Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
just Compassionately for her! Lord forgive me and my family, protect." Tashi yayi ya sanya hannun shi a goshinsa da gefe da gefen shi sannan ya sumbata, ya juya zai fito. Tsohon da yake kula da wasu al'amuran church din ƴace. "Idan kaddara ta shata layinta! Toh babu wanda ya isa kauce mata, kai me Sa'a ne. Ban tab'a yiwa wani Magana ba, amma yau nayi maka. Kayi ƙoƙarin ka amshi duk abinda yazo maka me kyau ko mara kyau a cikin su kuwa har da sabunta kanka da Wasu shatin kaddarar ka, dube tafin hannunka, ka gansu toh sune zanen kaddararka, tayu tun Haihuwar ka ce take zane tayu daga baya kaddarar tajuya maka. Koma ma menene, tabbas kai dan baiwa ne. Ba a cika samun irinka ba, miracles daga kwaryar idanunka kawai ya Wadatar. Lallai akwai al'ajabi a duniyar ka, akwai B'oyayyen al'amari da babu wanda yake son ya tallata maka. Sai dai taki kadan zaka yi, zai iya sauya maka kaddarar ka, har abada kai din ma'abucin tausayi ne, da kyakyatawa Yakini, zaka yi nasara amma dole sai ka same jajjirtacciya Wacce tasan me ake kira da Kaddara, wacce kome zafin Bala'i zata zame maka garkuwa! Wacce bata da wani dogon addiction akan ka, wato buri. Yarona kayi ƙoƙarin inganta gaskiyar ka kayi ƙoƙarin ka rike amanar duk wanda yake tare da kai, Lallai Ubangijin da muke bautawa ya boye wata al'amari a rayuwarka" Haka tsohon ya juya jikin shi na rawa yace. "Yau mun gana ba lallai bane wata rana muga juna, kayi hakuri da yadda kaddarar ka yazo a haka".. Shiru yayi yana kallon hannun shi, kafin ya d'ago kai mutum ya bata a cikin church din, A hankali ya juya ya bar gurin, yana mamakin yadda mutumin ya gaya mishi, tunawa da yayi ai kawai irin wannan a cikin addinin su, kuma da yawa adam suka fadi abu tankar wata alfarma ce, dan haka zai iya kiran da mutumin da Miracles, me al'ajabi, kuma zai so ya abinda ya faɗa mishi ya tabbata bada gaske. Tabbas zai iya yarda da hakan tattara zance yayi ya watsa a gefe sakamakon tunawa da cewa canfe ne babu kyau zai iya kai ga Yesu yayi fushi da mutum........ Tohfa kunji Yan Paid group sun ce ya isa batin da ake baku ya isa haka.... Inuwar Gajimare da Bahaushiyah sune ake sayarwa ne.... 08130269641..... Domin niman shiga paid group taboni ta nan..... [7/2, 8:56 PM] BAHAUSHIYAH🥰: BAHAUSHIYAH 𝘏𝘢𝘵𝘵𝘢𝘳𝘢 𝘠𝘢𝘯 𝘔𝘢𝘵𝘢 mock 𝘽𝙖𝙗𝙞-𝙨𝙝𝙖 𝙝𝙪𝙙𝙪... 𝘼𝙣𝙣𝙖𝙗𝙖𝙬𝙖 𝙜𝙪𝙙𝙖 𝙗𝙞𝙮𝙖𝙧 𝙙𝙖 𝙨𝙪𝙠𝙖 𝙛𝙞 𝙨𝙖𝙪𝙧𝙖𝙣 𝙙𝙖𝙧𝙖𝙟𝙖! 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖 𝙗𝙖𝙨𝙪 𝙈𝙪𝙟𝙞𝙯𝙖/ 𝘼𝙣𝙣𝙖𝙗𝙞 𝙄𝙗𝙧𝙖𝙝𝙞𝙢, 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖 𝙜𝙖𝙣𝙖𝙧 𝙙𝙖𝙨𝙝𝙞 𝙩𝙖𝙪𝙝𝙞𝙙 𝙩𝙪𝙣 𝙠𝙖𝙛𝙞𝙣 𝙮𝙖𝙨𝙖𝙣 𝙬𝙖𝙮𝙚 𝙨𝙝𝙞, 𝙨𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙢𝙖𝙛𝙞 𝙜𝙞𝙧𝙢𝙖𝙣 𝙈𝙪𝙟𝙞𝙯𝙖𝙣. 𝘼𝙣𝙣𝙖𝙗𝙞 𝙉𝙪𝙝𝙪 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖 𝙗𝙖𝙨𝙝𝙞 𝙢𝙖 𝙢𝙪'𝙪𝙟𝙞𝙯𝙖𝙣, 𝙨𝙖𝙞 𝘼𝙣𝙣𝙖𝙗𝙞 𝙈𝙪𝙨𝙖 𝙞𝙣𝙙𝙖 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙬𝙖𝙣𝙙𝙖 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖 𝙗𝙖𝙨𝙝𝙞 𝙢𝙪'𝙪𝙟𝙞𝙯𝙖 𝙩𝙖 𝙞𝙣𝙙𝙖 𝙮𝙖𝙠𝙚 𝙨𝙖𝙧𝙖𝙛𝙖 𝙨𝙖𝙣𝙙𝙖𝙧 𝙨𝙝𝙞 𝙯𝙪𝙬𝙖 𝙜𝙖 𝙢𝙖𝙘𝙞𝙟𝙞, 𝙙𝙖 𝙠𝙪𝙢𝙖 𝙙𝙪𝙠𝙖𝙧 𝙧𝙪𝙬𝙖𝙧 𝙙𝙖 𝙮𝙖𝙮𝙞 𝙠𝙤𝙧𝙖𝙢𝙖𝙧 𝙜𝙞𝙙𝙖𝙣 𝙛𝙞𝙧'𝙖𝙪𝙣𝙖 𝙩𝙖 𝙠𝙤𝙢𝙖 𝙟𝙞𝙣𝙞/ 𝙙𝙖 𝙨𝙖𝙪𝙧𝙖𝙣 𝙨𝙪. 𝙎𝙖𝙞 𝘼𝙣𝙣𝙖𝙗𝙞 𝙄𝙨𝙖𝙝/ 𝙬𝙖𝙣𝙙𝙖 𝙆𝙞𝙧𝙞𝙩𝙤𝙘𝙞 𝙨𝙪𝙠𝙚 𝙠𝙞𝙧𝙖 𝙁𝙖𝙩𝙝𝙚𝙧 𝙤𝙛 𝙈𝙞𝙧𝙖𝙘𝙡𝙚𝙨/ 𝘼𝙣𝙣𝙖𝙗𝙞 𝙢𝙪𝙨𝙖 𝙮𝙖 𝙬𝙖𝙧𝙠𝙖𝙧 𝙙𝙖 𝙢𝙖𝙠𝙖𝙛𝙞/ 𝙠𝙪𝙧𝙖𝙢𝙚/ 𝙮𝙖 𝙩𝙖𝙙𝙙𝙖 𝙢𝙖𝙩𝙖𝙘𝙘𝙞𝙮𝙖/ 𝙎𝙖𝙞 𝘼𝙣𝙣𝙖𝙗𝙞 𝙈𝙪𝙝'𝙖𝙢𝙢𝙖𝙙 𝙎.𝘼.𝙒) 𝙨𝙝𝙪𝙜𝙖𝙗𝙖𝙣 𝙙𝙪𝙠 𝙬𝙖𝙣𝙞 𝙢𝙖𝙣𝙯𝙤! 𝙇𝙞𝙢𝙖𝙢𝙞𝙣 𝘼𝙣𝙣𝙖𝙗𝙖𝙬𝙖/ 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖𝙮𝙞 𝙢𝙞𝙨𝙝𝙞 𝙩𝙖𝙨𝙝𝙞 𝙢𝙪𝙟𝙞𝙯𝙖𝙣 𝙨𝙤𝙨𝙖𝙞, 𝙨𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙙𝙪𝙠𝙠𝙪𝙣 𝙨𝙪 𝙗𝙖𝙗𝙪 𝙬𝙖𝙣𝙙𝙖 𝙮𝙖𝙠𝙚 𝙖𝙢𝙛𝙖𝙣𝙞 𝙙𝙖𝙨𝙝𝙞 𝙨𝙖𝙞 𝙙𝙖 𝙄𝙠𝙤𝙣 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝! 𝙈𝙖'𝙖𝙣𝙞 𝙄𝙭𝙞𝙣𝙞𝙣 𝙐𝙗𝙖𝙣𝙜𝙞𝙟𝙞. .... 𝘼𝙠𝙬𝙖𝙞 𝙢𝙪𝙩𝙖𝙣𝙚𝙣 𝙙𝙖 𝙨𝙪𝙠𝙚 𝙙𝙖 𝙗𝙖𝙞𝙬𝙖 𝙨𝙪 𝙃𝙖𝙠𝙖 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖𝙮𝙞 𝙨𝙪, 𝙨𝙪𝙣𝙖 𝙙𝙖 𝙢𝙖𝙩𝙪𝙠𝙖𝙧 𝙝𝙖𝙩𝙨𝙖𝙧𝙞. 𝘿𝙤𝙢𝙞𝙣 𝙗𝙖 𝙙𝙪𝙠𝙠𝙖𝙣 𝙨𝙪𝙣, 𝙨𝙪𝙠𝙚 𝙞𝙮𝙖 𝙨𝙖𝙧𝙧𝙖𝙛𝙖 𝙠𝙖𝙣 𝙨𝙪! 𝙎𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙖𝙠𝙬𝙖𝙞 𝙖 𝙘𝙞𝙠𝙞𝙣 𝙢𝙪 𝙝𝙖𝙪𝙨𝙖𝙬𝙖 𝙖𝙢𝙢𝙖 𝙬𝙖𝙣𝙞 𝙡𝙤𝙠𝙖𝙘𝙞𝙣 𝙜𝙖𝙣𝙞 𝙢𝙪𝙠𝙚 𝙠𝙖𝙢𝙖𝙧 𝘼𝙡𝙟𝙖𝙣𝙪 𝙣𝙚 𝙙𝙖𝙨𝙪, 𝙨𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙖 𝙮𝙖𝙣𝙠𝙞 𝘼𝙨𝙞𝙖 𝙞𝙧𝙞𝙣 𝙨𝙪 𝙄𝙣𝙙𝙞𝙖 𝙙𝙖 𝙗𝙖𝙣𝙜𝙖𝙡𝙖𝙙𝙖𝙨𝙝, 𝙨𝙪𝙣𝙖 𝙙𝙖 𝙞𝙧𝙞𝙣 𝙬𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙢𝙪𝙩𝙖𝙣𝙚𝙣, 𝙖𝙨𝙖𝙡𝙞𝙣 𝙨𝙪 𝙖𝙣𝙖 𝙠𝙞𝙧𝙖𝙣 𝙨𝙪 𝙈𝙖𝙨𝙪 𝙄𝙡𝙞𝙢𝙞𝙣 𝙩𝙖𝙪𝙧𝙖𝙧𝙞! 𝘼𝙢𝙢𝙖 𝙖 𝙢𝙪𝙨𝙪𝙡𝙞𝙣𝙘𝙚 𝙝𝙖𝙙𝙪𝙬𝙖 𝙙𝙖 𝙞𝙧𝙞𝙣 𝙨𝙪 𝙖𝙠𝙬𝙖𝙞 𝙝𝙖𝙩𝙨𝙖𝙧𝙞 𝙙𝙖𝙣 𝙘𝙞𝙠𝙞𝙣 𝙧𝙪𝙬𝙖𝙣 𝙨𝙖𝙣𝙮𝙞 𝙨𝙪𝙠𝙚 𝙩𝙪𝙧𝙢𝙪𝙨𝙝𝙚 𝙢𝙖𝙠𝙖 𝙞𝙢𝙖𝙣𝙞𝙣𝙠𝙖..... 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖𝙨𝙖 𝙢𝙪 Dace𖣔 ............ A yanzun Izgilanci da ake mana ya ɗan ragu amma bawai an daina bane, ana yi lokaci zuwa lokaci. Tunda yanzun sun fara cin gajiyar baiwar da Allah yayi mana. Sannu a hankali al'amuran rayuwa suka fara sauyawa daga tsana zuwa girmamawa. Zan iya cewa a yanzun fatan iyayena shine nayi aure, kuma har lokacin yanzun miji bai zo ba. Haka muke rayuwar mu da dadi ba dad'i. Mutanen unguwar mu sun dan fara damuwa sosai da rashin karatun yaran su musamman na islamiyya, a masallaci suke jajjantawa har suke cewa Baba ai jiya da bai zo sallah ba Ghaddafi ne yaja su Sallah shi ya kira sallah ma. Daga yadda suke nanata abin yayi musu dad'i, kawai sai Baba yace. "Idan kuna da bukatar karatun su za a bude musu islamiyya" "Ai wallahi HABIBU zamu so haka! Kaga yaro karami yadda yake karatun Alkur'ani, yo ni ko lokacin da na tafi hajji ai sai labarawan da suke jan mu sallar nan nake jin irin karatun nan." "Haba me gari! Ai mu a kaduna zaka ga yaro karami Allah ya bashi baiwar haddace Alkur'ani" Inji Baban mu, Shiru Mai gari yayi can yace. "Akwai abinda yake damuna! Duk shekara idan nake aikin hajji." "Subhanallahi! Toh meke nan?!" Baba ya tambaye shi. Ajiyar zuciya ya sauke, dukda akwai mutane a gurin sai da Yasaka fuska dan kar a rena shi yace. "Wato mutumin nan da ya b'ata mana! Lokacin aikin Hajji" Zuba mishi ido suka yi Baba ne ya samu damar magana tunda dashi yake. "HABIBU! Baka tab'a zuwa Makka ba, amma da kaje zaka ji ana cewa! Malam Hamza ya b'ata! Laaa baku ganshi bane, Malam Hamza ya b'ata" Sake baki Baba yayi da ido, yana jin jina karfin jahilci mutanen garin shi, girgiza kai yayi cike da tausayi tare da bakin cikin abinda yaji mutumin da duk shekara sai yaje hajji... "Allah ya taimake ka! Hajjinka bata yi!" Inji Baba, "Inji waye?!" Ya tambayi Baba a fusace, Gyaran zaman Baba yayi sannan ya shiga cewa. "Hajjinka bata yi ba inji ni! Labbaika Lallahummah Labbaika, Labbaikai laashaarika Labbaikai, Innalhamda wanna'amata lasharika Labbaikai, wannan shine abinda kake cewa Ana niman wani ya b'ata" (Sorry akan talbiyan idan nayi Kuskure! Ina karb'an gyara zaku iya gyara min Nagode) Sai dukkan mutanen gurin suka zubawa Mai gari da Baba Idanu, sabida shine ya fara jure Mai gari cikin lalluma. A dame me gari ya kalle shi sannan yace. "Habibu! Ashe duk shekarun nan shirme na nake zuwa yi, shi yasa idan na dawo kaga na muntika kina Kai kace tsutsa, gaskiya sai ka koya min. Dan ina son nake nayi hajji karb'abbiya" Nan Baba ya shiga musu bayani akan musulunci da shika-shikanta, da kuma abinda da ya shafi sallah. Sannan ya roke su da su bar yaransu suna zuwa karatu, gidan mu. Nan Baba Habu ya kwashe da dariya, sannan yace. "Toh bari ga yadda za ayi." Kai Baba Yawale yace. "In ruwa ta hura wuta ba" Tsakanin su da Allah suke Izgilanci ta sigar dariya, Baba bai kula su ba, dan ya musu uzuri a rayuwar shi, kuma zai cigaba da musu uzirin har karshen rayuwar shi, dan yayi alqawari bazai kuma fushi da abinda suke mishi ba. Sai da Me gari yayi musu barazanar kai su gurin me Littafi sannan suka daina mishi dariya. .... Muna zaune ana cin abincin dare, nan Baba ya ture nashi da hannu. Alamar ya koshi. Shiru yayi na wasu lokuta, sannan ya sauke ajiyer zuciya, zuba mishi ido muka yi kowa ya tsame hannun shi a cikin abincin muna kallon shi. "Kuci abincin ku! Yau naga abinda ya bani mamaki" Jin haka sai gashi mun cire hannun mu a cikin abincin mun zuba mishi ido. Nan ya zauna ya bamu labarin abinda ya faru, kai Abdul Mugu ne, na bugawa a jarida, dariya yake har yana tintsirawa. Kai Ghaddafi yace. "Toh shi malam Hamzan an same shi kuwa? Tunda ya b'ata ne lokacin aikin Hajji" "Ina kuwa Bawan Allah! Ai bazasu same shi ba, sabida ba b'atan yayi ba, kawai rashin mai da hankali ne irin na mutanen mu, kinsan Allah Innarsu! Sun rigani zuwa makarantar allo, amma Kinga wata shirme wai malam hamza wani ya b'ata." Ya karshe maganar cikin murmushi. Gyara zama nayi sannan nace. "Baba wannan garin akwai matsala sosai, musamman na rashin ilimin addini, matukar bazamu tashi tsaye ba toh wallahi idan fushin Allah ya tashi kama mu, sai mun wahala, dan haka yana da kyau abu de musu yar islamiyya tunda akwai karamar rumfa a waje, sai mu fara koyar dasu, su ahlari da kitabul Tauhid, tare da Littafin kawa'idi." "Wannan haka yake Addarmu,! Babu wasa Insha Allah! Da yardan Ubangiji sai mun wayar da musu kan su sosai." "Allah yasa idan su Yaya sun bar ku ba" Inji Innarmu, "Sallama dai! Wai Husnah tazo inji wani a waje" Kallona duk suka yi, na b'ata rai, na cigaba da gogewa Lu'lu'a hannunta, tana kallon na. "Addah zan rakaki?!" D'ago kaina nayi na kalli idanunta, Sunkuyar da kai tayi tare da gyad'a min Kai. "Husnah baki ji ana Nimanki bane?!" Mik'ewa nayi, sannan na nufi cikin dakin mu nasako hijab me hannu, na rike hannun Luluh muka fito. Daga yanayin mara mutunci na fahimci Manga ne! Karamin tsaki naja aikuwa suka fasa min dariya da wani katon muryan su. "Kunga itace nake son na mallaka daren mu na farko, awara da dundunkwalo zan kawo mana," Aikuwa suka kuma saka dariya,, dayan yace.. "Zamu na zuwa ganin irin soyayyar sharukan da karina" "Amma kasan ta tsufa a dandali wannan baza ka bita a nitse ba da zafi zaka bita," Suka kuma fasa dariya, "Kuma naji ance akwai kayan hutu, don Allah idan mun zo bazaka kore mu ba" Suka kuma fashewa da wani dariyar. Ba a tab'a min Izgilanci irin na yau ba, sai naji a raina, da zan iya musu wani abu ban ce kome ba, na juya abuna. "Laaa! Amaryan mu zata koma Cikin gida tsaya mana ko sumbatar nan a miki zaki yarda da Jarumin mu" Idanuna ko kallon gaba na bayi, na shiga cikin gidan, zama Luluh tayi jikin Baba tana gaya mishi abinda ya faru a wajen, bai ce kome ba sai ma bani hakurin da yayi. ......... A sannu muka fara koyar da karatun safe, wanda yaran basu wuce goma sha uku ba daga gidan me gari, idan aka tashi baba yana saya musu alewa, abinka da yara sai suka fara gayawa yan uwan su ai idan kazo makarantar malama Husnah ana raba alewa. Kafin wani lokaci har mun tara yara sama da 50, kuma suna fahimtar kome. Tafiya ta fara miƙewa, bakin ciki kamar ya kashe su Baba, amma basu da yadda suka iya damu. Sai dai Izgilanci kan babu lefi domin suna haduwa da iyayen yaran zasu fara musu dariya wai sun dauki yaran su . Sun kawowa karuwa. Basu masu kula su, domin iyayen yara since sun huta da fitinar da yaran su , kuma da suna jin dadin yadda yaran suke fahimta dan haka babu ruwan su a cikin al'amarin yaran su. Sannu a hankali kofar gidan mu ya kasa mana, dole muka raba abin wasu suka shiga zauren mu, Maryam da Ghaddafi suna koya musu. ....... Yau Alhamis babu makarantar, dan haka zan mai da Baba Asibiti, ina gama shiryawa, muka fito. Wannan karon ni da Ghaddafi ne sai Baba, haka muka zo bauchi muka gama abinda zamu yi sannan muka komo, gida Ban tab'a kudin Dr ba. Sai .a kokarin tattaro mishi duk ribar da na samu a cikin shagon mu. --- Bishop Yohana Chibok.. Kiran layin Dr Devanah take yi, amma fir yaki d'agawa. Joe ya kallon ta sai murmusawa mata yake. A dame ta kalli Mommah cikin zubda kwalla tace. "Mommah! Yaki dauka zan bishi. tokyo kawai" "Karki fara dan zaki samu saba'ni ne dashi." Inji Joe, Hararar shi tayi cikin jin haushi tace. "Munafiki! " Dariya yayi sannan yace. "Ban damu ba! Bature ne dai bazaki sane shi ba, dan koda kin kira ba zai dauka ba" Daukar matashin kuran tayi ta jefe shi da shi, tana kuka. Dariya Daniel ya yake musu, dan wani lokaci tsakanin Joe da Devanah kamar tom&jerry, haka tayi kukan ta, har ta koshi. Ita dole sai taje tokyo. Joe ya ce. "Zaki gwajin farko ne? Tunda kin san dai baiko kawai aka muku, kuma shi bai da ra'ayin gwajin kwayoyin halittar jikinsa." Kiran shi tayi cikin damuwa tace.. "Wallahi sai nayi maka rashin mutunci, kuma sai naje bazan dawo ba sai da ciki dan dashi za ayi bikinmu." Tana gama fad'ar haka ta bar falon zuwa sama.... --- Japan... In Tokyo Farin wanda har kasa ne a jikin shi, sai shimi, yayi rubda ciki, tare da kifa fuskarshi a pillow, yana juyar da kai yake cikin damuwa dan daga yadda yake juyar da kan shi zaka fahimci akwai matsala. Yasan dazun Samantha ta bashi ruwa dazun da tashigo, dan yana cin abinci ne ta shiga shi kuma bai dauko ruwa ba shine yace ta bashi ruwa don Allah. Tunda yaci abincin ya shiga wannan halin ko nace ruwa. Jin yayi an kwanta a bayan shi, tare. Juyawa yayi tabbas ita ce, cikin b'acin rai yace. "Me kika samin a cikin ruwan da kika bani" Zare towel tayi tare da kwanciya a jikin shi, dukda halin da yake ciki baya jin zai iya biye mata, tureta yayi. Ranshi a ɓaci yace. "Ki fita kafin na wulantaki," Ganin yadda ya birkice mata yasata mik'ewa da sauri ta saka kayanta. Ta ficce mishi daga gidan, drowe gadon shi yana da sauri ya ciro wata yar roba, ya bude kwayoyin magani ya hadiya har guda hudu, goran ruwan kusada shi ya daga sai da ya shanye tass, sannan ya kwanta. Bayan kamar minti goma kacal, barci me nauyi yayi gaba dashi. ....... A yanayin da suke ya tabbatar mishi cewa, ta tafi da duk wata damar da yake tanadin shi, sabida jin daɗin kasancewa shi da ita. Ya kara mishi kwarin gwiwar abinda take mishi. Wani irin abu yake ji, tare da rungume ta. Ji yayi an finciketa daga jin daɗin shi, ana tafiya da ita, shima kuma ana janshi. Kokarin kwace kan shi yake, domin inda ake jan shi, was so darkness, ita ce take inda haske ya, kwace rikon da aka yi mishi yayi ya falfala da gudu, sai dai an sami akasi domin akwai wawakeken ramin da ya shata tsakanin su. Durkusawa yayi ya kwalla mata kira da Hus......... Dr Aahil kana ruwa💔 Good Morning.... [7/2, 8:58 PM] BAHAUSHIYAH🥰: BAHAUSHIYAH 𝘏𝘢𝘵𝘵𝘢𝘳𝘢 𝘠𝘢𝘯 𝘔𝘢𝘵𝘢 Highlights Babi-sha-biyar Tashi yayi yaji gabaki daya ya zubda abinda yake dankare a matan shi, wanda har sai da yaga damshin sa a jikin farin wandon shi. "Husnah! Why she?! But Jesus why you sent in to my dream?" Wannan itace abinda Dr yake tambayar kan shi. Bai taba jin kome a ranshi ba, sai tausayi toh me ya kawota cikin mafarkin shi. Ganin hasken da wayar shi yayi yasa shi daga kiran sabida Sunan Blessing Mom, A kasalance ya d'aga Kiran ƴace. "Mommah!" "My Son! Ya kake?! Da fatan baka da wata matsala?!" Lumshe juyayye idanun shi yayi cikin nutsuwa, sannan ya sauke ajiyer zuciya yace. "Babu Mommah?!" "Toh Allah ya maka albarka! Amma me yasa kak'i daukar kiran Devanah?!" "Mommah! Karfe nawa?!" "Karfe huɗu na yamma," ta bashi amsa a takaice. "Toh mu nan hudu na safiya ne,! Kinga ta kirani tsakiyar dare ina barci kuma" Nan yayi ta mata bayani har ta fahimta. Har suka yi sallama bata daina jaddada mishi muhimmancin shi a rayuwar su ba. ...... Doris Yohana Chibok, yan asalin karamar hukumar Chibok ne na jahar Borno, Doris Babanta baban Reviren ne a church Catholic charities dake garin Chibok, Suna da kakkafewa akan addininsu na Kirista, nd basu da son shiga hidimar kowa, Mahaifin doris Amos Eshaya da Mahaifiyar Doris yara uku suka haifa, Jacob sai Doris da Ezrah, Mahaifin Devanah. Mr Yohana yaron Amos ne, yazo daga wani kauye kwandiga na cikin jahar Borno, karatun addinin Kirista gurin Mahaifin Doris, Kawai suka fada soyayya. Ganin Yohana mutum ne mai matukar biyayya da addini, tasa suka bashi auren Doris tare da bashi matsayi babba a church Catholic dake garin Chibok. Anyi Shagali sosai, sannan aka kai bawa ango matar shi, inda suka tafi can aka dagargaji amarci. Bayan shekara biyu, wasu irin falala da samu suka shigo rayuwar ma'auratan guda biyu, daga cikin har da samun karuwar yaron su wanda suka sanya mishi Bature kasancewa shi din yafi su farin fata. Shine suke kiran shi da Bature, sun kai shi. Church Baban Doris ya ganshi. Dafa kan shi yayi cikin damuwa sannan yace.. "This child! Yana da karfin miracle! Yana tare da mu'ujiza me ƙarfi zai ta muku abin al'ajabi bi, dan haka ku dauke shi ku tafi Rome dashi sabida haɗuwa da manyan manyan papa roma, domin killace shi har ya iya sanin kanshi. Karku gina shi da wata akida sai ta namu, domin idan kuka barshi zai iya zame mana kalubale. Karku bari mace ta shigo rayuwar shi, in ba haka ba zaku iya rasa shi, ku gina mishi zuciyarshi da kin mata, koda basu a kida daya, amma karku barshi ya kawo wacce yake so? Domin itace mafarkin rugujewarshi. Kunga yaron ku, ga line of destiny din shi, ga kuma line ko Ya'ya yayi Crossing dis line everything zai sauya, my Daughter and my Son In-law, ki k'iyayye, karku sake mace ta shigo rayuwar shi, Yarone da yake da kashin arziki! Yarone da yake da baiwar arziki duk wanda zai zo kusadashi, sai ya zama wani abu. Hanyar Arzikin ku ne yazo gare shi. Karku tab'a barin yayi fushi domin zai iya zame muku samuwa da rashi. Karku sanya shi yayi abu dole, sabida jinin shi cike take da Izzar attajirai! My daughter, yaron ki shine yaro mafi al'ajabi a wannan ƙarnin. Behind good and bad line! Akwai Love and Compassionate! Uwa uba! Line of destiny! So karku yarda da sadaukarwa! Daga ranar da kuka barshi ya sadaukar da wata abu daga cikin akidar mu! Ban san me zai faru ba." Daga haka yayi musu addu'a sosai, sannan ya kuma basu addu'o'in, musamman na Evil lady! Karta shigo rayuwar shi. Sannan suka tattara shi suka koma Rome dashi can aka haifi Joe da Daniel, Devanah kuwa mahaifiyarta baturiya ce. Kanin Mommah Ezrah ya aureta dake tare suke a can. A can Italy, a can suka zauna tsawon shekaru talatin da biyar, lokacin Bishop Yohana ya bautawa Addinin shi tun kafin ya dawo CAN suka bashi matsayi na Musamman. Tun Bature nada five years suka haɗu da Aahil Aliyu Maitama, Tun Doris da Bishop suna bakin cikin abotar Bature da Aanil, gashi basu kaunar fushin Bature shi yasa suka hakura, kuma abin mamaki yadda Allah ya bunkasa su. Dr Bature ya karanci anatomy me, yayinda Dr Aahil ya karanci Biology. Akwai banbancin halayyar tsakanin, domin shi mutum ne mai mugun kyamar zina, sabida tarbiyyar da yasa mu, baya son shiga harkan mata, sab'anin Aahil da ya zama na mamajo. Bature baya da yawan magana, sannan idan zai yi toh akan addinin su, a bangaren addini kuwa toh har tsoron shi wasu mutanen suke. Kowa na mamakin yadda abotar Bature da Aahil.. Har suka nemi aiki a A.B.U zaria ---- Ajiyar zuciya ya sauke, taryo tarihin shi, murmushi yayi sannan ya tashi zaune yana me jin dadin irin nasabar da yake da shi. 𖦹𖦹 Tambayar bazata ne ya zo min daga Baba, zufa da tsoro e suka kamani. "Asma'uh ! Baki bani amsa ba yaushe zaki koma makaranta, ina ta zuba miki ido, tsawon wata hudu mun shiga na biyar. Meye nufinki da zaman gida." Kafin na tattaro duk wata bayanin da zanyi mishi Mubarak ya amsa maganar da cewa. "Ai baba! Lokacin da ciwonka ya tashi kace ta dawo gida zamo koma Narabi. Dalilin da ya janyo tayi asarar wannan shekarar dole ta sake mai-maita shekara." Shiru yayi yana kallona nayi tsamotsamo, tare da zaro ido bakina yana rawa nace. "Dama ina son zan maka bayani lokacin da muja Bauchi na tura sako ta cafe, shine suka ce an dakatar da ni na tsawon shekara d'aya. Yanzun saura wata." Shiru Baba yayi amma da alamu bai yarda ba, kawai baya son zargi ya tabbata a tsakanin mu shi yasa ya share, ya kuma min fatan Alkhairi. .... Wannan yanayin da nagani a fuskan Babana, ya sanya ni kuka. Sosai sabida duk wata hope din da yake a kaina na kasa, sannan na fadi warwas. Allah ya isa min da abinda Dr Aahil yayi min domin ya gama cutana, ya rabani da duk wata burin da Iyayena suka daura a kaina. Dare mahutan bawa, amma Ni ina kan abin sallah ina kai karar Aahil ga Allah ina kuma niman karfin da zan rama abinda yayi min, a cikin wata biyar zuwa shida, nasan iya adadin bakin cikin da naci..... 𖦹𖦹 Karatun da muke na safe iyayen yara sun kara rokon Alfarmar ayi musu na yamma,, na dare ne dai nace a'a sai suka ce toh a bari ina koyar da iyayen yara daddare, haka ya kara bakanta ran yan uwan Baba. Har suka fara jifarmu da cewa. Ai koyawa mata yadda zasu yi lalata muke. Kai magana marasa mutunci da dadin ji, abinda ya basu haushi da suka gama surutunsu, sai ga mazajen da suka turo matan su suka musu caaa.. Rayuwa me tattare da kalubale, tankar baiwar Rahman Ubangiji ne, domin Kuwa mun zama nakiyan kan kabari maganin me kwalama, gamu nan dai amma mun gaggari yan tsurku. --- Adamawa State.. Tsakanin Alhaji Muhmood Dan Kasa da Imam Moddibo Usman, abun ya zazzafa Wanda takai, sai da Governo da Mai Lamidon Adamawa suka shiga maganar kasancewar Daga Moddibo har Dan ƙasa, dukkan su manyan mutane ne masu daraja da kima uwa uba, su din wasu j-j ne a jahar wato, Dan haka suka sanya su a gaba da cewa. "Imam Moddibo! A matsayin ka na babban malamin a cikin Jahar nan, mun hada ku Anan ne. Don ku sassanta kanku, wannan abinda kuke bai dace ba, kune jigon siyasar jahar nan, sannan ai ko ba kome Dan kasa kamar kanine maka, don Allah ki ajiye duk abinda yake tsakaninku." Shafa farin gemi shi Imam Moddibo yayi cikin dattako, sannan yace. "Allah ya taimaki Mai martaba, ya wuce a gurina. Abinda nake bukatan sani shine Yarona Fa'iz da yake hannun shi, ya sake min yarona" "Karka min sharri kazo ka zauna kamar mutumin Allah nan kuwa munaf....." "Hattara dai! Dan kasa a gaban Mai Martaba kake, ba ayi ya shashiyar magana. Dan haka akul kar harshen ka taja maka mummunan aiki!" Girgiza kai Imam Moddibo yayi, fatan shi Fa'iz ya fito daga hannun Dan kasa. "Toh wai ni kam meye janyo wannan al'amari?!". Taimakin Gwanman Adamawa yayi musu wannan tambayar. Gyara zama Ɗan kasa yayi cikin jin haushi ya fara magana. "Meye kuwa bayan mutumin nan me kama da jan gwanda ya k'amk'ame kome ya hana kowa cigaba. Baka isa ka sami kwangila a gwamnatin ban ba sai wannan mutumin banza yayi ma sanadin an hanaka, taya bazan ji haushin sa ba, da aka tashi bada appointment na siyasa, tunda aka janyo wannan mutumin aka bashi Kwamishinan noma ya k'amk'ame kome, yanzun kamfanin da za ayi na sarrafa takin zamani, ina saka ran zan samu ni da Yarona sai naji wai shine akan aikin da Injiniya Fa'iz, wai an basu aikin noma takin zamani." Nan ya dinga tonawa kanshi asiri da yadda ya tsanin Imam Moddibo, har yake gaya mishi ya kula dan bashi daya yake fakonshi ba, Akwai na jikinshi a musu kin shi kuma matuƙa bai dai na. Mamaye kome ba tabbas yayi kuka da abinda zai sami Fatima da Amina ba, dan ya lura kamar yadda yake nuna son kai a waje haka yake nunawa a cikin gidan shi. Imam Moddibo, mutum ne da Allah yayi mishi hakuri sosai, amma bai iya jure cin amanar ruhi, ajiyar zuciya ya sauke sannan ya kalli D'an kasa yace. "Toh naji zan janye daga duk wata abu da aka nime ni a kai, Sai dai nayi Imani da Allah ka kiyayye fushin Allah akan abinda kayi min, ka kiyayye fushin fusatace, ba ita Aminatu" Da sauri ya d'ago kai yana kallon shi. Yana nuna shi da yatsa. "Haka yace tabbas haka yace." Yana fadan haka ya tashi daga falon sulhun ya fita da sauri gudu gudu. Yana kuma mai-maita abinda yaji Moddibo ya faɗa. ...... Mamaki ne ya kama su Imam da Mai martaba da maitamakin gwamna, suka bawa Moddibo hakuri da kuma nuna mishi baso don ya ajiye mukaminsa, domin sun san sami karuwa da shi kan shi kanshi da dukiyarsa, domin yana iya saka dukiyar shi a cikin abubuwan gwamnati idan an samu riba a bashi hakkin shi. Daga fadar sarki Asibiti ya wuce. Inda Fa'iz yake kwance..... 𖦹𖦹 Alhamdulillah, makarantar ya bunkasa fa domin baba ya fara koyar da maza, musamman irin su Mai gari! Gudun kar a kuma Malam Hamza Wani ya b'ata (🤣😂👈🏻) kuma abin burgewa suna dauka, domin basu damu da zigar da ake musu ba. Kuma idan kaga yadda mata suke dauke karatu da sai kasha mamaki domin, ko wani abu ya shiga musu duhu zaku ji suna tambayar mu, haka ma mazan ma haka. ..... Muna wanki sai gasu Fadilah ta shigo, ta zauna tare da tura min baki, dalibana ce. Cire hannuna nayi a cikin wankin ina kallon ta. "Malama! Nifa bani da lafiya?!" Cike da mamaki nake kallonta sannan nace. "Kamar ya?! Baki da lafiya" Ganin yadda su Innarmu suka zuba mata ido, sai ta tashi ta rogo zaure, biyo ta nayi ina na tsaya daga bakin kofar, ina kallon ta. Kuma da matar aure ce, ba a jima da auren bane, shine take min shiririta, dake tun last week nace mata kamar tana da juna biyu, tayi ta min shirme har da kuka ita babu ciki yaushe ma ta yarda da mijin, ba koda aka yi sai biyu ne! Sai da na toshe mata baki dan zata fara yanko min wasu manyan bayanan tsaron sirrin ta. "Kin kira ni kuma kina ta min shirme! Baki ina wanki bane?!" Juya min baya tayi sannan tace. "Malama! Maganarki ya tabbata, juna min biyun ne dani" Takowa nayi inda take na dafa kafad'arta, nace. "Na tayaki murna! A yanzu za a zama Uwa ko? Toh idan kin sami lokaci gobe kizo na duba ki.". Juyata nayi naga tana kuka, riko hannunta nayi, na kanta d'akinmu, nace. "Menene na kuka?!" "Malama bana son Shine, ni da nake son na fita naje nayi karatu irin naku, taya zan

Chapter 7 of 10