa cikin Zuri'ar, domin dama ita ce babba kaf cikin su, itama din auren dangi aka yi mata da dan yayan Alhaji Nasir wanda shima shi ne babba a cikin jikokin gidan. Jafar, Lukman, Aminu da Hamza su ne manya a ciki, su ne aka fara aurarwa bayan auren Bara'atu, duk auren gida aka yi musu domin anji dadin na farko. Dukkan su sai da suka yi digirin farko, wasu sun yi na biyu wasu kuma sai da akai musu aure sannan suka yi digirin na biyu. Haka Zuri'ar ta zamo ta 'yan boko, hatta mu ma da ba wani bokon muka yi ba sai muka taso kamar 'yan boko, domin muna auren 'yan bokon, ga kuma 'ya'yan mu 'yan boko. 35 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Kasancewar mu daga tushe daya muka fito duk dinmu Fulani ne kuma na yanki daya, sai aka dinga kiran ZURI'Ar mu da gidan farare. Maganar kyau kuwa muna alfahari da ZURI'Ar mu, don wasu suna dauka ccwa muna da dangantaka da Larabawa, nan kuwa basu sani ba asalin Fulanin Rano ne". Haana tayi dariya ta ce, "Kai Granny, irin wannan kura kai haka". "Ba kurara kai bane, gaskiya na fada domin mu Fulanin na yankin mu daban muke, kuma kema kin san haka a gareki". Haana tayi murmushi ta ce, "Granny na yarda, ci gaba da labarin ki, ina son ki ci gaban naji an fara gangarowa don kina ta samin kaunar ZURI'A ta har na matsu naji karshen labarin". "Lokaci guda Zuri'ar mu ta fara yaduwa domin 'ya'yanmu sun fara ajje mana jikoki, haka muka dauki soyayyar mu duk muka dora su akansu. Sai dai kaf cikin Zuri'ar babu wanda yayi farin jinin Abdulhameed dan Alh. Jafar, domin yaro ne abin so daga zuciyar mu baki daya. 36 Zuri'a Daya-I Sa'adaty Muhammad Waziri Ba komai ne ya jawo haka ba domin shi ne jika namiji na farko a cikin Zuri'ar, sauran duk mata ne, don an haifi har (twins) suna mutuwa, akansa ne dai suka fara tsayawa. Shekarun Hamecd biyu aka yi auren Mustapha da kannen sa uku, Amina, Hajara da karamar su Maryam, duk cikin dangi suka samu mazajen su, Mustapha ne dai'ya dage sai da ya auri ba 'yar dangi ta jini ba, ita 'yar aminin Alh. Nasir ce, mutanen Garo ne, suma Fulani ne na asali, suma haka suke kamar Larabawa. Hameed ya tashi cikin gata da soyayyar iyaye da kakanni, domin kowa da irin son da yake nuna masa, har gatan ya so ya yi masa yawa, ba ya laifi ayi masa fada. Ganin yadda ZURI'A ta soma yawa farin ciki yana ta samuwa a cikinta yasa Alh. Nasir yin tunanin yiwa yaransa gini yadda za su hadu guri daya har karshen rayuwar sa, don baya son ya ga abin da zai raba kansu. Don haka ya samu katon fegi (wato fili) iya ganinka ya ce anan yake son ya gina ma zuri'ar sa gidaje inda za su dunkule guri guda har 37 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri zuwa lokacin da kowa zai yi nasa iyalin suma su zauna ciki. Lokacin duniya na kwance, ga filayc nan ko ta ina, kuma gashi babban mutum da sukc da alfarma a wannan gwamnatin, don haka ya zuba kudinsa sosai ya samu abin da yake so don har matansa mun fara yi masa surutu ya ce mu dai mu barshi, yasan abinda yake, kowa ya zo ya ga filin sai ya girgiza kai. Haka aka fara gini iri daya har gidaje sama da sha biyu, kuma duk tsarinsu iri daya, sai dai guda daya da ya bambanta da sauran wurin girma. Nan ya fara gaya mana cewa gida ne zai gina tunda yara maza har mata kowa ya dawo gurin da mazajen su, wanda kuma ba su yi aure ba gashi nan guri yana jiransu. Kowa ya shiga nuna murnar sa yiwa Allah godiya ganin inda aka tanadar musu don rayuwa guri guda. Tunda aka yi kokarin daina nuna wariyar daki da daki sai rayuwar tayi dadi, kowa ka gani yana farin ciki da abin da dan uwansa zai samu. Soyayya da kaunar juna ya gama kewaye zuri'ar, babu wani mai kuka da dan uwansa. 38 Zuri'a Daya- Sa'adatu Muhammad Waziri Nan ma ya je Kaduna ya kara gina wasu gidajen masu tarin yawa, duk don yaransa da 'yan uwansa. Tarin ariziki dai na ko maye Allah Ya bawa Alh. Nasir, sai dai fatan samun na labira shi din ma a zahiri kowa yana hango masa hakan. Shekaru biyu da gama ginin ya tattara kan ZURI'Ar sa guri guda, shima yana cikin su, kowa da gidansa a ciki mata da maza. Burin sa ma sen ganin zuri'ar sa guri guda ya cika, don haka ko da yaushe yana tare da su idan ya fito daga gidansa ya ga tarin gidajen 'ya'yansa saı ya shiga farin ciki da yıwa Allah godiya da Ya yi masa arzikin yara da na dukiya, yana fatan Allah Ya hada kansu. Gidaje ne a jere wasu na'kallon wasu, ko da yaushe Alh. Nasir yana tare da jikokin sa a falon sa suna ta zuba hira, don a lokacin yana da tarin jikoki sun kai kusan goma. Babban wanda ya yi fada da farin jini shi ne Hamced. Kullum burin Hameed Allah Ya bashi kanwa mace, amma har yanzu shiru domin Gannen sa duk maza ne a cikin family din, duk lokacin da ya tamibayi kakansa cewa shi fa yana 39 Zuri'a Dage-i Sa'adalu Mukammad Waziri son a haifo masa kanwa mace sai ya cc ya kwantar da bankalin sa gashi nan iyayen sa kwanan nan za su haifa masa duk kanne mata. Lokaci guda aka yi haihuwa hudu duk maza ne, nan fa Hamecd ya yi ta rigima wai shi bai ga mace ba a ciki, duk kanne maza aka yi masa. Hatta mahaifiyar sa Ilaj. Asiya itama namiji ta haifa, sai Haj. Aisha ce mátar Mustapha ita ce kadai a cikin su bata haihu ba. A icker's ne Haj. Asiya ta се, "Abdulhameed ka kwantar da hankalin ka, kaje. gidan Ammin ka Aisha ita ce zata haihu, sai ka ce mata ta haifo maka kanwa mace". Abinka da yaro da kuma abin da yake so, nan kuwa tayi masa hakan ne don ya yi mata shiru daga rigimar da yake damunta da shi. Yana fita daga gidan kuwa bai zame ko ina ba sai gidan Ammin sa, nan ne ya iske mu ni da Aisha da Mustapha muna zaune a a falo muna hira, sai gashi nan ya shigo. Cikin harshen Fulatanci nayi masa magana, naicc ya zo gurina. Da yake lokacin muna yi musu duk sun iya sosai, sai ya make 40 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri kafada ya ce shi ba gurina ya 2o ba, gurin Amminsa ya zo, duk sai muka sa dariya. Sai ta kira shi, ya zo jikinta ya kwanta yana taba tudun cikinta. Ta ce, "Hameed me kake so na baka nc? Oya fada min". "Ammi baby girl nake so ki haifo min na samu kanwa, Mama ce ta ce na zo gurinki na fada miki ki haifo min baby girl tunda su basu haifo ba". Dariya muka yi gaba dayanmu, domin abin nashi gwanin dariya, nan ta cе. "To Hameed, kai tayi min addu'a idan kayi sallah, Allah Ya sauke ni lafiya na haifo maka baby girl din da kake so". Haba! Nan da jin ta fadi haka ya shiga murna yana tsalle wai za a haifa masa baby girl, bai jira kowa ba ya juya ya koma gida a guje yа fadawa Maman sa. Tun daga ranar kullum Hameed sai ya zo gidan wai ya duba ko an haifa masa baby girl dinsa, lokacin yana da shekara shida a duniya. Jin shiru baby bata zo ba ya fara nuna damuwar sa, lokaci guda ya dauke kafa ya daina 41 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri zuwa, a ccewar sa ya yi fushi tunda Ammi ta ki zhaihuwa. Nan ta shiga nuna masa lokaci ne bai yi ba, ya kara hakuri. Ya ce, "To tunda haka ne zan dawo gidan na jira har sai kin kawo min babyn". Gudun fitinar sa yasa ta ce masa to, nan ya juya ya koma gida ba jimawa sai gashi da kayansa tili a hannu wai ya dawo gidan gaba daya sai lokacin da babyn ta dawo zai koma gidansu. Duk wanda yaji labarin sai yayi dariya ya jinjina rigimar Hameed. Ganin da gaske yake nan Aisha ta shiga addu'a Allah Ya bata diya mace don ta cika ma Hameed burinsa, duk da kuwa itama burinta kenan haihuwar diya mace. Kullum idan ya tashi babu abin da zai tambaya sai cewa, "Kin haifi babyn nawa?" Sai ta ce a'a, addu'a ce baya yi sosai idan yayi sallah. Sai ya cc, "Eh haka ne, jiya sau haka nayi addu'ar". (Ya nuna yatsun sa guda biyu) 42 Zuri'a Daya-! Sa'adatu Muhammad Waziri Tayi murmushi ta cc, "To dinga yi sau da yawa zaka ga na haihu lafiya, na kawo maka baby girl din taka". Nan zai shiga murna, ya cc, "Tam". Cikin yardar Allah wata Alhamis da daddare Allah Ya sauki Aisha lafiya, ta haifi katuwar 'yarta mace jajir da ita, lokacin IHamced yana bacci bai tashi ba. Cikin kankanin lokaci labari ya iske ko ina cikin Zuri'a, tun daren aka cika gidan da murna. Aisha ta yiwa Allah godiya da Ya cika mata burinta Ya bata abin da take son samu. Bayan an dan nitsa ne nan aka shiga taya Hamced murna ya samu abinda yake so, ba а tashe shi ba sai da garin Allah Ya waye tangaran, lokacin ne ya farka. Kukan baby din ne ya tashe shi, zumbur ya mike ya ce. "Lah! Ammi kin haifi baby girl din ne? Don jiya na yi miki addu'a da yawa sosai". Murmushi tayi ta ce, "Eh mana, ai tun jiya kana barci kanwar taka take ta neman ka baka tashi ba, shi ne yanzu ma take kuka da bata ganka ba". 43 Zuri'a Daya-i Sa'adatu Muhammad Waziri Dariyah ya saka yana kallonta, ya ce, "Lah! Ammi dama ta sanni nc?" Gaba daya dariya gurin aka saka, nan ya shiga murna da rawar kafa wai shi a bashi ita ya dauke ta, nan dai aka taimaka masa ya daukc ta ya shiga murna hade da yin shirmen sa na yara. Haba! Abin nema ya samu gurin Hameed, sam bai son abin da zai raba shi da 'yar kanwar sa, ko da yaushe yana like da Ammin sa, da ta fara kuka zai tambayi me aka yi mata take kuka? Haka zai ce a bashi ita ya rarrashhe ta. Haka dai ya zamana shi ma ya zama dan riano, don haka zai zauna ya tankwashc kafa а dora masa ita ya rike, da ta soma kuka zai cе a karbe ta. Ranar da Alh. Jafar ya zo ganin yarinyar lokacin ba ya gari akai haihuwa, da ya ganta zai tafi sai ya се. "Hameed, ai sai ka shirya mu koma gida tunda anyi maka abinda kake so". Ya tuburc ya ce ai shi babu inda zai tafi, ya dawo gidan Ammi tunda ita ce ta haifa masa baby girl, ba zai koma gidan Mama ba tunda ya ce ta haifo masa baby girl ta ki. 44 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri Dariya aka yi gaba daya domin shirmen Hameed din ko yaushe gaba yake yi, hakan yasa kowa yake son zaman sa a gidan domin yana nishadantar da mutane. haka?" "To idan na kenan na fadawa maman taka Ya gyada kai alamar, "Еh". Haka nan kuwa akai fafur ya ki komawa don haka dole aka barshi zuwa kwana biyu, ana tunanin da kansa zai nemi gida. Ranar suna jaririya ta ci sunan murgayiya 'yar uwata Aziza, mahaifiyar sa. Ni ce na ce a saka, da shi sunana ya ce, na ce masa a'ah gaba a saka ni. Ni da kaina na ce kada wànda ya boye mata sunanta, kowa yana kiranta da haka domin zan dinga jin dadı ina yawan tuna 'yar uwata. Haka kuwa aka yi, Aisha ce kadai ke kiranta da Ammi na don alkunya, haka sauran surukan amma cikin yara kowa da sunanta yake kiranta, ni kuma nafi son haka, dole sauran iyayen ma maza suke kiranta da haka. Abin kamar wasa Hameed kememe ya ki gidan su, dole haka aka hakura ya dawo gidan 45 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri gaba daya. Tun daga nan ya zamo dan gidan, har zuwa girman sa. Amma kafin nan kusan kullum da shi ake rainon Aziza, idan Aisha tana aiki shi ne yake zaune yana kula da ita. Wani ikon Allah 'ya tana girma kamanninta yana fitowa sak da na mai sunanta, tamkar ita ce ta haife ta. Iko ne na Allah, babu abinda ba ya iyawa tabbacin Shi ne Yake da komai a hannun sa. Tsananin shakuwa da kauna gami da sabo shi ne ya kullu tsakanin Ammi da Hameed da kanwar sa Aziza, don yadda suke a yanzu ko mahaifiyar sa bais shaku da ita ba kamar suka shaku da Aisha. Kowa ya yi farin ciki da hakan domin shi wata rana ma mantawa yake da zmaman sa, haka yake jinsa cikin wani sabon duniyar. Azizas haka ta soma wayo, babu wanda ta fi sani a rayuwar ta daga Amminta sai Hameed dinta. Haka yarinya ta taso da karsashinta da komai, kowa yana son ta domin kaf cikin su ita kadai ce;ya mace kamara. Haka kowa ya dauki son duniya ya dora shi akan Aziza. 46 uri'a Daya-1 __Sa'adatu Muhammad Waziri Kullum gidan cike yake da yara, cikin

Chapter 2 of 9