Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 9
kukan ba don komai ba sai don tausayin Abba, yadda yą gama yarda da shi amma ace shi ne ya yi sanadin jefa rayuwar 'yarsa cikin wannan halin. Tabbas yasan ba zai taba gafarta masa ba har zuwa karashen rayuwar sa. ya ce. Bayan sun dan nutsa sai Uncle Mukhtar "Yaya Mustapha to me yasa tun farkon zuwan mu nan basu yi mata wankin ciki ba? Ai da tuni an zubar da shi. To yanzu meye abin yi don ba zamu barta da cikin wani ba wanda bamu san asalin sa ba". Alh. Jafar da Asiya hade da dansu suka hada idanun su guri guda cikin rudani. Cikin alhini Mustapha ya ce, "Mukhtar nima nayi musu wannan tambayar, sun ce min duk abin da nake tunani sai da suka yi a farko, suka ce idan an kawo yara da hakan ta faru da su 144 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri shi ne abin da suke fara yi. Mu aynzu babu abinda za muce sai yadda Allah Ya yi da ita". "Yaya mu fitar da cikin nan daga jikin ta, shi ne kwanciyar hankalin mu". "Mukhtar meye ribar mu na yin haka? Idan mun kashe rai me za muje mu ce da Allah tunda Shi ne Ya aiko hakan ta faru to da sanin Sa, sai mu tsaya mu ga yadda Zai canza mana. Amma ni dai da hankalina ba zan ce a cire cikin nan ba, idan kuma an samu akasi an rasa ranta da abin da yake cikin ta ka ga mun yi laifi biyu, dole haka zamu hakura mu karfi kaddara. Idan kana jin tsoron surutun jama'a to kowa yasan ba rashin tarbiyya bane ya kaita taje tayi cikin, cikin karfi aka hakke mata. Haka idan kana tunanin cikin ZURI'A kake tunanin ayi mana gori, to duk ZURI'A DAYA muke, duk wanda yake cikinta abin nan ya shafe shi. Don haka mu dai mu yi fatan Allah Ya raba ta da shi lafiya, su kuma wanda suka aikata ko ya aikata gashi nan ga duniyar, Allah Yana gani, Ya fimu sanin me Ya tanadar masa, ko iya hakkin mu ma ya ishe shi kafin aje gare ta". 145 Zuri'a Daya-! Sa'adatu Muhammad Waziri Gaba daya duk wanda yake gurin babu wanda jikinsa bai yi sanyi ba, domin kalaman sa sun taba zuciyar kowa a gurin. Gumi ne ya keto a jikin Alh. Jafar, domin bashi da wata kalma da zai iya fada sai cewa yake. "Allah Ya kyauta". Haj. Asiya kuwa ban da kuka babu abin da take yi, haka tayi sallama da mu ta ce ba zata iya tsayawa a gurin nan ba, da tasan haka zata zo taji wannan bakin labarin da bata zo ba. Babu wanda ya iya cewa da ita komai, haka ta fice tana kuka, kowa da abin da yake ji cikin ransa. Hameed ne ya mike daga inda yake ya nufo kan gadon da take kwance hawaye na zuba a fuskar sa, ya zo kanta ya tsaya ya sa hannu ya shafa kanta, baccinta take abinta, nan ya shiga kuka mai tsuma rai domin ya kasa ya furta komai banda kuka. Na karaso gurin na dafa kafadar sa, na ce. "Abdul babu abin da zamu yiwa Aziza sai addu'ar Allah Ya raba ta lafiya da abin da yake jikinta, tawakkali shi ne abin yi a gare mu ba 146 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri kuka ba tun da abin haka yake tun ran gini tun ran zane". Daga kai ya yi bai iya cewa komai ba banda tsabar malala da hawaye suke a fuskar sa. syb Aisha na gefe tayi jigum bata iya wani kwakkwaran motsi tsabar kaduwa da jin abin da ya faru da diyar ta, sam ta kasa yin kukan sai na zuci da take yi sv .30 к Наmеed na mikewa zai fita sai Aziza ta farka daga baccin da take yiutana farkawa sunan Abbata fararkira, otzil ey aan ab πενί si sniDa sauri ya kárasa gurinta yana tambayar larmedako so? ko me yake mata ciwo2slal ccad Jin nuryar Aziza yása Hameed ya kame a Isaye, watonlyay yiN mutuwartsaye. Nan take zuciyar sästaoshigar bugawaakai-akai, domin tsoro ne yalgama kama shiusb sER падоя вов! "Abba kai na,skainag zais cire, rzafivyake min, wayyo ciwo abba, don Alláhrikemin kaina zai fashoAbinida dake fadi kenansbsl BT Da sauri Abban ya rike mata kanokamar yadda ta nemayya shigaitofa matá addu'a, nan da nan ta soma lumshe ido alamui ta fara jin yana lafa mata. 201 147 Zuri'a Daya-i Sa'adatu Muhammad Waziri Daga masa hannu tayi alamun ya fara saki, ya ce. "Ya daina miki ciwon ko?" "Eh".Ta fada. Haka ta dinga bin kowa da kallo daya bayan daya, ta ga duk dinsu cikin tashin hankali, ta so tayi magana sai ta fasa. Can ta hangi Hameed ya ba da baya ya tsaya kyam, sai hankalinta ya yi wajen sa, ta се. "Abba wancan wane ya tsaya haka?" Nan da nan ya kirkiro murmushi ya ce, "Yayanki nc, yana ta zuwa baya ganin ki kina ta bacci lokacin. Hameed, zo ga kanwar ka tana tambayar ka, yau da rabon za ku gaisa". Ji yayi kamar an dauki guduma an doka masa a tsakiyar kansa, nan take yaji kafar sa tana kokarin kasa daukar ganganr jikinsa, ya ji juyawar ma tana gagarar sa. "Hameed!". Ta fada hade da runtse idanunta na dan waşu lokaci. Damm! Yaji hantar sa tayi rawa, ya yi kamar ya furtsa da gudu. 148 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri Sunan ta ci gaba da maimaitawa, ko yana jinta. Jin yawan ambaton sunansa ya kara tsinkewa, gabansa ya ci gaba da dakan uku-uku, haka ma Alh. Jafar shima rudewa yayi dolc kasa komai yayi yana jiran ya ga me ya yi saura? Sai dai cikin ransa yana ta kiran sunan Allah. Runtse idanu Hameed ya yi kawai ya saddakar, ya juyo ya nufo gurin lokacin ita kuma hankalinta ya fisga zuwa wani guri. Yana zuwa kusa da gadon ta juyo, tana ganinsa ta ji wani irin mugun firgita ta sosai, nan da nan ta shiga saukar numfashi akai-akai, ta saki baki hade da tsananin tsoro da ya mamaye fuskar ta. Wata muguwar kara ta da kururuwa ta sa, nan da nan ta rungume Abbanta tana kankame shi jikinta na rawa, nan take hankalin kowa ya tashi. Nan take Alh. Jafar ya dakawa Hamced tsawa akan ya zo ya fice daga dakin tun da bata son ganin shi. Mustapha ya ce, "Haba Yaya, meye na daukar zafi haka? Ammi na ba wani bane fa yayanki Hameed ne, bude idanunki ki ganshi". 149 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Girgiza kai tayi ta kara rungume shi tana kuka, jikin kow aya yi sanyi, nan kowa ya shiga zancen zuciya yana mamakin wannan al'amarin. Hamced ne ya yi karfin halil ya zo da sauri ya kama hannunta ya dago ta yana kuka yana cewa. "Aziza na kalle ni sosai ki gani, ni ne yayа Hameed dinki ba wani bane, ki cire idonki ki kalle ni sosai don ki shaida ni". Yanayin kukan da yake da irin nacin da yake akan Aziza ta dago ta kalle shi ta ki, hakan sai yasa kowa yaji tausayin sa. Da kyar ya samu ta dago ta kalle shi, amma cikin rudani, tana kallon sa tana ajje numfashi da sauri irin na razana. Da sauri ta fisge hannunta daga nashi ta koma jikin babanta tana cewa. "Abba bana son shi, bana son shi, Abba (please) ya tashi bana son shi". Tana fada idanunta a rufe. Nan ta shiga kurma ihu dole Alh. Jafar yasa sai da ya fice sannan aka samu tayi shiru. Ana cikin haka sai ga (Nurses) guda biyu sun shigo dakin cikin sauri don suga me yake 150 2 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri faruwa, nan daya ta tsaya tayi ta koma taje ta kira likita. Nan da nan sai gasu su biyu, nan suka zo suka ganta a dimauce, suka nemi a basu guri su duba ta, haka suka fito jiki a sanyaye muna ta jima me hakan yake ufi? Sun dan dauki lokaci zuwa can suka fito, Mustapha kawai suka nema akan yaje suna son ganinsa, har Alh. Jafar zai bisu suka ce ya yi hakuri shi kadai suke bukatar gani. Bai yi musu ba ya barsu suka tafi tare abin su, haka suka shiga (offuce) abinsu. Hankalin Alh. Jafar ya yi mugun tashi, domin bai san me za su frada masa ba, amma haka ya yi kokarin danne tashin hankalin sa don kada a gane yana cikin rudani a zargi wani abin. Guri suka bawa Mustapha ya zauna, nan daya daga cikin su ya сс. "Alh. Mustapha don Allah muna son yi maka wasu tambayoyi duk da kuwa ba aikin mu bane yin bincike". "Ina jinka Doctor, wani abu ku ke son sani a garc ni?" 151 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri "Eh, akan ma'salar yarinyar gurinka ne, domin yadda binciken da gwajin da muka yi ya nuna mana tunanin ta yana son dawowa a kowane irin lokaci, domin a yanzu wani abu ta gani da ya razana ta yake son tuno mata abin da ya faru da ita". ya ce. Wani farin ciki ne ya bayyana a fuskar sa, "Kai Allah na gode Maka". "A cikn ku wane bakon fuskar da ta gani ya ta da mana da hankali wanda ganinsa ne yasa wurin ma'adanar tunaninta ya dan soma motsawa, sannan meye dangantakar sa da ita?" Shiru Mustapha ya yi yana musu wani irin kallo na rashin fahimta, can ya ce. "Wai me kuke magana akai ne?" "Alh. Mustapha ka kwantar da hankalin ka, muna son gano wani abu ne, amma don Allah kayi hakuri". "Yayanta ta gani ta razana". "Ba kwa yin zargin cewa ko shi ne ya yi mata wannan aika-aikar? Domin ba karamin razana tayi ba da ta ganshi wanda hakan yasa (memory) dinta ya kusa dawowa yadda yake". 152 Zuri'a Daya-l Sa'adatu Muhammad Waziri Cikin zafin nama ya daki tcbirin gaban Dr. Sa'id yana mai huci, ya cс. "Kaga Doctor ka tsaya iya aikin ka, wannan ai cin fuska kakc son yi min, kasan yadda muke da uban yaron nan kuwa? Ubanmu daya da shi, ZURI'A DAYA mukc, me zai kai shi ya yi mana wannan illar? Sam kada na kara jin wannan furucin a bakin ka gudun kada ka zo ka jefa zumuncin mu cikin matsala". "(Relax) Ranka ya dade, duk abin bai kai ga daga hankali haka ba". Dr. Umar ya ce. "Haba Doctor, maganar tashi ce bata yi min dadi ba, me yasa zai sa zargi akan dan dan'uwana? Allah Ya kiyaye hakan ma ya faru a cikin mu". "Amcen". Dr. Sa'id ya fada, kana ya ci gaba da cewa, "Mu ma bama fatan hakan a garc ku, abin da aikin mu ya nuna mana shi ne yasa har muka yi maka wannan tambayar, amma don Allah kayi hakuri zamu yi abin da ya dacc akai, za muyi wani gwaji don mu sake dubawa ko dai kwakwalwar ta ne ya dan motsa yasa hakan ya faru. Amma don Allah kayi hakuri don naga ka 153 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri fusata sosai, ni kuma na fadi haka ne ba don wanzi abu ba". "Shi kenan Doctor naji, ya wuce, Allah Ya taimaka, da fatan zan iya tafiya ko?" "Za ka iya tafiya, amma yanzu ba ma son kowa ya shiga gurinta domin muna son gwada wani abu a tare da ita na zahiri, don mu gane me hakan yake nufi? Don haka klu jira mu". "Babu laifi". Ya fada a lokacin da yake kokarin tashi daga inda yake zaune, shi ya fara fita sannan suka tsaya suna dan tattaunawa. Haka ya zo ya same mu tsaye bakin dakin yanayin sa duk ya sauya, Alh. Jafar ne ya yi saurin tare shi yana tambayar sa me suka ce da shi? Sakin fuska ya yi ya ce, "Cewa suka yi suna son duba kwakwalwar ta su gani, domin ihun da tayi ya yi yawa, don su gano ko wani abu ya faru da ita". Sakn ajiyar zuciya yayi, ya cc, "Mun gode Allah, Allah dai Ya bata lafiya don girman Manzon mu". Duk gurin aka ce, "Amcen". 154 : Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Muna tsaye a gurin sai ga likitocn nan s'ın dawo, wannan karon har da wasu samari su uku, babu wanda suka yiwa magana, suna zuwa suka tsaya sai suka tura wani daga cikin matasan nan guda uku cikin dakin da Aziza take. Yana shiga bai fi minti uku ba sai muka jiyo Aziza na ihu kamar yadda tayi lokacin da ta ga Hameed, jin haka sai suka sake tura mutum biyun nan, nan ma dai wani ihun ta shiga saki babu kakkautawa tana cewa. "Ban son ganin ku, bana son ganin shi, Abba! Abba!!". Cikin gaggawa likitocin suka bude kofar sai ga mata sannan sun fito, su kuma sai suka shiga ciki, wannan karon har damu domin cewa suka yi muma mu shiga. Sai da muka shiga Aziza na ganin mu ta fito daga inda take 6uya da sauri ta zo ta rungumc Abbanta tana ccwa. "Abba mc yasa ka bari suka shigo? Tsoron su nakc ji, Abba don Allah kada ka tafi ka barni su kara shigowa". 155 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Likitocin cikin hikima da dabara suka samu suka yi mata allurar bacci, nan da nan bacci ya dauke ta, nan suka nemi a basu guri. Sun jima tarc da ita sannan suka fito gaba daya iyayen mazan suka nema su biyo su, haka suka je, Alh. Jafar da Mukhtar, sai Abban ku duka suka dunguma. "Alh. Mustapha ina me neman afuwar ka dangane da furucin da nayi maka dazu". Cewar Dr. Sa'id. Ya cc, "Babu komai Doctor, na fuskanta yanayin aiki ne, kuma komai ya wuce". "Madallah na gode, sai magana ta gaba, yadda muka bincika a zahiri da kuma na'ura mai kwakwalwa ya nuna mana cewa Aziza a yanzu tana tsoron dukkan wani da namiji matashi wanda hakan ya nuna cewa su ne suka yi mata wannan ta'asa. Tun da hakan ya faru bata taba razana irin na yau ba, domin ganin matasan da tayi hakan ne ya razana ta har take son tuno wani abu da ya faru da ita a baya. Don haka muddin zata na ganinsu to zata ci gaba da zarana wanda cikin biyu dole ayi daya, ko dai (memory) dinta ya 156 Zuri'a Daya-1 Saladatu Muhammad Waziri dawo ko kuma wata matsala ta faru da kwakwalwar ta, Allah Ya kiyaye don ba ma fatan haka a gare ta". Gaba daya suka ce, "Ameen". Dr. Umar ya kara da cewa, "Don haka dolc a kiyaye sanin su wane za su dinga zuwa dubiya gurinta, domin gudun afkuwar wani tashin hankali. Tabbas tun da muke bamu taba samun (patient) mai irin wnanan lalurar ba, sai dai mun taba samun wata wadda ita kuma maza ne gaba daya bata son gani daga babba har yaro, tana ganin mun zo duba ta zata shiga ihu da razana, dole muka hakura sai 'yan uwanta mata ne suka shiga duba ta. Sai ita kuma wannan nata daban ne, matasa take jin tsoro, kasan abin na Allah kowa da irin nashi lalurar". Alh. Jafar ya ce, "Gaskiya ne likita, mun gode, kuma insha allah zamu kyaye mu saka ido, kuma insha Allah ba zamu sake barin Hameed ya zo nan asibitin ba har sai ta warke sosai". "Shi kenan Alhaji, ba ma shi kadai ba duk wani matashi da zai sa idan ta gashi zai razana ta bama fata ya zo gurinta, domin hatsarin da yake 157 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri cikin al'amarin, nasara ce da kuma rashin ta, kaga abin ya zamo (fifty-fifty)". Mukhtar yа сс, "Hаkа ne likita, amma ni ina da magana da Yaya zai yarda da an raba yarinyar nan da cikin da ke jikinta, kaga sai taji da daya, amma ace ga wannan ga wannan abin ai ya yi mata yawa, yarinya karama da ita, shakrunta fa sha hudu zuwa sha biyar har yaushe zata iya jure rainon ciki?" Mustapha ya dafa Mukhtar ya ce, "Mukhtar ka saki ranka, ka dauka wannan duk yana cikin jarrabawar rayuwar Aziza da mu iyayenta baki daya, don haka Allah Yasan abin da bamu sani ba, don haka bamu san dalilin faruwar hakan ba, sai dai mu dauki yarda da kaddarar Sa mu jira muga ikon Allah. Murnar mu daya da ba ita ce taje yawon banza ba ta dauko shi, karfi aka nuna mata". Jikin Alh. Jafar ya yi matukar sanyi, ya kasa cewa komai, banda idanu da kunne da ya zuba babu abin da ya iya tofawa, sai fama cewa Allah Ya kiyaye Ya bata lafiya dai. Nan suka gama abin da ya kaisu, sannan suka fito suka dawo gurinmu. Alh. Jafar bai jima 158 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri ba a gurin ya ce zai tafi, nan ya tambayi ina Hameed? Nan muka ce tun dazu ya yi nan bai dawo ba. Sallama ya yi damu ya bi bayansa, haka nan Abban ku suka sanar mana duk yadda suka yi da likitocin, mu dai addu'a muka yi akan Allah Ya fitar damu cikin wannan hali da muke. Alh. Jafar zaune yake cikin motar sa shi kadai yana faman sauke numfashi da ajiyаr zuciya, domın dai yana cikin (tention) ba kin Karawa, Allah Ne ya taimake shi Ya rufa masa asiri, amma ba don haka ba yau d aya kwashi borin kunyar sa. Tabbas yau ya so ya shiga cikin tsaka mai wuta, amma sai gashi Allah Ya rufa masa asiri, abin da yake tunanin zai faru Allah Ya kiyaye. Sai da ya dan samu nutsuwa sannan ya fara tunann matar sa da Hameed, ina suka shiga? Nan da nan ya fito cikin motar ya shiga dubсdube babu wanda ya gani cikin su, dolc ya hakura ya dawo ya shiga motar sa ya koma gida. A falo ya iske Haj. Asiya tayi shiru abinta, daga ganin idanunta kasan ta sha kuka na kin karawa. 159 Zuri'a Daya-l Sa'adatu Muhammad Waziri "Ina Hameed yake?" Ya jcfo mata wata tambaya cikin kaushin murya, don a fusace yake. Daga kai tayi ta kalle shi, cikin sanyin jiki ta ce. "Ban gane wacce irin tambaya kake min ba, awa ta nawa da bairn ku tare zaka zo kana yi min wnanas tambayar?" "Ya baro ni a can nima, nayi tunanin ko ya gamu da ke ne kun taho gida. Ina zaton tunda motar haya ya biyo yanzu za ki ganshi ya shigo cikin gidan". Yana gama fadin haka ya cire babbar rigar sa ya ajje gefe, ya samu guri ya zauna. Kallo daya zaka yi masa kasan ba ya cikin nutsuwa. "Daddy, yanzu wacce mafita ka aje mana a cikin gidan nan game da wani sabon tashin hankalin da ya same mu? Kasan dai yanzu dole kayi wani abu akan wannan al'amarin, don abin yanzu ya zarce dukkan tunanin mu". Cikin kaushin murya ya ce, "Mc kikc so nayi bayan wanda nayi tun farko? Ai magana ta riga ta wuce, fatan mu Allah Ya yayewa yarinyar nan abin da ba zata iya ba". 160 Zuri'a Daya-1 fa'adatu Muhammad Waziri "Kai Alhaji ka ji tsoron Allah kuma ka dinga tausayi da sa tsoron Allah a zuciyar ka, ai kuwa duk mai tausayi da imani dole ne ya tausayawa yarinyar nan irin halin da take ciki, daga wannan sai wannan, bata fita daga wannan halin ba sai gashi tana fadawa cikin wani. Ni dai shawara ta dole nc mu sanar da iyaycn yarinyar nan cewa ga wanda ya jefa 'yarsu cikin wannan gararin, tabbas idan muka yi haka zamu samu saukin tsangwamar da zamu fuskanta, amma muddin muka bar wannan al'amarin ran da duk asiri ya tonu to zamu fi kowa jin kunya a cikin ZURI'A, domin wasu sai sunce mu ne muka sa shi yaje ya yi mata hakan. Ina ganin gwara tun wuri mu yiwa tufkar hanci". Cikin zafin rai da daga murya sama ya ce. "Asiya ban san wanc irin gaddama da taurin kan da ke gare ki ba, sau nawa zan fada miki maganar nan da ki rufc ta amma sai kina dawo da abin baya? Don haka ki sani baki isa ki sa ni abin da ban yi niyya ba, ya kamata ki saurara min. Wannan ita ce rana ta karshe da za ki sake min irin wannan batun, kin dai ji na fada miki'. 161 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Yana gama fadin haka yasa kai ya fice daga falon cikin fushi da 6acin rai. Binsa tayi da kallon takaici, nan take hawayc ya zubo a cikin idanunta, a bayyanc ta cc. "Jafar ka cika marar tausayi da son zuciya, kuma insha Allah sai Ya bayyana gaskiya komai dafen dadewa, kuma matukar ni cc na haifi Abdulhamced sai na sa shi yin abin da ranka baya so, naga yadda zaka yi dani". Tana gama fadin haka ta samu guri ta zauna tayi tagumi abin yana matukar ta da mata rai, domin har yanzu ta kasa samun dukkan farin ciki a wannan ranar tun da ta samu labarin cewa Aziza na dauke da ciki". A can cikin daki Alh. Jafar ya kasa zaune ya lkasa tsayc, haka ya dinga shiga da fice don jiran dawowar Hameed amma yaji shiru, gashi har misalin karfe goma na dare babu shi babu labarin sa. Nan hankalin sa ya kara tashi, wannan karon har kofar fakinsa yasa mai gadi ya zo ya jijjige, tunanin sa yana ciki zai yi musu irin na rannan, amma da aka cire kofar sai aka ga 162 Zuri'a Doya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri dakin wayam, babu kowa a ciki, baka ya kara jcfa shi cikin damuwa. Har gari ya wayc babu Ilameed babu wanda aka samu ya zo da labarin ya ganshi, kwana daya, kwana biyu babu Hamced babu labarin sa, pan hankalin ZURI'A ya tashi saboda da kansa ya shiga fada ma 'yan uwansa bai ga Hameed ya dawo ba, yau kwana uku. Kowa yaji abin sai kansa ya daure, domin gakan bata taba faruwa da shi ba. Nan hankalin kow aya tashi, haka aka shiga cikiyar sa har gidan (radio) amma babu wani labari da aka samu a wannan lokacin. Kallo daya zaka yiwa Alh. Jafar kasan yana cikin tashin hankali mara misaltuwa. Ganin yadda yayi mugun tashin hankalinsa akan rashin ganin dansa Haj. Asiya tana kallon sa amma ita abin ko a jikinta don abin da ta fada masa cewa tayi ita bata sin ta sake ganin Hamced a gabanta domin tana ganinsa jefa ta cikin tashin hankali da damuwa yake yi, yaje can ya karata. Tun da ta fada masa haka ya shiga fushi da ita, hade da fada mata cewa duk abin da ya 163 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri facu da dansa ba zai taba yafe mata ba tun da baki tayi masa. Hakan yasa ya dauke mata wuta, sam ba ya sauraronta, haka duk ya bi ya dugunzuma, ya hana ma kansa kwanciyar hankali. Tsananin damuwar da yake ciki yasa ko aiki ya ki fitayana ta yawon neman labarin inda dansa ya shiga, amma shiru babu labarin sa. * * Yadda al'amarin yake, tun sanda Hameed ya fito daga cikin asibitin hankalin sa ya yi mugun tashi jin labarin Azizan sa na dauke da cikin sa, hankalin sa ya yi mugun tashi yaji gaba daya duniyar tayi masa zafi, yaji sam baya sha'awar son ci gaba da rayuwar duniyar gaba daya. Haka ya dinga jin kamar bashi da kowa, bashi da komai a duniya, haka ya dinga jin yaje ya yi rayuwar sa shi kadai babu kowa a cikin rayuwar sa. Haka ya fito bai san inda zai jc ba, sai dai ko kadan bai sa ma ransa ccwa zai koma gida ba, domin bai ga wani amfani da zai sake a rayuwar sa ba tunda har ya jefa Azizan sa cikin wannan 164 Zuri'a Daya-I sa'adatu Muhammad Waziri bala'in na datse mata dukkan farin cikin rayuwar ta da burinta, ya kuma illata rayuwarta gaba daya don ya kassara ta baki daya. KUNAR ZUCI da shi ya wuni a wannan ranar, ayan ya bar cikin asibitin, haka yana lafiya daga nan sai ya tafi can, don haka ya yanke ma zuciyar sa cewa dole ne yaje ya nemi kotun Musulunci ya gabatar da laifin sa don a hukunta shi. Bai san ina zai je ba domin bai san ina zai samu kotun ba, don haka da yaga dare ya yi bai yi nasarar abin da yake nema ba, wani masallaci ya samu ya kwnata a gurin yayi barci a can Hausawar Sabon titi, sa safe ne ya samu limamin masallacin da bayan sallar asuba. Bayani ya yi masa sosai, bai 6oye masa komai ba, ya gaya masa irin halin taskun da yake ciki, da kuma abin da yake so ayi masa na hakkin Allah. Jikin liman ya yi mkatukar sanyi, ya yi matukar tausaya masa tare da jinjina irin karfin imanin da yake da shi, nan ya kara tabbatarvva da cewa yin hakan ba halinsa bane, iftila'i ne da rudin zuciya da kuma sharrifn shaidan. 165 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Nan ya ce, "Yaro lallai kam kana cikin tashin hankali da rudin rayuwa, hakika wannan shi ne tsoron Allah na hakika, tabbas da za a dinga samun mutane masu irin wannan laifin suna bayyana kansu ana fitar musu hakkin Allah akan su to da tuni duniyar tana nan zaune lafiya. To amma ina! kullum abubuwan sai dada tabarbarewa suke yi. Dama dole ka shiga damuwa da rashin samun nutsuwa cikin ranka, domin agbin da kayi ba karami bane, sannan duk wanda yaji me ya faru sai ya yi tsinuwa ko la'antar wand ayayi mata wannan al'amarimka ga kuwa nutsuwa a gurinka ba zata taba samuwa ba tunda baka bayyana cewa kaine ba a yafe maka. Amma tunda kayi nadama ka dage akan kana so a fitar da hakkin Allah akan ka, idan yaso daga baya zaka koma ka bayyana gaskiya, to zan taimaka maka, kuma na tabbata idan an fitar maka da hakkin Allah zaka samu nutsuwa har cikin zuciyar ka. Kuma Allah Zai taimaka maka ta sauran hanyoyin da zaka cira, amma ina son ka kudura a ranka cewa ba zaka kuma kusantar inda zina take ba. 166 Zuri'a Daya-I sa'adatu Muhammad Waziri Ka duba ka ganka shekarun ka basu fi ashirin ba zuwa da daya, amma ka jefa kanka cikin tashin hankali haka". Hawaye ne ya shiga zubowa a fuskar sa, ya ce. "Baba ina cikin wani irin rudu da damuwar da ban taba tunanin wani cikin rayuwar nan ya shiga irinta ba, wallahi Baba na yi maka alkawari ba zan kuma yin zina ba har na koma ga mahalicci na". "Shi kenan Abdulhameed, insha Allahu zan taimaka maka aa fitar da hakkin Allah akan ka, tunda hakan ya faru, amma kasan dole sai munje kotun tare sun yi maka tambayoyi sannan su aiwatar maka". Murna ce ta bayyana a fuskar Hameed, ya tashi ya rungume Malam Liman yana kuka, nan take tausayin Hameed da kaunar sa suka cika ransa, nan ya tambaye shi akan ya fada masa cewa ina iyayen sa suke da zama? Ya kada harshe ya ce, "Baba kamar yadda na fada maka cewa mahaifina baya goyon bayan da a hukuta ni, don haka yasa na na gudo nan har Allah Ya hada mu da kai, don haka ka wakilci 167 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri iyayc na ka zama cewa kai yayan Bababane ne na zo maga da wannan labarin shi ne ka kawo ni nan don ayi min bulalar". Liman da kansa ya bashi masauki a a gidan sa cikin dakin yaransa manya guda uku, ya hada su guri daya shi kuma ya bashi daki daya don ya samu ya sake sosai. Kwanan sa biyu a gidan ranar nan sun dawo daga kotun

Chapter 7 of 9