Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
10 / 10
to a lokacin mu ke da 'yancin kaita wannan wane irin rashin imani ne, Baba na ya karbi Nur a hannun Nana ya juya da 68 niyyar kaita gidan su Nazir da kansa, kawai sai mu ka ga Anas a tsaye ashe tun da na shigo da gudu shima ya biyo ni baba don Allah kuyi hakuri ni na dauko ta a hanya wallahi da ta fada min ba zan kawo ta ba, asibiti zamu tafi ya karbi Nur ya ce taho muje mu kaita mu ka tafi kai ta har da mahaifiyata. Munje mun sami ganin Likitar yara Doctor Fiddausi ta shiga kula da yarinyar ta ce zafin zazzabi shi ya haifar da jijjigar nan da nan aka yi ma ta wata allura sai kuma ta samu bacci gado su ka ba mu ma'ana dai an kwantar damu mahaifiyata ta ce bari ta kawo mana abin da muke bukata, Anas ya ce bari in kaiki in yaso nima sai in kawo abin da suke so su ka fita tare. Na kife kan gado ina kuka saboda bakin cikin kishiya da na miji yanzu ni Nazir ya ke wulakantawa haka bai ga abun da matarsa ta yi wa 'yarsa ba wai Nur din da Nazir ya ke raba dare ya na kallonta saboda dadewar da muka yi ba mu samu haihuwa ba ita ce wacce bai damu da ita ba, yanzu haka rayuwata zata kasance? Amma fa ina ganin laifina ne tunda ni ce wacce na nuna ina sonsa har aka kai ga hada auranmu, to ai Nazir ya so ni so ba na wasa ba, babban takaicin ban iya son wani in ba shi ba shi kadai zuciyata ke so, Allah ka yaye min son Nazir don sonsa ba shi da wani amfani a gurina. 69 Doctor Fiddausi ce ta ce, ke bacci kikc har drip din da aka sa ma ta ya kare, jinr har ya soma shiga rabo na dago idanu a kode na ce wallahi ba bacci nake ba, ta kalle ni ta ce haba 'yar uwa ki daina damun kanki za ta warke yanzu abun da kananan yara suke fama da shi kenan, ta kalle ni ta ce sai dai na rasa dalilin kumburin fuskarta ko wani abu ya fado ma ta, saboda bakin ciki ya na cin zuciyata ban san sanda na ce ma ta marinta aka yi. Dr. ta zaro ido ta ce mari dan rashin Imani wanne yaron ne ya yi mata wannan marin? Abikiyar zamana matar mahaifinta, kuka ya kwace min ta tsaya kawai tana kallona can ta ce ni sai naga kamar na sanki ko kuma in ce ana nuno ki cikin TV kina wa'azi kuma kenan kuna samun matsala ita dcai ba ta kara magana ba ta ci gaba da sharar hawayenta. Bayan Anas ya kai Nana gida kai tsaye gidan Nazir ya zarce su na falo su na kallo ya yi sallama shi kadai ya amsa ya samu tsarabar harara wajan Ummu, kai ashe kana da lokacin kallo gudar jininka wacce matsiyaciyar matarka ke son halakawa ta na can asibiti rai ga hannun Allah yanzu kai ba ka jin tsoron haduwar ka da Allah? Ka tuna fa Nur amanace a gare ka, kukan da Ummu take yi shi ya katse Anas yayin da ya kuma tunzura Nazir yanzu darling kana kallo kaninka ya na ce min matsiyaciya bayan jiya a gabanka ya mare ni ba ka 70 dauki mataki ba to wallahi ni bazan zauna wani kato na shigowa har gidan mijina ya na ci min mutunci ba, dole ne Anas ya daina shigowa tunda ba gidansa ba ne, takaici ya kama Anas ya rasa bakin magana, shi kuma ganin ta dauko mayafi tana kuka wai gidansu zata tafi bai san sanda ya yi kan Anas yana zuba masa ruwan bala'i, Anas bai tanka ba ganin ya kawo masa mari yasa ya rike hannu ya ce kar ka yi kuskuran marina, dan wallahi sai nayi maka dukan da zan kunyata ka gaban matar, so gidanka in dai ni Anas ne na daina zuwa ka sani Allah ba ya bacci hakkin Shema'u Allah ba zai kyale ku ba, ke kuma kiji tsoron ganin karshenki ya juya ya fita idanunsa na zubar hawaye. Daga nan gida ya zarce yaje ya sa wa matarsa ubar ni yai girkin da za'a kai asibiti dan bai dade da aure matar tasa ba ta fi watanni uku a gidan ba. Yanzu Anas shi ne a 6angaren da Nazir ya tashi, Aina'u matar Anas ta ce waye a asibiti ya ce Anty Shema'u ce Nur ce babu lafiya ta ya Allah ya sauwake amma dan honey tare zamu kai abincin ko ya ce yadda kike so haka za a yi, ta yi murmushi ta shige kicin ta na kokarin dora girki. Anas dakin Alhaji ya yi, yayi sa'ar samunsa lafiya na ganka haka dan Alhaji mutum ne mai lura ya ce Alhaji gaskiya ba lau ba, nan dai ya labarta masa komai, ran Alhaji ya бaci, ya ce abin da ya ke min kenan 71 har ya na neman hada ni da aminina wanda bani da tamkarsa wayc silar zuwana Yola yanzu ka ce yana gida nan ya dauki waya ya kira shi ya ce maza yazo gida ya na nemansa. Anas ya ce yadda tsarin gidan Nazir ya ke kana zuwa za ka san Shema'u a takure take, ya ce to ni Hajiya ta fada min cewar Shema'u ke azabtar da kishiyarta, dan kwanaki can cewa ta yi dole in yi wa mahaifinta magana yaja kunnan 'yarsa to amma ka san mata shi yasa ban dauki maganar ba, Anas ya ce duk girman gidan Nazir Shema'u daki daya ne da ita sauran kayanta na zube a gare ji ko ina da ka sani na gidan Alhaji kayan Ummukulthum ne. Su na cikin tattaunawa Nazir ya shigo ta in da Alhaji ya shiga ba tanan ya ke fita ba, Nazir sai haku ri ya ke bayarwa daga nan asibitin su ka nufa koda su ka je yarinyar na ta fisge-fisge anan san diban ruwan kashin gado bayanta amma Shema'u ta kasa rike ta Alhaji ne ya dauke ta ya na ta yi mata tofi, ya rike ta aka diba jikin Nazir ya yi sanyi shi kansa Alhaji bai za ci ciwon ya zafafa haka ba, kullum Alhaji zai dauko mahaifin Shema'u su zo su ga jikin Nur duk kuma abin da ake bukata Anas ne ke yi, don Nazir tun wannan zuwan bai kara ba, ita kanta Ummu ba ta zo ba da ya ke uwarta 'yar siyasa ce zuwan ta nawa, kullum muna tare da mahaifiyarta da Aysha da Aina'u matan 'yan uwansa kullum sai sun zo gaishe ta har Nur ta ji sauki 72 kwanan mu ishirin da takwas aka sallame mu, gidan mu na fara zuwa sannan dare naje washe gari Alhaji ya zo gidan ya sa daga ya hada mu ya yi mana fada ya ce kuma in daina zaman daki in fito falo duk abin da zan yi in yi gida gidan mijina ne babu wacce aka yi wa get to farko farkon dawowata daga asibiti abin kamar gaske, dan duk me girki a dakinta zai kwana to amma fa daga karshe abin sai nake ganin kamar ya zarce da. Na shirya zan tafi makarantar da na ke koyarwa na same su a falo suna yin lido ya kalle ni Maman Nur sai ina na ce Yayana zan ta koyarwa Ummu ta yi tsaki ta ce ni dai kalma nan ta Yayana ta na bakanta min rai domin ai wannan shishshigi ne darling ta yaya ka zama yayanta ai wannan kalmar daga bakina ya kamata ta fito wai wani Yayanta har wani kashe murya kike darling daga yau na soke, ya kalle ni ya ce kina ji daga yau ki sake min suna wannan bai yiwa Tamusamman ba, haushi da takaici su ka sa na ce na ki din ai tun kafin kizo na ke fada masa bare kice yau nasa saboda haka ba ki isa ba, ke kin san abin da kike cewa ni ce fa ishashshiya a gidan nan sai na ga dama ake komai kanki ake ji ni na tafi gurin samun lada, darling wai don Allah saboda me ka batarta take koyarwa wai ba kudi ta ke 73 nema ba kai ka abin kunya ne aced wai kamar ka matarka na fita neman kudi ka tuna mahimmancin karatuna Likita fa amma na hakura saboda in tsare mutuncinka a idanun al'umma gaskiya ya kamata ta daina duk wannan surutun da ta ke yi kafofin yada labarai ra ta daina wata fi sanin Allah, kamar me jiran umarninta ai kuma ya ce ke Shema'u daga yau na soke zuwa koyarwa ko wani yawon lacca da sauransu, ta juyo zata shigo Ummu ta kaikaci idanunta ta yi mata gwalo ta ce ni ce fa, sai fa naga karshen na ci gidan nan sai kin barshi ta shige dakinta. Washe gari taje ta samu mahaifin mijinta akan cewa ita gaskiya tana son ta ringa koyarwan nan amma da ya yi kiran Nazir fur ya ki da yaga za a takurfa masa shima sai yaje ya fada wa mahaifinta, mahaifinta ya bata hakuri ya ce ta yi zaman aure wanda ta yi da, Allah ya ba ta lada haka ta hakura ta zauna a gida ta zama 'yar girki kuma in ta yi ma ace ta bade shi da magani, kai tana ji tana gani Nazir fin sai ya bar kasar ya dawo iya kacinta da shi ido, sai ta yi sati ko wata ba ta da kwandala daya, duk ta bi ta lalace ta rame abin gwanin tausayi, daga ita har 'yarta Nur duk fa wannan ba dakala da ake me karatu kar ya manta amarya Ummulkulthum watannin ta shida a gidan 74 ake wannan takun sakar da ita. a yanzu tana dauke da ciki na wata shida. Wannan tafiyar da Ummu aka yi ta don da zai ta fi Dubai tare su ka ta fi don zata je siyayyar kayan baby babu kunya mahaifiyarta ta dawo gidan wai jiran dukiyarsu ta ke. Duk da cewar Ummu ba ta ne turaren magani ba daina ba a gudan da ace zan daka ta wannan tsohuwar sai mun ba wa hammata iska, shi yasa ba na zama sai in tafi gidanmu in zauna in bar mata gidan, amma in na dawo haka zan ga an fade min kofar daki da magani iri-iri. Satin su biyu su ka dawo kayan baby sai da aka yi daki guda da su dan wani abin haushi har kirana aka yi in gani aka bude min komai na gani na saka albarka to wannan karon Nur ta samu tsarabar akwati guda na kayan da zata yi fitar suna wai in an yi mata kani domin dan tunkan ta haife shi aka ce min namiji ne kai ita dama ta ce min ita maza ta tazo haihuwa ba mata ba, wai haihuwar mace ko wahala me zata gada. Lokacin tafiyata Misira yazo ina ta murna dan dama un yi da Nana Nur a wajanta zata zauna, kowa na taya mu murna sai shirye-shirye nake saboda Allah ya taimake mu babu abin da gwamnatin jiharmu ba ta yi mana ba, haka 75 mahaifina da mahaifiyata tunda sun san irin zaman da na ke babu mai tunanin Nazir zai iya taimaka min hatta mahaifinsa ya ban kudi masu tsoka sai shirye-shirye nake sai da ranar tafiya ta yi 'yan uwa kowa na taya ni murna amma me sai me gida Nazir ya ce wai shi bai san da tafiyar ba da mahaifinsa ya ce haba Nazir ya zaka ce haka buda idanbunsa ya yi tar ya ce abu na farko yanzu shi ne Ummu ta kusa haihuwa in ta tafi wa zai ringa taimaka mata, sannan kuma wai na nuna shi bai isa ba don ko kwabonsa ban nema ba, sai taje wadanda su ka bata kudin su bata izinin tafiya, mahaifin sa ya yi ya yi ya amince ta tafi ya ki daga karshe dai ya ce ta zabi daya ta tafi karatu Masar ko kuma auranta. Mahaifinta ya ce ta yi zaman aure idan kina da rabo gaba kije ta yi kuka ta yi kuka don da ita ce karatunta zata zasa wannan aure ko kai ya babu. Dadi ya cika Ummu dan makiyar ta bata samu abin da take so ba don tasan in har ta saka ta tafi to wallahi in ta dawo ta yi mata zarra yanzun ma yaya bare taje Masar takaici sai da ya kwantar da ita don sai da ta yi rashin lafiya duk me son ta sai da ya ji mata takaici mahaifin mijinta ya biya mata Hajji don ta ji sanyi a zuciyarta amma shima 76 da lokacin tafiya ya yi sai da aka yi rikıci da Ummu da Nazir dan Alhaji bai sanar ba sai da ya zama saura sati ta tafi nan fa daga ji zata yaye Nur ta tafi ya yi tsalle ya dire shi ba za ta yaye masa ya ta tafi ba sai dai ta hakura wata shekarar saje da Tamusamman ran Alhaji ya бaci ya ce yaya ne dai ba ka so sai yanzu kasan Nur 'yarka ce Alhaji ya ce Hajji ne Allah ya kirawo ta sai kuma zata tafi da 'yarka ba zata yaye ta ba shi kenan. Ummu ranar kwana tayi tana kuka saboda Shema'u zata tafi Makka ga shi cikinta wata bakwai ne amma ka ce yau zata haihu saboda girma, da lokacin tafiya ya yi ko Allah ya kiyaye ba ta ce da Shema'u ba ita kuwa su ka nu fi kasa mai tsarki don saukr farali. Da lokacin dawowa ya yi ta dawo cikin koshin lafiya ita da 'yarta ga shi ta yi siyayya sosai abun gwanin sha'awa da ta dawo ta ba wa Ummu tsaraba ta ce ta ki karba wai ta wuce nan ita kuwa ko a jikinta shi kuwa Nazir da ta kawo masa ya karba. Haka dai su ka ci gaba da shimfida rayuwar kishi a cikin gidan dan yanzu Shema ta dan yi baki wani lokaci takan rama abin da ta yi mata tunda ta dawo Nazir ya shimfida dokar yi mata girki irin wanda ta ke so saboda cikinta ya ısufa 77 da kyar ta ke tashi ga wani uban kumburi da kafafunta su ka yi ga shi asibiti an hana ta cin gishiri yanzu da ya ke cikinta ya tsufa in dai ranar girkin Shema'u ne in ya raba dare a can zai sulalo ya gudo nan ya kwana abin ma nasa in ya sa wa Shema'u haushi wani lokaci sai yaba ta tausayi. Yau dai tun safe Ummu ke neman fitina don ko ogan ba ta barshi ya fita ba su na master room a jibge yau tunda na tashi ya ke sani girki ya ce in dafo wannan in na kawo ta ce ba ta so takaici kuwa kamar in yi ihu illa daya ba na iya yiwa Nazir musu ko me ya sani zan yi. Bayan sallar Isha aka dauke wuta baby Nur ta ringa rigima saboda zafi na leka master room na same shi ya na zaune ta ce baban Nur kasa a kunna mana inji ya ce babu mai an tafi siyowa ta fito daga wani daki da ta ke ta ce nima candled na kunna kema ki kunna nace Nur ke jin zafi saboda in kunna mata AC ko fanka, cikin gadara ta ce to ba za a kunna injin ba yau in yaso ta mutu tana kada kaina zuwa kicin ina goyo da Nur na zubo abincin na kawo in da su ke ta ringa budewa a yatsine sannan ta ce gaskiya darling ni ba zan ci ba ka rasa fada ba na ji ta hankadani ta fita da gudu gaba daya muka bi bayanta ashe ta kasan kofa ta hango wuta tana ci kafin muyi wani 78 yunkuri gidan gaba daya wuta ta kama, da kyar mu ka soma laluben fita saboda yanda wutar ta ke ci BA BA BA BA amma ina mun rasa hanya. Mu hadu a kashi na biyu MAMAN SHUREEM Allahumma salli ala Muhammad, wa'ala ali Muhammad, kama sallaita ala Ibrahim, wa'ala ahli Ibrahim innaka hamidul majid. TUNATARWA Dan Allah maza ku daina yo min waya, domin ni matar aure ce muryata haramunce a gare ku, in kuna da wata tambaya kwa iya aiko da ita ta text message. Mai kaunarku: ZAHRA'U BABA YAKASAI 79 LITATTAFAN MARUBUCIYAR UWAR MIJI KO KSHIYA? 1 & 2 BAN SAN HAKA KAKE BA! 1 & 2 HADIYYA 1, 2 & 3 TARKON SO 1, 2, 3 & 4 FUREN KAN JUJI 1, 2 & 3 ZUMUNCI KO ANINCI 1,2&3 HATTARA MATA 1,2&3 HUDUBAR MAZA 1, 2 & 3 HUZAYYA 1 & 2 GANI GA WANE... AWARWARO PRINTED BY: AL-AMIN B/PRINTING & PUBLISHING COMPANY No.; 156 S/TITIN MANDAWARI KANO CITY. 08028411703 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 10 of 10