Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 9
su babu wanda ya isa ya taba ta sai Hameed ya bashi dama. Idan kuwa aka samu wani abu na sabani ya shiga tsakanin su, to ranar baka isa ka ga Azizan sa ba, don ko kofar gidan ba zaka zo ba bare ka shiga gidan nasu. Haka yaran za su ta kawo masa (sweet) daya nashi daya na Aziza, duk wanda bai kawo na Aziza ba to ranar ba za ayi wasa da shi ba. Lokacin da Aziza ta cika shekara uku haka tayi wayo da surutu cakwai kamar kanari, gata 'yar dabas a kasa, sai dan banzan wayo da surutu. Tun rana karama Allah Ya dasa mata kyau, wayon ta da surutun ta shi ne ya kara mata farin jini har sai da ta zo ta zarce farin jinin Hameed. Ita kuma tunda Allah Yasa tayi kafa ta zamo bata son zama, kullum ta shiga wannan gidan ta fito wannan, haka ZURI'A gaba daya ta dauki son duniya ta dora shi akan ta. Kowa so yake ta zo gurinsa, kuma duk wata fita da iyayenta maza za suyi sai an kawo mata tsarabarta daban. 47 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Duk ranar da Hameed ya dawo daga makaranta bai ganta ba haka zai ta da hankalin sa ya fita neman ta gida-gida har sai ya nemota sannan ne hankalin sa zai kwanta. Nan zai ta yi mata fada yana cewa ta daina fita yawo, idan ba haka ba zai daina kawo mata (sweet) daga makaranta. Hkaa zata ce masa ta daina, gobe kuma sai ta sake. Haka wata rana ta faru lokacin Mukhtar ya zo ya fita da Aziza suka tafi yawo har lokacin dawowa daga makarantar Hameed yayi ya dawo gida bai ganta ba, ya shiga duk inda yake tunanin zai ganta bai ganta ba. Bayan an fada masa ga inda suka je haka ya je ya tsaya da (uniform) bai cire ba ya tsaya bakin get yana jiran dawowar su yaji shiru, da yake dama shi din dan shagwaba ne nan ya samu guri yana kuka wai Azizan sa. Haka ya zauna yana kuka, nan ya hangi motarsa ta dawo, nan ya hangi Aziza ta fito da gudu daga motar ta zo ta rungume shi tana tambayar cewa. "Yaya Hameed me aka yi maka kake kuka? Ko Ammi ce ta dake ka?" 48 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri Turc ta yayi ya ce, "Ba ke ce na ce ki daina fita yawo ba sai ina nan mu fita tare, kin ce kin daina sai kuma gashi kina tayi". Mukhtar ya ce, "(Sorry) Hamced, laifin (Uncle) ne ba na Ammi na bane, shiru ka daina kuka tunda mun dawo". Nan ya share hawayen sa ya ce, "To (Uncle) nayi shiru". Ya sa hannu ya goge hawayemn sa, sannan ya mika hannu zai riko Aziza, ta ture masa hannu wai ita tayi fushi, ta wani make kafada. Mukhtar ya rike haba, ya ce, "Ammi na ya haka? Kin manta da Yaya Hameed dinki ne? Baki ga akan ki yake kuka ba da bai ganki ba? Oya maza bashi hakuri". Turo baki tayi gaba, bata ce komai ba sai ta mika masa hannu wai ya rike ta su tafi. Dariya da mamaki ne suka kama Mukhtar, ya jinjina irin tarin karancin shekarunta sai wayon tsiya da yin abu kamar 'yar shekara goma. Anan dai suka shirya ta dalilin sa. Tsananin shagwaba da rashin kwaba da sangarci gurin Hameed ba a magana, domin baya 49 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri yin komai sai abinda ransa yake so, don haka 6aci yake yi son ransa ana biye masa, domin abin d ayake na shagwaba Aziza ma bata yi tsabar gata da yake samu ta kowane bangare na iyayen sa. Alh. Nasir yana matukar farin cikin ganin yadda 'ya'yansa suka hada kai guri guda suna zumuncin su yadda yake so, hakan yasa ya kaга gina musu wasu gidajen a can Kaduna, ganin wasu suke rike da manyan kamfaninsa a can, don haka yadda ya gina na Kano haka ya gina tsantsarin su daya komai da komai, don haka ya ce, ko da wasu za su koma can ya kasance kowa yana da nashi a can, don bai son ya ga ya raba kan yaransa ta kowane fuska. Kullum burinsa akan yaransa shi ne su hada kansu guri guda su yi zumunci kada su bari wani ya zo ya shiga tsakanin su har a zo a raba musu zumuncin su. Sau da yawa haka zai zhada su yara da mu ioyayen su yana ta yi mana nasiha akan zumuncin Allah. Aziza na da shekara biyar aka yi mata kani mai suna Nasir, a lokacin ne ma aka haifi Muhammad kani na biyu ga Hameed. Sannan sai 50 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri a shckarar Allah Ya bama Maryam haihuwa, ya bata da namiji, ta yiwa Mustapha takwara, wato Ya Abban ki. Sannan kuma a wannan dai shekarar Murja matar Alh. Aminu dan wajen Haj. Saude itama ta haifi da namiji mai suna Sameer. In takaita miki a shękarar nan dai sai da kusan duk yaran mu suka haihu, a kalla cikin shekaru biyu sai da muka yi jikoki sun kai bakwai, kuma duk maza, mata biyu. Amma bayan shekara daya sai da muka rasa mutum uku, cikin su na farko Kabir wanda yake bin Hameed, sai Nasir kanin Aziza, sai kuma Fiddausi 'yar wajen Hajara. Shekarun Aziza goma a duniya lokacin Allah Ya dauki ran Alh. Nasir, rasuwar da har yanzu bamu mayar da gurbinta ba, tsayawa baki zlabarin irin tashin hankalin da muka shiga ba zai yiwu ba, domin kowa yasan mun yi rashin babban bango. Ya je wata Umra ne cikin Azumi yana dawowa da sati biyu Allah Ya aiko masa da ciwon ajali, wani zazzafan ciwon ciki ne ya 51 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri kwantar da shi, kwana biyu Allah Ya amshi abinsa. Babu wanda bai ji mutuwar nan ba cikin Zuri'ar, to amma babu yadda za muyi dole muka hakura muka dauki dangana da ta zamo mana dole, domin kowa dan haka ne. Bayan sadakar uku haka dangi suka hada mu suka shiga yi mana nasiha mu da yaran mu akan mu hada kanmu domin wannan shi ne babban burin dan 'uwansu, da wasu maganganu da suka dinga fada mana wanda mu kanmu bamu sansu ba, suka ce duk shi ne ya basu wasiyya idan ta Allah ta kasance gare shi to sai su sanar mana. Nan dai muka kara yin kuka da jin irin abubuwan da ya so ganin munyi. Tafiya ta soma tafiya babu wata matsala, domin manyan da suke tare damu suna dora mu akan hanya, haka aka ci gaba da gudanar da rayuwa tamkar mai gidan yana nan, sai dai abin da ba za a rasa ba. Haka manyan yaranmu suka tsare mana mutuncin mu, babu abninda muka nema muka rasa. F 52 furi'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri Lokacin da aka zo rabon gado al'amarin ba karmain bamu mamaki yayi ba na jin irin tarin dukiya da kadarorin da ya mutu ya bari, sai a sannanZuri'a ta kara tabbatarwa cewa Alh. Nasir ba karamin miloniya banc, tsayawa na fada miki irin tarin dukiyar da kowa ya samu bata lokaci na. Abin godiyar Allah Zumuncin mu haka ya ci gaba da dorewa ko da yaushe, sai dai abu daya ne ya soma bamu tangarda akai, shi ne Hameed. DOmin sam baya ji, tsabar gata da shagwaba da yake samu yasa ya fara kawo matsala, sai yanzu ne aka fara gano cewa yawan gatan da yake samu nes yasa ya dawo baya jin tsoron kowa. Hameed ya fara bawa kowa matsala da ya fara abu anyi masa fada sai ya hau yin fushi da mutum ko ma waye, ganin yawan fadan da Abban ku yake masa akan rashin jinsa yasa ya bar gidan ya koma gaban mahaifansa, nan suka gyara masa daki ya koma abinsa. Shiru kwana biyu Hameed ya diana shigowa gidan, Amminsa da kanta ta zo gidan wai ta zo bikon danta. Lokacin suna zaune a falo ita da Haj. Asiya wato mahaifiyar sa ta ce. 53 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Yaya na biyo sawun dana, kwana biyu naji shi dif, ke kuma ba ki dawo min da abina ba, ko nima har dani a cikin laifin? Don naga da ya ficc bai kara waiwayo ni ba". "Hmm! Ai kin san halin dan naki da taurin kai da kafiya, tun jiya nake cewa ya koma yana ce min wai shi takura masa ake yi". "Yaya takura kuma? Kin san halin Abban su dai, nasan akan yawon nan da ya fara ne suke samun takun saka". "To ai shima bai kama ta yana yi masa haka ba, nawa Hameed din yake da za ana matsa masa kamar wani mace?" Muryar da suka ji ta doki kunnen su nan take suka juya suka ga Alh. Jafar ne yake maganar, kai tsayc yanayin fuskar su ta sauya. Kallon junan su suka yi jin irin furucin da yayi, ko da yake Aisha ce kawai ta fi nuna mamakin saßanin ita Haj. Asiya. "Aisha kar ki damu, Hamced ya same ni da kansa ya ce ya gaji da zaman can ya dawo nan ya dan huta don ya bukaci can ya dawo, don haka ina son a bashi wannan damar domin da can shi ne ya nema muka bar shi ya dawo 54 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri hannur ku, amma tunda yanzu ga abin da yake so sai ku barshi yayi, da fatan ba za ku damu ba tunda yanzu ya fara girma bana tunanin za a hgana shi samun 'yancin sa ba". Aisha taji kalaman nasa sun yi mata wani iri, don bata taba zaton wannan furucin daga bakin babban yaya ba. Ta cc, "Shi kenan yaya Jafar, zamu bar shi mu gani ko kwana biyu zai hucc". "A'a ku barshi dai kawai, bana yin tunanin ma zai koma ma gaba daya". Gabanta ya fadi ta ce, "Yaya na ga kamar cikin bacin rai kake, ko ya fada máka anyi masa wani abu ne da ya 6ata maka rai?" Girgiza kai yayiya ce, "Ko kadan kada ki sa ma kanki damuwa, shi ne dai ya bukaci haka a ransa, ni kuma nake son nayi masa abin da yake so". "Shi kenan Yaya, babu laifi tunda ka ga hakan ya fi kuma mu ba zamu yi fishi da shi ba, muna nan muna jiran dawowar sa nasan da ba zai fushi da iyaycnsa ba". Tana gama fadin haka ta mike cikin sanyin jiki. 55 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Haj. Asiya ce ta rako ta har bakin get din gidan, ta cс. "Aisha kada ki nuna damuwar ki, naga kamar ranki bai so ba, ni na rasa me yasa Daddy ya fada miki wannan maganar, amma don Allah ki nuna komai ba komai ba, wannan sirrin mu ni da ke ba tun yau ba yake son Hameed ya dawo hannunsa, nayi-nayi ya fada min dalili amma yaki, dole na rabu da shi tunda haka ya faru ki bar shi mu zuba masa ido, nasan halin Hameed, muna nan zaune zai ce zai koma gidan su. Ran Aisha yayi fari domin jin kalaman da Haj. Asiya ta yi mata, bata san lokacin da ta saki murmushi ba, ta ce. "Yaya na gode sosai, insha Allahu nima zan bar wannan maganar cikin rai na, babu wanda zan tonawa ita". Nan dai suka yi sallama cikin dadin rai, amma dai cikin ran Aisha ta tafi a was-wasi na cewa to mene ne dalilin da yasa yaya Babba yake son Hameed ya bar gurimu ya dawo hannunsa bayan irin tarin zumuncin da suke yi da dan uwansa, domin kaf cikin DANGIN JUNAn ba sa taba yin abu kansu tsaye ba tare da 56 Zur'a Daya-I Sa'adaty Muhammad Waziri sun yi shawara da shi ba tsabar girman da suka bashi, haka kuma ya samo asali ne gurin mahaifinsu. To amma mai zai sa a fara samun baraka ta gurinsa yana matsayin shi ne babba cikin (family)? Dolc ne ta boye wannan matsalar, ba zata bayyanawa kowa ba, domin ta hango so da kaunar dansa a idanunsa wanda take tunanin matukar za a nuna ja akan abin da yake so to tabbas wata matsala na iya faruwa. Don haka duk ma mai zai faru ba zata taba bari Mustapha ya fuskanci komai ba cikin wannan lamarin, domin zai iya yin wani tunani da zai zo ya cutar da ZURI'Ar su, saboda haka ita kuma ba zata bari gakan ya faru ba cikin yardar Allah. Aziza ta shiga nuna damuwar ta ganin kwana blyu ba ta ganin Ya Hameed dinta, domin kwana blyu ba sa taßa 'yar tsamar da suke yi da juna. Kai tsaye gurin mahaifinta ta nufa ta ee, "Abba wai me yasa Ya lameed ya ki dawowa ne? Na je gidan Daddy na ee masa ya dawo ya ki, wallahi nima zan koma can kuma idan na tafi Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri ba zan taba dawowa ba sai ranar da ya dawo sannan zan dawo". Murmushi yayi ya cc, "Ammi na kenan, to ya zan yi da yayanki? Baya jin magana, na san fushi yayi da ni amma na san zai hucc, amma idan kinga za ki koma can to bi shi, nasan idan ya ganki wata kila ya yarda ya biyo ki ku dawo gida tare". Haba! Nan Aziza ta shiga murna da tsalle wai za ta koma gidan Daddy gurin Ya Hameed dinta. Da gudu ta nufi dakin Amminta ta na fada mata abin da Abba ya се. Itama murna ta nuna domin dai tasan irin shakuwar da ke tsakanin Hameed da Aziza ta tabbata daya ba zai iya rayujhwa ba tare da dan uwansa ba, dole ta san duk inda daya yaje sai dayan ya bishi. Nan da nan ta kwashi kayanta bai fi kala uku ba ta juya ta fice da gudu tana murna. Mustapha da Aisha suka bita da kallo suyna mata dariya, domin ganin irin murnar da take yi. Mustapha уа сс, "Aisha zan so naga kaunar nan da yaran nan sukc wa junan su ta 58 Zuri'a Daya-1 Sa'adntu Muhammad Waziri dore har zuwa girman su, domin sai na hada auren su cikin yardar Allah, saboda na yarda da kaunar da sukc wa junan su". Murmushi tayi ta cc, "Allah Ya nuna mana hakan, da kuwa an karfafa zumunci domin wannan shi ne burin Alh. Abbas kuma insha Allahu sai mun cika masa burinsa wanda yana kwance cikin Rabarinsa rahma zata na zuwar masa domin ZURI'A DAYA za su hadu su yi ta yada Zuri'u cikin yardar Allah". "Allah Ya amsa wannan fata naki, Ya hada kan ZURI'A dinmu ta zamo DAYA, yadda babu inda baraka za ta zo mana". "Ameen". Ta fada cikin farin ciki. "Ya Hamce! Ya Hameed!! Ya Hamced!!! Kana ina ne ina ta kwada maka kira ka ki ka amsa, Aziza ce fa". Da sauri ya fito daga shiryayyen dakinsa daga shi dogon wando da farar singilet a jikinsa, don kwanjinsa ya fara fitowa na matasan samari, lokacin shekarun sa sha shida. Farin ciki ne ya bayyana a fuskar su lokaicn da suka ga junaware hannu ya yi ta zo ta 59 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri fada jikinsa ya wani runtse ido na jin dadi, daga nan sai ya sakcta, ta сс. "Ya Hameed (guess what)?" Ya runtse ido ya bude, ya ce, "(No idea)" Murmushi tayi ta ce, "Baka ga me yake hannuna ba? To nima na gudo daga gida na biyo ka gidan Daddy, nima ba zan koma ba sai lokacin da zaka koma sai mu koma tare". Tsalle ya yi ya rike hannunta, ya ce, "Yauwa Aziza na, wallahi dama kullum tunaninki nake yi, sai naji kamar naje na sato ki ki dawo gidan Daddy mu zauna da ke, amma sai ina jin tsoron Abba kamar ba zai barni ba. Kin san Abba yana da fada da tsawa, ni kuma bana son fada shi yasa na dawo nan, da na fadawa Daddy ya cè na dawo ba zan koma ba". "Nima ba zan koma ba, a nan zamu yi ta zama ni da kai tunda Abba yana maka fada da tsawa, kuma ni bana son naga an yiwa Ya Hameed na tsawa da fada". Murya suka ji ance, "Yauwa yaran Daddy, ku shirya ku zo mu fita abinmu ajc a siyowa Aziza komai sabo, ba zata yi amfani da kayanta 60 furi'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri na gidan Abbanta ba, daki itama za a gyara mata irin na yayanta Hamecd". Juyowa tayi cikin farin ciki da ta ganc wanc yake maganar, Daddy dinsu nc. Da sauri ta jc ta rungume Daddy, ta dce. "Yauwa Daddy na, kaima baka so na koma ko?" ta cc. Cikin murmushi ya ce, "Iih Ammi na". Nan Haj. Asiya ta karaso gurin ckCKın fara'a "Aziza waio kema kin biyo yayanki kun yiwa Ammi da Abba yaji ko?" "Eh Mami ba zamu koma ba tunda Abba yana yiwa Ya Hameed dina tsawa da fafa, shi kuma baya so, ya ce ba zai koma ba, anan zamu yi ta zama tare ko Ya Hamced?" Daga mata kai yayi yana ta murmushi alamar ch haka nc. "Mami ina ne dakina da za a gyara min na kwana? Amma fa ni kadai ba zan kc kwana da su Muhammad ba tunda ni ce babba irin Ya Hamced". сс. Dariya suka saka gaba dayan su, Daddy ya 61 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Gaskiyar ki Ammi na, dole ne a baki daki a shirya miki shi sosai har sai ya fi na yayanki kyau". Murna da tsalle ta shiga yi tana cewa. "Ych! Daki na zai zama (very beutiful) ya fi na Ya Hameed". Ta shiga yi masa gwalo, nan da nan ya kufula doimin dama sun saba da hakan dama kwana biyu ba su tabа ba. Abinka da Aziza dama gata gwanar tsiwa da tsokana shi kuma Hameed da bi sanin ya fara girma haka ya biye mata suna ta guje-guje a cikin falon, iyayen na musu dariya. Nan dai ta samu ta buya jikin Daddy doinsu, babu yadda zai yi dole ya rabu da ita yana cewa zan kama ki ne za ki gane kuren ki". Haka dai rayuwar su ta ci gaba da gudana, tuni Aziza zamanta ya koma gidan su Hameed, kowa ya yi farin ciki da hakan. Sai dai ni ce kawai da naji raina bai so ba, ba don komai ba sai irin sake da nake hangowa a cikin gidan domin kaf cikin Zuri'ar mu babu gidan da Turanci ya ratsa da boko irin gidan Alh. Jafar, domin ganin yadda naga suke rayuwar su na 62 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri sakc. Sam ba ya tsawatar wa yara, yaro sai abin da ya ga dama shi zai yi ba kuma wanda ya isa ya hana shi. Na so na nuna ccwa Aziza ta dawo gida, amma gudun kada na haifar da wata matsala cikin ZURI'A sai na ja baki na nayi shiru, domin da na ce wani abu za a iya canza min abin da nakc nufi. Hakan yasa na yi wata hikima nayi shiru, sai dai abu daya na sa cikin raina zan saka idanu akan rayuwar Aziza a cikin gidan, domn ban so ta tana mace ta taso da tarbiyyar taurin kai. Haka na yi wata hikima da wayo da dabara, nakan shiga gidajen sauran yaranmu ba don komai ba sai don kada su gano cewa gidan Jafar kadai nake zuwa ayi tunanin da bana zuwa sai da jikata ta koma gidan sannan na tsiri zuwa, sai na mayar da abin cikin hikima yadda babu wani da zai zarge ni da wani tunani, yau naje gidan wannan gobe naje gidan wancan, hakan yasa na fara janyo Aziza jiki na. A duk ranar da naje gidan nasu nakan ganin abinda raina baya min dadi, domin sai ina ganin Hamced na yawan jan Aziza jikinsa, wata 63 Zuria Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri rana idan tana zaunc zai zagayo ta baya ya rungume ta a gaban kowa a cikin gida yake yі. Ranar nan na zo gidan nayi mata wayo na cc ta zo mujc gidan kawunta, nan nake mata fada cikin wayo ina ccwa. "Ki daina bari yayanki Hamced yana kwanciya a jikinki ko ya rungume ki haka kawai, domin yin hakan babu kyau. Amma idan wani guri yajc ya dade ba ki ganshi ba za ki iya yi masa oyoyo. Kał ki manta fa girma kike yi, wata rana Abbar ki ma da kansa za ki daina yi masa haka". Nan dai da dabara na ganar da ita, wata rana kuwa da na zo gidan da kaina naga tana cewa ya daina yi mata haka, bata so. A gaban iyayensa hkaa suka ji kunya, amma sai suka basar kamar ba su ji me take fada masa ba. Da kamar abin ya yi sauki, wata rana da naje gidan sai na ise shi da ita da Kannen sa а falo ya kwanta daga shi sal singileti da wando gajere, wal ya gaji suna yi masa tausa, ita kuma kadai ee mace eiki. 4 uri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri Nan na zo na tsawatar masa, nace kada ya sake ya Kara yin haka, wai bai san ya fara girma ba? Ina fadin hkaa karaf a kunnen Jafar ya shigo cikin falon, nan naga yanayin sa ya sauya. Nima sai nawa ya sauya, na cc. "Jafar, wai me yasa za kuna barin yaran nan haka ne ba za kuna nunawa Hameed girma yake ba?" Allah za a "Ayi hakuri Gwaggo, insha kiyaye. Kai Hameed maza tashi ka bar gurin nan". Ransa 6ace ya bar gurin yana kumburo baki abinsa, jikina babu dadi muka gaisa ban wani jima ba na fito na tafi gidan Aisha. Nan na labarta mata da abin da yake faruwa, nan ta kwantar min da hankali, ta ce. "Ummah kada ki ji komai, na tabbata Yaya Asiya za ta lura da su, cikin ikon Allah Zai kare komai". Duk irin nusarwar da take min na jita ne kawai, amma bana jin jikina da zuciyata sun amince min. 65 Zuri'a Daya-I sa'adatu Muhammad Waziri Kullum hankalina ba ya kwanciya da tunanin haka nakc kwana nake tashi, ganin rai na ya kasa kwanciya yasa na tari Mustapha da maganar, nan ya kwantar min da zuciyata da kuma nuna min matukar muka nemi Aziza ta dawo gida za su zargi wani abu, amma shi da kansa zai je ya kwaso su tunda dama nasa ne. Jin haka sai raina ya yi sanyi domin na tabbatar idan yaran a gurin Aisha suke babu abin da zai daga min hankali, don nasan tana da kula duk da kuwa ba yara ne a gabanta ba amma tyayi na riko na gani. A cikin kwanaki uku da muka yi maganar sai ga Aziza da Hameed sun dawo gida gurin Aisha, sai a lokacin hankalina ya kwanta domin nasan dole ne Aisha zata na kula da su duk da kuwa irin tsohon cikin da take da shi. Tun sanda suka dawo Hamced ya dinga jinsa duk a takurc, ko me yake yi sai yana ji kamar ana takura masa. Haka ya koma shan ruwan tsuntsayc, yau yana nan gobe yana can, haka ya sabar ma Aziza yau idan bata ganshi ba gobe zata ganshi. Hikimar sa nana ko zata koma ta bishi amma sai ya ga ta ki komawa, dole sai 66 Zuri'a Daya-l Sa'adatu Muhammad Waziri yakc dawowa, domin sam beya sakcwa idan yana gidan domin baya samun dama yana hada jikinsa da nata. Ana cikin wannan halin ne Allah Ya sauke ta lafiya, ta haifo ki, kyakkyawa da ke kamar 'yar uwarki Aziza, domin tun zuwanki duniya kowa ya zo ya ganki sai ya ce kina kama da Aziza, kamar daga jikinta ki ka fito don kama. Haba! Murna gurinmu babu misaltuwa, nan muka godewa Allah da zuwanki duniya". Haana tayi murmushi ta ce, "Kai Granny dama dani? A raina na zata wani ne ko wata, amma gaskiya kin iya labari". Murmushi tayi ta ci gfaba da cewa, "Aziza ta shiga murna da tsalle wai itama tanyi kanwa su zamo su biyu, ta daina zuwa gurin kowa tunda ga shi itama an yi mata baby girl abin da take so kenan dama. Tsananin kaunar da Aziza take nuna miki ya yi yawa, domin bata barin kowa ya dauke ki sai ita, don sabod ake ma sam bata son zuwa makaranta, kullum sai anyi da gaske sannan take tafiya. 67 Zuri'a Daya-I _Sa'adatu Muhammad Waziri Haka Hameed shi ma ya shiga nuna miki Kauna, don haka kowa sai da ya nuna farin cikin zuwan ki duniya. Ranar suna aka rada miki sunana Raihanatu, domin dama burin Mustapha kenan ya haihu ya yi min takwara. Tun bayan sunanki da sati Aziza ce da kanta ta ce ita zata zaba miki sunan da za ana kiranki, ita ce ta zaba miki suna Haana, madadin ana kiran ki Raihanatu. Kowa yaji dadin sunan, haka kuwa kowa yake kiran ki har yanzu. Tunda aka haife ki Aziza bata kara yarda ta je gidan kowa ba, haka Hameed yayi zuciya tun da ya koma gida bata yarda ta bishi ba, dalilin haka yayi fishi ya daina zuwa gidan gaba daya. Sai a lokacin ne hankali na ya yi matukar kwanciya tun da Hamced ya fita daga cikin rayuwar Aziza, ni dai ban san meye dalili ba haka kawai nakc jin ban son naga tasu ta zo daya, saboda wasu dalilai da yadda nake jin wani abu a cikin rai na. Haka kullum zai zo yana ta lallaba ta akan ta dawo gidansu don yafi son yana ganinta 68 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri kullum a kusa da shi, shi idan yana nan shi sam a takure yake saboda haka ta bar nan su koma gida. Ta ki yarda ta ce shi ya dawo dai ita ba zata iya tafiya ta bar Haana dinta ba, dole ya hakura ya rabu da ita. Cikin watanni biyu zuwa bakwai sai da muka samu karuwar haihuwar yara mata har biyar, Haj. Bara'tu ta haifi Fadila, Asiya Haaya, Aisha ke, Maryam Rauda, Habiba matar Mukhtar ta haifi Sameeha. Mun yi farin ciki Zuri'a sai kara habaka take, sai ya kasance gida dai dai ne a wannan lokacin ake haifar da namiji. Shekarun ki biyu da watanni a duniya, lokacin ita kuma Aziza ta shekara sha uku cif, kasancewar ta mai garin jiki ga kuma jin dadi da kwanciyar hankali babu abinda yake damunta, nan da nan ta fara zama budurwa, haka nan kyanta ya sake bayyana, kowa yana yaba kyawunta da surar da take da shi. Loakcin shi kuma Hameed yana da shekaru sha tara domin anyi-anyi da shi a fitar dashi waje karatu ya ki wai shi a nan zai yi wai 69 Zuri'a Daya-1 _Sa'adatu Muhammad Waziri don ya gama karatun sa ya auri Aziza, domin shi ya ce ita zai aura. Haka kowa ya yi murna domin dama kowa ya saka ran haka, ba don komai ba sai don sanin shakuwar su da irin muna kaunar da ya yi mata tun ranar da aka haife ta haka dama iyayen suka kulle cewa za a hada su aure idan har sun girma. Tun lokacin da Aziza ta fara zama budurwa shi kenan Hamced yake kiranta da mata, baya jin kunya a gaban kowa da haka yake kiranta kasancewar ita din mai kunya ce a duk lokacin da ta ganshi cikin jama'a sai tana buya don bata so yana sa ta jin kunya. Haka zai taso wata rana haka zai ke rikota yana son hada ta da jikinsa, ita kuma sai tana

Chapter 3 of 9