Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 10
da ya ke muna jarabawar karshe ina sauri saboda yau muna da gasa karatu ga shi ina daga cikin daliban da jaharmu ta dauki nauyin mu zuwa Misira kowa ya na ta ya ni murna amma Ummu ko kallo. ban isheta ba, dama ita tunda ta debi kayan kicin dinta sai ya zama koda ta yi sha'awar yin girki sai ta yi a falo ko a jikina domin ban da tsinke cikin falon balle wani akasin ya faru a sha dani na yi shiri dan har na goya Nur zan tafi na samu Nazir da Ummu za su fita na ce Yayana don Allah in hanya daya zamu yi ku rage min hanya, ya kalli Ummu ya се Tamusamman kina jin abin da Shema ta fada, tana yatsina ta bude jakar ta ta dauko naira dari wai in shiga taxi, su sauri suke, takaici ya kama ni Nur ta sa kuka ta na mika wa mahaifinta hannu ya kalli Ummu ta ce ka dauke ta ta raka mu, yasa hannu zai fige ta a bayana na ce uh'um makaranta zani ka bar min yarinyata, ta kalle ni sannu me 'ya, ko kunyar fada ba ki ji ba ya fige yarinyar ya mika ba ta wani rungume ta kamar gaske, ta kalle ni ta ce awon kaninta zamu kinga kuwa ya kamata tayi mana rakiya, su ka ja mota su ka tafi nima ta tafi ni dai haka na kammala pepar nan amma bani da natsuwa ina kammalawa na dawo gida har na dawo ba su dawo ba, kwanciya nayi saboda a 65 gajiye nake. Sai La'asar na farka, ina tashi na fito falo, a falo na same ta tana wasa ita kadai na juya na shiga wanka ina fitowa na tada Sallah. Nur da ke wasa a falo ta nufi show glass din Ummu ta na wasa, daidai lokacin Ummu ta shigo falon, ke ke ta daka mata tsawa kaga shegiyar yarinya za ki cuce ni ki fasa min kaya 'yan uwa kar ku manta Nur fa a lokacin shekarar ta daya, iri ta soma tafiyar nan dan ko kwari bata yi ba ba ku ga fincikar da ta yi ma ta ba, taja ma ta kunne ki ka kara zuwa gaban show glass dina sai na ci ubanki ko kayan uwarki ne yarinyar ta kwalla kuka wanda ina Sallah ya gigita ni, duk da dai ban san yadda aka yi na sallame sallar ba na tsince ni ne a hanyar falo a daidai lokacin da ta ke wannan fadan shi kuma Nazir shi dá kaninsa Anas sun shigo falon nima na kawo falon da niyyar in zo in dauke 'yata ganin na taho da hanzarina ya sa ta dauke yarinyar da mari, kafin in kai in da su ke yarinyar ta kife akar ko motsi ba ta yi, kafin in je Nazir da gudu ya dauki yarinyar ya na fadin kina da hankali kuwa, shi kuwa Anas bai yi wata-wata ba ya dauke ta da mari ji kake tas! ya sake kifa mata ta wani 6arin, shi dai Nazir ko ta kanta bai biya ba ya na ta girgiza Nur amma ko motsi, ya rikice gaba daya sai mikawa Anas ya ke ya na 66 cewa kaga ni ta mutu ko Anas ya karbe ta ya saba a kafada ya fita shima ya bi bayansa na kasa komai sai kuka saboda nasan yarinyar ta mutu ne ko ni Ummu ta daka sai naji jikina balle 'yar shekara daya. Ba su su ka dawo ba sai bayan Sallar Isha. fuskar nan tata gaba daya ta kumbura aka dawo min da ita Anas sai ban hakuri ya ke shi kuwa uban gayyar ya kasa magana cikin dare jikin Nur ya yi tsananin zafi saboda zazzabi na jika tawul ina goga ma ta can yarinya ta ringa fisge-fisge na rása in da zan yi da raina na tashi na yi master room ina nocking din kofar kuma ina jin surutan su amma an ki a bani damar shiga, ganin halin da Nur ta ke ciki yasa ni danna kai cikin dakin na yi nadamar abin da na gani, kuma nasan a yau nice da girki koda ya ke ni kaina bazan iya tuna ranar da Nazir ya kwana a dakina ba ya na tashi ya zabgan mari wai ni wacce irin mahaukaciya ce na nuna masa Nur da ta ke a sume na ce ka gani Nazir ka gani zata mutu kuma in ta mutu matarka ta kashe min yarinya ya ce to ta mutu mana ina ruwana ko an ce miki na damu na dawo daki ina ta tofa mata addu'o'in da su ka sauwaka a gare ni. Gari na wayewa ko wanka ban yi ba salla kawai na yi na goye Nur a bayana ina fitowa a falo na same su na durkusa na gaishe shi na ce Nazir ga Nur fa ciwon 67 ta yayi zafi ka taimaka ka kaita asibiti ya ce na gaya miki ba damuwata ba ce, kije ki kaita mana in ta mutu Allah ya jikanta, hawaye yha biyo fuskata na mike jiki babu kwari yayin da Ummu ta rinka jifana da wani matsiyacin kallo takaici ya kama ni saboda yau da gobe sai Allah na duba ma'ajiyata ko ficika bani da ita, ga shi daga nan zuwa gidanmu tafiya ce mai yawa, haka na daure na fito, tafiya nake ba ta wasa ba saboda na gaji ai ni naji ana yi min hani na duba sai naga Anas ne ina zaki ne? Na je duba Nur aka ce ba kya nan, zan je gida ne a kasa kike nufin za ki tafi, na girgiza kai kasan safiya ce motoci suna wahala mai ya hana mijinki fita da ke na ce yau baya jin fita shigo in kaiki na shiga baya tun muna mota tana goye a bayana na ji tana wannan fisgefisge ya na tsaida mota tun kafin ya yi magana nayi fid na fice da gudu na shiga gida na kunto Nur tana fisge-fisge mahaifiyata tana tambaya ta lafiya? Ina kuka na ke fada ma ta abin da ya faru, ta juyo da niyyar zuwa gun mahaifina ashe ya na tsaye ya na jinmu ta ce Malam bari in shirya mu ta fi asibiti baba na cikin fushi ya ce ba zai yuwu ba ba hakkinmu ba ne mu kai ta asibiti tunda ya na da iyaye bani yarinyar in kai wa mahaifansa in suma sunga ba za su kaita ba to a lokacin mu ke da 'yancin kaita wannan wane irin rashin imani ne, Baba na ya karbi Nur a hannun Nana ya juya da 68 niyyar kaita gidan su Nazir da kansa, kawai sai mu ka ga Anas a tsaye ashe tun da na shigo da gudu shima ya biyo ni baba don Allah kuyi hakuri ni na dauko ta a hanya wallahi da ta fada min ba zan kawo ta ba, asibiti zamu tafi ya karbi Nur ya ce taho muje mu kaita mu ka tafi kai ta har da mahaifiyata. Munje mun sami ganin Likitar yara Doctor Fiddausi ta shiga kula da yarinyar ta ce zafin zazzabi shi ya haifar da jijjigar nan da nan aka yi ma ta wata allura sai kuma ta samu bacci gado su ka ba mu ma'ana dai an kwantar damu mahaifiyata ta ce bari ta kawo mana abin da muke bukata, Anas ya ce bari in kaiki in yaso nima sai in kawo abin da suke so su ka fita tare. Na kife kan gado ina kuka saboda bakin cikin kishiya da na miji yanzu ni Nazir ya ke wulakantawa haka bai ga abun da matarsa ta yi wa 'yarsa ba wai Nur din da Nazir ya ke raba dare ya na kallonta saboda dadewar da muka yi ba mu samu haihuwa ba ita ce wacce bai damu da ita ba, yanzu haka rayuwata zata kasance? Amma fa ina ganin laifina ne tunda ni ce wacce na nuna ina sonsa har aka kai ga hada auranmu, to ai Nazir ya so ni so ba na wasa ba, babban takaicin ban iya son wani in ba shi ba shi kadai zuciyata ke so, Allah ka yaye min son Nazir don sonsa ba shi da wani amfani a gurina. 69 Doctor Fiddausi ce ta ce, ke bacci kikc har drip din da aka sa ma ta ya kare, jinr har ya soma shiga rabo na dago idanu a kode na ce wallahi ba bacci nake ba, ta kalle ni ta ce haba 'yar uwa ki daina damun kanki za ta warke yanzu abun da kananan yara suke fama da shi kenan, ta kalle ni ta ce sai dai na rasa dalilin kumburin fuskarta ko wani abu ya fado ma ta, saboda bakin ciki ya na cin zuciyata ban san sanda na ce ma ta marinta aka yi. Dr. ta zaro ido ta ce mari dan rashin Imani wanne yaron ne ya yi mata wannan marin? Abikiyar zamana matar mahaifinta, kuka ya kwace min ta tsaya kawai tana kallona can ta ce ni sai naga kamar na sanki ko kuma in ce ana nuno ki cikin TV kina wa'azi kuma kenan kuna samun matsala ita dcai ba ta kara magana ba ta ci gaba da sharar hawayenta. Bayan Anas ya kai Nana gida kai tsaye gidan Nazir ya zarce su na falo su na kallo ya yi sallama shi kadai ya amsa ya samu tsarabar harara wajan Ummu, kai ashe kana da lokacin kallo gudar jininka wacce matsiyaciyar matarka ke son halakawa ta na can asibiti rai ga hannun Allah yanzu kai ba ka jin tsoron haduwar ka da Allah? Ka tuna fa Nur amanace a gare ka, kukan da Ummu take yi shi ya katse Anas yayin da ya kuma tunzura Nazir yanzu darling kana kallo kaninka ya na ce min matsiyaciya bayan jiya a gabanka ya mare ni ba ka 70 dauki mataki ba to wallahi ni bazan zauna wani kato na shigowa har gidan mijina ya na ci min mutunci ba, dole ne Anas ya daina shigowa tunda ba gidansa ba ne, takaici ya kama Anas ya rasa bakin magana, shi kuma ganin ta dauko mayafi tana kuka wai gidansu zata tafi bai san sanda ya yi kan Anas yana zuba masa ruwan bala'i, Anas bai tanka ba ganin ya kawo masa mari yasa ya rike hannu ya ce kar ka yi kuskuran marina, dan wallahi sai nayi maka dukan da zan kunyata ka gaban matar, so gidanka in dai ni Anas ne na daina zuwa ka sani Allah ba ya bacci hakkin Shema'u Allah ba zai kyale ku ba, ke kuma kiji tsoron ganin karshenki ya juya ya fita idanunsa na zubar hawaye. Daga nan gida ya zarce yaje ya sa wa matarsa ubar ni yai girkin da za'a kai asibiti dan bai dade da aure matar tasa ba ta fi watanni uku a gidan ba. Yanzu Anas shi ne a 6angaren da Nazir ya tashi, Aina'u matar Anas ta ce waye a asibiti ya ce Anty Shema'u ce Nur ce babu lafiya ta ya Allah ya sauwake amma dan honey tare zamu kai abincin ko ya ce yadda kike so haka za a yi, ta yi murmushi ta shige kicin ta na kokarin dora girki. Anas dakin Alhaji ya yi, yayi sa'ar samunsa lafiya na ganka haka dan Alhaji mutum ne mai lura ya ce Alhaji gaskiya ba lau ba, nan dai ya labarta masa komai, ran Alhaji ya бaci, ya ce abin da ya ke min kenan 71 har ya na neman hada ni da aminina wanda bani da tamkarsa wayc silar zuwana Yola yanzu ka ce yana gida nan ya dauki waya ya kira shi ya ce maza yazo gida ya na nemansa. Anas ya ce yadda tsarin gidan Nazir ya ke kana zuwa za ka san Shema'u a takure take, ya ce to ni Hajiya ta fada min cewar Shema'u ke azabtar da kishiyarta, dan kwanaki can cewa ta yi dole in yi wa mahaifinta magana yaja kunnan 'yarsa to amma ka san mata shi yasa ban dauki maganar ba, Anas ya ce duk girman gidan Nazir Shema'u daki daya ne da ita sauran kayanta na zube a gare ji ko ina da ka sani na gidan Alhaji kayan Ummukulthum ne. Su na cikin tattaunawa Nazir ya shigo ta in da Alhaji ya shiga ba tanan ya ke fita ba, Nazir sai haku ri ya ke bayarwa daga nan asibitin su ka nufa koda su ka je yarinyar na ta fisge-fisge anan san diban ruwan kashin gado bayanta amma Shema'u ta kasa rike ta Alhaji ne ya dauke ta ya na ta yi mata tofi, ya rike ta aka diba jikin Nazir ya yi sanyi shi kansa Alhaji bai za ci ciwon ya zafafa haka ba, kullum Alhaji zai dauko mahaifin Shema'u su zo su ga jikin Nur duk kuma abin da ake bukata Anas ne ke yi, don Nazir tun wannan zuwan bai kara ba, ita kanta Ummu ba ta zo ba da ya ke uwarta 'yar siyasa ce zuwan ta nawa, kullum muna tare da mahaifiyarta da Aysha da Aina'u matan 'yan uwansa kullum sai sun zo gaishe ta har Nur ta ji sauki 72 kwanan mu ishirin da takwas aka sallame mu, gidan mu na fara zuwa sannan dare naje washe gari Alhaji ya zo gidan ya sa daga ya hada mu ya yi mana fada ya ce kuma in daina zaman daki in fito falo duk abin da zan yi in yi gida gidan mijina ne babu wacce aka yi wa get to farko farkon dawowata daga asibiti abin kamar gaske, dan duk me girki a dakinta zai kwana to amma fa daga karshe abin sai nake ganin kamar ya zarce da. Na shirya zan tafi makarantar da na ke koyarwa na same su a falo suna yin lido ya kalle ni Maman Nur sai ina na ce Yayana zan ta koyarwa Ummu ta yi tsaki ta ce ni dai kalma nan ta Yayana ta na bakanta min rai domin ai wannan shishshigi ne darling ta yaya ka zama yayanta ai wannan kalmar daga bakina ya kamata ta fito wai wani Yayanta har wani kashe murya kike darling daga yau na soke, ya kalle ni ya ce kina ji daga yau ki sake min suna wannan bai yiwa Tamusamman ba, haushi da takaici su ka sa na ce na ki din ai tun kafin kizo na ke fada masa bare kice yau nasa saboda haka ba ki isa ba, ke kin san abin da kike cewa ni ce fa ishashshiya a gidan nan sai na ga dama ake komai kanki ake ji ni na tafi gurin samun lada, darling wai don Allah saboda me ka batarta take koyarwa wai ba kudi ta ke 73 nema ba kai ka abin kunya ne aced wai kamar ka matarka na fita neman kudi ka tuna mahimmancin karatuna Likita fa amma na hakura saboda in tsare mutuncinka a idanun al'umma gaskiya ya kamata ta daina duk wannan surutun da ta ke yi kafofin yada labarai ra ta daina wata fi sanin Allah, kamar me jiran umarninta ai kuma ya ce ke Shema'u daga yau na soke zuwa koyarwa ko wani yawon lacca da sauransu, ta juyo zata shigo Ummu ta kaikaci idanunta ta yi mata gwalo ta ce ni ce fa, sai fa naga karshen na ci gidan nan sai kin barshi ta shige dakinta. Washe gari taje ta samu mahaifin mijinta akan cewa ita gaskiya tana son ta ringa koyarwan nan amma da ya yi kiran Nazir fur ya ki da yaga za a takurfa masa shima sai yaje ya fada wa mahaifinta, mahaifinta ya bata hakuri ya ce ta yi zaman aure wanda ta yi da, Allah ya ba ta lada haka ta hakura ta zauna a gida ta zama 'yar girki kuma in ta yi ma ace ta bade shi da magani, kai tana ji tana gani Nazir fin sai ya bar kasar ya dawo iya kacinta da shi ido, sai ta yi sati ko wata ba ta da kwandala daya, duk ta bi ta lalace ta rame abin gwanin tausayi, daga ita har 'yarta Nur duk fa wannan ba dakala da ake me karatu kar ya manta amarya Ummulkulthum watannin ta shida a gidan 74 ake wannan takun sakar da ita. a yanzu tana dauke da ciki na wata shida. Wannan tafiyar da Ummu aka yi ta don da zai ta fi Dubai tare su ka ta fi don zata je siyayyar kayan baby babu kunya mahaifiyarta ta dawo gidan wai jiran dukiyarsu ta ke. Duk da cewar Ummu ba ta ne turaren magani ba daina ba a gudan da ace zan daka ta wannan tsohuwar sai mun ba wa hammata iska, shi yasa ba na zama sai in tafi gidanmu in zauna in bar mata gidan, amma in na dawo haka zan ga an fade min kofar daki da magani iri-iri. Satin su biyu su ka dawo kayan baby sai da aka yi daki guda da su dan wani abin haushi har kirana aka yi in gani aka bude min komai na gani na saka albarka to wannan karon Nur ta samu tsarabar akwati guda na kayan da zata yi fitar suna wai in an yi mata kani domin dan tunkan ta haife shi aka ce min namiji ne kai ita dama ta ce min ita maza ta tazo haihuwa ba mata ba, wai haihuwar mace ko wahala me zata gada. Lokacin tafiyata Misira yazo ina ta murna dan dama un yi da Nana Nur a wajanta zata zauna, kowa na taya mu murna sai shirye-shirye nake saboda Allah ya taimake mu babu abin da gwamnatin jiharmu ba ta yi mana ba, haka 75 mahaifina da mahaifiyata tunda sun san irin zaman da na ke babu mai tunanin Nazir zai iya taimaka min hatta mahaifinsa ya ban kudi masu tsoka sai shirye-shirye nake sai da ranar tafiya ta yi 'yan uwa kowa na taya ni murna amma me sai me gida Nazir ya ce wai shi bai san da tafiyar ba da mahaifinsa ya ce haba Nazir ya zaka ce haka buda idanbunsa ya yi tar ya ce abu na farko yanzu shi ne Ummu ta kusa haihuwa in ta tafi wa zai ringa taimaka mata, sannan kuma wai na nuna shi bai isa ba don ko kwabonsa ban nema ba, sai taje wadanda su ka bata kudin su bata izinin tafiya, mahaifin sa ya yi ya yi ya amince ta tafi ya ki daga karshe dai ya ce ta zabi daya ta tafi karatu Masar ko kuma auranta. Mahaifinta ya ce ta yi zaman aure idan kina da rabo gaba kije ta yi kuka ta yi kuka don da ita ce karatunta zata zasa wannan aure ko kai ya babu. Dadi ya cika Ummu dan makiyar ta bata samu abin da take so ba don tasan in har ta saka ta tafi to wallahi in ta dawo ta yi mata zarra yanzun ma yaya bare taje Masar takaici sai da ya kwantar da ita don sai da ta yi rashin lafiya duk me son ta sai da ya ji mata takaici mahaifin mijinta ya biya mata Hajji don ta ji sanyi a zuciyarta amma shima 76 da lokacin tafiya ya yi sai da aka yi rikıci da Ummu da Nazir dan Alhaji bai sanar ba sai da ya zama saura sati ta tafi nan fa daga ji zata yaye Nur ta tafi ya yi tsalle ya dire shi ba za ta yaye masa ya ta tafi ba sai dai ta hakura wata shekarar saje da Tamusamman ran Alhaji ya бaci ya ce yaya ne dai ba ka so sai yanzu kasan Nur 'yarka ce Alhaji ya ce Hajji ne Allah ya kirawo ta sai kuma zata tafi da 'yarka ba zata yaye ta ba shi kenan. Ummu ranar kwana tayi tana kuka saboda Shema'u zata tafi Makka ga shi cikinta wata bakwai ne amma ka ce yau zata haihu saboda girma, da lokacin tafiya ya yi ko Allah ya kiyaye ba ta ce da Shema'u ba ita kuwa su ka nu fi kasa mai tsarki don saukr farali. Da lokacin dawowa ya yi ta dawo cikin koshin lafiya ita da 'yarta ga shi ta yi siyayya sosai abun gwanin sha'awa da ta dawo ta ba wa Ummu tsaraba ta ce ta ki karba wai ta wuce nan ita kuwa ko a jikinta shi kuwa Nazir da ta kawo masa ya karba. Haka dai su ka ci gaba da shimfida rayuwar kishi a cikin gidan dan yanzu Shema ta dan yi baki wani lokaci takan rama abin da ta yi mata tunda ta dawo Nazir ya shimfida dokar yi mata girki irin wanda ta ke so saboda cikinta ya ısufa 77 da kyar ta ke tashi ga wani uban kumburi da kafafunta su ka yi ga shi asibiti an hana ta cin gishiri yanzu da ya ke cikinta ya tsufa in dai ranar girkin Shema'u ne in ya raba dare a can zai sulalo ya gudo nan ya kwana abin ma nasa in ya sa wa Shema'u haushi wani lokaci sai yaba ta tausayi. Yau dai tun safe Ummu ke neman fitina don ko ogan ba ta barshi ya fita ba su na master room a jibge yau tunda na tashi ya ke sani girki ya ce in dafo wannan in na kawo ta ce ba ta so takaici kuwa kamar in yi ihu illa daya ba na iya yiwa Nazir musu ko me ya sani zan yi. Bayan sallar Isha aka dauke wuta baby Nur ta ringa rigima saboda zafi na leka master room na same shi ya na zaune ta ce baban Nur kasa a kunna mana inji ya ce babu mai an tafi siyowa ta fito daga wani daki da ta ke ta ce nima candled na kunna kema ki kunna nace Nur ke jin zafi saboda in kunna mata AC ko fanka, cikin gadara ta ce to ba za a kunna injin ba yau in yaso ta mutu tana kada kaina zuwa kicin ina goyo da Nur na zubo abincin na kawo in da su ke ta ringa budewa a yatsine sannan ta ce gaskiya darling ni ba zan ci ba ka rasa fada ba na ji ta hankadani ta fita da gudu gaba daya muka bi bayanta ashe ta kasan kofa ta hango wuta tana ci kafin muyi wani 78 yunkuri gidan gaba daya wuta ta kama, da kyar mu ka soma laluben fita saboda yanda wutar ta ke ci BA BA BA BA amma ina mun rasa hanya. Mu hadu a kashi na biyu MAMAN SHUREEM Allahumma salli ala Muhammad, wa'ala ali Muhammad, kama sallaita ala Ibrahim, wa'ala ahli Ibrahim innaka hamidul majid. TUNATARWA Dan Allah maza ku daina yo min waya, domin ni matar aure ce muryata haramunce a gare ku, in kuna da wata tambaya kwa iya aiko da ita ta text message. Mai kaunarku: ZAHRA'U BABA YAKASAI 79 LITATTAFAN MARUBUCIYAR UWAR MIJI KO KSHIYA? 1 & 2 BAN SAN HAKA KAKE BA! 1 & 2 HADIYYA 1, 2 & 3 TARKON SO 1, 2, 3 & 4 FUREN KAN JUJI 1, 2 & 3 ZUMUNCI KO ANINCI 1,2&3 HATTARA MATA 1,2&3 HUDUBAR MAZA 1, 2 & 3 HUZAYYA 1 & 2 GANI GA WANE... AWARWARO PRINTED BY: AL-AMIN B/PRINTING & PUBLISHING COMPANY No.; 156 S/TITIN MANDAWARI KANO CITY. 08028411703Gani Ga Wanest NA ZAHRAU BABA YAKASA! (Mrs. Dan Ringim) GANI GA WANE. 1 NA ZAHRA'U BABA YAKASAI (Maman Shurcem) 08020863615 1 GODIYA Ga Allah Subahanahu wata'alah, wanda cikin yardarsa da ikonsa muke baza muku irin baiwar da ya yi mana. SAKON TAYA MURNA Ga Uncle dina da Allah ya sauki Auntyna lafiya, Allah ya raya mana MARIYATUL KIFDIYA Tasi'u D. Yakasai (Baba Wali) INA TAYA KA MURNA ALLAH YA RAYA MANA Hauwa'u Ibrahim Umar Makaruma (Malam Sabo) GORON AMARCI Kinsha kamshi tsohuwar gidanmu. SAFIYA DAHIRU YAKASAI UMMI da Angonta NURA ABUSAKA YAKASAI Allah ya kawo kazantar daki. INA SANE DA KAI Bashir Sa'id Kyautah 2 MASOYA NA GARI, ALHERIN ALLAH YA KAI MUKU Hauwa K. Umar College of Education Minna. Hussaina B. SKK Hauwa Ali Gwambe Abubakar Haruna Albasu Asiha Ishak 'Yar Magaji Ibrahim A. Bauchi Maryam Suleman Giade (Ummce) Hadiza Adam Hajara Abdullah Baba Sokoto Hadiza Usman (Hadee Queen) Zahra Ahmad Babangida Kumo Bello M. Hauwa Mohd Loddo (Maman Ukasha) Suwaiba Musa Faruk Umar Gamawa Fa'iza Moh'd Gaya MJB Hauwa Usaini Bichi Maimuna Musa Soja Abdurrashid Abdun kwallo Amina Abdullah Ghana Ahmad Paris Bookshop Samirf Sha'aibu Jangulu Kazaure Fatima Adamu Yana Rukayya Mai dinki D/Kaigama 3 Deeni Alasan Yana Mudansuri A. Badamasi Hadiza Ali Sokoto Aysha Sokoto H.J.A Sumayya Mohd Sury (Maman Fadila) Ahmad Tijjani (Abban Mohd) Abdullah Dalhatu (Abban Humaira). GAISUWA TA MUSAMMAN GA MASOYANA Na kasashan ketare kamar: Kamaru, Ghana, Abijan, sannan Saudiyya, Paris, da kuma Libiya. 4 SHIMFIDA ota cc kirar Jeep baka kirin sai M daukar ido takc kamar wanda aka shafc ta da mai (oil), ya fito daga cikin wannan mota, abisa dukkan alamu da akwai masu gidan rana (kudi), dogo ne fari mai dan kauri irin mazan da akc kiran su tall man din nan ne fuskar shi ta kunshi annuri kasancewarshi mai sakakkan fuska. Cikin iko da takama irin na ma su akwai, ya fito ya rufe motarshi, ya doshi cikin gidan. Gida ne hadadde flat irin ginin zamani wanda aka dauko hotonshi daga London, gida ne wanda ya kunshi kayan more rayuwa na bil-Adama domin tsayawa misalta wannan gida 6ata lokaci ne sai dai ku biyo ni a sannu ku ji komai. Ya na shigowa cikin gida kwatsam ya yi for cyes da wacce ya tsana ko kuma in ce aka cusa mashi tsanarta don ba wai a son shi ba ne. "Sannu da zuwa." Ta fada mashi amma ko ya kulata, sai shigewa bedroom dinshi ya yi, kulawa Mà yabawa ne in ji Hausawa. Ya danna inter come ya kira ta musamman kamar yadda ya ke kiran amaryarshi wato (ta musamman) a maimakon sunanta na yanka wato Ummulthum, ta fito cikin yanga da jinkai a daidai falo ta hadu da wacce ta tsana kuma ta ki jinin ta 5 Fafi ido ta ganta harara ta sakar matga ta shiga dakinshi cike da kwarkwasa da kissa, shi kuwa tuni va rude nan ya rungumo ta jikinshi ya fara sumbatarta nan da nan su ka manta a wace duniya suke. Bayan sun nutsu ne ta dube shi cikin kashe ido ta ce "Darling yunwa nake ji." Ya zaro ido, Shema'u ba ta baki abinci ba ne.?" Jikinshi na 6ari bai jira amsarta ba ya fito falo ya iske ta na kallon TV tashan Aljazeera ya dube ta "Ke me yasa ba ki ba wa Ummu abinci ba? Ta dago kai ta dube shi da kyau, ta ce a baki zan bata ko me? Ran shi ya бaci wane irin zancen banza ne kike min haka? Cewa ta yi tana jin yunwa sai ta ajiye remote din hannunta ta kara ganinshi da kyhau cike da mamaki da al'ajabi ta ce to ai sai ta shiga kitchen din ta duba ko anyi mata dokar shiga ne? Sai Ummu ta fito amma kin san ba a nuna wa ido bacci da

Chapter 5 of 10