Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
juya ina kallon shi, mika min yayi sannan ya ajiye nashi a baya. "Tabbas rayuwar ki tana cikin matsala! Domin yanzun haka Aahil ya shiga da korafin kin b'ata mishi suna, ana gab da auren shi, dan haka ga abinda ke faruwa a group ɗin mu na A. B. U." Ya wurgo min da wayar cinyata, tattaunawar da ake a kaina na ga, wasu suna cewa. Koreni masu goyan bayan shi wasu suna cewa kar a koreni tunda saura kwanaki mu gama Jami'ar." "Shekaru biyar ana niman na shida, kika bata shekaru biyar baki b'ata rayuwarki ba ke kuwa me yaja ki da wannan al'amari." A yanzun babu kuka sai dai wani irin bakin ciki nake ji wanda yake shirin tarwatsa min zuciyata, wani irin nadama nake ji mara amfani. "Kaicona! Me ya kaini aikata wannan mummunar aikin, juyawa nayi sannan na juyar da kaina gefe. Sannan nace. 'YA CE kamar kowa wadda ta taso cikin ɗabi'a da al'ada irin ta BAHAUSHE! "Me ta ke so? Me nene burinta?" Babu wanda ya taɓa tambayarta. Kalma ɗaya ce ko yaushe take hawa kanta "KE BAHAUSHIYA CE! Ko me da ke gareki zai zama irin na Hausawa ne." Tabbas Bahaushiya itace macen da ke shimfiɗar da rayuwarta dan kula da mijinta da yaranta. Itace mace guda da ke killacewa ƙarƙashin igiyar riƙon Ɗa Namiji, da ke kiran shine mafi rinjaye akanta. Sanan Kalma guda da yake nanatawa, Rayuwar 'YA MACE kamar gilashin da ke riƙe a dungulumin hannu ne, ko wani lokaci zai iya faɗuwa dan ya tarwatse ne. Idan aka ci gaba da ganinsa to zai zama shuɗaɗɗen labarin rayuwarsa. Tabbas bayan karatun allo babu buƙatar biyantar da kururuwar zamani wajan tsoma hannayenta dumu-dumu dan janta da tafiya a ƙarƙashin hasken Nasaran da ke da jajayen kunnuwa. Ka fahimci wacece BAHAUSHIYA! Mu a cikin al'ummar Hausa an haife mu ne dan muma mu haifa, sannnan Na ajiye mune dan biyar bukatan kai.... ---- Sabon Gari Narabi... A karamar hukumar Toro, na jahar Bauchi, Mahaifina asalin yan Jahar Kano ne, fatauci ya kawo kakansu Garin Narabi, Malam Korau daga karamar hukumar kura. Amma zuwan mu garin Narabi muka zama yan Bauchi ko nace yan Toro. Gidan Malam Manga shine gidan kakan mu, kasancewar shi din d'an gargajiya ne, Malam Babba yana da yara Goma sha biyu, Baban mune na biyar, a sha biyu nan, hudu ne mata. Baba Yawale shine babban, Sai Goggo Shatu, Kafin Baba Bala, sai Baba Kabiru, sai Baban mu Habibu sai Goggo Hajaran Baba Haruna, sai Baba Iro, da Baba Isuhu,Sai Baba Habu, sai Goggo Kande, da Goggo Auta. ..... Murmushi na sake me ciwo, kafin wani siririn kwalla ya zobo min, sannan na cigaba da cewa. "Dukkan su nan basu jituwa kamar su kashe juna suke, Ba dan komai ba sai dan dukiyar da aka bar musu. Baban mu ya tafi yawon almajiranci anan Allah ya hada shi da wani, mutumin Kaduna ya dauke shi, har yayi karatu zuwa aji biyar na Sakandire. A lokacin da Malam Babba yaji labarin Baba na karatu, boko kuma bayan gidan su ba ayi, sai ya tura aka dawo dashi. Dan dama yayi sauka, karatun bikin ne yake yi domin tsira da kimar shi, amma yan uwanshi suka Zuga iyayen su ya dawo. . Tunda ya dawo Alhaji Abubakar yazo sau uku dan ya koma Malam Babba ya hana, dan haka ganin kar Baba tafi aka mishi baiko da Zainab, Innata kenan. Dr ban san yadda zan maka bayani a yadda aka tsani boko a gidan mu ba, domin duhun kan iyaye da kakanni har yau gidan mu suna dashi. Idan nace zan maka bayanin yadda Babana yake bazaka yarda ba, domin shi farine sosai kamar bashi ya haife mu ba. Dan ko Innarmu tana da hasken fata. Lokacin da aka yi baikon babana da Innata basu da wasu shekaru dan Bana Shekarar shi ashirin da daya ne, Inna ce ne shekaru sha huɗu. An saka auren su bayan kaka, lokacin sanyi. Babana yana da matukar kulafucin boko shi yasa yaki tsayar da tunanin shi akan Innarmu balle su shaku, daga sabon garin Narabi, yake garin gumau yaje makarantar boko a boye, ban san yadda zan maka bayanin yadda aka tsani boko a gidan domin duk wanda ace yayi boko toh kafiri ne, dan gani suke kamar yayi ridda ya bar addinin Muslunci, bari na gaya maka akwai wani da yayi karatun Boko, wallahi gudun shi ake ta yi, wai ya kafurta, abin tausayi karshe bin shi kayi da jifa, wai kar ya kawo mana masifa gari. Babanmu ya taso da burin karatun boko, sai bai samu halin yi ba, dake ya fara a inda yake almajiranci, sai Allah ya taimaka ya samu wayewa, domin kana ganin shi bazaka tab'a yarda bai yi zurfin ilimi ba. Idan ka ganshi da yan uwansa sai ka zata haihuwar shi suka yi, sabida tsabar fitinar da suka sanyawa kansu. Nayi auren Baba da Innarmu, cikin amincin Allah, kuma suka zauna lafiya ba a jin kan su. Sai dai tunda aka yi auren ko shekara bata rufa ba aka sanya su a gaba, wai yaki Haihuwar sabida ya sanyawa ranshi karatun kafirci, al'amarin da ya kai har kunnen Malam Manga, ai HABIB yaki haihu ne saboda yayi karatun Boko. Yadda aka zuga Kakanmu sai ya haura yayi fam, dan haka bai yi shawara da kowa ba, washi gari bayan sallar asuba aka daurawa Baba Aure da Rakiya wata yar abokin kakanmu. Shigowar Rakiya gidan bata rufa wata ba, sai gata da ciki. Abinda ya kara rura wutar rikicin tsakanin yan Uwa Baba da Innarmu kenan, ayita mata gori da habaici, shagube da banzar magana. Sam Inna kamar bata dauki sunan Zainab din ba, dan ta cika sanyi da yawa. Wani abu tausayi, sai da cikin ya isa wata hudu ya zube, wanda Yadiko tayi kamar bazata tashi ba, ga Baba Yaso a kaina asibiti a gumau amma fir Malam Manga yaki, haka baba Yasaka hannu bibbiyu ya zuba tagumi har cikin yana zaune har aka ce cikin ya fita, sabida unguwar zoma ake kira. Iya wahaltuwa Yadiko tasha amma dake bata da Cikakkun hankali. Tana samun lafiya ta cigaba da zabgawa Innarmu rashin mutunci, abinda ya kai har tayiwa Innarmu sharri, wai itace ta zubda mata ciki. Duk yadda Innarmu taso kare kanta abun ya faskara, dan haka ta amshi laifin da banata ba. ........ Goge kwalla nayi. Sannan na cigaba da cewa. "A bangaren Baban mu yaki yarda Innarmu zata iya zubda cikin Rakiya, haka suka ci mutumcinta, ta kwana tana kuka. Da zazzaɓi ta kwana har gari ya Waye,ta gayawa Baban mu. Cikin hikima da dabara ya dauke ta suka tafi asibiti, Allah cikin ikon shi, ana gama dubata akace cikine da ita. Farin ciki kamar Baba ya zubda ruwa a kasa yashi...... Karku manta Wannan book kuɗi ne. Idan ta bank ne=200 Idan kuma katin mtn=300 Gama su bukatar VIP=500 bank account Kuma katin mtn ne=600 Acct: 0472282105 GTBNK Ramlat Abdul Rahman Manga Idan ka biya ka sanar dani ta wannan number08130269641👈🏻 Thanks........ Idan kuma kana son Inuwar Gajimare! Kayi min magana ta wannan number! Shima. [7/2, 8:47 PM] BAHAUSHIYAH🥰: BAHAUSHIYA 😭𝘏𝘢𝘵𝘵𝘢𝘳𝘢 𝘠𝘢𝘯 𝘔𝘢𝘵𝘢💔 𝙆𝙖𝙘𝙤𝙠𝙖𝙣 𝙇𝙞𝙩𝙩𝙖𝙛𝙞𝙣 𝙎𝙖𝙙𝙖𝙪𝙠𝙖𝙧𝙬𝙖 𝙘𝙚! 𝙕𝙖𝙞𝙣𝙖𝙗 𝘼𝙗𝙙𝙪𝙡𝙡𝙖𝙝𝙞 𝙒𝙖𝙯𝙞𝙧𝙞! 𝙈𝙖𝙢𝙖𝙣𝙖🥰 𝙈𝙖𝙝𝙖𝙞𝙛𝙞𝙮𝙖𝙩𝙖 𝙩𝙖 𝙠𝙖𝙞𝙣𝙖! 𝙄𝙣𝙖 𝙩𝙨𝙖𝙮𝙚 𝙣𝙚 𝙨𝙖𝙗𝙞𝙙𝙖 𝙠𝙖𝙧𝙛𝙞𝙣 𝘼𝙙𝙙𝙪'𝙖𝙧 𝙙𝙖 𝙠𝙞𝙠𝙖 𝙢𝙞𝙣 𝙩𝙪𝙣𝙙𝙖 𝙧𝙖𝙣𝙖𝙧 𝙙𝙖 𝙠𝙞𝙠𝙖 𝙝𝙖𝙞𝙛𝙚 𝙣𝙞 𝙝𝙖𝙧 𝙕𝙪𝙬𝙖 𝙔𝙖𝙪😘🥰😍, 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖 𝙜𝙖𝙛𝙖𝙧𝙩𝙖 𝙢𝙞𝙠𝙞 𝙙𝙖 𝙍𝙖𝙝𝙖𝙢𝙖!🥰😍 My Mistake Babi-shida Ranar da aka muka zo registration ban haɗu da kome ba, asalima nasiha ce tsakanina da iyayena, amma babu addu'o'i niman kariya, daga mugun abu. Innarmu ce ma tayi min fada da na kama kaina, na tsare mutuncina. Sosai tayi min fada akan ba ruwana da Kawayen banza amma bata yi nazarin bani wata addu'o'in ba dan niman kariya daga shaidanun mutane. So bayan mun iso zaria nan sai aka kama min daki a cikin makarantar, tare da wasu abubuwan Amfani na Baba ya nuna min muhimmancin barin cikin su nazo karatun suna da burin na zama wata aba ce a cikin al'umma. Bayan tafiyar su ne na fara fuskarta rayuwar da nazo yinta, na nutsu sosai asalima kaman tsoron mutane nake, wata na uku a makarantar su babba suka dawo kaduna. Sai ya zamana duk karshen sati suna hanya zuwa duba ni. Kuma dukkan su biyar har da Innarmu. ... Wata na hudu mu kayi jarabar zangon farko, da murna na tattaro na dawo gida, a gaskiya muna cikin yalwanta Ubangiji, sabida. Nayi hutuna a gida inda muka ji dadin rayuwar mu ta nan kaduna. Hutun mu na karewa na koma makaranta. ...... Duk wani abinda zai kare mutuncina nayi, tun daga shigar da nake. Ina kyakyawa mu'amala da abokan karatu na. Hatta yan Ajin mu sun san bani shiga damuwar kowa, idan ka tambaye ni me kika zo yi karatu zance maka, kuma har yau ban tab'a fashin karatu ba, Ni dai abinda na sani ina da zafi. Idan ka tab'a ni amma bayan haka bani da wata halayyar. ..... Ina da shekaru na biyar aka kawo mana Dr Aahil, lokacin ban san tare aka kawo ku ba, ni dai ina ganin shi a makaranta. --- Kallona yayi sannan yace. "A'a ba kawo mu akayi ba, mun tafi karo karatu ne, shi ya gama nashi." Shiru yayi sannan ya cigaba da danna wayarsu shi wanda kusan Halayyar shi ce. Idan ka cire koyarwa zai iya b'ata lokaci me tsayi yana latsa waya har. "Dare nayi kuma baki gama bani ba, kuma na gaya miki ina da night service." Shiru nayi Sannan na cigaba da bashi labarina. --- Bazan tab'a mantawa ba, wata rana ya shigo ya gama mana lecture zai fita. Sai wata daga bayana tace. "H²Manga! Malamin nan zai tafi yabar kayan shi." Siririn tsaki naja sannan nace mata. "Yana sane ya bari, dan haka sai ki tuna mishi." Juyowa yayi tare da zuba min ido, na kauda kaina na cigaba da abinda nake. Tun daga ranar Aahil ya shigo rayuwata, duk da yazo dai-dai lokacin da zamu tafi IT, amma haka ya matsa min, kome Husnah HABIB Manga. Idan yayi koyarwa amadadin ya nutsu abinda ya shigo dashi sai yayi ta tsokanata, wanda a Gaban mutane yake nunawa yana hauka a kaina,, sai aka fara cewa ai dan nayi sa'a yana kulani ne, dan ban san waye shi bane. A gaskiya ban yarda dashi ba sai lokacin da ya fito kirkiri ya nuna shifa aurena zai yi. Amma ba damuwa na tafi IT na dawo, lokacin da zan tafi dan an rabamu gurare, sai gashi yake gaya min ya samo min pass zan zauna a zaria nayi it. Matsalar da na fara fuskanta dashi shine zai tab'a ni, ko ya rike hannuna, idan ta kama ya kwace abuna yace na amsa idan ina da karfi. Ban tab'a kawowa akwai katon matsala ba, sai da tafiyar ta fara nisa, zai turo min sako na dauki Hotona na tura mishi, ba kaya. Sai na share shi ko kuma ya shiga bani labarin banza, bani bin takanshi. Akwai lokacin da na tafi kasuwa aka sace min waya . Da ya tashi saya min waya sai da ya bani tsoro, domin ya saya min waya ce na manyan yara. Sai aka barni da b'oyewa, idan muka yi waya dashi sai yace min Kinga videos din cikin wayar kuwa. Murmushi nake nace eh. Ashe yasan tanadin da yayi a cikin wayar, ranar ina wani aiki a cikin internet, sai nake son sauke wani littafin biology, kuma dama itace course din da yake mana kenan, kullum sai yazo yana mana fada munki musayi book din shi idan ya bada Assigment, toh ranar Cape din makaranta sai an rasa gurin zama. Toh ina son saukewa a waya ce, sai naga bani da space, kawai na shiga cikin wayar, na fara dubawa, a hankali idanuna ya sauka akan wani kazamin video, kawai ban san lokacin da na sake wayar a kasa ba. Tsabar tsoron, kashe laptop din nayi sabida shi Baba ne ya saya min, duk wani abu indai karatu ne, toh iyayena suna kaina. Goge komai nayi sannan na kirashi na nuna mishi b'acin rai na, sai ya nuna min Kuskure ne don Allah nayi hakuri. Dan haka cikin dadin baki ya lallabani muka shirya. Haka kawai zai kirani yayi ta gaya min bashi da lafiya, yana cikin damuwa. Duk sai na rud'e, domin zuwa lokacin na fada wata mahaukaciyar soyayyar shi. Wanda hakan ya janyo min damuwa idan naji bai da lafiya. Lokacin da na fara zuwa gidan shi ya gaya min halin da yake ciki, a ranar na fara gwaninka dukda baka shiga ajin mu, naji ana cewa baka cikakkiyar zama na sati a makarantar amma kai ma malamine. Amma ban tab'a sanin kai din Christian ne, kuma babba a cikin a church, ban yarda ba sai da nazo naganka da wata karamar Bible. Idan baka manta ba, sai da ka tambaye ni meye ya kawo ni. "Nazo niman aljuhun baya ne" Ya fada min, kai tsaye, sai kunya ya kamani, sabida ido da ido nayita ci masa fuska, dan a lokacin ban san yana jin hausa ba. Shiru nayi sannan na cigaba. A lokacin kirana yayi wai zai mutu, don Allah nazo da sauri, na kawo mishi dauki. A ranar na kunshi bakin ciki biyu. Dan na same shi cikin dakin shi, a kwance. Kin shiga nayi yace min na shigo naki, karshe sai ya balbale ni da fada. Haka na shiga a tsorace, nuna min bakin gado na zauna. Mun jima muna zaman kurame. Kafin ya tashi ya shiga min chakulkuli. Daga nan bazan iya cema na iya sarrafa kaina da zuciyata ba, ni dai iya sanina. Iyayena basu kasance masu lalata ya'yan wasu ba, amma ni na sake soyayyar wani ya gurba min tarbiyata,. Kuka ne ya kwace min, ina yi ina karawa, sosai nayi kuka. Sannan na zuba ido ina kallon gefen hanya da ya zama babu kowa, sabida sha biyu ta kusa, tadda motar yayi, muka shiga barin gurin. Tunda ya sami biyar bukatan shi, ya shiga ban daki ina kwance, a gadon wayata tayi kara, ina dauka aka gaya min Babana yana asibiti. Ko jikina ban gyara ba, na tsallake zan fita dai dai fitowar shi, riko hannuna yayi ya turani ban daki, yace nayi wanka. A gurguje nayi na fito, zan tafi ya kalle ni, sannan yace. "Meye faruwa." "Zan tafi Kaduna ne?! Babana bai da lafiya" Buɗe drowe yayi ya ciro kuɗi, ya mika min. Kallon kudin nayi sannan nace. "Me zanyi dashi" "Karba bani son gardama." Babu yadda na iya na amsa, nayi mishi godiya sannan na bar gidan. Duk wanda yasa mace matuƙar ya ganni a lokacin toh tabbas zai fahimci nayi wasa da kimata, dan a ranar na wuce kaduna. Ban tsaya a gida ba na wuce asibiti. Tunda naje Innarmu ke bina da ido, amma cikin hikima nake dai daita kaina. Sai da ta min magana me yasa me ni, nan na mata karyan cewa na fadi a ban dakine, wallahi iyayena sun tsare min kome na. Abincina, suturana, hatta material din da za a nuna a makarantar ina kiran Baba zai saya min. Kuskure na shine makaho soyayyar da na fada, kuma gashi na fita a lokacin da idanuna suka Zama basu da amfani., Babana yana fama da cutar iskar dalma, sakamakon tu'amali da yake da inda ake tonar ma'adinai, dan haka aka daura shi a magani. Dan ciwon ta tab'a mishi huhu, dukda kudin magani da komai yabiya, dan yana da dan rufin asiri. Sai dai ciwon yazo mishi a bazata, dan kuwa bayan nagama IT, muka dawo makarantar, tun dan haka zamu biya kudin makarantar, da sauran watannin da suka rage mana. Abin tausayi Baba nacan yana fama da jinya, wanda ya kai shiga salama a gurin aiki. Dake Innarmu nada kokarin Niman kudi, da kudin hannunta akayita jiyar shi. Har Allah ya bashi lafiya, bawai ya warke ba, dake Mubarak yaki karatu yana sana'ar bakin mai. Shima yana taimakawa Innarmu. Alhamdulillah, domin bani da abinda zancewa iyayena, sai ma na rike su yafeyar su, domin Dr Aahil ya mai dani tankar matar shi, akaina yake kashe gobaran shi. Nagode da ƙoƙarin ankarar dani Kuskure na, ban gane. Ni a zatona baka son tarayya ta ce da abokinka, ashe kai guje min fadawa Hallaka kake. Tashin hankali biyu ya same ni lokaci guda, ga mahaifina ba lafiya ga makaranta ina da yakinin korata zasu yi, dan haka ka kaini tasha zan tafi Kaduna yau.." "Me zaki gaya musu idan kin tafi yau!" Ya tambaye ni, " zan gaya musu cewa bazan iya samun nutsuwa ba idan banga halin da Babana yake cikin ba" "Ok! Muje na kaiki gidan wata yar church mu!" Sauya akalar motar yayi inda ya kai ni, sabon Gari Zaria. Gidan matar da ya kai ni me suna Ruth tana da kirki, amma ban sake jiki da ita ba, sabida yadda gidan ke tashin karni. Tsabar kyankyame ban iya barci rai na cikin sallama ba. Dan ko da nayi sallah akan dan kwalina nayi. Zan iya cewa tsabar na saka iyaye na, a raina har mafarkin su nayi. Tunda nayi sallar asuba nake zaune a akan dan kwalina, dole na dauki Azumi, dan niman rahamar Ubangiji. --- Tunda ya isa gida ya zube a kujeran falon shi. Yake sauke wasu tagwayen ajiyar zuciya, sabida da tsabar tausayin yarinya da ya ratsa zuciyar shi. Ba dan komai ba sai dan yadda iyayenta suka sadaukar da rayuwarsu domin ita, itama da laifin ta. Tunda taki zama a matsayin ta ma bahaushiya me cikekken kamun kai tayi watsi da darajar ta, uwa Uba musulma. --- Ina zaune na kifa kaina da kujerar da nake kai. "Sallama! Gafaranku dai!" Kallon agogo nayi sha biyu saura minti biyar. Sunkuyar da kai nayi sannan nace. "Good Aftenoon Dr?!" "Miss HABIB Manga! Afternoon, da fatan jiya kinyi mafarkin Dr Aahil." Shiru nayi kaina a sunkuye, matar tafito cikin murmushi tace. "Pastor Bature! Bakuwar mu taki cin abinci fa?" "A'ah Aunty Ina Fasting ne!" "But yau ba Monday and Thursday bane, ko kina rama wanda kika sha ne" Yayi maganar kasa kasa, kamar bashi ba. "Hmm! Na niman yafiya ne?" " Cikin littafi Mai Tsarki, Yusha'u yayi magana da ya dace. ". Sunan Ubangiji kamar ƙaƙƙarfar hasumiya ne, inda adali yakan shiga ya zauna lafiya." Wato abinda na lura dashi shine, sam bai damu da halin da nake ciki ba. "Dr Nagode! Ina son zan tafi kaduna yau." "Ok! Muje na Kai ki tasha." Cikin sauri na mike, na isa kofar kitchen din Matar nayi mata godiya da sallama sannan na fito. Ni a tunanina Tasha zan kaina amma sai gashi ya kawo ni har kaduna. "Meye sunan unguwar ku?!" "A'a nagode!" "Kinga ki gaya min na kusan rasa jirgi na dan yau ne daurin Auren Dr Aahil!" ...... Karku manta Wannan book kuɗi ne. Idan ta bank ne=200 Idan kuma katin mtn=300 Gama su bukatar VIP=500 bank account Kuma katin mtn ne=600 Acct: 0472282105 GTBNK Ramlat Abdul Rahman Manga Idan ka biya ka sanar dani ta wannan number08130269641👈🏻 Thanks........ Idan kuma kana son Inuwar Gajimare! Kayi min magana ta wannan number! Shima. Long page.... [7/2, 8:48 PM] BAHAUSHIYAH🥰: BAHAUSHIYA 😭𝘏𝘢𝘵𝘵𝘢𝘳𝘢 𝘠𝘢𝘯 𝘔𝘢𝘵𝘢💔 𝙆𝙖𝙘𝙤𝙠𝙖𝙣 𝙇𝙞𝙩𝙩𝙖𝙛𝙞𝙣 𝙎𝙖𝙙𝙖𝙪𝙠𝙖𝙧𝙬𝙖 𝙘𝙚! 𝙕𝙖𝙞𝙣𝙖𝙗 𝘼𝙗𝙙𝙪𝙡𝙡𝙖𝙝𝙞 𝙒𝙖𝙯𝙞𝙧𝙞! 𝙈𝙖𝙢𝙖𝙣𝙖🥰 𝙈 𝙖𝙝𝙖𝙞𝙛𝙞𝙮𝙖𝙩𝙖 𝙩𝙖 𝙠𝙖𝙞𝙣𝙖! 𝙄𝙣𝙖 𝙩𝙨𝙖𝙮𝙚 𝙣𝙚 𝙨𝙖𝙗𝙞𝙙𝙖 𝙠𝙖𝙧𝙛𝙞𝙣 𝘼𝙙𝙙𝙪'𝙖𝙧 𝙙𝙖 𝙠𝙞𝙠𝙖 𝙢𝙞𝙣 𝙩𝙪𝙣𝙙𝙖 𝙧𝙖𝙣𝙖𝙧 𝙙𝙖 𝙠𝙞𝙠𝙖 𝙝𝙖𝙞𝙛𝙚 𝙣𝙞 𝙝𝙖𝙧 𝙕𝙪𝙬𝙖 𝙔𝙖𝙪😘🥰😍, 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖 𝙜𝙖𝙛𝙖𝙧𝙩𝙖 𝙢𝙞𝙠𝙞 𝙙𝙖 𝙍𝙖𝙝𝙖𝙢𝙖!🥰😍 sudden. Babi-bakwai. "No nagode sosai!" Nace mishi da sauri ina ƙoƙarin niman inda zai sauke ni. "Look at me!" Kasa kallon shi nayi, sannan ya cigaba da cewa.. "Ohk! Take the code is 2356! Make sure ranar monday kin dawo Zaria, nd keep your mouth quite, don't let anyone know what is going, in ba haka ba zaki iya rasa one of your family, ba a gayawa iyaye any nonsense problem, ana raba wasu tsakanin zuciya da ciki ne. you understand what I'm saying!" Gyad'a mishi kai nayi, sannan nace. "But Dr! Ni ban san ya zanyi da Atm ɗin ba, idan Innarmu ta gani zata min fada tace ko." "Ranar can da guy din nan ya baki me yasa baki gaya mishi about your family ba, when dem saw you with money, Ni taimako nayi idan yayi miki fine idan bai miki ba you can keep it nd go" Shiru nayi ina share kwalla. "By now you have two challenging, firstly pregnancy test! Secondly any diseases test, example, HIV!" . Da Mugun sauri na d'ago kai ina kallon shi. "Yes da nakira Pregnant Baki razana ba, sai HIV! infection, da sauran dangin wasu diseases." Haka ya gama ruda ni sannan ya samu gefen titi yace. "Ki gaida min Parent dinki Dan nasan su din Mutanen kirki ne, Sabanin You," Sauke numfashi nayi sannan na daga Atm na ajiye mishi a gaban motar zan fita ya riko hannuna, a tsorace na juya. "Ban tab'a kyauta anyi min rejected din shi ba, ni ban ce ke na bawa ba, ki Mubarak Zakiwa Explain zaifi kowa fahimtar ki, and please karki saka damuwa a ranki, wanda zai sanya su fahimci kina da matsala." Fita nayi daga motar, sannan na sunkuya dai-dai window nace. "Thank you for your help! Dr " "Mr Arrogant!" Shiru nayi na juya baya ina share kwalla, fitowa yayi daga motar. "Heyyyy! Miss HABIB Manga! Kuka kuma? Shi Ubangiji da ya halicce mu yayi mu da mabanbantar halayyar mu" Gyad'a kai nayi sannan na juya, me zancewa Mutumin nan. Komawa nayi daya gefen na tari Napep, inda nace ya kaini, Tudun wada. Muna tafiya hankali na duk ya tashi, har na isa Unguwarmu, Bashi kudin shi nayi sannan na nufi taburin Mubarak, wanda yake sayar da bakin mai. "Muba! Ya jikin Baban?!" Murmushi yayi sannan yace. "Da sauki, amma suna Asibiti." Yadda yake maganar kawai ya tabbatar min akwai matsala, "Ki shiga daga ciki, Maryam tana." Da sauri na shiga, na sameta tana girki, "Addarmu." Ita da Abdullahi suka ambace suna na. Da gudu yar yarinyar da bata fi shekara biyar ba tafito tana me fadawa jikina. Kasancewar Innarmu ta daina Haihuwa, sai Kaninta Kawu Tanko ya bata Lu'lu'a. Muna kiranta da Lulu. Yarinyar ta shiga ranmu sosai dan sonta muke kamar me, kuma bata tab'a rikici ba a kai ta gurin Iyayenta. Kallon Maryam nayi nace. "Meemah! Ya jikin Baba!" "Hmm! Da sauki." "Wani asibiti ne?!" "Specialist" Ta faɗa min a takaice, Shiga dakin nayi na duba kwatina, kudin gurin Dr Aahil na dauka sannan na fito, da sauri ko sauya kaya banyi ba na nufi waje. Ina fitowa Muba ya mike tare da ciro wata fatattake Naira dari biyu ya mika min cikin damuwa yace. "Addarmu! Ga wannan kiyi kudin mota. Ga Maryam bata gama abinci ba" "No need, Ina son karaka ni na samu abin hawa." A hankali muke takawa, ina ta kame kame, can daure na yanki mishi karya. "Muba! Kasan wancan satin akayi bikin dan Governon CBN! Toh Amaryan kawarmu ce Dan haka mun je bikin, inda aka bamu kudin ƙawance,, kasan harka da manyan miliyan daya aka bamu muka raba kowace tasamu dubu dari biyu." Shiru yayi kamar bada shi nake magana ba, har na fara tsargu yace. "Ai kardai kin san! Faruq Aashiq Muhammad! Ikon Allah! Shine jiya kika ki saurarona." Tausayi ya bani nima kuma na bawa kaina. Mika mishi kudin nayi na cire wanda za a bukata, sannan na shiga Napep. Inda na tadda yan mata biyu. Dake na rufe fuskana da nikab. "Hmm! Ai ance haka yan matan jami'a suke, zubda kimar su na ya'yan mata suke, sannan a koro su." Sai naji na tsargu da kaina musamman idan aka ce abu ya same ka. "Eh ai ance sau uku yana mata ciki na karshen ne yaki amsa shine ana ruwan sama jiya dan taji zaiyi aure shine taje mishi tujara, shi kuma yayi mata duka, karshe aka watsota daga Jami'an, mata sun koma kamar dabbobi." Wato idan na fahimta labarina ne ake yawo dashi, kwalla ne ya cika min ido, na kauda kaina. Muna zuwa ya sauke su, har zasu sauka nace musu. "Bayin Allah! Karku manta ku mata ne? Kuma iyaye ne?! Babu amfanin kalubalantar bahaushiya yar uwanku dan zanen kaddararta ya shata cikin wani halin rayuwa. Karku manta idan muka tozarta junarmu. Duniya tozarta mu zata yi, alakulli halin mu kasance masu yi wa juna uzuri, da girman ka sai kaga Allah ya jarabce ka da abinda baka tab'a yi ba. Muje Malam, fata na gari lamiri, kar ya dawo kan yaranmu.". Sai naji na sauke nauyin dake zuciyata, har na isa asibitin, ina fita zan biya me Napep din yace. "Y'ata bar shi, Nagode, ki Cigaba da rike gaskiya Allah zai dafa miki, karki yarda a hada kai dake a cuci wani." "Nagode sosai Baba" sannan na juya ciki. Innarmu na hango tana share kwalla, still Tana murmushi, da sassarfa na isa gareta nace. "Innarmu! Lafiya kike kuka?" Wani irin kuka Innarmu ta sake, har da shasheka tace. "Yanzun wani wanda bamu sanshi ba ya biya kudin asibitin, har da kudin jinya da wanda zamu sayi abinci." Zama nayi dabas nima na shiga tayata, sai da muka yi ya ishemu sannan muka nufi dakin da Baba yake, Allah sarki rai ba a bakin komai yake ba, baba ya fita hayacinshi kamar ba shi ba, duk wani taimako ta hanci ake bashi, hatta iskar shaka. Muna tsaye aka kai shi wani daki na daban asali gurin babu hayaniyar mutane, Aminety. Waye wannan yayi sudden din mu, hawayen dake bin idanuna babu iyaka domin ban san waye ya sudden me lokaci guda. Duk inda yake ina mishi fatan Alkhairi. Ina kallon Baba yadda yake barci sai ya bani tausayi, sabida yana kwance a gurin ne b'cos of me! Yasha wuyar yan uwan shi sabida ni. *Allah ya isa min Aahil, bazaka tab'a samun Successful a rayuwarka ba, sai kaga bakin ciki iya ganin idanunka._* "Ke Ban son shirme Waye kikewa Mugun fata haka." A farkon na dawo hankalina, na shiga cewa. "A'a wani ne ya zalinci Teemah!" "Ayya Allah zai bi mata hakkinta." "Amin" --- A hankali ya isa airport, cikin mutuwar jiki, ya gama kome sannan ya nufi inda jirgin yake wanda aka rubuta CAN airplanes. Ma'ana Christian Association of Nigeria. A hankali ya zauna nan wasu yan mata suka shigo kawo mishi abin rab'awa har da wine. Murmushin sa me tsada yayi sannan ya girgiza kai. Alamun baya bukatar. Dauko wani abun puzzles ya ciro a aljuhun Inda yake, sannan ya fara murzawa, yana bukatar ya hade kowani color a mazaunin

Chapter 3 of 10