Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
9 / 9
'yan bori Mustapha ya yi da ya gama fahimtar bayanin da Hameed yake masa, nan take wasu zafafan hawaye suka zubo a cikin idanunsa ya ji komai na cikin duniyar nan ya masa zafi, haka itama aisha sai yanzu ta gane me yake nufi. Da sauri ta zo ta cakumi Hameed tana kuka tana cewa. "Hameed ka cuce mu, ka ci amanar yarda da kaunar da muka nuna maka. Ashe 193 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri dama kaine ka yi mata wannan aika-aikar? To Allah Ya isa tsakani na da kaiba zan taba yafe maka ba, kaje insha Allah zai ka dandana kuncin da yafi wanda ka jefa mu". Nan take ya fara kuka yana cewa dor Allah ta yafe masa, haka ta ture shi taje ta zauna tana kuka. Haka yaje gurin Mustapha ya tsuguna gabansa yana kuka yana rokon zya yafe masa. Cikin kunar rai ya daga hannu ya wanke shi da mari, ji kake tasss! "Idan baka tashi ka bar gurin nan ba zan yi kasa-kasa da kai naga uban da ya tsaya maka, mara mutuncin banza, munafukin wofi". Ya fada cikin daga murya. Mikewa ya yi daga wurin da ya fadi domin ya yi mutukar jin marin, nan ya saker dawowa gabansa yana kuka, ya се. "Abba duk abin da zaka yi min kayi min matukar zaka huce daga facin ran da na saka, wallahi sharrin zuciya ne da rudin shaidan, duk su ne suka debe ni da aikata haka". 194 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri Wani mari ya sake kai masa a karo na biyu nan ma ya kara samun sa, a karo na ukun ne nayi sauri na saka hannu na tare, na сс. "Mustapha barshi haka tunda abin da zai faru ya riga da ya faru, kai kuma tashi ka tafi abimka Allah Ya shirye ka, zalunci kuwa ka riga da kayi mana shi, kai namu ne babu yadda za muyi da kai, amma ba don haka ba ni da kaina zan sa a rufe ka a gwada maka hankali ka gane abin da ka yi mana". Rarrafowa ya yi ya zo ya rike ni yana kuka yana cewa. "Granny wallahi na tuba, ku yafe min, hakika na san abin da nayi ban kyauta ba, Ammi kema ki yafe min". Sauri tayi zta dauke kallonta gare shi zta се. "Kadfa ka kara kira na Ammi, ni ba Ammin ka bace Hamecd, yanzu abin da zaka saka mana da shi kenan? Kaje abinka insha Allah sai Allah Ya yi mana sakayya da halin da ka jefa mu ciki, domin Allah basya bacci, Yana 195 Zuri'a Daya-1 _Sa'adatu Muhammad Waziri amsa addu'ar wanda aka zalunta cikin gaggawa". Cikin kuka ya cc, "Ammi ku yafe ni, nasan ban kyauta ba, amma ku yi min duk abin da zai fanshi bacin ran da na saka ku matukar yin hakan zai sa ku huce". "Hameed ka tashi ka bace min daga nan domin bau son jin duriyar ka a gurin nan, domin kana kara haifar ma da zuciya ta damuwa. Ka cuce mu ka jefa mu cikin tashin hankali, tsakanin mu da kai sai dai Allah Ya yi mana sakayya, amma maganar yafiya tsakanin mu babu, kaje can ka karata, ka jira ganin sakayyar abin da kayi mana, domin Allah sai ya biwa 'yar uwarka hakkin ta". Cikin uka Aziza ta ce, "Ammi kada ki kara kirana da cewar ni 'yar uwarsa ce, idan da ni din 'yar uwarsa ce ba zai yi min haka ba. Bai tausaya min ba, bai kuma duba zumuncin mu ba sai da ya hakke min, to ya żan yi na yafe masa?" Nan kuka ya ci karfinta ta fado jikina tana yinsa, tana cewa. 196 a Zuri'a Daya-1 Sa'adalu Muhammad Waziri "Ya Hamecd ba zan taba yafc maka ba". Dukkanin mu kuka muka ci gaba da yi, aka rasa wane zai iya rarrashin wani a cikin mu. Hameed ya matso gurina zai fara rokona na daga masa hannu akan ya yi min shiru, ganin yanayi na yasa bai iya furta ko da kalma daya ba dole ya ja bakin sa ya yi shiru. Cikin fushi Mustapha muka ga ya damki wuyan rigar sa ya ja shi sun yi waje ba tare da ya ce da shi uffan ba, haka suka yi waje tare, da har nayi tunanin naje na bisu na tambayi ina za su? Sai na dawo na tsaya, nan muka zauna muna. ta jimami da nuna alhinin faruwar al'amarin, muna cikin wannan halin sai ga Maryam nan ta zo. Bayan mun sanar da ita abin da yake faruwa hankalin ta ya yi mummunan tashi, itama kukan tayi mai isar ta domin abin ya daga mata hankali. Tun da ya yi (parking) motar sa a cikin (estate) din ya shiga kiran sunan duk wanda ya 197 Zuri'a Daya-1 Sa'adatu Muhammad Waziri zo bakin sa, haka ya zamo kamar karamin mahaukacі. Kai tsaye kofar gidan Alh. Jafar ya nufa rike da rigar Hameed, shi kuma binsa yake bai ce da shi kala ba, domin ba shi da abin da zai iya cewa da shi. Alh. Hamża da Alh. Lukman su suka fara fitowa suka hangi Mustapha ya nufi gidan Alh. Jafar, sauri suka yi suka mara masa baya, suna hango shi da Hameed sai farin ciki ya kama su domin tunanin su ya gano Hameed daga batan da yayi. Haka suka nufo gurin cikin farin ciki tare da yi ma Allah godiya na bayyanar yaron su, domin dama kullum suna cikin zulumi. Cikin daga murya ya shiga kiran Alh. Jafar babu kakkautawa, a sukwane ya fito shi da Asiya. Yana ganin su ya hankada Hamced gabansu ya je taga-taga zai fadida sauri zmahaifin sa ya tare shi amma duk da hakan sai da ya fadi. Dai-dai lokacin da su kuma suka karaso, nan take suka yi turus cike da mamakin abin da 198 Zuri'a Daya-I Sa'ndatu Muhammad Waziri suka ga yayan su yayi, take abir ya daure musu kai hade da mamaki. Cikin daga murya ya cc, "Jafar ka bani mamaki kai da azzalumin yaron ka, ashc ku dama maha'inta ne ban sani ba? To wallahi yau babu mai raba ni da ku sai kotu tun da kai da danka azzalumai ne marasa amana". "Kai Mustapha, nutsu kasan wane furuci kake yi da sanin wa kake jifa da wadannan kalaman, domin ba zan iya jurc daukan su ba". "Dole ka jure su kuwa domin babu yadda zaka yi, ban san rashin imanin danka ya kai haka ba, haka kuma kai ma ban yi tunanin zaka yi min haka ba. To amma tunda Allah Ya bayyana mana gaskiya to ai shi kenan, dole gobe ku ga sammaci kai da danka a kotu, domin babu abin da zai sa na hakura tun da ku azzalumai ne". сe. Alh. Hamza ne ya matso kusa da shi, ya "Subhanallahi! Yaya Mustapha mene ne ya yi zafi haka kake wannan furucin? Don Allah kayi hakuri ko ma meye ya faru a 199 Zuri'a Daya-I Sa'adatu Muhammad Waziri tsakanin mu za mu iya maganta shi ba wai sai mun tozarta kanmu ba duniya ta jimu, domir wannan babban abin kunya ne a ce daya dag cikin mu ya maka fan uwansa a kotu sabod wani abu da ya faru tsakanin mu". "Hamza ka rufe min bakin ka a gurin nan, bari na gaya maka babu wanda ya isa ya hana ni aiwatar da abin da nayi niyya turi da abin ya shigo da munafurci da rashin imani. To bari na fada maka, ko kasan cewa Hameed shi ne ya yiwa Ammi na fyade har ciki ya shiga wata ukи?" Gaba dayan su rudewa suka yi, Alh. Hamza da Lukman duk suka fito da idanun su waje, tsananin mamaki da tashin hankali ne ya bayyana a fuskar su. Nan take suka shiga raba idanu da kallon juna. Nan take ya zayyane musu duk abin da ya faru, jikin su yayi sanyi, yana fada musu hawaye na zuba a fuskar shi. 200 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 9 of 9