Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 10
har za ki ce na shj madafi na diba, ta juya, darling rabu da wannan matar duk bakin kishi ne ya ke damunta, kuma a haka zata kare. Shema'u ta ci gaba da canja tashoshi ba ta sake kula su ba, yana tsaye ranshi ya dada baci yaje ya kashe TV din to ba zai yiwu ba, Shema'u na ga kina son kawo min matsala gidana ki shiga hankalinki ban da abunki ai Ummu yarinya ce kuma naga kina so ki saya wa kanki raini amma zan yi maganin ki, ya juya zai koma dakinshi ta dubi 6 ummu ta ce ki kuma kiji tsoron Allah, nan na fito da abinci na kira ki amma kika cc min ba yanzu ba, shi ne yanzu don makirci za ki ce na hana ki abinci? Nan Ummu tasa kuka wa Shen a'u da zage ta ya fito ranshi a 6accd ya cc "mujc Mr. Biggs." Ta shiga dakinta ta dauko gyalen da shi da babu duk daya, irin gyalen da mazan da ba sa kishin matansu su ke saya musu ta sa takalmi masu tsini zai fita Shema'u ta cc ga abincinka can fa ya cc sai ya dawo su ka fita. Bayan dawowar su nc Ummu ta cc, ai wannan abincin Shema'u ta saka magani kuma idan ya ci gaskiya ranta ba zai mata dadi ba. Nan ya hakura kasancewar baya iko da kanshi a takaice duk sanda Shema'u ta yi girki Nazir ba ya ci, wai ana saka masa magani bai san yana kwana cikin magani ba, karewa ma ba ci ba. Kullum kwanan duniya Ummu ba ta san yau kwanta ne ko na 'yar uwarta ba, don kafin ya shiga dakin Shema'u sai ya gama komai da Ummu sannan ya shiga dakin Shema'u, wataran sai ya kai karfe daya sannan ya fito daga dakin (ta musamman) ya shiga in da ba ya son, wataran kam sai ya dau kwanaki bai leka dakin Shema'u ba, Shema'u ta bi ta lalace duk ta rame ta rasa yadda zata yi. Yau ta na dakinta kwance da baby dinta tana tunanin yau nice Nazir ya ke gasa wa gyada a 7 hannu, alhalin da kyar ya yarda ya aurı Ummu, duk da 'yar uwarshi ce amma da cewa ya yi mcyc zai yi da wannan mace ba wani diri ba komai sai kace (tabarya) amma yanzu ka shi mai kama da tabarya ta fita mutunci a gun miji amma sai dai komin daren dadewa gaskiya zata yi halinta, karya furc take kuma komai na duniya ya na da iyaka. Ummu ta fito ta iske baby Nur tana zaunc akan keken yara na koyan zama, tana zuwa tra fara mata wasa tana tura ta akan keken da yake baby yarinya cc nan ta fara 6al6ala dariya. Nazir ya na shigowa yaga Umu na yi wa 'yarshi wasa, nan ya ji dadi ya ziyarce shi a take ya sake jin son Ummu a ranshi, sai ya shiga tsokanar su ya na yiwa babyn wasa ya dauki baby su ka shige dakin Ummu, nan da nan bakin ciki ya ziyarce ta ta 6ata fuska ta karbi babyn ta aje ta ta ce gyara na maka tausa, don yanzu lokacina ne ba na baby na ba dariya ya yi ya ce (ina son haka tawan) nan ta shiga yi mashi kissa da kisisina, shi ko dadi ya ke ji. Duk wani dangin Nazir Ummu ta gama dasu duk sun fi sonta akan Shema'u duk in da ta zauna sai ta yi ta bakanta Shema'u kasancewar Ummu 'yar uwa ce a gidan su Nazir amma ta wajen Hajiyar Nazir. Kullum idan ta shiga gidansu Nazir abun da zata ce shi ne, gaskiya ita fa idan tana bacci takan yi mafarkin abun tsoro har wani yana zuwa mat ata windonta yana cewa ta fita nan ba gidan zamanta ba ne, to anan fa gurmi ya farfa tashi wai a ne ma mata taimako kada yar uwarta ta haukatata ko ta yi mata lahani, Allah Sarki. Ita ko Shema'u da take zaune a gida ita da babu dun daya bata son ma me ke faruwa ba ashe dangin Nazir har cewa suka yi Ummu ta daina amfani da ruwan famfon gidan da abu ya yi abu har ta daina shan ruwan gidansa (pure water) ko maltina ko swan. Kasancewar Nazir Business ya ke daga Yola zuwa (Dubai), a duk san da zai tafi to kudin kashe ko na dawainiyar gida yana hannun Ummulkulthun, gaba daya dangin mijin sai su ka. fara (Respicting) dinta don duk wanda ya ce ga bukatarshi to zata dau kudin Nazir ta yi musu ko nawa ne, shi kuma ba shi da bakin yin magana, ba a kwana uku sai mahaifiyar Ummu ta aiko a karba mata kudi sai ka ce (bank). Kuma koda Nazir ya tashi yin tafiya dole sai yaje ya sallami mahaifiyar Ummu don dolen shi ne ya je in ba haka ba ya gamu da bacin ran Ummu. Kawar Ummu tazo gidanta ta kawo mata ziyara suna cikin daki sai Hani ta dubi Ummu ta ce Anutynki bata nanne? Ummu ta yatsina fuska ta tura baki tana dakinta kinsan yanzu falon ya mata zafi don ba na ragar mata. Hani ta ce gaski, ba kya 9 kyautawa don Allah ki dinga ragar matga kada wata rana kashinki ya bushe, Ummu ta yi dariya ta ce, wallahi karya take yi, domin naje fa ba cafe kuma a haka zata kare sai bakin cikin ya kashe ta tunda dani zata ja, kuma na riga na zame mata kadangaran bakin tulu a karni akar tulu a barni na 6ata ruwa. Hani ta yi dariya tace "To Allah ya shirye ki Ummu." Ta tabe baki dama can a shirye nake, Hani ta ce "To amma dai wannan takun saka ya yi yawa ku dan sassauta ke fa kece karama, hum zancen kishi fa ba wata waye-waye, kuma kishiya ba abun yarda ba ce ko kanwarka ne ta zama kishiyar ka to sunanta kishiya, Hani ta katse ta, to sarkin kwaba me ya kawo maganar kanwar ka ta zama kishiyarki in ban da shirmen ki, Ummu ta yi dariya ta ce, to ai ke kin zake da yawa irin wannan ketente ne gida haka, azo garin ku a fiku iya rawa, hum ke ma kin san kowa samu rana...dole ta yi shanya, in ji Tani. Ummu ta nisa ta ce, to ai ni ba ki sani ba wai jibi Nazir zai tafi (Kwatano) kuma wallahi ni yanzu bana so ya yi nisa dani da kullujm idan ba na tare dashi bana jin dadi kuma gashi ya riga ya sabar min da wasu abubuwa...Iye? Ummu me kike fada? Lallai na yarda shiru-shiru a layi amma yanzu d akika yi aure duk sai ki ka zama iwa uwar mata su ka wakwashe da dariya su ka tafa, Hani ta ce to 10 Allah ya shirye ki Ummu ta ce dama can a shirye nake. ASALIN LABARI Nazir da na ga Alh. Yusuf amma ba shi ba ne babban dan shi, shi ne kusan dan shi na shida amma a gun mahaifiyarshi shi ne na uku mata, Alh. Yusuf uku ne H. Aisha ita ce uwargida sai H. Halima sai amaryar su Hauwa amma ita b ai kai ta Makka ba, Alh. Yusuf dan kasuwa ne kuma shahararren mai kudi amm ba ya nuna wa duniya wai shi mai kudi ne sabanin sauran masu kudi. Alh. Yusuf mutumin Zaria ne a wani kauye da ake kira (Hunkuyi), ba zazzage ne na asali amma sai Allah ya sa arzikinsa yana garin (Yola) a nan ya auri Aisha 'ya'yansu biyu ya auro Halima su ka fara jera haihuwa da uwargidanta Aisha har Allah ya kawo Hauwa. Nazir ya na da yayu maza uku mata biyu Rakiya da suwaiba sai Ibrahim, adam Nura, sai kanne Abdullahi, Khadija, da kuma Halima, takwarar Hajiya karama wato Hajiyar su Nazir, Nazir dangata ne a gun mahaifiyarsu amma shi fari ne, sauran yayun shi da ya ke bi masu bakeke ne babbar 'yarshi Hajara ta na aure a Zaria sai 'ya'yanshi Abbakar sai sauran kannenshi to kasancewar shi ne ya karanci Business sai mahaifinshi ya dora shi akan dukiyarshi tun suna 11 safara tarc har Alh. Yusuf ya daina komai Nazir ne mai yi ya na tafiya Kotono, Fatakol, da sauransu to kasancewar shi ne dan zirga-zirga a garuruwa, sai ya samu daukaka a gidan don komai shi ne mai yin hidima a gidan sabanin yayunshi, Nazir irin mutanen nan ne masu kamun kai ba shi da hayaniya, nutsattse ne. Nazir ya na da wata yarinya da su ke soyayya Jamila, kowa ya san su tare kwatsam Malam Jibrin aminin mahaifin su Nazir ya na zaune tare da 1yalansa gwanin ban sha'awa suna dan taba hira ya dubi matarsa ya ce "Ya kamata yan wannan yaro Zakariyya ya fito a gama magana da yarinyan nan don ina so ta yi azumi a dakinta. Nana Bilki ta dube shi wato matarsa ta ce "Hum, ai an ba shi 'yar'uwarsa wai hadin gida zasu yi amma shi ya ce baya sonta, Malam Jibrin yayi dariya ya ce yaro kenan, lallai zamani ya canja har iyaye su ce ga wacce za su ba ka amma don taurin kai irin na yaran zamani sai su ce ba haka ba. Gaskiya bai kamata ba, an sai dai Musulunci ya ba da dama ka zabi matar da ka ke so to amma dole ne ayi musu biyayya ko dan samun kyakkyawan karshe, Nana ta ce kai ma dai kasan yaro idan ya kafe sai dai addu'a ya ce to Allah ya rufa asiri. Su na cikin hirar su yaro ya yi sallama, wai Shema'u tazo in ji Zakariyya da ma ta na daki Baba 12 nc ya ce wa yaron je ka cc ya shigo, Zakari ya shigo msu ka gaisa Baba ya cc Zakariyya ba mahaifinka ya yi maka mata ba? Kanshi a sunkuye ya ce Baba ai ba mu daidaita da ita ba, Baba ya yi dariya ya ce ba mahaifinka ba ne ya zaba maka ita ba? Shi ne, sai Baba ya fara mar nasiha kamar haka. "Ina so ka kasancc mai biyayya ga iyayenka kayi hakuri ka karbi tayin da su ka yi maka, insha Allahu ba za ka tabe ba, kuma ka zama mai yarda da kaddara kairi wa sharri (mai kyau ko mummuna), kayi hakuri kuma insha Allahu idan Shema'u rabon ka ce sia kaga ka aura idan kuma ba rabon ka ba ne to Allah ya sa haka shi ya fi alheri, Zakariyya na tsugune ido sun kada har tausayinshi ya kama ni saboda nasan ciwon so. Da Baba ya gama yi mashi nasiha, ya mike jiki babu laka ya yi zauren mu, gurin da muke hira, Baba ya ce "Shema'u ga Zakariyya ya na jiranki, Nana Bilki ta ce ko akwance ta ke, Shema'u ta fita jiki babu kwari tashi ta yi hanyardakin zaure wato dakin Kabiru yayanta, ta shiga da sallama ya na une kan kujera a sanyaye ya amsa kasancewar asan halin da ya ke ciki bai nuna masa komai ba, ta ya zakariya sannu da zuwa, ya dube tga da kyau ya kare mata kallo a zuciyarshi ya ce zan yi missing dinki amma a fili ya ce da girman kujerar ki, ta yi dariya yaya kake? Ya yi tsaki mits, babu yadda nake 13 Shema'u ta zaro ido mc ya faru? Ajiyar zuciya ya yi ya cc, "kina nufin ba ki san komai ba ne, a game da halin da nake ciki? Ranta ya dan baci da ya tuna mata wannan takkin orber da ake shirin yi musu, ta dan kanne damuwar ta ta ce, to meye what? Kina nufin ke bai dame ki ba? ashe dai ni kadai nake haukana? Please Zakariyya ba haka ba ne kasan komai mukaddari ne to amma tunda da abu ya zo haka ina mai baka shawara komai ka gani daga Allah ne, so dan haka kayi fatan alheri a game da wannan lamari, ni kam Allah ya na gani ba ni na ki ka ba......dakata Shema'u wannan yarinyar da aka ba ni fa tafi ni a haife kusan sa'ar uwatayes ana haka ai, tunda Annabi Muhammad (S.A.W) ya auri matar da ta fi shi shekaru, so ashe don ka aure ta ba laifi ba ne, ranshi ya dagule ya mike zai fita ta tsaya a bakin kofar kayi hakuri idan ranka ya baci ba wai na fada da wata manufa ba ne bai saurare ta ba ya fice ran maza ya 6асі. ** Hadiza ce ta shigo da sallama Shema'u zo ki raka ni School dinmu na karbo testimonial dina nayi nayi yaya ya kaini ya ki na ced ki fada wa Nana Hadiza ta shiga daki ta gaida Nana Bilki, Nana Bilki ta tambaye ta su Hajiya da sauran yara, ta ce duk lafiyarsu kalau, suna gaishe ku muna 14 amsawa idan kin tashi tafiya ga sako zan ba ki ki kaiwa Hajiya Babba, to dama ina son Shema'u ta raka ni School ne zan kar6o takardana naji 'yan ajinmu sun ce wai an fara raba (testimonial) Nana Bilki ta ce to kada kudaďe Baba zai muku fada ku dawo da wuri su ka cc to Nana mun gode suna murna su ka fita a hanyar su ta tafiya ne su ka hadu da Zakariyya Hadiza ta tsaya suna gaisawa Shema'u kuwa ta wuce ba ta tsaya ba Hadiza ta ce, ranka ya dade yaya yau nagan ka beari lazyhate me ya faru? Ya yi dariya ya ce babu komai kawarki ce take waina ni ta yi dariya ta ce mc ka mata take wainaka? Yo ina na sani kinsan ku mata da mulki my bc mulkin ce yau ta motsa, a'a Zakariyya ruwa ba ya tsami banza amma dai ka bari mu dawo kada mu yi latti ina zaku je haka? Wallahi zamu school din mu ne naji an ce wai 'yan JSCE ana raba musu (testimonial) dinsu shi nr zan jc na karba, to ko nazo na kai ku ne? A'a bari kawai yanzu zamu dawo, to sai kun dawo zan jira ku ta ce to Hadiza ba ta samu Shema'u anan kusa ba sai da ta yi nisa sannan ta ji rata ta iso ta same ta, amma kin ban kunya mutum ya hadu da masoyinshi amma ko ya kula shi yau an gan ku a rana, Shema'u ta ce, share shi kinsan meye? Sai kin fada." In ji Hadiza, Shema'u ta karkata kai ta ce ai tun da naga kin tsaya kuna ta wani surutai nasan ba ki san komai ba a 15 game da lamarin shi ba, ni kam faďa min don Allah ba na son wani dogon sharhi, hum "Zakariyya ammashi mata, wai aure dangi za'ayi mashi Hadiza ta zaro ido da gaske wallahi ke kinsan waye matar shi? Hadiza ta ce a'a sai kin fada ta tabe baki ta cс wai Ruky, Rukaiya zai aura wannan 'yarshi ce da gaske kike ko da wasa? Da gaske nake miki wannan zance to amma shi ya nuna min wai ba ya son wannan aure ni kuma duk jinshi nake kinsan su maza su na ba sa son mace amma da zaran an yi biki za ki ji su shiru Hadiza ta ce to 'yan keya ya ku ka yi? mtsi....ta yi tsaki wai yanzun ina tausar zuciyata ne tun daga yanzu na fara hakuri da son sa kin san ma meye? wai yanzu yazo ya na ce min wai shi me zai yi da Rukayya da sauransu ni kuma na ce masa ai komai nufin Allah ne. Sun dawo sun iske Baba a gidan Alh. Yusuf ya na ta yi mana fada wai mun dade ranar a gidan su Hadiza mu ka kwana saboda nasan Zakariyya zai zo gidanmu sai na tura Hadiza taje ta fadi wa Nana Bilkisu. A washe gari da safe kawai sai ga Nazir ya shigo, muka gaisa da shi sai na ji su Hajiya su na cewa yaushe ka dawo? Ya ce shigowar dare mu ka yi aka kwance tsaraba mu ne yan fasa kwakwa, muna cikin yin haka aka kawo abarba mu ka hau yankawa, muna ta sha na dubi Hadiza na ce "Hadiza 16 ina ma acc na auri Nazir ya yi ta kawo min tsaraba, Hadiza ta dauko min kujera ta sa a bayana muna ta dariya wai santin zakin abarba nake yi muka yi dariya son ranmu har su Hajiya su na cewa wannan dariyar haka ai sai ace kunyi gamo ne. Da ya ke Hadiza ta fi ni wayo, ko a haife ma ta dan fini sai ta yi ta zuga ni wai wallahi na fada wa Baba ni har na manta sai ta ce wai na fada ni kuma da ya ke bani da wayo sosai, don duka-duka shekaruna sha hudü ne, ranar mu na zaune ni da Baba na ce "Baba wallahi ni kam ina son Nazir din gidan Alhaji, Baba ya yi dariya ya ce "Allah Shema'u? Da gaske kina son sa?" Na ce "Wallahi Baba ina sonsa." Baba yazo ya- samu Alhaji Yusuf a gida bayan sun gaisa ya sanar da shi na ba wa dana Nazir Shema'u, Alh. Yusuf ya yi murna ya ji dadi sosai, ya ce Allah ya saka da alheri na gode, Allah ya dada girma, Allah ya sa a yi damu. Baba ya ce "Babu komai, Allah ya ba su zama lafiya." Alh. Yusuf ya shiga gida ya shaidawa matansa, ai kuwa kowa ya yi murna da farin ciki Alh. Yusuf ya kira danshi ya shaida masa, nan Nazir ya rude saboda ya ji abu ba zata gashi kuma ya na da tashi masoyiyar wacce su ke soyayya unguwar su daya ya ce Alhaji ina da wacce na ke so, kuma mun yi alkawari, to ka yi hakuri tunda ga wanda mu ka zaba maka, tashi kaje. 17 Dakin Hajiyarshi ya shige ya sanar da ita komai, ta ce to meye ne don an baka Shema'u? Gaskiya ni Hajiya ba na sonta, ina da wacce nake so kowa ya sani a gidan nan, Jamila na ke so shi kanshi Alhaji ya sani, to kuma shi ne yanzu a ce na auri Shema'u, ni kam ba na sonta, Hajiy. ta harare shi tunda ba ka sonta sai ka je ka samu Alb ji ko Baban ku Jibrin ka fadi mashi, tashi ka bani guri ya na tsugune bai tashi ba ta share shi ta ci gaba da gararinta. Nazir kai ya dau zafi, ya rasa meye abun yi ya samu Sulaiman abokinsa ya sanar dashi halin da ya ke ciki, Sulaiman ya bashi hakuri, Nazir wannan zabi da iyayanka su ka yi maka insha Allahu ba za ka yi deegreating ba, so don haka ka yi hakuri ka karba me laifin Shema'u? Mace ce har mace duk in da ka ke son haduwar mace Shema'u iyaka cе. Nazir ya katse shi cafanen Likita ce fa? Meye abun sha'awa ga farar mace? Na ji ban ga abun sha'awa ba, amma dai ya zama dole kayi biyayya ga iyayenka, me ka gani? Nazir ya na shiru bai kula shi ba, can ya nisa ya ce "Sulaiman ina son Jamilash don babe din ta hadu sosai, Sulaiman ya ce to ka yi hakuri dai mu mika lamarin mu ga Allah Ubangiji ya zaba mana abun da ya fi alkairi, Nazir ya nisa ya ce amin. 18 Nazir ya samu Hajiyarsu a daki ya gaishc ta ya na tsugunc a gurin bai ce kala ba, ta dubc shi ta ce lafiya? Ya sunkuyar da kai kasa ya ce Hajiya ni fa gaskiya ki fada wa Alhaji wannan magana na Shema'u a barta, tsawa ta daka mashi ba ka isa ba, ai mu mukia haifc ba ba kai ka haife mu ba, kuma na ji ka ce za ka bar garin, to duk in da kaje za ka dawo kuma ka same ta don haka dabara ta rage naka, aure babu fashi nan da sati biyu tashi ka bani waje. A rude ya shiga dakin Sulaiman ya yi bala'in gigicewa ya fada wa Sulaiman duk abin da ake ciki, Sulaiman ya ce don Allah ka nitsu ka kwantar da hankalinka komai ya yi farko zai yi karshc, Nazir ya katse shi wallahi Sulaiman na tsani Shema'u, kai duk wani dangidan......Sulaiman ya katse shi ya isa haka, ka kwantar da hankalinka yanzu meye abin yi? Sulaiman ya tambaye shi Nazir ya nisa ya ce ka je ka samu Alhaji ka ce ba na son ta ina da wacce na ke so. Sulaiman ya kwashe da dariya, ya cc saboda ni ne tsagera? Sai na je na soke aure ko, to bari ka ji, ni dai nasan meye soyayya, kuma na taba yinta naji yadda take, nasan zakin ta na kuma san dacinta, don haka ina mai ba ka shawara ka karbi zabin da iyaye su ka maka, Allah ka samu ka rabo, kuma kaima 'ya'yanka za su yi maka biyayya, please Sulaiman 19 sati biyu fa su ka ce two wecks fa yanzu mc Jamila zata daukc ni? Kuma tasan ina sonta, kai dai yanzu duk wannan ba ta taso ba, kai dai kawai kajc ka samu Jamila kayi ma ta bayanin duk halin da ka kc ciki, kada ta ji a bakin wani ta ce ka munafurce va, kasan su mata ba a musu gwaninta bai ce komai ba ya yi tagumi kamar wani mutum-mutumi, haka Sulaiman ya lallashe shi su ka dunguma gidan su Jamila, kasancewar bayan layinsu ne ba wani nisa ba ne dasu, sun ci sa'a kuwa sun same ta amma tana fitowa su ka gane ta ji labari, amma ta dan boye damuwarta, su ka gaisa ta dubi Nazir ta ce "Ango da ma ka na ganuwa? Ya kwakwalo dariyar karfin hali ya ce gani kuwa? Ta dubi Sulaiman ta ce ku ana shirin angwanci ana kiba amma ku sai ka ce kudin guzuri. Sulaiman ya yi dari ya ce, kinsan mutun zaj shiga sabuwar rayuwa dama haka ne, amma dai ga ki ga Nazir, za ki ji komai daga gare shi." Nazir ya dube ta cike da sha'awar irin dressing din da ta yi, ya karkata kai ya ce, Jamila da farko ina son ki sani komai nufin Allah ne, kuma duk iya kokarin ka ga ka samu abu idan Allah bai nufa ba to babu mahalukin da zai ba ka komin yaya.....ta katse shi wai duk wannan dogon sharhin na menene Nazir? Ka fadi abin da zaka fada, ya yi shiru bai ce komai ba, can ya nisa ya ce "Jamila sanin kanki ne 20 kinsan ina Kaunarki, to amma wai yau an wayi ga an cc za a min auren dole da wacce ko kusa dani in nace tazo zata ji tsoron zuwa, amma wai yau ita za'a aura min, sai ka ce mata sun kare? Jamila ta ce na ji labari amma sai na musa saboda Shema'u ba ajinka ba ce, amma sai naji da kunnena kai da kanka kana cewa za a maka auren dole to ai sai ka so tunda kai ne me auranta ba ita ce mai auranka ba. yanzu dama Nazir duk fata min lokaci da ka yi ya tashi a banza kenan? Ka sa na kore samarina waton ita Shema'un da aka yi mata snaching din saurayi shi nc ta rama akaina? Yanzu kai kana nufin shi kenan mun rabu kenan?" "No, ba mu rabu ba, kinsan ba zan iya rabuwa da ke ba, in Allah ya yarda za ki shigo gidan nan nawa kuma kece first lady dina kin dai gane? Ya dube ta, yes na gane amma gaski......sai ta yi shiru, ya sake dubanta gaskiya meye? "Babu komai." Ta fada ** Ana saura sati bikin Shema'u da Nazir, Nazir bai taba zuwa hira ba kuma ko sun hadu idan ta gaishe shi bai cika amsawa ba, ranta ya dan Gaci kadan amma sai ta share. Idan ta hadu da Jamila sai bakaken maganganu, gashi uwar Jamila irin 21 matannan ne 'yan duniya wanda ba ta ji ba ta gani wajan nema wa 'ya'yanta 'yanci in ji ta. Mun dawo unguwa ni da Hadizan su Nazir, mu ka yo kwanar gidan mu sai mu ka ga Nazir su na tsaye da Jamila su na hira, raina ya dan sosu amma na dakc naki kula su, muka wuce Hadiza ta cе Shema'u don Allah kiyi hakuri nasan dole ne ranki ya baci, na kalli Hadiza na ce ai duk kc ki ka cисe ni kika zuga ni har naje na fada wa Baba ina son Nazir, kuma ni kam da zai yiwu da na je na ce wa Baba na fasa. Hadiza ta ce "Wallahi kada ki kuskura ki fasa, ai in kunyi aure zai daina wuya ne dai ku zama mallakin juna, kuma sai ya zama tarihi. Ana bikin wata Haule duk kawaye ne da Hadiza da su Jamila to kasancewar Shema'u ba tsarar su ba ce saurin girma dai kawai ta yi Hadiza ta sa haule ta gaiyaci Shema'u suin je wajan (Deener) kowacce ta ci kwalliya da ya ke Jamila tana da rawar kai da kwadi ita kuma Shema'u ta na da miskilanci don har jama'a suna cewa ta fiye jin kai kuma ba haka abun ya ke ba, (natural) dinta ne haka, gaskiya kuma Shcma'u fara ce kyakkyawa ga diri gaba dayansu sun hallara a ball din can sai ga Jamila sun isò ita da saurayin da ya ke nema ya zama mallakin wata. Jamila ta kalli haduwar da Shema'u ta yi ta ja tsaki duk sauran kawayenta sai da su ka juyo, 22 Hadiza ranta ya baci sai Nazir ya yi mata alama da su zauna su ka nemi waje su ka zauna, Jamila ta sake jan tsaki Nazir ya tambayc ta lafiya? Ta muskuta ta cc babu komai su ka ci gaba da harkokinsu, Shema'u ta ce Hadiza ni kam zan tafi gida dan mc? Tа сс "Babu komai Hadiza ta gane dalilin da ya sa ta cc zata ta fi gida, sai itama ta mike "Mu tafi Shema'u." Ta cc 'a'a kiyi zamanki ai ba a gama ba tunda ko farawa ba ayi ba, No, muje kawai su ka dau jakarsu za su fita Jamila ta cc Hadiza ina zuwa? Hadiza ta yi kamar ba ta ji ba ta fice ta iske Shema'u a waje su ka tsayar da masu mashin kasancewar babu masu tasi motocin 'yan biki kuwa ba su fara diban jama'a ba. Su na isa gida Shema'u gidansu ta wuce, kowa ya shiga nasu gidan Hadiza komawa gida ta fadi komai duk abun da Nazir ya ke yi wa Shema'u, Hajiya ranta ya 6aci sosai. Ita kuwa Shema'u ta na shiga gida randa ta nufa ta debi ruwa mai sanyi wai dan taji sanyi zuciyarta, Nana ta kalle ta ta ce lafiya a'a babu

Chapter 6 of 10